Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

niyyar mallakawa, ita din mace ce mai mutuqar muhimmanci a gareni, zan'iya sadaukar da rayuwata domin ta.... Dalilin hakane yasa na mallaka mata wannan company, ba kowa bace face AISHA"

Daukacin mutanan wajan Nan da Nan suka dauki tafi.
Ramadan yajuya ya kalli munirat da gumi ya wanke wa fuska, ya kalli Shahaab yasaki wani irin murmushi, yasan mutane dayawa zasuyi tunanin mama yabawa company duba da yanda yafara da yabon ta, sannan Kuma da kasancewar ta itama sunanta AISHA, wata irin dariya ce ta kama Ramadan yayi qasa da Kansa ya tuntsire da dariya domin Gano inda maganar abokin nasa tanufa.

Dam dam, gaban munirat yafadi, lokaci daya gumi ya wanke mata fuska, mutanan data gayyata kuwa gaba dayansu juyowa sukai suna kallonta jin labari yasha bambam

Shahaab kuwa yana gama wannan jawabi yad'auki takardun company, wajan da mamallakin company zaiyi sign yakalla, shiru yayi yarasa wanne irin sign zaiyi mata? Baisan Yaya take signature dinta ba, danhaka yabi shawarar zuciyar sa yayi mata sign da ASH~HAB







(yau Shahaab yataro December awajan munirat =ØÞ<ØÃß<Øûß
@&þDan yawuce march)





Littafin SHAHAAB na kudi ne, duk wadda taqi biyan kudi ta karanta bazan ta6a yafe mata ba, har abada, ki biya naira 300 kacal ta account dina


0164549488
Amina muhammad
GTbank

Kokuma katin MTN ta

Katsura shedar biya ta wannan number 08033300034







Mrs Usman ce
'<Øûß






Page



27



Mama tagirgiza kanta, tasan de bada ita Shahaab yake ba, domin kuwa idan itace bazaice Aisha Kai tsaye ba.

ta juya ta kalli Ramadan, taga yanata dariya,ahankali ta rage muryarta tace "wacece Aisha?"

Cikin sauri Ramadan ya kalleta, dahar zaice Aisha ai tana tare dake mama, Sai yayi tunani Gara taji daga bakin Shahaab din, tunda yasan dole zaiyi mata magana cikin fahimta, Girgiza Kansa yayi yace "jinake ke yake nufi mama"

Mama ta kalleshi tayi murmushi, tasan Dama bazai fada mata gaskiya ba, Amma babu abinda bai saniba akan Shahaab tunda tare suke komai.

Cikin iya kissa munirat tatashi tana dariya wadda tafi kama da yaqe, Sai firfita take da hannunta ta silale tabar wajan,
Qawayanta suka Mara mata baya.

Mama kuwa bata tafi ba, saida aka gama taro da'ita, har zuwa lokacin Ramadan yana tare da'ita, mutane Sai zuwa suke suna gaishe ta, saida mutane suka Dan ragu, sannan Ramadan ya rakata mota tatafi gida.
Mama tana zuwa gida tasamu Aisha afalo tana kallo, tana ganin Zuwan mama tatashi tsaye, cikin ladabi tace "mama sannu da zuwa"

Mama ta zauna a kujera tana cire agogon dake daure a hannunta tace "sannu Aisha, yagida? Kina zaune ke kadai bakya gajiya da wannan kallon ne?"

Murmushi tayi tace"mama agida Bama kallo, shiyasa yanzu yake birgeni, Amma idan bakya so insha Allah zan Dena"

Cikin sauri tace"a a, yi abinki, idan nahanaki kallo menene ribata? "

Cikin ladabi tace"to mama nagode, nakawo miki abincin danayi miki?"

Murmushi mama tayi tace"saida kika yi girkin de, tojeki kawomin "


Cikin murna ta wuce kitchen tazubowa mama dambun shinkafar datayi Wanda yaji kayan hadi harda su hanta yanata turiri, mama tace "masha Allah, Aisha kece kikai wannan?"

Murmushi tayi tace"nice nayi mama, ko nazauna nabaki?"
Tace"A a karki damu, zanci dakaina,Amma ki ajiyemin shi da daddare zan sake ci, yanzu de jeki kiramin Munirat"

Cikin sauri ta kalli mama, itafa batason shiga sabgar wannan matar tasa,ko kadan batasan abinda zai hada su, cikin sanyin jiki tace"mama ai bansan part dinba"

Mama tayi murmushi tace"a a, baki ta6a zuwa bane?"

Daga mata Kai tayi,mama tace" a a baki kyautaba Aisha, masu suna Aisha fa sunada kirki, ko baki San Nima sunana Aisha ba?"

Kallon tayi tace"bansani ba mama, ashe haka sunan ki"

"haka sunana, Kuma nasan duk me suna irin nawa tanada kirki, saboda haka kede baki kyautaba da baki ta6a zuwa kun gaisa da munirat ba,karki damu da halin ta,haka take, Nima haquri nake da'ita,idan kika fita zakiga wani part daga hannun damanki, kije kice mata tazo in jini"

Tace "to mama"
sannan ta juya tafita.

Ta danyi tafiya medan Nisa sannan ta qaraso part din, wasu ma'aikata tagani a tsaye daga Gefe, gulma ta rufe musu ido ko lura da Aisha basuyi ba, daya daga cikin su yace"ai yau yalla6ai yayi maganin wannan matar tasa, muda mukaje muka tsatstsara wajan muka share, mu akai komai akan idonmu, kamfanin fa ta fadawa mutane ita zai Bawa, habaaa! yalla6ai yana tashi saiya Bawa Hajiya Mama kamfani, bakuga yanda take gumi ba"

Wani zai sake magana Aisha tace"dan Allah inane qofar shiga part dinnan?"

Juyowa sukai suka kalleta, saikuma suka fara kuskurin kunya, suna tunanin taji abinda suke fada Kuma suna tsoron taje ta fadawa mama, ita kuwa suna nuna mata ta wuce, tana shiga part din taga yasha bambam da'irin na mama, tsaruwar Kam harta yi yawa, idan anan part din take 6ata lokaci zatayi wajan kallon part din kawai.
Munirat tagani a zaune da wasu mutane su su hudu, Dan kwalin kanta yana riqe ahannunta, ta hargitsa gashin dokin kanta, masifa ta rufe musu ido basu maji shigowar Aisha da sallamar taba, ikee tace "waima wacce shegiya ce wannan Aishan?"

Kai tsaye munirat tace"uwarsa ce mana, da'ita yake"
Ajiyar zuciya ikee tayi sannan tace"ni narasa abun damuwa anan munirat....tun farko fa kece kikai wasa da damar ki da har Zaki Bari yadinga fifita wannan tsohuwar sama dake"

Hauwi tace "Allah natuba mezatai dawani company yanzu? Taci zamaninta tana neman shiga naki zamanin keda mijinki, Shima da niyya yabata ai, yasan tana mutuwa kudin de nasane"
Qanwarta Maryam tace"amma Anty ya Yaya Mahmud zai mana haka? Mommy tana can gida fa tayi gayya, tun jiya muke hada abincin baqi saboda mutanan data gayya ta"

Munirat ta goge Hawayen idonta tace"Dama mamarsa ta tsaneni, narasa Mena tsare mata, da kunne na naji yana cewa zai Bani, Amma nasan inde yafada mata Dama zata hanashi yabani,tunda gashinan anrubuta sunanta akan takardun ai shikkenan,Kuma wallahi Saita gane...."

Maganar ta ce ta maqale ganin Aisha a tsaye abakin qofar Dakin, cikin masifa tace"kekuma ubanme kike akanmu? Munafuka muna magana kinzo kin tsaya mana aka wato Zaki kwasa kije kifada mata ko?"

Cikin sauri tace"mama ce tace kizo tana kiranki "

Cikin tsawa munirat tace"fice kibarmin Nan kona tashi na kakkarya ki,annamimiya"

Cikin fishi Aisha ta juya tabar mata part dinta, qasa qasa tace"wallahi Bani ba saide ke"

Ikee tace "wacece wannan din Kuma?"

Munirat tace "baquwar uwarsa ce, shegen cusa kaine da yarinyar natsane ta wallahi"

Maryam tace "tabdi, lalle Anty akwai aiki a gabanki, kina zaune da wannan yarinyar a gidan Nan? To Bari kiji daga baqunta tana Dan kula da mahaifiyar sa zata zarce kulada mijinki, ke bakiga dirin yarinyar bane?"

Munirat tace "nikuwa ninaga uban diri ma,ai Ina ganin iya duniyanci awajan wannan tsohuwar, rannan daga zuwa na part din zuciyata daya Naga takama yarinyar ta rirriqe masa shikuma Sai ta6awa yarinyar nono yake"

Hade baki sukai atare sukace "nono?"

Tace "nono kuwa, tundaga ranar nasan banida maqiyiya irin mama, yaza'ai yarinya danya sharaf kamar wannan zaka turawa namiji baligi kamar Mahmud ita yana ta6a mata nonuwa,yanda nasan mijina idan yagani ma Hankalinsa tashi yake, bare Kuma ace anbashi yata6a, Sai kinga gashin tama shegiya kamar aljanna, sauqi na daya nasan Mahmud din yanmata basa gabansa, Aida yanda zai dinga Binta saina raina kaina"

Hauwi tace "tabdi, yanzun made karki zauna kisa musu ido, tashi zakiyi tsaye munirat"

Haka suka dinga tattaunawa suna zagin mama da Mahmud din Kansa.


Tana komawa wajan mama tace "mama tana tareda qawayenta, nace kina nemanta to Amma sai fada takemin"

Mama ta Girgiza kanta tace "Allah ya shirya, Dauko Mai ki shafamin a qafafuna"

Cikin sanyin jiki tace"to mama"sannan ta wuce d'akin.

Bayan ta Dauko man zama tayi ta dinga shafa mata suna hira kad'an kad'an, saida yamma taraka mama daki itama tatafi dakinta, har zuwa lokacin munirat batazo Kiran da mama tayi mataba.

Da daddare suna zaune afalo, mama ta kalleta tace"Aisha jeki zubomin sauran dambun Nan danace ki ajiyemin zanci da daddare "

Cikin ladabi tace" to mama "

Kitchen din ta wuce, anan ta tarar da masu aiki suna wanke wanke kwanukan dasuka gama amfani dashi na girkin dare, abincin ta zubowa mama sannan tahado mata da lemuka da ruwa, cikin nutsuwa ta ajiye mata sannan ta zauna tace"in baki ne mama ko zakici da kanki?"

Murmushi tayi tace"zoki Bani"

Zama tayi akan kujerar, tafara bata abincin, mama tace"Aisha girkin yayi dadi sosai, kinsan rabona da dambu na Dade, duk wadannan masu aikin basu iya irin wannan girkin ba, yawanci saide qauye"

Aisha tayi murmushi batace komai ba, mama tasake cewa"qirjin de yadena miki ciwo ko?"

Cikin kunya tace"eh yadena"

"to Bayan fa?"

Aisha tace"Shima yadena"

Kafin tasake jefo mata wata tambayar yayi sallama yashigo falon, wani soja ne a bayansa yabiyo shi da wata breaf case me kyau,wani irin farinciki ne yakama shi yanda yaga tana Bawa mama Abinci, Kota wannan Fannin bazai ta6a hadata da munirat ba, saboda tana kula da mahaifarsa ,tana daga gefen hannun Daman mama, shikuma yazaune agefen hagun ta,tareda kallon Aisha Qasa qasa, ajiye masa brief case din sojan yayi, sannan yajuya yafice,Suna hada ido tayi sauri tayi qasa da kanta, ahankali ta ajiye abincin zata tashi, cikin sauri mama tace "Aisha zauna mana, Ina zakije kina Bani abinci?"

Ido yazuba mata kamar yasamu TV, ita kuwa kanta yana qasa tace "mama jinake Zaki qarasa da kanki"

Cikin sauri mama Tace"A a zauna kibani,saida kika sangarta ni dabani abinci sannan Zaki gudu? Wannan dakike Gani ba Bani zaiyi ba saide ma yafara min shagwa6a nabashi"

Ta qarasa maganar tana nuna mata Shahaab, batayi gigin kallon inda yake ba tace"yalla6ai Ina wuni"

Wani iri yaji, yalla6ai? Me yarinyar Nan take nufi? Jin yayi shiru yasa Mama ta kalleshi tace"narasa meyasa idan Aisha ta gaishe ka bakason amsawa, Karage qiyaiyarka ga mata mana"

Murmushi yayi cikin shagwa6a yace"mamaaah..."sannna yad'ora Kansa a cinyar ta, yazagayo da hannunsa ta hips dinta, ahankali Aisha ta zauna, tana zama taji ya mintsineta Adede kan hips dinta, kallon sa tayi taga Idonsa a Lumshe kamar bashi ba, mama ta kalleshi tace"baka rabo da fitina Mahmud,mekakeso yanzu?"

Wani irin taqaici ne yakama Aisha, tad'an kalli mama taga Sai wani riritashi take kamar wani jariri, tunanin tane ya tsaya lokacin dataji yana shafa hips dinta,gabanta ne yafadi, tasake kallon sa taga Idonsa a rufe, shi ko tsoron mama ma bayaji, Bayan tsoron taji motsin hannunsa, ahankali taji yace"mama nagaji ne"

Mama tace"tun safe kunata aiki ai dole agaji "

Tajuya ta halli Aisha tace"Aisha laifin me kikayi wa Abbanki ne ya turo ki aiki wajena?"

Cak Shahaab ya tsaya da abunda yake, sakamakon tambayar ta mama ta shige shi, shi Kansa yanaso yaji dalilin zuwan ta gidan, yasan idan ya tambayeta bazata kulashi ba, tunda yaga alama har yanzu bata huce ba.
Gaban tane yafadi, cikin sanyin jiki tace"Mama wani suke son su auramin, nikuma Bana sonsa, akwai Wanda nakeso, shine Abbana yace Gara yaturani aiki inyi nesa da gida saboda karna dinga haduwa da Wanda nakeso din"

Mama tace"subhanallah, Aisha ai ba'a bijirewa iyaye, duk abinda suke so shi akeyi, Amma menene laifin shi Wanda suke so subakin?"

Cikin sanyin jiki tace"bashida laifi mama, yanzu ma nakoma sonsa, shizan aura"

Cikin sauri Shahaab yabude Idonsa ya kalleta, lokaci daya fuskarsa tayi kicin kicin 6acin rai da tsananin kishi yafuto qarara, mama kuwa murmushi tayi tace"ikon Allah, har tsuntsun yatashi daga kan Wanda kike so din? To meyasa kika haqura da za6in naki? Inde har yanzu kina sonsa, Sai muje dake har Garin naku inyi musu magana cikin fahimta subarki ki auri Wanda kike so din"

Cikin sauri tace"A a mama, Aina haqura dashi, saboda ya yaudareni, ya6oyemin gaskiyar waye shi, Bayan nagane Kuma naji duk na tsaneshi"(=ØFÞ<Øûß
@&þ=ØÞ)

Runtse Idonsa yayi, cikin 6acin rai ya d'ago Kansa daga cinyar mama ya kalleta yace"kozaki danyi shiru please?, banson jin wannan shirmen "

Mama ta kallashi da tsananin mamaki tace"menene abun 6acin rai anan? Kai take Bawa labarin?"

Cikin masifa yace"mama I'm tired... tazo tasani agaba tanamin wani zancen banza da wofi... "

Idon Aisha yaciko da qwallah, yanda taga ransa ya6acin Nan saita tunada ranar dasuka fara fada yake mata kashedi akan ogonsa Mahmud Wakili, cikin kuka tatashi da gudu ta wuce daki, bayanta yabi da kallo, yanda take gudun yasa hips dinta suke rawa,wani irin jarabben yawu ya hadiye saida yaga shigewarta daki sannan yasaki wani irin tsaki.

Mama ta kalleshi fuskarta d'aukeda damuwa tace"meyake damunka ne? Yarinya tana bakin qoqorin ta akaina bata gajiya, sannan muna Dan zancen mu kazo kasata kuka ka Koreta, haka kawai badakai take magana ba kahauta da fada, ko tunda kake zuwa falon Nan ka ta6a ganin ta tazauna?"

Cikin kishi yace"mama Kuma saita zauna tanata cewa ta tsaneshi ta tsaneshi kinajin ta bazaki hanata ba? Tace ya yaudare ta kinyi shiru baki dauki mataki ba, tadawo tace ta tsaneshi Shima baki hanata ba, Kuma idan tace bata sonsa fa kwata kwata?"(>Ø#Ý)

Mama tace"saime? Dakai take? Kai tace ta tsana?"

Cikin kumburi yace"a a "

Tace"to banaso, yanzu kasa tana kuka idan tafara wannan shegen fishin Nata Allah ne kadai yasan ranar dazata sauko, tashi kaje dinning Kaci abinci katafi part dinku"

Cikin shagwa6a yace"mama korata kike ko?"

Tace"nibana korarka,Kai dinne wani lokacin kacika rigima,kabar matarka acan nikuma kazo Nan ka dameni"

Murmushi yayi yace "shikkenan naji zan tafi, tashi muje kibani abinci"

Cikin sauri tace"me amfanin matarka?Nima Aisha ce tabani"

Murmushi yayi cikin ransa yace"aikuwa Nima saita Bani"
Amma a fili saiyace"to Bari in Dan kalli labarai idan zan tafi inkwnta saina ci abincin"

Tace"toshikkenan saida safe zanje in kwanta Nima,tunda ka kori yar hirar tawa,"

Cikin jin dadi yace"to mama saida safe"

Harta juya zata tafi saita dawo tace"yawwa wacece Aisha ne?"

Cikin sauri yajuyo ya kalleta yakasa bata amsa, tace"ka tsareni da ido baka Bani amsar tambaya taba"

Cikin wata irin kunya ya sunkuyar da qansa tareda shafa sumarsa yace"mama ai kece"

Murmushi tayi tace"banason qarya Mahmud, wacece Aisha?"

Cikin kunya yacigaba da shafa sumar sa,saide Kuma yaqi kallon ta, ahankali yace"wata ma'aikaciyar muce"

Murmushi tasake yi cikin ranta tana qara godewa Allah Dan da alama Mahmud din Nata soyaiya yake batare data Sani ba, cikin murmushin tace"ma'aikaciyar takuce zaka iya sadaukar da ranka saboda ita?"

Cikin shagwa6a yace "mamaaaah...."

Dariya tayi tace"to in tayi tsami naji, saida safe "

Cikin sauri yace"to Allah yakaimu mama"

Saida tashige daki sannan yasaki wata irin ajiyar zuciya, saida yayi Zaman minti ashirin shi kadai a falon, sannan yatashi yanufi dinning, yau da Kansa yazuba abincin acikin wani plate Mai kyau.


Sannan yad'auki gorar ruwa guda daya, yad'auki brief case dinsa yawuce Dakin Aisha.

Handle din dakin yakama sannan yashiga tareda rufowa, duhu ne ya wanzu a Dakin da alama ta kashe wutar ne ta kwanta, kunna wutar yayi lokaci daya ya hangeta kwance akan gadon jikinta a rufe ruf da blanket.

Hasken data Gani a idonta ne yasa ta bude idonta, lokaci daya idonta ya sauka akansa yana kokarin ajiye kayan dake hannunsa.




Shahaab littafin kudi ne, nera 300 na kacal

Zaki tura 300 ta wannan account

0164549488
Amina muhammad
GTbank

Kokuma katin MTN tareda shedar biya ta wannan number 08033300034





Mutara zuwa gobe=ØOÞ<Øûß






El Yaqoub
'<Øûß


BASAJA TAKU NA BIYU




Ummah da Abba suna tsatstsaye atsakar gida suna kallon ikon Allah, Hajja ta riqe waya a hannu Sai zagaya tsakar gida take tana mita.

Abba ya kalleta yace"Hajja da haquri kikai da Kiran wayar nan haka, yanzu karfe goma saura, itama idan kin sameta ma may be basa tare Dame wayar, kokuma sunyi bacci"

Cikeda masifa tace"mamuda kaifa nariga nagama sanin baka damu da yarinyar Nan ba, inda kadamu da'ita lokacin data bugomin waya nace bazan bata kaiba Aida haquri yakamata kabani inhadaka da'ita, Amma saika yi mursisi kakara redio a kunne, nafi sati Ina Kiran yarinyar wayar taqi shiga, tayaya Hankali na zai kwanta?"

Umma ta kalleta tace"Hajja to tunda taqi shiga kibari mana gobe saiki kirata"

"bazan Bari ba Hadiza,kunga banfa riqeku ba, kuje kuyi kwanciyar ku, Amma nikam yau saina ji muryar mesunan qawa zan iya runtsa wa, haba dadewar ai tayi yawa, Yan birni da suka 6aci dason duniya waya Sani ma kohar sunyi tsiren ta"

Ummah ta sunkuyar da kanta tayi shiru, Abba kuwa kujera yaja ya zauna, Ina ya'isa yaje yabar Hajja awaje? Aikuwa da basu wanye lafiya ba gobe.



******


Bayan ya ajiye kayan zama yayi aqasan d'akin tareda daure fuska yace"sauko magana nazo muyi"

Babu musu taja hijabinta tasaka, sannan ta sakko Qasan Dakin ta zauna kanta aqasa hannunta duka biyun suna cikin hijab dinta.

Ajiyar zuciya yasauke yace"ba gaisuwa?"

Kanta aqasa tace"yalla6ai Aina gaisheka dazu"

Cikin sauri ya katseta "ke da Allah banason wannan yalla6ai-yalla6ai din,shikkenan dan abu yafaru bazaki tsaya ki saurari abinda zan fada miki ba, saiki yanke min hukunci, agabana kina cewa Wai wani kike so, ni kin tsaneni ko maaamah?"

Yaqare maganar da wata irin murya kamar zai Fashe da Kuka.

Hakanne yasa zuciyarta ta karye, Nan da Nan tafara hawaye, cikin kuka tace"bakaine ka yaudare niba, kasa Abbana ya rabani da Hajja yakawo ni wani waje aiki,aidama baka sona matarka kakeso tunda Qin fadamin kokai waye kayi" taqare maganar tana turo bakinta gaba

Cikin sigar rad'a yace"Amma nabaki haquri..."

Cikin kuka tace"ainima bance komai ba,kawai de karabu Dani kafita daga rayuwa ta, tun farko ma da nasan cewa kaine Mahmud Wakili bazan saurareka ba, sawun giwa ai ya take na....."

Cikin sauri ya katseta"maaamah.... Tun farko nasan cewa bakya sona, ranar Dana fara haduwa dake ma nasan cewa bakya sona..." matsowa yayi gab da ita, yasaka hannunsa biyu yariqe fuskarta,yasake yin qasa da murya yaci gaba da fadin"amma ni Ina sonki maaamah..."

Lumshe idonta tayi, Hakanne yabawa Hawayen idonta damar zubowa akan kumatunta, ahankali ta bude idonta, sannan tasaka hannu ta janye nasa hannun daga kan fuskarta, ta kalleshi tace"bazai iyu ba, saboda Abba na bazai baka niba, maqocinmu yaganni lokacin dana shiga motar ka, Kuma yaganni lokacin Dana futo, Abba na yayi fishi Dani Kuma duk kaine sila, tun farko inda kayi magana dashi dole zai fahimceni"

Tunda tafara magana ya zubawa lips dinta ido yana kallo, kawai moment dinsu na cikin mota yake tunowa lokacin dayake kissing dinta.

Ajiyar zuciya yayi shibaiga abun damuwa anan ba, ahankali yace "to maaama munshiga mota me mukayi? Meyasa Dan kin shiga motata Abba zaiyi miki wata fahimtar, ai babu abinda mukai..."

Cikin kuka ta daga murya tace"basaida ka tsotsi bakinaba, Kuma aina hanaka Amma shine kaqi denawa"

Murmushi yayi, yace"ni nama dade da mantawa maaamah, jinake kema kin manta, maaama akwai dalilin dayasa na 6oye miki kaina, mama da Ramadan sune suka sakani hakan"

Cikin sauri ta d'ago ta Kalle shi, jijjiga Kansa yayi yace"yes.... Saboda wani dalilin su Wanda nikaina banga amfanin saba, Sai Bayan nahadu dake ne Naga amfanin hakan tunda gashi nagane kina sona da gaskiya, ba kudina kikeso ba, bakisan waye niba Ina dashi banida shi Amma ahakan kika saurareni, maaamah...Ramadan koda yaushe bashida burin yaga naqara aure, mama kuwa tayi maganar tayi maganar harta gaji,kiduba shekaru na maaamah har yanzu banda yaro ko daya, mama kullum burinta shine taga naqara aure ko Allah zaisa na haihu, Amma naqi yarda saboda inason matata munirat banason nayi abinda zaisa hankalin ta yatashi har tayi tunanin nadena sonta, naje Asbiti andubani, doctor's dayawa sun tabbatar min qwayoyin halittana lafiya suke, zan iya haihuwa a kowanne lokaci, Amma munirat bataje ba, koda yaushe tana fadamin haihuwa ta Allah ce,yafimu sanin halin damuke ciki, Kuma ita gidansu sunada gadon haihuwa tunda ba'ita kadai mamarta tahaifa ba, muma idan mukai haquri Allah zai bamu watarana, tafi tunanin rashin lafiyar daga nine, hakanne yasa na shirya har qasar waje naje akan hakan suma sun tabbatar min lafiya ta kalau, hakan Dana fadawa mama da Ramadan shine yabasu damar da suka sake damuna akan maganar aure.

Bayan haduwa ta dake, ban 6oyewa Ramadan komai ba, saboda a ranar ma dashi muka fara zuwa garinku, har fadan mu saida nafada masa, daga lokacin da nabar garinku ban sake tunanin komawa ba, saida tunanin ki yamin yawa sannan, tunda Ramadan ya lura da tunanin danake nakuma fada masa komai daga Nan yafara cusa min ra'ayin ki araina daga qarshe harna gane Ina sonki, kullum Ramadan fadamin yake karna kuskura nafada miki koni waye, yakamata ace nagama sanin halin ki, shin zamuyi abota dake ta Amana kokuwa? Banta6a tunanin akwai soyaiyar gaskiya a duniya ba Sai ranar dakika Bani kyauta kika fadamin kudin karatun qaninki ne da kike Tarawa kika siyomin agogo dashi, kin sake shiga raina a ranar, kin birgeni yanda bakya zato, na fadawa Ramadan komai, shine yasake Bani qwarin gwiwar dazan tunkareki da maganar soyaiya, inba hakaba to shi zaizo har gidanku yace yana sonki, hakan ne yasa nafada miki Ina sonki, Sai Bayan kin amince da soyaiya ta shine Zaki gujeni?"

Sauran Hawayen idonta ta share, sannan tace"kaine kaje super market akano koba kai hane? "

Ahankali yace"nine, kuma tun a ranar nayi DANA SANI akan rufe miki koni waye danayi, inda kinsan cewa nine Mahmud Wakili da tuni na bayyana a gabanki na tambayeki waye wannan Yaron dayake tare dake?"

Cikin shagwa6a ta turo bakinta gaba tace"niba saurayi na bane, saurayin fati ne"

Cikin kishi yace"koma waye maamah banason kisake sauraren kowanne namiji, Rasa control din kaina nake, Bana son sake ganinki da kowanne namiji this is the first and last kinji ko?"

Cikeda yarinta tace"um"

Wayarsa yadauko dake gefe, yayi Dialing wata number, yasaka ta a hands-free, ringing hudu aka amsa cikeda nutsuwa, kallansa tayi tarasa bakin magana, ahankali ya jijjiga mata Kai yace"your brother..."
tareda bata wayar.

Cikin mamaki ta kar6i wayar tace"jabir...."
Saita Fashe da Kuka

Shahaab ya Girgiza Kansa, cikin ransa yace"Yarinyar Nan batada damuwa, abu kadan kuka na farinciki Dana baqinciki"

Daga d'ayan bangaren cikin wani irin farinciki jabir yace"takwarar Hajja,Wai kece?"

Cikin sauri Kuma tasaki dariya tace"Dalla nice"

Cikin mamaki tace"amma Yaya akai Naga kin kirani da number Yaya Mahmud?"

Cikin sauri tace"yaya akai kasan shi?"

Yace"muna waya dashi sosai, amma ban fada masa yayata tana aiki a gidansa ba, yacemin ogansa ne yad'auki nauyin karatu na"

Hararar wayar tayi, sannan ta juya ta harari Shahaab, cikin sauri tace"bawani ogansa, shine, Kuma idan nakoma gida ma saina fadawa Abba da Hajja da Umm...."

Kafin taqarasa maganar Shahaab yayi sauri zai qwace wayar, itama tafara kokarin hanashi,basusan sun kashe wayar ba Garin kokawa kowa yanaso ya kar6i wayar, saida ya Kar6a sannan yace"miye haka? Meyasa Zaki fada masa?"

Hawaye ne yasilalo daga idonta, cikin kuka tace"to meyasa Shima zaka masa irin nawa?"

Wayar yasakar mata, sannan yariqe fuskarta da hannu biyu yace"sokike nafada masa nine na dauki nauyin karatun sa? Menene abun birgewa to? Nayi ne Dan Allah,sannan Kuma danke, dakika dauke kudinsa da kike Tarawa zai tafi makaranta kika min kyauta dashi, to gashinan nahutar dake, Saudia Kuma Dama ai kece Zaki kaimu ko...?"
Yaqarasa maganar cikin sigar tsokana, cikin farinciki takai masa Dukan wasa a hannunsa, sakinta yayi yana murmushi, sannan yadauko abincin sa ya ajiye akan cinyarta yace"dazu kinbawa mama, nikuma kika hanani, yanzu saiki Bani Nima"

Cikin sauri tace"kaje Kaci afalo, kaga yanzu goma da kwata, dare yayi, baka tsoron matarka tasan kana zuwa dakina?"

Fuskarsa yadan daure yace"kinaso na kwana da yunwa?"

Cikin sauri ta Girgiza masa Kai, yace"to bani"

Kallan abincin tayi tace"to ai babu spoon"

Cikin shagwa6a yace"da hannu"
Cikin ranta tace"nashiga uku"

Afili kuwa saita Girgiza masa Kai tace"um um ni bazan iyabb....."

Kafin ta qarasa maganar cikin sigar rad'a yace"please"

Badon tasoba tasaka hannunta tafara bashi abincin, duk lokacin dazata saka masa a bakinsa saiya Lumshe Idonsa sannan zai fara ci, mamaki ne ya kamata ganin yanda yakecin abinci kamar bayaso, har qaguwa tayi yagama saboda ita Bahaka mama take cin Nata ba, wanne irin cin abinci ne wannan saikace mace.

Saida yaci yaqoshi, sannan yariqe tsintsiyar hannunta, yafara tsotsar Yan yatsun data bashi abincin, Idonsa a Lumshe suke yana tsotsar yatsun kamar wanda yake shan sweet, kallansa tayi tanajin gabanta yana faduwa, wani irin yanayi yana shiga jikinta, ahankali tazame hannunta daga bakinsa, babu musu yasaki, cikin wata irin murya yace"Albishirin ki"

Cikin sauri tace"goro"

"to menene Goron albashir dina?"

Fari tayi da idonta tace"duk abinda kake so"

Yace"kinyi alqawari?"

Tace"inde baifi qarfi naba"

Briefcase dinsa yabude, yad'auko wasu takardu yad'ora mata akan cinyarta yace"kyauta ce daga masoyi zuwa masoyiyarsa, kyautar amsa tayin soyaiya ta dakikai, fatana ki kasance tare dake da dadi ba dadi,da kudi ba kudi,kici gaba da sona fiyeda kowa a duniyar Nan Bayan iyayenki, kibani kulawa fiyeda wadda Zaki Bawa 'ya'yanki,kijani ajikinki, muyi rayuwa tare har abada, kyautar sabon company n Dana bude yau ne"
Yad'ora hannunsa akan takardun tareda bude wani shafi, can qasan page din ya nuna mata yace"kinga sign dinki daga yau, a ko'ina haka Zaki dinga yi,Ash-hab sunan yamiki dadi ko?"

Yaqarasa maganar tareda Dagowa yana kallon ta, tunda yafara maganar Aisha take kallon sa, wanne irin mutum ne Shahaab? Dama haka halaiyarsa take? Duk wannan abun dayake saboda kawai tana sonsa ne? Yakai mahaifin ta umara, yakai qaninta karatu qasar waje, duk wannan abubuwan da wannan facaka da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

3 Comments On SHAHAAB
avatar
fateema

7 months ago

Reply

Allah yakara basira

avatar
taskar

7 months ago

Reply

Replying to fateema

Ameen

avatar
ummu-swabir

2 months ago

Reply

Thanks

Please Login or Register in order to submit comment