Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yaji Sabida yanda yaga ko Sallar asuba nakasa tsayuwarta,Yanzu da safe kuma nakasa tafiya shine yakemin wani gashin banda na dare da yaimin.

" Sannu"

Kauda kaina nai ina sharar hawaye wani shegen zafi nakeji har yanzu wajan saidai ba kamar yanda natashi ba.

Da kanshi ya sanyamin kaya tare da fesamin turare,Yana kallon wayarshi da aketa kiranshi akai akai Amma yakasa d'auka Sam beson fita yau bemayi niyyaba,Amma yasan koda Abbanshi yake yawa dole saiya lek'a asbt.


"Zaki iya fita kuwa ko na amso mana break dinmu nan?

Cikin sanyin jiki yabar d'akin.

Hamdala yayi ganin maman bata falo kawai saiya sami babban tire ya jero komai dayasan na buk'ata ne Ya fice.

Banwani tsaya Jan raiba sabida yunwar da nakeji,Saida naci na koshi sannan yaban magani nasha,duk abinda yakeyi yanayine yana kallon lokaci Amma sabida beso yatai yabarni da buk'atar wani abu shiyasa yakemin komai anatse.


Saida ya kwantar dani tare da lullube Sannan ya sumbaci goshine bayan ya ajemin wayata kusa dani,Lokacin goma na safiya yayi.
" Ga wayarki nan kusa kome kikaji ki kirani dan Allah zan dawo.


***
"Ah babana kafara wasa da aikinka ko? Jiya ka makara yauma kalli lokaci lafiya ko? Itakanta cikin zuciyarta Addua take Allah yasa bakuma yin wani abu yaiba,Lallai da ya amsa sunan mutun Mara tausayi.

Shafar kanshi yayi yana d'an kauda fuska" Mun d'an makarane mama Amma aigashinan zanfita yanzun din.

To Allah ya tsare yabada sa'a Amma ban ga ayshan ba yau,Lafiya ko?

"Lafiya lau mama shiryawa takeyi,Da sauri ya lallaba yabar d'akin kamin asirinshi ya tonu.

Fuskarshi d'auke take da yalwa taccen farinciki Addua yai tare da zama cikin motar yafice.

Wani barci me nauyi yai gaba dani,Sabida yanda nasami nutsuwa Sannan narage jin duk ciwace ciwacen da nakeji da.


**

Agaggauce ta gama shirinta tsaf kamin ta d'auko garin magungunan ta zuba cikin jaka,Duk da cewa tasan da wuya idan maganin arziki Amma saitasami kanta da adduar Allah ya bata sa'a ta aiwatar da komai cikin nasara.

" Ke kuma ina zaki kikai wannan gayun?

Gyara zaman Jakarta tai kamin tace"Dinkina zan amso Amma zan biya gidan mama hauwa in dubo amarya tun ran biki ban komaba.

Tsaki maman tasaki tare da harararta,Itakuma tasakai ta fice.


***
Barci nai sosai,Dan sai wajan gefin azahar naji muryar mama sama sama tana tashina.

Da sauri natashi zaune ina murzar ido"Sannu mama ina kwana yau banfitaba kiyi hakuri.

"Ke kwantar da hankalinki babu komai ai,Zuwana hudu kenan amma sainaga baki tashiba,Shine nafarajin tsoro naga garadai in tasheki kodan yunwar cikinki.

Kuma sadda kaina k'asa nai inajin kunya balle da idanuna suka kai kan agogo kenan sallah akeyima wani wajen.

Yunkurawa nai ahankali na mike sainaji jikina yad'an saki ba kamar d'azu ba shiyasa sai na mike ina fadin" Ganinan zuwa yanzu mama.

Har nakai kofar bayin sainaji muryarta tana fadin"Ki kuma shiga ruwan dumi kinji ko?

Idasa shigewa nai tare da rufe kofar ina zare ido.



Ban cuci kainaba na tsaya nagyra jikina sosai Sannan na d'auro alwala nafito.
Wayata na duba kiran Dr. Bakwai Saina mamana biyu na abbana daya sai yaya maryam ita babu dadewarnan ma tayoshi ina wanka tunda be wuce minti shidda ba.
. aje wayar nai nai shiri na anatse nai kwalliya cikin wata bak'ar doguwar Riga me adon blue din duwatsu agabanta da hannuwanta,Rigar tai kyau sosai na d'aure d'an gyalenta sannan na tada Sallah.

Addua nai sosai Akan Allah ya kareni daga dukkan sharrin Abinda ya halitta,Sannan nai addua akan Allah ya k'aramin hakuri da juriyar zama da Dr. Sai yanzu nake tuna wata hira da mukai da ya fati,Inda ranar nakeceta wai naga tunda nazo gidannan baki da nutsuwa idan zaki fitsari ko wani abune?

A lokacin hararata tai kamin tace Aysha kincika sa ido wallahi,Ciwo nakeji idan zanyi fitsari da kyar ma nakeyinshi,Naima Dr. Bayani amma yakasa ganewa.

Tabe bakina nai kamin ince uhumm to idan bazaibaki maganin da zaki warkeba kawai kije kiga wani likitan mana,Ai bakya zauna da ciwoba kilama infection ne.

K'aramin tsaki taja lokacin kamin tace babu wani infection wallahi tsabar jarabarshi ce kawai da be gajiya.
Ganin ina kallonta yasa tatashi tabani gu alokacin,To tabbas yanzu na fahimci inda waccan maganar ta dosa Sam Dr. Bazaiyi wani hakurin kirkiba.

Tashinai jin anakuma kiran wayata,Ya maryam ce,Da sauri na d'auka tare da gaisheta.

"Lafiya lau k'anwata lafiya ko? Yanaji muryarki haka? Meya faru?

Idona ya ciko da kwalla dan wallahi tausayin kaina nakeji" Babu komai yaya inasu abulkhairi?

D'an jimm tayi kamin tace "Shikenan Ammadai kinsan baki da kamarmu ko? Idan akwai wata damuwa ki gayamin kinji Auta? Dayake wani lokacin suna kirana da hakan sabida nice mace auta cikin d'akinmu.

Shiru mukai sai sheshshekar kukana da take Saurare" Aysha,Dr. Ne ko?

Ahankali nace eh ya maryam ni ban sonshi.

Inajin saukar numfashinta kamin tace "To kiyi hakuri kowace mace saita fuskanci hakan kamin tasaba,Danhaka kidage da sama jikinki ruwan dumi bawai me zafin ba sosai,Kidinga sakarmai jikinki sosai banda kuma gardama,Ahankali zaki dainajin komai,Ki daina kuka kinji?

Kaina kawai na d'aga mata Sannan taimin sallama na ajiye wayar,Turare nakuma fesawa nabar d'akin bayan na gyara inda zan gyara.


Duk wanda zai kalli fuskata saiya gane nai kuka Sannan kwata kwata babu kuzari ajikina balle gashi na yini barci duk jikina yagama mutuwa.
Ganin mama da bakuwa yasa na gaisheta ina niyyar zama maman tace" Kinga wuce kici abinci tukunna Saikizo ki zauna din.

Haka kawai sainaji banji dadin ganin bakuwar mamanba hasalima sainaji hankalina yaki kwanciya d irin kallon da takemin.

Daga inda nakecin abinci ina hangen yanda taketa mutsu mutsu kamar tanaso ta fiddo wani abu.

Bansan me tacema mamanba tunda akwai tazara tsakaninmu Saidai kawai naga tataso ta nufo wajan da nakecin abincin.

Agaggauce na dinga Sauri shiyasa bata jima da zama ba nikuma na mike to dama ba wani na kirki naciba,Sabida yanayin bakina.


Da kallo tabiyoni Sannan ta zauna tana zuba abinci.


Kwanciya nai saman kujera kozanji dadin jikina,Inda maman ketamin sannu nikuma kunya na kamani Ashe ta gane halin danake ciki.

Hira take Jana dashi saidai nauyinta da nakeji yau din ya hanani sakin jiki muyi hirar kamar yadda muka saba.
"Mama wannan ma diyar cikin gida ce? Can family house dinsu Abban.

Murmushi tayi kamin tace " A a diyar k'anwatace suwaiba wadda tazo kwanaki nacemiki k'anwatace to diyartace.

Shiru nai ina tuno kallon danaga matar na bina dashi aranar,Saikuma na tsinci muryarta tana fadima maman cewa"Oh Ahmad da kwashe kwashe wannan ma ai yarinyace k'arama bata wuce sa'ansu zaitunaba,Banda abinshi me zaiji jikin wannan kwailar.

Kauda tunanin nai kamin ince"Ashe tanada 'ya'ya da yawa?

"Eh aiko yaranta Tara ta aurar da hudu mata yanzu akwai biyu gabanta waccan da k'anwarta Sauran maza ne.

Shiru nai ina tunanin anya akwai jituwa tsakanin maman da 'yan uwanta kuwa?

Katsemin tunani tai da fadin" Duk 'yan uwana sun gujeni matan sabida kawai k'addarar mijinki shiyasa nima nafita harkarsu yaransuma da basu zuwamin saida k'anwar mamarmu taimusu fada Sannan suke d'an gittoni nidai iyakata dasu ido.

Yamutse fuska nai kamin ince uhumm Allah ya kyauta to Ammadai basu kyautaba gaskiya,Tunda shima ai ba akan son ranshi abun ke faruwa ba.

"Ai su basusan hakanba.

Kiran da akaima maman yasata tashi ta nufi d'aki nikuma Saina lumshe idanuna,Murmushi nasaki lokacinda na karanta message din dr.daya shigo wayata yanzu" _Pls_ _Babyna_ na _tuba_ _dan_ _Allah_ _ki_ _d'aga_ _wayata_ _jikinki_ _kawai_ zan _tambaya_ .


Dora wayar saman kirjina nayi kawai na rufe idanuna na tabbata ko ina yake yanzu zai shigo gidannan danni kaina na fara lura da irin zazzafar soyayyar da yakemin.

Wani irin mugun nauyi naji kaina yaimin wanda narasa dalili,Kuma kamar an hanani bude idanuna balle inga meke shirin faruwa dani haka nan kusa?

Motsin Leda yasani bude idanuna,Fes na saukesu akan budurwa Dana bari tanacin abinci,Toma meya kawota saman kaina?

D'an Murmushi tayi kamin tace "Sannunki da hutawa" kuma har lokacin hannunta na cikin Jakarta tana liliyar ledar danajejin motsinta har lokacin.

Tuno wulakancin da sukeyima mama yasani yimata wanikallon banza kamin nace"Lafiya kike tsaye saman kaina?

Ta 'yan duniya zatamin,Dankuwa wani murmushi tai daidai lokacinda ta zaro hannunta naganshi da kwantattar Leda da alama koma menene cikin ledar shirin watsashi kawai akayi dama.

Tuni na mike tsaye nauyin jikin da nakejima na nemeshi na rasa rike hannunta nai gam ina harararta duk da cewa agirme zata girmeni kuwa.

Tana k'okarin ta kwace hannunta ina tambayarta uban me zata zubamin jikina.

Mamace ta fito da sauri tana ajiye wayar ta akan kujera ta rikone aysha saketa dan Allah yi hakuri ki kyaleta kinji?

Idanuna har sunyi ja"Nace mama wani abu zata zubamin a jikina fa nace ta gayamin mene zata zubamin shine zata tsaya yimin shirme,Kuma wallahi kota gayamin mene ko yanzu naimata tsinannan duka.,Nai maganar ina huci duk da nasan cewa babu abinda zan iyaci jikinta dan tamafini girma,Amma zuciya tariga tazomin wuya ina tunanin zan iyamata komaima.


Shigowar Dr. Yasa kwalamai kira har lokacin tana tsakaninmu tana bani baki Amma hakanan nai biris da ita.

Kusan da gudu ya k'araso wani bak'in ciki na tasomai wato kowane shege ya d'auko shararshi saiyayo kan matarshi kenan,Itama aysha ba kanwar lasa ba"Lafiya meya faru?

"Nimadai ban saniba wallahi wayata aka kira na shiga d'aki,Itakuma ayshan kwancema take to kuma saidai na fito na gansu haka bangane komaiba.

Marairacewa yai yana kallona dan beso yakuma wani laifin,Akan wanda yayi" Kinga baby sakarta saiki gayamin meya faru?

"Cikin tsiwa nace wallahi ban sakinta saita gayamin maganin mene zata watsamin ina kwance.

Duk faduwar gabace ta samesu kamin ya bude hannunta wanda yake cikin nawa aiko saiga magani cikin Leda duk yai zufa sabida yanda ta matseshi gakuma rikon da naima hannun.


Wani matsiyacin mari ya kifa mata kamin yace" Ke dan ubanki maganin mene wannan?

Tuni tafara kuka yayinda mama ta toshi bakinta,Tsoro na bayyana k'arara afuskarta.


Sakin hannunta nai nakoma can gefe na zauna tunda naga yafara d'aukar mataki.

Wani Marin ya kifamata wanda saida ta kai k'asa sannan ya kwace maganin ya watsamatashi har a fuska da jikinta"muguwa kawai koma menene ya koma kanki babu abinda zai sami aysha da izinin Allah tashi kibar gidannan kamin inkira police suyimin gaba dake.

Da gudu tafita tana kuka yayinda jikinta babu inda be rawa,.



Tofa akace inzaka Gina ramin mugun....





Labarin JARUMA na kudine.


Acct no.
0005074141,Aisha sabiu ja'iz bank.

Kokuma atuntubi wannan layi.

08142643253.





Haske writer's association.
12/10/20, 2:32 PM - Naffy Aliyu Umar: 39




Wani irin shiru falon yayi ko wanne da kalar tunanin da yakeyi,Saidai daga inda nake zaune inajin yanda Dr.ke huci,Saina tuna wani lokaci da yaya fati ke cemin"Dr. Zuciya gareshi yanada tsananin fushi idan ka taboshi.
A lokacin nima cemata nai to ina ruwana da wani fishin ya dama waye baida zuciya.


"Kai ni Bansan me suwaiba ke nufi daniba wallahi Dan Allah yanzu maganin menene hannun kausar da take niyyar watsawa aysha shi? Cewar mama cikin tsananin bacin rai.

Saida ya fitar da wani uban huci kamin yace" To mama waye yasan mata komadai menene ai Yanzu saiya koma kan diyarta kuma wallahi bazan kyale duk wanda yace zaitabamin aysha ba.

Harara na wurgamishi aiko muka hada ido dashi.
Murmushi yayi tare da kashemin ido daya duk da cewa kuwa har lokacin ranshi abace yake,Soyake mu koma bangarenmu amma yana tunanin ta yanda zaimin magana.


Nidai ina zaune ban tankaba dan bama tasu nakeba Hankali ya karkata ga tunanin abinda kausar tai niyyar yimin Allah be bata sa'a ba.

"Tashi kije ki huta aysha insha Allah wataran sai labari ahankali zaku fahimci juna dasu kedai kita hakuri kinji ko? Cewar mama cikin yanayin damuwa.


Tashinai tsam nabar falon inda nabarsu nan duk suka bini da kallo sosai tafiyata ta sauya dan jikin yakuma min tsami.

Jiyai hankalinshi nakuma tashi,Sabida ganin yanayina tunaninshi kodai akwai ciwo ne jikina be saniba.

Mikewa yai da niyyar biyoni ta dakatar dashi tana kallonshi" Ahmad magana kakeso ka jawomin kome kake nufi?

Sosa kanshi yai batare da sanin inda maganar ta tadosaba"Kiyi hakuri mama"

Ni bance kaban hakuriba babana Ammadai kaje ka duba yarinyar mutane sannan dan Allah kai hakuri ta huta tukunna banso inkumajin kukanta kaji ko? Wai dama rashin hakurin ka har ya kai haka?


Akunyace yabar falon,Shi kanshi sai Yanzu yake ganin rashin dacewar abinda yayi to Amma yasan ba laifinshi bane besan abinda yajashi harya kuma aikata abunba Amma yai farinciki ba k'arami ba.


Idanuna alimshe naji k'amshin turarenshi hancina.
Kuma damke idanuna nayi musamman danaji ya zauna gefena.

"Babyna tashi muyi magana mana"


Wasu hawayene suka zubomin nasa hannuna na share,Amma ban iya kin amsa kiran da yaimin ba shiyasa natashi zaune ina kuma share hawayena.

Rungumeni yai yana sumbatar goshina,Kiyi hakuri kwanta inga wajan.

Kwanciya nai kamar yadda ya buk'ata,Da kanshi ya zare pant din dake jikina tare da bude min k'afafuna,D'an matse jikina nai ina turo baki Amma yakuma budewa sosai yana fadin"Saki jikinki mana baby ba tabawa zanyi ba.

K'okarin maida wondan nayi Amma ya rikemin hannu idanunshi lumshe"Karki maida bar wajan haka yasha iska bari inje insamomiki magani wani kalar jikine dake da beson wahala,Amma ahankali zaki saba kinji?

Cikin shagwaba nace nidai gaskiya a a babu wani sabawa da zanyi bazan kuma yadda kaiminba tunda kai mugune maye kawai.

Dariya yasaki yana matse hannuna"Naji ni mayene dama kintaba cemin haka ai tun kina gida shiyasa nasa maitar tawa harna aureki yanzu kuma zan dinga cinki kadan kadan kamin na cinyeki gaba daya kowa ya huta da bakin tsiwa.

Kuka nasaka yayinda shikuma yafita yana dariya.




***...

Saida ta tabbata da tagama daidaita kanta sannan ta shiga cikin gidan.

Mamarta da k'aninta ne kawai zaune suna kallo"Mama nadawo"

"To Sannunki Amma da wuri haka kingano amaryar kuwa?

" A a mama naga ankusa la'asar shine saina hakura sai gobe sai inje in yini can,Marata ke ciwo shiyasa nadawo.

"OK aigashin fuskarki duk ta jeme ki nemi magani kisha.


Toilet tashige tasaka kuka sabida tsoron abinda kaje ya dawo tsoron abinda zai iya samunta dan ita kanta tasan cewa maganin bawai na arziki bane.

Da gudu tafito jin wayarta na ring, Tunda taga number aboye tasan ko waye.

Cikin kuka tafara magana bakinta har rawa yakeyi" Ka temakamin dan Allah wallahi nasami matsala wannan maganin ni mijinta ya watsama shi ina fatan bana cutarwa bane?

"Hahhhhhah kinyi wauta yarinya magani bana cutarwa bane na mutuwane gaba daya danhaka ki saurari k'arshenki danni daga yanzuma bazaki kuma jinaba.


Kuka tasaka ganin ya kashe wayar,Nan tai zaman dirshan tanacigaba da kuka.

Taso ta gayama mamanta abinda ya faru yanda ko mutuwa tai za a dorama Ahmad din laifi saidai Kuma tana tsoron abinda zai faru idan har akaji itace taso tazubama ayshan magani dole za aji na mene Sannan dole zatagayama duniya wa inda takema aiki,Wanda fasuwar wannan daidai yake da rushewar rayuwarta dama ta ahlinta,Kamar yadda yaimata kashedi dama.


K'okarin kiran wayar taitayi Amma abanza dankuwa Sam bata tafiya,Hayewa gadonta tai tanacigaba da sharar kwalla.
Kausar macece wadda bata damu da addini damacan shiyasa koda wannan abun yafaru da ita ko addua daya bataiba tai kwanciyarta tana kuka yayinda wani shashe na zuciyarta ke nanatamata kilama duk burga yaimata babu abinda zai faru da ita.



"*"*"*

" Hello Dr. Idan kana gida ganinan shigowa sabida nazo garin zanga amarya kuma gobe da asuba zan wuce.

"OK ban gida amma yanzu zan koma shikenan saika shigo din.

K'aramin tsaki ya saki kamin yace" Ahmad ina rabaka da wannan arnen banzan wallahi yakamata fa kasan inda dare yaimaka ni Wallahi wannan Daniel din be minba gabadaya zubin azzalumai gareshi,Ka kiyayi kanka da sakarmai fuska har yaga iyalinka wallahi!!!

"Himmm kaidai kawai damacan baka sonshi salim Amma Daniel beda wata matsala data wuce kasancewarshi Arne amma inaimishi fatan shiriya ai komai na Allah ne.


" Wani mugun tsaki salim din yasaki kamin yace"To dama mene hadina dashi da har zakace wai ban sonshi? Kafirine fa? Me zamuyi da makiyanmu na bayyane Ahmad? To wallahi karaba kanka dasu domin bazasu taba sonmuba,Saidai sushiga jikinmu dan kawai su sami damar cutar damu.

"Shikenan karka damu daga wannan zuwan idan yayi zansan yadda zanyi inga na rabu dashi,Yanzu meyakamata muyi akan kausar?

" Aidama kullun haka kakecewa,Amma Bansan dadin me kakeji nayin abota da arne ba,ita kuma kabari sai gobe saimuje mu lallasheta muji waye yabata maganin da take niyyar zubama ayshan inba hakaba to bazamu gane wanda ke kulla tsiyarba dan da alama itama sata akai..



Anan suka rabu yayo gida da maganin daya fita nema.


**

Biyar na yamma,Ina zaune saman dardumar danai sallah har lokacin ban tashiba sabida jin jikina nake da wani irin nauyi haka kawai.

Sannu da zuwa nai mishi bayan amsamishi Sallamar da yayi,Wani irin tausayina yakeji,Yana mamakin yanda fushi baisa in yimishi wani rashin d'a a daban.

D'agoni yai gaba daya Ya maidani saman cinyarshi yana shafar Lib's dina da yatssanshi."Babyna Sallah kika gama? Taho na shafamiki maganin ya jikin da sauki ko?

Kaina na d'agamishi tare da kuma lafewa kirjinshi.

"Baby"

Yamutsa fuska nai amma ban amsaba.

"Kinji? Ki dinga sakin jikinki sosai Bansan wannan shiru shirin da kikeyi idan kuma wani waje yanamiki ciwo to ki gayamin kinji ko?

Kaina nakuma d'agamishi.


" Yauwa autar mata,Yanzu tashi ki shirya zamuyi bak'o abokina Daniel zaizo ku gaisa yanzu.

Yamutse fuska nai kamar zan yi kuka kamin nace"Daniel arnefa kenan?

"Eh bawani abu gaisawa kawai zakuyi.


Da kanshi yaimin wanka duk da irin tirjewar da nakeyi.

Shirinma kusan duk shi yaimin nidai inata binshi da kallo,awaje bazaka taba tunanin zai iyabawa mace lokacinshiba balle tasami kulawarshi Sabida tsabar tsare gira da shan k'amshi, Amma ni saima naga kamar kulawar da yake bani tamayi yawa.

Janbaki yashafamin Saidai kamin wani lokaci ya manne bakina da nashi,Saida yaga ya tsotse janbakin tas Sannan ya sakeni yana maida numfashi," Yaimiki kyau da yawa banso ya kalla yaji wani abu.

Turo bakina gaba Nai kamin nace"Saikace angayamaka kowama mayene kamar kai.




Tunda yakirashi awaya yace gashinan ya iso naji kawai hankali yatashi Sam banji dadin zuwan bakonba,Amma saikawai nabar hakan amatsayin sabida ya kasance ba musulmi bane shiyasa nakejin hakan.

Falon mama ya ajeshi suka gaisa da maman kamin ya gayyaceshi bangarenmu.

Ina zaune Saman kujera suka shigo..

Kallo d'aya naimusu na kauka daina,Da kyar nasamu naimusu Sannu.
Saida muka gaisa dashi Sannan na gabatar mishi da dambun nama da lemo dan abincin da akai da rana ya k'are kuma ba agama na dareba.



"Dr.wannan karon baby ka aura gaskiya naganta yarinya sosai kuma kana iya kusantar ta Ahaka? Kamar ma bata da lafiya ko?

Samun kanshi yai dajin haushin maganar denial din,Amma ya kanne" Yeah aysha kenan inasonta sosai kuma inajin dadin zama da ita sosai fiye Dana bayama,Kuma lafiyarta lau barci tatashi.

"Oh sorry" Yaushe zaka shiga abuja ne?

Lemo ya tsiyaya yasha Sannan ya kalkeshi"Gaskiya bazan iya shiga abuja yanzu ba,Bammaso inje ko ina Yanzu Sabida kadda nabar Babyna.

Dariya sukai atare Sannan sukaci gaba da hirarsu irinta abokai wa inda suka Dade tare.


Zamana nai cikin d'akin shi dan nan yafimin kusa,Sama sama nakejin hirarsu har ya mike da niyyar yimishi rakiya zai wuce.
Dr.ne yashigo tare da maidamin hijab dina jikina"Zomuje kimishi Sallama zai wuce,Amma dan Allah ki saki fuskarki haba madam ai saiyace bakiyi maraba da zuwanshi ba,Alhalin kuma wajanki yazo.

Bakina naturo gami da harararshi, Ni bawani wajena yazoba kawai dai wajanka yazo danni wallahi inbacin ka matsamin da babu abinda zaisa in gaisa da k'aton Arne.

"Naji dai kiyi hakuri shima daga yau bazai kuma dawowa ba insha Allah.


Yana rike da hannuna muka nufi falon,Mugun yana tsaye amma idanunshi gaba daya yagama zubeminsu.

Bansan harararshi nakeba Saida naji Dr. Na matsar hannuna.

Kayan daya shigo dasu ya turo gabana" To madam ayi hakuri gashinan babu yawa amma next time zanshigo miki da tsaraba OK?

Wata shegiyar harara nasakarmishi wadda ta juya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment