Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

zataje taga amarya,Amma kuma cikin Jakarta d'azu ramla ta kawo kudi har kimanin naira dubu Dari biyu,Bansan kona meneneba bataimin wani bayaniba.


Kan maman ne yakuma d'aurewa kamin tace" To Allah ya kyauta,Ammafa cikin zuciyarta tanata mamaki da al'aljabi to anyama suwaibar tasan abinda kausar din ke shiryawa kuwa? Kodai kudi aka bata domin tai wannan aikin kasadar kuma abin ya juye kanta?
Ganin tambayar duk bata da amsa yasa ta watsar tare da shigewa inda zata gabatar da Sallar ta.




***


"Haba dan Allah kadda ki wuce kijira aci abincin mana.

" Dariya tasaki tana goya baby ayshan"A a wallahi wucewa zanyi gashican yana jirana dama cewa yai abincin kawai zasukai yazo mu wuce kumamafa ni yau azumi nakeyi ramuwa kuma na gayamiki d'azu.

"Kai Innalillahi Ammadai banso ba,bari inbaki khumra Saikiyi amfani da ita nagode sosai ai inanan zuwa yini insha Allah.

Godiya taimin sosai Sannan muka rabu dayake sundawo yana falo yana jiranta.


Cabeni yai cikin jikinshi bayan yadawo rakiyar salim din.
Dariya nake ina kuma makalkaleshi sabida yanda yaimin d'aukar yara.

D'akina muka shige yana sumbatar kuncina" Baby abarni in huta mana nagaji yau gashi har yanzu bugun zuciya ta be komai daidaiba ko zaki temaka ya daidaita??

Yatsana nake turawa cikin kunnenshi yana dariya,Sannan nace to me zanyimaka?

Kannemin ido d'aya yai yana murmushi "Ah wai in d'anyi abun ko d'an mitsi ne.

Manyan idanuna nazube cikin nashi kamin in tsuke fuska" Nidai gaskiya a a wlh ban warkeba.


"OK to Allah ya k'aramiki lafiya muje inyimiki wanka Sai muzo inbaki wani labari.



""""


Cikin yanayin tashin hankali yake had'a kayanshi sai zufa yakeyi sabida tashin hankali da damuwa duk irin iskar dake busawa cikin d'akin Amma zufa yake ga jikinshi dake wata rawa rawa.

Tun jiya yake tsumayin jin an sanar da mutuwar Amma shiru kakeji yasandai indai anci wannan abun to mutuwa ta tabbata to inkuma ba'aci bafa?
Yasan tabbas asirinshi zai tonu, Yasan waye Ahmad ya tabbata suka had'u saiya kusa kasheshi shiyasa ya gwammace ya gudu kamin ya farga yafara nemanshi.






Haske writer's association.
12/10/20, 2:33 PM - Naffy Aliyu Umar: 42





"Mama kici abincin mana kin tasashi kinkasa ci"

"Uhum Bari babana wallahi abinne ya d'auremin kai,Duk iyakar bincikena na gano babu ruwan suwaiba hasalima batasan me yarinyar take aiwatarwaba, Saidai wasu kudi da akabata sannan tabayin waya da wata lamba wacce aka boye,Shine nake tunanin kodai aiki aka bata tayi batasan kona meneba kaikuma ka watsamata shi jikinta?
To kuma yanzu da kakebani labarin Daniel din saina fara tunanin to kodai shine yasata? To kuma gaskiya ina tunanin idan da shine to da bazaizo yakawo wani Abu daban ba.

Huci ya fitar yana shafar kanshi,Shi kanshi yasan cewa cikin kwanakinnan yanada damuwa me yawan gaske musamman tsakanin shekaranjiya jiya dakuma yau,Abinda yafaru shekaran jiya kusan tsoro akaso bashikuma sosai ya tsoratan da kyau da kyau,Saikuma ga wa innan abubuwan dake faruwa daki-daki yanzu tunanin irin azabar da zaima Daniel kawai yakeyi idan yakamashi,humm bacin salim ya tausheshi lallai da kila yanzu yana prison, Dan ya tabbata saiya kasheshi har lahira yanda zuciya tagama zuwa mishi wuya.


" Ki kwantar da hankalinki mama insha Allah komai zai warware tunda har gashi yanzu anfara gano inda matsalar take,Mama aysha alkhairice arayuwata,Shiyasa komai nata yake daban,Banso komai ya cutar da ita mama duk rigimarta bata damuna nidai fatana kadda Allah yasa koma menene yasami damar cutar da ita!!!



"Insha Allah babu abinda zai Sameta kai dai ka kwantar da hankalinka kuma ka dage da addua tashi kaje ku kwanta dare yayi kilama tanacan tana jin tsoro,Dan tunda nadawo gidannan na lura kamar bata da walwala dan Allah ka dinga kulawa da ita sosai kaji ko?

" To mama insha Allah, Abba be shigoba har yanzu?

"A a yashigo tuni ya kwanta maganin mura yasha.



****


Ina shafa addua yashigo cikin d'akin" Babyna har zaki kwanta babu jira?

Idanuna na zubamishi kamin nace"A a nai tunanin fita kayi ne shiyasa da zan kwanta.

"Oh no baby ai kince bakiso shiyasa bazan kuma fitaba indai ba wani babban abu ne ya tasoba kinji? Kina kyautatamin aysha be kamata nima nakiyin duk abinda kikeso ba,Danhaka ki kwantar da hankalinki duk abinda kikeso shi zan yimiki,Samomin tea nasha Dan Allah.


Dogon hijab dina na zumbula na nufi bangaren mama dan komai nacan.



Cikin nutsuwa nagama had'a tea din Saidai juyowar da zanyi naga wata doguwar inuwa wadda nake hangen tsawonta takusa tabo rufin falon.

Jujjuya idanuna nai Amma banga zahirin meneneba balle ace shine yai wannan inuwar haka.

Cikin zuciya ta nafara addua yayinda wani irin matsanancin tsoro ke tasomin tunda yatsan k'afana har cikin kaina,Da alama yanda nai tsaye ina kallon inuwar itama haka take kallona dan tsaye take kamar yadda nake tsaye.

Duk adduar Dana kamo ban tunanin INA kaiwa k'arshenta dan da wuri nake kamo wata,Motsawa nai da niyyar in wuce ,Amma ga mamakina sainaga itama ta motsa kamar zatayo wajena.

Wani uban ihu nasaki wanda ya karade duk girman gidan,Nafara jawo duk abinda ke gabana ina jifan inuwar dashi kumabakina bebar fadin duk adduar da nasan ta Neman tsarice ba.

Dagashi sai tawul haka yafito yayinda mama da Abba ko wanne ya fito daga d'akinshi,Lokaci guda na watsa falon da kayan danaita jefowa batare Dana bude idanuna ba.

Duk hankalinsu yai mugun tashi ganin kamar nafita daga hayyacina.

Ta baya ya tsafkoni tare da sakani cikin jikinshi gabadaya jikina rawa yake,Wani ihun nasaki jin ankamani,Agaggauce ya danna bakinshi cikin nawa yana k'ankameni.




10;37 pm.
Babu me magana cikin su Saini daketa Sauke ajiyar zuciya akai akai duk da cewa ba kuka nayiba kuwa.
Mama da Abban suka gyara falon yayinda Dr. Ke rungume dani afalon yana jijjigani har lokacin.


"Tashi kuje ku kwanta Ahmad,Cewar Abba yana sakin hannun rigarshi daya nade.


Ko dire k'afana kasa kinyi nai saidai ya d'aukeni gaba daya muka nufi bangarenmu.

Kwantar dani yai dan ko wankan be gamaba Amma nasamai kuka dole ya dawo ya kwanta gefena tare da rungumeni yana shafar duk jikina tare da huramin iska cikin kunnena.
Da niyyar lallashi yake shafar jikina,Saidai kunsan abu ga me Lafiya.

Inajin lokacin da yai Nisan kiwo cikin jikina Amma tsabar tsoratan da nayi tun farko shine yasani kasa ko motsin kirki balle in gujemishi.

Saida naji yai nisa cikin jikina sannan nasaki kuka dan yauma jinai kamar yaimin fami wajan.



*"*"*

Tunda naji yagama nai shiru da bakina kuma zuwa lokacin nasami nutsuwa sosai hankalina ya kwanta shegen tsoron dake cikin rainama na nemeshi na rasa.

Cikin muryar lallashi yace" Babyna muyi wanka ko?

Makale kafada nai ina kuma shigewa jikinshi tare da turo bakina.

Rungumeni ya kumayi yana tofamin addua,Saida ya tabbata barcina yai nisa Sannan ya lallaba ya tashi.

Wankanma agaggauce yagamashi yadawo gefen gadon ya d'auki al'k'ur,Ani gani yakeyi kamar idan yai barci to fa wani abu zai iya Samuna,Shiyasa ya gwammace yai karatun ko hakan zai iya zama mafita gareshi.





***

Asubanci ya doka daga katsina zuwa abuja,Wanda tsananin gudun da yayi yasashi kaiwa akan kari.


Nan dinma be tsaya bata lokaciba ya nemi yanda zaiyi ya canza gida tunda dama cikin asbtn da yakene akabasu gidaje,Kawai saiya fara Nema waje inda babu wanda ya sanshi.




***

Tunda nasamu nai sallar asuba nakuma lafewa jikinshi nakoma barci bayan gama azkar dina,To shimadin kwanciya yayi kusa dani yana d'an matsamin cinyoyina tunda sunfi matsamin da ciwo,Kamin wani lokaci shima barcin yai gaba dashi.

Dalilin dayasa muka makara kenan.

Tuni salim yazo gidan saidai iyakarshi falon mama tunda tace bamu fitoba ma.

Hirar abubuwan dake faruwa da Dr.din suke kuma tattaunawa,Dan abubuwan nada d'aure kai sosai.


Gajiya yai da zaman ya kuma dannamishi kira akaro na barkatai,Dan Yasan zai iya ganin laifinshi daga baya.


Da kyar yasamu ya d'an muskuta ya jawo wayar,Azabure ya mike ganin Tara na safe.
Dafe kanshi yai kamin yace "Kai innalillahi yauma sai mama ta gane na taba yarinyar nan tunda har nai wannan makarar.

" uhum uhum" Nasaki wata sheshshekar shagwaba ina kuma shigewa jikinshi.

Cikin lallashi ya fara shafar fuskata"Yi hakuri babyna rana tayi akwai inda nakeson zuwa kinji! Dan Allah tashi inyimiki wanka mama na jiranmu.


"Hello Salim yi hakuri ganinan fitowa.

Lallabani yaitayi har mukayo wanka" Yauwa babu inda kemiki ciwo ko?

Idanuna anarke na d'agamishi kaina.

Sumbatar kuncina yai yana murmushi,Nikam fuskata babu yabo babu fallasa.

Saikace me tarairayar baby haka ya dingamin nikuma sai basar wa nakeyi,K'aramin bakin nan nawa adane.

"Babyna muje"

"Hannuna na mikamishi shikuma ya rike yana kallon cikin idanuna,Idan har ya lura da kyau saiyaga kamar yau idanuna sun fada.



Da sallama muka shiga cikin falon.
Kwace hannuna nai daga cikin nashi na nufi mama tare da shigewa jikinta ina gaisheta Sannan na gaida salim dakuma Abba duk dake falon.
12/10/20, 2:34 PM - Naffy Aliyu Umar: 43




"Muje ki karya baby.

Akunyace ya idasa maganar sabida ganin yanda iyayen ke kallonshi,Shiko salim Sadda kanshi k'asa yai yana murmushi.


Kuma mak'alewa nai jikin mama ina turo bakina gaba.

D'an fiddomin idanunshi yai alamun umarni,Nikuma na makale kafada ina harararshi.

Murmushi yai tare da cewa" Mama kisata taci abinci.

Tashi yai ya nufi wajan cin abincin Saida ya kammala Sannan yadawo falon yana kallon salim"Muje .

Abbane ya kalleso tsaf kamin yace" Ban yarda da wannan shirin naku ba ina zakuje haka tun safe kuma ya maganar ayyukanku?

Sosa kai Salim yai kamin yace"Abba ba jimawa zamuyiba rubutu zamu amso!


"To Allah ya tsare saikun dawo ayi adduar fita data hawa abin hawa dan Allah ku dunga kula da titi.

Idanunshi na kaina yabar falon,Niko rufe idanuna nai sabida Bansan kallon da yakemin.
Muryata can k'asa nace" Mama nan gidan akwai wata doguwar inuwa jiya da dare itace Saura kadan ta kamani.

"Kaina maman ta shafa" Karki damu aysha babu abinda zai sameki da izinin Allah tunda kinayin Addua,Muma nan muna tayaku da addua insha Allah babu abinda zai kuma faruwa na damuwa saidai na farinciki kinji ko?

Kaina na d'aga mata inakuma lamkwashewa jikinta,Dan sosai nakejin duk jikina namin ciwo,Wannan karo na uku kenan Dr. Na shiga jikina Amma har yanzu banji wani dadi da ake cewa anajiba Sai shegiyar wahala da ciwon jiki.

"Tashi muje kici wani abu Saikisha maganin zazzabi jikinki yai dumi da yawa" cewar mama tana tasoni daga jikinta.



***

"Allah ne yaimin gata salim,Allah ne ya soni da rahmarshi daya bani Aysha yanzu, Allah ya mallakamata komai mutumina, Shiyasa rigimarta bata damuna wallahi,Kullun jin soyayyarta sabuwa nake cikin jinina kullun kuma ninkuwa soyayyarta takeyi cikin zuciyata,Fatana Allah yasa itace abokiyar rayuwata ta har abada inasonta wallahi.

Dariya salim din yasaki kamin yace" Ah lallai ka zurma da yawa gaskiya to Allah ya tabbatar mana da Alkhairi,Ni k'arfin halintane ke birgeni da ita kenan har inuwar ma bazata kyaleba,Kamar bata da tsoro sosai yarinyar ko?

"Eh gaskiya bata da wani tsoro irin na bada labari dinnan,Amma dai naga tanajin tsorona, Ya idasa maganar yana dariya.

Shima salim din dariyar yasaki kamin yace" Mutumina ai dole taji tsoronka tunda taji zahirinka,Ammadai ka dinga binta ahankali gaskiya dan duk cikin matan dakayi tafisu k'ankanta.

"Hakane kam ai ina rike kaina sosai insha Allah babu matsala.

Da wannan hirar suka k'arasa gidan Dr. Daniel,wanda yake nan katsinan,Saidai ga mamakinsu sai me gadinshi ya tabbatar musu da cewa ai asubancin barin gari yayi dan shima bemai sallamaba saidai ya duba yaga bashi.

Godiya sukai mishi dayake shi musulmi kuma iyalinshi ma na cikin gidan daga gefe inda ya waremusu.


Jimmm sukai cikin motar sai sake sake sukeyi.
" To wai zaman me mukeyi anan kawai kajamu zuwa abujan danni wallahi ko bazakajeba to lallai yau sainaje da izinin Allah.

"Ai nima ba cewa zanyi bazanjeba Amma ina tunanin mu fadi gida gaskiya.


" a a babu gidan da zamu fadi domin bazasu yardaba muje kawai idan Allah yasa mun sauka lafiya Sannan saimu gayamusu inda mukaje,Cewar Dr. Din yana zare ido.

Take motar salim yai suka d'auki hanya.



***

Kwance nake nai lamo d'akin mama dan yau na rantse ban kwana kusa dashi tunda beda tausayi,Saidai tunanin inda ya shige yinin yau shine ya hanani sukuni inajin yanda mama ke nemanshi ta waya akai akai Amma shiru kakeji.

Sainayi kamar in shareshi Saikuma inji hankalina be kwanta da hakanba,Dayake yaudin gidan rasuwar muka yini dan sai daf da la'asar muka dawo gida tokuma yanzu gashi ana maganar sallar isha'i.

Shigowar mama yasani lumshe idanuna kamar wadda barci ya kwashe wajan.

"Aysha barci kikayi kenan?

Mika nai tare da bude idanuna" A a mama idanuna biyu barcin dai nakeji amma inaso nai sallar isha'i ne.

"Eh hakan yayi dama cewa nai ko kinji su babana na maganar zuwa wani waje banda anso rubutun da sukace sabida nidai wannan shirun ya dameni d'azuma hafsat ta kirani wai ina su salim sukaje sunta Neman wayarshi Amma bata shiga.



Tashinai zaune kamin ince to mama ni Bansan inda zasuje ba,Ammadai ina tunanin sunyi abuja wajan wannan Daniel din dannaji suna tsara hakan.


" Innalillahi nabani basu hakuraba kenan? Kai wa innan yaran bansan lokacinda zasuyi hankaliba wallahi shikenan wace kalar masifa zasuyi can?

Tagumi na zabga dan sai lokacin naji nima hankalina yatashi tun safe Amma gashi shiru kuma wayoyinsu duk rufe nasan dan kadda aimusu fad'a ne kokuma ahanasu zuwa,Lallai Ashe suma duk 'yan rikicene.





Abuja.

Agajiye suke likis dakyar suka samu suka kama d'aki wani k'aramin hotel me kyau da tsada duk da cewa sun shiga da wuri amma kwanciyarsu sukayi kuma babu wanda ya bude wayarshi,Musamman Dr. Din wanda tsananin kewar Amarci ke nukurkusarshi Amma haka ya d'aure dan Yasan babu wanda zai yadda da wannan tafiyar Sannan koda suka zo dinnan za a iya cewa yai hakuri ya kyaleshi shiko yai Alkawarin saiyaji wannan cin amanar duk da cewa wajan kafiri bawani abune bane yin hakan.



Cikin dibara da taka tsan tsan suka fara Neman inda Daniel din yake aiko kamar yadda suka zata wato yabar asbt.
To abunku ga babban likita kuma kowa zai iya sanin inda yake.
Wajan k'arfe goma na dare aka turomishi sakon inda Daniel din ya koma dan hadda number din gidan.


Sai lokacin suka bude wayoyinsu,Kuma adibarance suka turama iyalansu massage dan hankulansu su kwanta,To nidai lokacinda wannan sako yazo ma tuni na manta nai barcina.




Washe gari.

K'arfe shidda sukabar hotel din dasuka kama zuwa gidanshi,Dayake yasan kan garin besha wata wahalar kaisu k'ofar gidan ba.

"Ka dainaji abinda nace maka dan girman Allah kabari muji komai cikin nutsuwa kadda ka hargitsa komai kuma muzo bamu fahimci komaiba.


Sunjima suna kwankwasar kofar gidan Amma shiru sabida ko me gadi be kaiga d'aukaba tukunnaba.

Saida ya tabbatar da koma waye yagama gajiya Sannan ya fito daga shi Sai Tawul dan wanka yake niyyar shiga dama.

Saida ya bude k'ofar sannan yake tambayar waye ke buga k'of......Tuni Sauran maganar ta mak'ale jikinshi ya d'auki rawa.

" Dr. Kune? Sannunku da zuwa Sannunku,Yai maganar murya da jiki da tsuma.


Dak'yar salim ya taushi Dr. Din ya zauna,Sabida tsabar yanda yakeji kamar ya kama Daniel din ya shakeshi Saiyaga ya daina motsi.

Tuni yagama rudewa yarasa inda zai tsoma ranshi be taba tunanin cewa zai iyajin kunya irin wannan ba.

Cikin bacin rai yafara magana"Bansan jin wani abu daga bakinka indai har be shafi abinda nakeson saniba yanzu danhaka ina me umar tarka da ka gayamin meka sani game da matsalar da kuka mak'alamin?


Ajiyar zuciya ya sauke yanajin wani d'aci cikin mak'ogoronshi,Sam be zaci zai iya fuskantar wannan damuwar ba,Musamman idan ya tuna da yanda abokansu suka dinga k'yamatarshi da sukaje karatu Amma Ahmad dinne kawai ke kulashi wanda daga k'arshema suka koma d'aki daya duk sabida yanajin tausayinshi tunda alokacin kusan shi kadaine Arne cikin su.

"Kayi hakuri Dr. Na munafunceka Kuma naci Amanarka Amma kaimin hakuri dan darajar ibadarka,Ba laifina bane....


" Kaga dakata dalla can idan zaka gayamin kawai ka gayamin tunkamin in kasheka wajannan wallahi.Ahmad din ya katseshi azafafe dan yafara gajiya da rainin hankalin da yake k'okarin yimishi.


"Kabari muji abinda zaice Ahmad dan Allah,Salim ya tari numfashinya shima.



Daniel" Lokacinda nakoma domin gyara jarabawata wadda banyiba kwata kwata,Alokacinne na had'u da wasu abokai wa inda suke duk mabanbantan k'asashe tunda alokacin ku duk kun dawo gida babu wanda yai saura acan,Da farko ban fahimci abinda sukeyiba sai ranar da naga sun kamo wata yarinya baturiya agabana suka yankata kuma suka gyara namanta.
Na kwana cikin tashin hankali da damuwa wanda rana guda kawai na zabge,Idan baka mantaba na kiraka wata nan Sunday da sassafe nake gayamaka zandawo bazan tsaya inyi gyaran ba Kaine ka tirsasani cewa indai gyara din tunda sun buk'aci hakan.

Ahmad alokacin komai yafara bansan ta yanda akai na fara wannan harkar ba,Tun ina sha'awar abinda suke saigashi sunfara bani bansan ya akai nafara cin naman mutunba Dr. Amma amfani mukeyi da jinin sabida yawaitar dukiya, duk matanka dake mutuwa babu sa hannuna ciki sai matarka guda d'aya lokacinda tai bikin walima naje tundaganan har can alhalin lokacin bakanan kokai bagayama zanjeba sabida kadda kai tunanin wani abu saidagaba baya ne matarka ta gayamaka sabida kyautunan danabata kayi hakuri nine nabada jininta kuma john ya kasheta da hannunshi,Daganan ban kumaba sai wannan danaje nakaimata gift domin taci ta mutu, Bazan kumaba Ahmad kayi hakuri nayi Dana sanin cutar dakai danayi.


Wani mugun naushi yakai mishi a fuskarshi kamin yace,Bakai Dana saniba dan uwarka dan inda kayi da baka koma zaka kashemin babyna ba.
Menai maka Daniel? Menaimaka da zafi haka da ka keson ganin kukana?

Idan ba Kaine ke kashesuba ubanka ya kashe sauran?

"Ka yarda dani Ahmad matarka d'aya na kashe itama bada niyya naiba sai wannan kuma nasan hakana be cimma ruwaba tun ranar danaje.

Rikeshi Salim yai ganin yakuma kaima Daniel din naushi wanda yai sanadiyyar fara zubar da jini daga hancinshi.



Shiru sukai tsawon lokaci ko wanne da abinda yake sak'awa yayinda Dr. Keta fitar da huctsafin baki da hanci sabida masifar dake makare akirjinshi.

Ganin kamar ya hakura ne yasa salim din Sakinshi yakoma ya zauna,Saidai kamin ya idasa ajiye mazaunanshi k'asa Dr. Din ya rufe Daniel da wani irin matsayacin bugu hannu da k'afa.

Da k'yar yasamu ya kwaceshi wanda tuni ya had'amishi jini da majina sabida tsabar mugun bugun da yaimishi na kwaf daya.

Yana kwance yana maida numfashi tare da share jinin dakebin bakinshi da hancinshi,Yaji sautin Dr. Din na fadin" Kodai ka gayamin gaskiya akan mutuwar matana kokuma wallahi yanzu yanzu in kasheka in kashe banza.


Cikin wahala yafara magana"Na amince kayi bincike idan har naimaka k'arya kaimin duk hukuncin da kaji zaka iya Ahmad Amma I yakar gaskiya ta kenan kayi hakuri,Yanzu haka k'ungiyar ta watse sabida abinda ka k'ona tsafin da kanshi ke rikida yashiga cikin jikin mutun ya halakashi kaikuma ka k'oneshi kuma ya shude har abada yanzu zamu fara girbar danasani kamar yadda nafara gani yanzu kayi hakuri iyakar gaskiya kenan Amma tabbas akwai wa inda keda sa hannu wajan kisan matanka Amma banibane guda d'aya kawai na kashe.

Dafe kanshi yai yana sauke numfashi,Lallai yana cikin masifa towai mutane nawa ke bibiyar rayuwarshine kuma meyai musu?



Salim ne yai gyaran murya"Kana nufin yanzu babu abinda zai sami ita matarshi d'in?


Gyara zamanshi yai yana yamutsa fuska sabida yanda ko ina ya d'aure jikinshi"Babu abinda zai sameta domin abinda zai cutar da ita din ya koneshi,Kuma wuta ta cinyeshi k'urmus kuimin hakuri Salim bazan kumaba kuma na tuba nai danasanin cutar da mutumin da ya kyautata min"


"Shikenan babu komai k'addarace babu yanda zamuyi Kaine sanadin mutuwarta dole bamu da mafita akan hakan Amma daga yau inaso kasani babu Ni babu kai karma
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment