Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

na waiga naga babu kowa,takalmina na cire tare da Dora k'afafuna saman nashi nai d'age na hade bakina da nashi,Abinda ban tabayiba.
Tallabo k'uguna yai yana sakin numfashi dan sosai abin yai matukar tafiya dashi.

Da kyar na kwace bakina idanuna har wata kwalla-kwalla yake Tarawa tsabar yanda naji riko"Haba yayana pls mana dan Allah ka barni Allah sha'awar naman sunan nakeyi kasan yafi dadi kumama ai gidan babu nisa yanzu zanje in dawo kaji?

Fuskata ya tallabo kamin yace"Naji Amma ki tafi da wayarki dan innaji shiru in biyo hanya.

Sumbatar kuncinshi nai kamin infice gidan ina dariyar naimishi wayau.



Rungumeni mamansu zainab tai cike da farinciki"Ga amarya ga amarya Sannu da zuwa Ah lallai alhamdulillah haka mukeso ai auren ya AmshekiSannunku da hanya ina shi me gidan yake?

Fuskata cike da farinciki nace yana gida tare da Abba Amma anjima da dare zamuzo mu gaidaki.




"""

"Ina jinka Ahmad kace saikazo zamuyi magana meya faru? Ina fatan bawani laifi take makaba ko?


" A a Abba Lafiya lau nake zaune da ita dama dai akan abinda ke faruwane.


"To to ina jinka ansami wani ci gaba ne?


Labarin abubuwan da suka faru yabashi kaf kamin ya Dora da fad'in " Abba gadai wa innan da suka faru Amma har yanzu inaji ajikina akwai Saura,Dan alamu sun nuna cewa sam ba mutun d'aya ko biyune ke bina da wannan sharrinba,Kaga Daniel, Abubakar so daya yaimin sai wannan,To kaga in hakane ai akwai Saura.



Nisawa yai kamin yace"Eh abinda kace gaskiya,Amma karka damu insha Allah komai zai warware tunda dacan ai duk ba asan hakanba sai yanzu,Danhaka adduar dai zamu dage da ita insha Allah komai zai warware,Amma a bangarenta babu matsala zaman naku ko?


Kuma sadda kanshi k'asa yai kunya na kamashi"A a Abba babu matsala Yanxu haka jira nakeyi lokaci ya yi in sama mata gurbin karatu a can 'yar aduwa tunda naga tanason karatun sosai.



"To Alhamdulillah hakan yayi Allah yayi albarka,Yanzu katashi muje wajan baba malam muji ko akwai shawarar da zai baka.



***

" Oh aysha Kinga irin kyan da kika k'ara kuwa?
Allah yasani kin had'u wallahi dama ni.

"Kai saji kina zaune da mijinki Lafiya Amma kina hango wani gashi hadda Albarka kinfara samu.

"Hakane kam Amma canzawar da kikeyi tai yawa wallahi,Kilama cikine dake.

Wata uwar harara na wurga mata kamin ince" Keni dallah bani naman sunan mu wuce dannace bazan jimaba Sannan inajin marata na murzamin wlh.




Kaf gidajen dake layinmu saida nashiga na gaidasu,Daga baya na nemi yafiyarshi dannasan bazai bari inshiga indai na tambaya.




Dare.

"Tashi kije mijinki na kira"

Mama dan Allah ki kyaleni in kwana bayanki dan Allah wallahi babu abinda zanyi mishi.

Makemin baki tai kamin tace"Aysha badai haka kike gudunshiba ko? Maza tashi ki wuce ga farfesun kifi can ki wuce mishi dashi,Wallahi ki kiyayi kanki da gudun miji kinji ko?


Kwallah na share kamin ince"wallahi marata ke ciwo mama,Kuma idan naje zai iya cewa zaimin wani abu.

Kauda kanta gefe tai kamin tace"Aysha ina tunanin kinfara hankali Ashe har yanzu shegen taurin kanki na nan ko?


Hijab dina naja nai gaba ina turo baki dannasan duk abinda zance bawai yarda zatayiba.

Jawoni tai ta fesamin turare Sannan ta turani tana hararata.



Tsaye na taddashi bakin kofa da alama leke yakeyi ma.

Jana yai jikinshi tare da rungumeni yana shak'ar k'amshin jikina,Yayinda bakina ke d'ane sabida haushi,Tunani nakeyi idan fa na kyaleshi zai iya yimin wani abu fa cikin gidanmu.




Wannan labari na kudine.

300 shine kudin biya.



Atuntubi wannan layin domin samunshi kai tsaye.


08142643253.




Haske writer's association.
12/10/20, 2:34 PM - Naffy Aliyu Umar: 46




Amsar kayan dake hannuna yai yana kallona,Saida muka zauna saman katifar dake d'akin Sannan ya d'allemin baki" Baby kincika tsiwa wallahi yanzu menene abin bata rai a nan?

Bakina nake shafawa idanuna na cikowa da kwalla"Ni babu ruwana dakai wallahi ni wajan mama zan kwana.

Murmushi yai tare da sumbatar kuncina"Bazan iyaba baby Inda zan iya to da tun da na kawoki zan koma gida,Amma bazan iyaba shiyasa na jira gobe saimu wuce gida ko?

Da sauri na kwace jikina ina fiddo manyan idanuna waje"Kace me? Gobe fa?
Kasan Allah babu Inda zanbika gobe inma zakai tafiyarka to kayi,Danni sainagama bin gidajen 'yan uwana kaf Kai nifa bama zan koma wannan gidan naku da kullun ake kawomin hari ba.


Shigar dani yai jikinshi yana danne bakina da halshenya wanda ya tilastamin yin shiru.

Da gaske yakeson kusantata cikin gidanmu wai meyasa wani lokacin namiji beda kunya ne? Musamman akan abinda yakeso.

"Tsaya Dr. Me zakaimin dan Allah?

Idanunshi duk sun birkice,Yace " haba babyna hakkina zakiban mana.

"Dan Allah kai hakuri wallahi banda lafiya marata kemin ciwo kaji.

Kwantar dani yai yana shafar lafaffen cikina" Wai kina nufin duk irin aikin da nayi ban aje komaiba baby?

Harararshi nai ina turo bakina gaba dan tuni na hararo Inda ya dosa kai namiji akwai kunya,Dan ba'ace bata ba.

Da gaske abinda yai niyya yakeson aiwatarwa.
Mutsu-mutsun kwace kai nafara Amma yasamin k'arfi dole nai lif cikin jikinshi inajin yanda yake cud'ani.

Sam na manta da abinda nasha yinin yau Saida naji yafara sakin wani sautuka danakasa gane kona menene gani ni kaina inajin wani irin abu da ban isa in misaltashiba lokacin.
Da sauri nasaki damtsen hannunshi Dana rike na rufemishi baki Dan kiran sunana yake akai akai batare da koshi Yasan yana hakanba.


Cikin zuciyarshi yake godemin akan temakon da naimishi na rufemishi baki,Dan Yasan bazai iya rufe bakinshi ba lokacin.



***

"To kinji dai yanda duk ya gayamin,Wallahi shiyasa bake tausayawa yaran,Shiyasa dama baba malam yace akwai abubuwa da yawa akan yaron Amma insha Allah komai zai wuce ta dalilin auran ayshan shiyasa kikaga lokacin na rufe ido nace nabashi ita.


" innalillahi wa ilaihirraji'un, Kace Ashe da saidai muji bak'in labari? To Allah ta ya k'ara tsaremana ita, Ni kaina hankalina har yanzu be kwantaba Sabida zullumi da tunani ,Ammadai munata Addua Allah shine Yasan komai takuma tsara komai saidai mu nemi Sauki daga gareshi,Amma naga suna kulawa sosai da ita musamman mijin nata,Shiyasa yanzuma na koramishi ita,Nasan sabida beson barinta shiyasa ya amince ya kwana nan shima,Ammadai naso ya barmin ita tad'anyi kwana biyu.

"Uhum kinjiki da wata magana tunda kikaga haka ai kulafucinta yakeyi danhaka ki bari yatai da abarshi inkuma ya barta dan kanshi to shikenan Ammadai duk yanda yayi to hakan za ayi banso muyi magana yaga kamar munaso ta zauna nan din,Amma koni inaso in ganta.

" Numfashi ta sauke kamin tace amma kana ganin bawata matsalar ko?

Gaskiya inma akwai to bansantaba Amma dai zamuyi addua.

Da wannan hirar sukai shiru kamin su tashi dan nemama yaran nasu sauki da sassauci daga zazzafar k'addarar dake kansu.




***

Saida yaimin biji biji Sannan ya sararamin,Ina rungume jikinshi yana jijjigani gamida sumbatar duk Inda yaso, Jiyake kamar ya hadiyeni ko zai sami nutsuwa gaba daya,Gaba d'aya beji ya k'oshi ba shiyasa yaketa Kuma likewa yana shigemin jiki,Nikuma gajiyar da nayi yasa nai luf jikinshi.

"Meyasa kika rufemin baki baby?

Wata uwar harara na wurgamishi duk da cewa akwai duhu Cikin d'akin,Amma shi kanshi Yasan cewa idanuna na nan kamar zasu fado lokacin.

Dariya yasaki kamin ya sumbaci goshina" Ke ta dabance Baby kin daina jin ciwon marar ko?

Ni saima lokacin na tuna da wani ciwon Mara da nakeji da,Tuni Yakama gabanshi shima.

Da kyar yasamu nai wanka dan wani irin barci daya sakkomin lokaci guda.

Yana like dani haka muka kwanta,Ban tunanin yayi wani barcin kirki ranar dan duk motsawar da zanyi sainaji ya sumbaci wani wajen cikin jikina.


Nikuma sai barcin nawa ya zama raba da rabi sabida tsoron danaji nai mafarki Mara dadi,Shiyasa naita mutsu-mutsu shikuma sai yai tunanin ko murzar da yaiminne yasa nakasa barci me dadi.


Da asuba ma yana dawowa ya d'ora daga Inda ya tsaya,Yanzu ko na kukan sangarta naimishiba kukane na tsantsar wahala da Neman temako.

Babu kalar surutun da beyiminba,Alokacin Kuma ina jinshi,Danni banji masifaffen dadin da zan rasa Inda kaina yakeba.


Yana kwance yana barcinshi hankalinshi kwance na wuce na gyara jikina cinyoyina sai ciwo sukeyi kamar wacce ta kwana ta yini tana tafiya.

Saida na kintsa Sannan na kalleshi har lokacin barci yake yawani shigar da filo kirjinshi kila tunaninshi nice ko? Harararshi nai kamin ince"Jibeshi dan Allah saikace gidansu.

Wucewa nai zuwa falon mama itama fishi nake da ita tunda Ai itace ta matsamin Sainaje.

Yanayina kawai ta kalla ta d'auke kai tana mamakin mazan wannan zamanin masu idanu agaban goshi.

Cigaba da aikin hada abincin tayi yayinda take nazari na daga Inda take.

"Zonan ki kwashe kayan nan aysha!!!

Jikina Sam babu kuzarin kirki dan jinake ko nauyi na rage,Ahaka na kwashi kayan abincin datagama shiryawa zuwa Inda mukecin abinci wata babbar kafet ce wajan duk nan mukecin abinci dama.


Jana tai cikin d'akin ta tana murmushi" Zonan ishalle meya faru kiketa turo baki kalli yanda fuskarki tatashi badai kukan ragunta kikemishiba ko?


Kukan gaske na saka da kwalla share-share"Mama wallahi mugunta yakemin shi.


"Ke dallah rufe ma mutane baki wawuya kawai!!Kowa ba daurewa yakeyi harya saba ba? Ashe sakarci kike mishi ko?

Hadiye kukana nai ina turo bakina gaba.

" Banda abinki ai hakan shine so ki ganshi fa namiji cikakke wanda kowa keson Samun irinshi shine ke zaki tsaya shirme ko?

"Kai mama mayen?

Baki bude take wangen k'ofar shigowa ganin babu kowa yasata makemin baki,Ke ubanwa yacemiki maye ne? Wato ana rabaki da kiwon akuya kina kyalla ta haihu ko?


Marairaicewa nai ina kauda fuskata dan kadda ta yarfamin mari nasan kad'an daga aikinta.


Riko hannuwana tai" Kinga aysha dan Allah ki daina fad'in hakan kamin yaji bazaiji dadiba wallahi,Yanzu tunda kin fahimci yanada yawan buk'atar mace kusa dashi ai saiki d'auki matakin gyaran jikinki dan ku zauna lafiya ko? Bawai ki zauna kita koke kokeba wanda bazai hanashi abinda yai niyyaba saima raini da kukan zai jawo miki kinji ko? Bance kisha wani magani da sunan na mataba fruit kawai ya isheki saiki dinga yin kunun aya da zallar kwakwa da madara insha Allah sun wadaci jikinki yauma zanyi miki kisha kinji.

Tuno irin yamutsar danasha yasani Saurin girgiza mata kaina"A a mama kadda kiyi dan Allah idan nakoma can zan dingayi.

Dariya tasaki kamin tace"Raguwar banza to sainayi kuma shi nakeso ki maida ruwan shanki,Dannaga da alama so kike ki rako mata.

Sosai ta dinga K'okarin ganin ta fahimtar dani wasu abubuwan kamin tace inje in tasosshi ya karya inkuma kawomishi za ai can to.



"""

Jawoni yai jikinshi tare da sumbatar kuncina"Barka da safiya babyn yayanta,Kintashi Lafiya ko?

Cizon yatsanshi nai daya sakamin cikin bakina Sannan nace"Ni babu abinda zaka gayamin tunda haka kake kumama ko kunya bakaji gidanmu fa?


"Yo kunyar me zanji ai nima nan gidanmu ne,Ammadai banyi surutuba ko?

Dariya nasaki kamin ince aiko sosai har sunan maman kaita kira kuma naji kamar ta amsa maka ma.

Duk Yasan be d'aga sautinshiba Amma tunda ya ganni cikin nishadi alamun na huce sai kawai ya zaro idanunshi waje" Da gaske kike babyna? Kice yau bazan iya had'a ido dasuba kenan?


Dariya naita mishi,Shikuma yana biyemin dan abincin ma cewa yai inkawomishi nashi nan bazai fitaba,Ammadai bari yafito ya gaishesu tukunna.





***

Katsina.

Rasa Inda zata sakata tai sabida murna da farincikin ganinta,Maman nata haba haba da ita itakuma tanata binta da kallo.

"Sannun ku da hanya inna wallahi jiya nake cema suwaiba yakamata atura agayamiki rasuwar nan tunda ba asami wayarkiba gashi har anyi addua.

Macece me faran faran da sakin fuska bazaka taba cewa wai tasan wani abu mugun abuba gata tsaf bazata ma taba cewa kauye take zauneba" Wallahi nima basiru ke cemin dayazo katsinan yaga iyali makocin su ita suwaiba din kuma ya gayamusu rasuwa to nidai saima narasa gane waye ya rasu dan bemin cikakken bayaniba Ashe Ashe kausar ce kwana ya k'are?


"Wallahi kuwa inna,Mutuwa farat d'aya kamar almara.


Saida taci ta koshi,Sannan ta nad'e k'afa" Wai nikuwa ina matar Ahmad ne ban ganshiba itama banga giccintaba ba naji ance tare kuke zaune ba?


Dariya maman tasaki kamin tace"Aiko kunsami sabani wallahi dankuwa jiya ya kaita ganin gida shine saiya tsaya ya kwana Amma anjima zai dawo sabida d'azu da mukai waya yacemin zai dawo da ita nace a a yabarta can ta kwana biyu taga 'yan uwanta.

"Kashhh dabakice ya bartaba.Cewar tsohuwar tana yamutsa fuska.

Kallon mamaki maman ke binta dashi shine Saita wayance tace" Uhumm naso mu had'u mu gaisa dan ban santaba sabida bawani shagalin biki akai ba balle muzo,Kuma gashi shima zaki hanashi sakewa da matarshi Alhalin yanzu suke kan ganiyar amarcinsu ko.


D'an kauda kai maman tai tana murmushi,Lokuta da dama tana mamakin irin son da k'awar mahaifiyarsu keyima Ahmad din"Bari inkira usman saiya kaiki gidan suwaibar in kirata in gayamata isowarki.




"Hello suwaiba ga inna Ganbo nan zuwa gidanki yanzu ta iso.

" Ah a Gaskiya kadda tazomin gida wallahi matar da aketa rade-radin cewa mayya ce shine zakice zatazomin gida wato ta kashemin wani cikin yara kenan Alhalin ko gama kukan Wani banyiba ko?


"Ke Bansan hauka dallah dan mutane suna zarginta shine kema zaki amince da hakan? Uwar mu ce yanzu bamu da kamarta sabida duk iyayenmu sun rasu saura ita kadai tokuma saiki amince da sharrin mutane? To gatanan zuwa idan tazo saiki korota.

Inna Ganbo k'anwar mahaifiyarsu ce ita kad'ai taimusu saura afannin iyaye,Sannan ita Allah be bata haihuwaba sai yaran dangi da take rikewa Saidai shekaru takwas da suka wuce aka dinga cewa wai maita takeyi,Wanda lokacin 'ya'yan 'yan uwanta suka jajirce saida maganar ta mutu tunda babu wata shaida taka mai mai dama watace tahau iska tace itace ke musu barna cikin garin batare da mutane sun farga da abinda takeba.
Saidai abinda basu saniba shine tabbas itadin mayya ce kuma haka kawai tasami kanta cikin maita,Ta dalilin wata k'awarta wanda da farko bataso hakanba Amma kamin wani lokaci tazama gawurtatta.

Cikin aminci take barnarta sabida ita din afuska bazaka taba cewa wai tasan wani abu me suna zalinciba.

Da yawa daga danginsu sun yarda da maganar haka kuma wasu daga ciki suna ganin sharrine kawai ake mata kamar mama itama har yanzu tana ganin kawai sharrin mutane ne Sabida kawai anga bata da yara.



***

"Wai Kai bazaka tashi ka wuce gida bane rana tayi fa?

" Haba babyna tare zamu wuce fa!!!


Tab bakaji da kyau wallahi,To idan nabika yau muka koma ince nazo gida?
Banfaga yayuna ko d'ayaba ko gidan baba malam banjeba kai babuma Inda naje kaidai kawai kai tafiyarka idan nagama ziyara indawo kokuma in kiraka kazo mu koma ko?

Hararata yai kamin yace"Lallai kimma rainani wallahi,


Gaskiya ta na tsaya na gayamishi dan wallahi bazan tafi yauba.

Da ya lura lallai da gaske nake saiyace to inyi kwana uku zai dawo ko da yammane ran kwana ukun saimu koma.

Saida yagama nukurkusheni Sannan ya wuce bayan yaima su mama Sallama.



Yana barin gidan nafara shiri dan nida zainab zamu wuce Saikuma abinda Allah yai dan gaskiya zansha yawo,Bawani jimawa naiba Amma jina nake kamar Nai shekara,Batare Dana waiwayi gidan ba.



***

Tunda yai nufin komawa gidan yaji wani irin kunci da damuwa dake tasomishi Amma sai yabar hakan amatsayin kewata da zaiyi.

Saidai ga mamakinshi shine yana kuma kusantar gidan yanajin wani tashin hanakalin wanda har saida bugun zuciyarshi ya sauya nan take.




Wannan labari na kudine.

Domin samunshi zaki biya 300 ta wannan tsarin.

Acct no.
0005074141,Aisha sabiu,Ja'iz bank.


Kokuma kati ta wannan layin.
08142643253.




Haske writer's association.
12/10/20, 2:35 PM - Naffy Aliyu Umar: 47




Rashin nutsuwar da yasamu kanshi ciki yasashi d'aukar hanyar gidan Salim hankalinshi yafi kwanciya da yai tafiyarshi can kawai.

To bazai samu wata matsala tunda bangaren salim din da ban yake da Inda iyalinshi yake din,Kuma yanada key Ahannunshi.


Ko salim din besan ya dawo garin ba,Dan kwanciyarshi Yai kuma yai sa'a barci yai awon gaba dashi,Duk da cewa tuni kewar matarshi tafara nukurkusarshi.




"""**"""

Babu wani sakin fuska da tasamu shiyasama takasa zama gidan gaisuwar tace zata koma.

Abun yabata mamaki dan ko tayin ruwa bata samu daga suwaibar ba saima bak'ar magana da yaranta ke jefomata a fakaice.



Cikin Sanyin jiki ta dawo gidan maman.

"Ah inna harkin dawo?


" To ba dole in dawoba,Suwaiba sai Neman zagina takeyi da yaranta,Ni Bansan abinda naima mutaneba suke jifana da wannan mugun abu haba,Tuni tafara sharar kwalla.

"Subhanillahi haba inna menene abin kuka dan Allah kiyi hakuri zanyimata magana yanzu, Ki daina kuka.

Cikin bacin rai ta kira Wayar k'anwar tata Saidai ga mamakinta Saita ga taki d'aga wayar wanda dama tasan za ai hakan.

Hakuri yacigaba da bawa innar kamin tace ta huta kamin Ahmad ya dawo ya mayar da ita gida tunda tace ba kwana zataiba dama gaisuwar tazo tayi.



Kallo d'aya yaimata yaji beso suka had'a idoba,D'an rusunawa yai ya gaisheta kamar yadda yasaba tunda tana matsayin k'anwar surukarshi ne.

Wucewa yai d'akinshi yayinda tabishi da kallon taga nama.


Bin bayanshi maman tayi danyimishi sannu da zuwa" Alhaji inkawo maka abinci ne?

"Cikin rashin walwala yace " A a barshi saida yamma Yanzu nasha fura wajan alhaji isa daga can nake,Ashe inna tazo?


"Eh tazo wajan gaisuwa ne yanzu ma ta dawo so nake idan babana yadawo ya mik'ata gida tunda tace yau zata koma.


Kai kawai ya d'aga mata tare da kwanciya.




"""
Sai wajan uku na yamma ya baro gidan salim din yayo gida.


Wani irin mummunan faduwar gabace ta sameshi lokacin da suka had'a ido da ita,Yarasa abinda yasa Amma duk idan zai ganta to lallai saiyaji wannan faduwar gaban yarasa meyasa.

K'arasowa yai cikin falon yana dariyar yake,"ah tsohuwa saukar yaushe haka?


Harararshi tai kamin tace"Eh kacemin haka mana,Sabida Allah Amadu yaushe rabon da in ganka? Sannan ko kishiyar baka kaiminba balle in ganta inga dame ta fini ko?

Dariya yasaki yana zama saman kujera"ah lallai ma ai amarya tafiki komai kam,Gashi ansami sabani jiya na kaita gida wallahi taje ta gaishesu.


"Haka mamanku ke gayamin ai babu komai dama zuwa nai inyi gaisuwa kuma inga kishiyata,Yayinda cikin zuciyarta take tsinema ayshan wadda tacika taurin kan tsiya acewarta.

Sama sama sukai hira ana kiran la'asar yabar gidan batare da ya amsa maganar maman ba da takecemishi yazo ya kaita gida,Shiyasa ya ajiye mata kudi yabar gidan.




***

Yawo nasha nida zainab,Dan duk fadan mama rufe kunnena nai,Sosai k'afafuna kemin kaikayi,.

Gidan ya maryam mukai magriba kuma mukai zamanmu balle da ya dalha yace Idan mun kammala zai kawomu gida.

" yauwa aysha d'azu muna magana kikai shiru kimin bayani mana idan akwai hanyar temakawa saimu had'u a rufama juna asiri kindaisan baki da kamar mu ko? Cewar ya maryam tana murzar hannuna.


"Cikin shagwaba nace da gaske nake yaya babu wata matsala Ammadai yanada fada sosai ga zuciya,Ammafa yana so na sosai Wallahi.

" Alhamdulillah ai haka akeso wa innan duk dama sai kinyi hakuri sabida babu namijin da bedasu Saidai wani yafi wani kedai shawarar da zanbaki anan shine lallai lallai ki tsaya Ki fahimceshi insha Allah hakan zaisa ku zauna lafiya kinji ko?


Kaina na d'aga mata ina yima abulkhairi wasa.

"Me kikesha na gyaran jikinki?

D'an kallonta nai kamin in turo bakina gaba" Ni wallahi banshan komai abinda babu komai ciki Sai wahala,Shikuma bejin tausayina.

Idanuna kamar zasu fado sabida harara yayinda nikuma na kauda kaina dama zainab na falonta da yara suna kallo.

"Sai in makeki wallahi,Sakarya kawai,Ko kayan lambu bakisha kenan?


Matsawa nai daga kusa da ita,Sannan nace inasha kullun mamansu ke murzamun inasha.

" To shikenan zamuga abinda za ai kamin ki koma tashi kiyi Sallar isha'i Yanzu zai dawo saiya maidaku gida kadda Abba yai fada.

Muna cikin mota
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment