Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Compiled By Umar Dalha Funtua.



_*♡AHUMAGGAH🌺*_



_A nigerian historical fiction_
*WATTPAD SURAYYAHMS*_
_Brilliant writers association_


_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_


_In honour of my 2nd version,am not dead if ure in this world,my blood, my flesh. *ZAYNAB TEMI TOPE ADENIYI ABUBAKAR LAWAL.*._

_Bismillahirrahmanirrahim._



_1⃣-The horn of Africa♡_



Misalin karfe 6 na safe ne,Juyi nake ina kikkiftawa salon kwace baccin gajiyar da har yanzu yake bibiyan idanu na.

"Yau ma Daga inda nafi kwanciya a chan dungun daki na tattaro karfi na duka nayi mika don na watseke,da kyar na waro idanuna dan kuwa Bibbiyu nake gani har wani jiri ke deba na,hakan kuwa bai hana ni daddagewa na zauna tsam ina muzurai ba sai dai duk da haka idanuna sunyi dishi dishi kamar wata mai kallon gajimare.
sanda na dauki mintuna uku da hannun dama na ina yarfe su kafin suka dawo min normal sai dai har yanzu Basu nuna min abbu na ba.

'Wani irin faduwar gaba ne ya taso min"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun! Na furta acikin zuciya na.Wani mugun fargaba ne naji ya rufe ni atake,a hujajan na mike tsaye ina dube dube dan bansan sanda sanyin sautin murya na ya fidda sautin sunan sa ba'..cike da damuwa na fito ina cewa
ABBUH...!

...jiya cikin dare Abbu ne akwance kusa dani kamar gawar da yaki kabarin sa.

Dan Daga ni har shi bansan ya akayi safiyan yau ta riske mu ba.

duba shi na shigayi sai dai ina dora kafata bakin dakin daya raba jingar karar dake tsakar gida sai na hango rayawar karan masara har an sakaye kofar bayi dashi alama nacewa da mutum aciki yana zagaye.

'Bayin nadan bi da ido na dan wani lokaci domin na tabbatar ko shine aciki,bayan kamar minti biyu nayi ajiyan zuciyan tare da sauke boyayyen nishi nan na juya na koma cikin dakin dana fito.

"...Yagaggen Tabarman kajinjinin dabinon da muke kwana akai na dora hannu na akai na jawo shi batare da na nade ba na karkade duk kasan dake kai na fito dashi waje.

A jikin dangar kara daya suturce mana asirin jimammiyar muhallin mu na tsaya,sanda na zare kararen da suka rage mana na hura wuta sannan na yarfa tabarman akai na juyo tsakar gida.

Daga nan A Gaban wata dakilalliyar ramin murhu nayi tsugune,Hura wuta na shiga yi da gaske domin sanyin safiyar mu ta sha banban dana kowa a yankin mu.

"Sunana Bahiyyah Ahmadu Alba.
ni Bansan daga ina muka fito ba bare nace na san asalin mu amma yanzu haka a wata katafaren yankin jeji mai tsananin sanyi da duhun itacuwa muke zaune nida iyaye na da jinsin zuriar wasu fulani wanda su ba bakake ba kuma su ba farare ba.

Nan din Yanki ne
Daya tsaga tsinin kahon nahiyar africa,Kenan mu ba acikin wata kasa muke ba.

A cikin kasashen afurka da suke zageye damu kuwa sun hada da ethiopia,somalia,djoubuti da cibiyar bahohin ruwa guda biyu wato quardafui da somalian sea,sai kasar kenya dake gudu maso gabas.


Shiyasa ma idan anka duba yankin mu da kyau sai inaga kamar muna cikin wani tsauni ne a chan Cikin dajin daya ya raba gulf of eden da kuma bahar maliyar(red sea).

Tsawon shekaru na a duniya na dauka acikin wannan yanki aka haife ni,Sai dai nasha mamaki sosai a lokacin da ammu wato mahaifiya ta tazo gaban ta na mutuwa.

Anan ta take sanar da ni cewa ita cikakkiyar yar kasar somalia ce.

A somalia jinsin yare biyu ne,ko ka kasance arab ko dan somali.

Toh Ammu na balarabiya ce tar dan cemin tayi bata ma jin yaren su na somali a duk dama larabci da somalin suka dai ne yaren da ake yi a kasar..

Tace min Abbuh wato mahaifina kuma dan yankin ethopia ne gaba da baya,A wajen cin kasuwanci a boader chan mahadan su dake wajen kasar djibouti ta hadu dashi.

soyayya mai tsananin karfi yayi sanadiyar auren su.

Daga nan A takaice Iyaye na sukayi zaman aure a kasar ethiopia wato garin mahaifina sai dai Rayuwa na shudewa dangi suna ta mutuwa,kafin a hankara rayuwar iyaye na ta koma garin mogadishu wato state capital na kasar somalia nan inda aka haifeni.

Anan ma Ko shekara guda banyi ba Koluluwar Yunwa
Da jarabar tsiyan talauci irin na kasar somalia ya sa akayi wata karamar yakin daya rabamu da kowa da komai namu a duniya.

Dan haka muka yi hijira muka bar somalia,dan tun ina Jaririya hijirar ya kawo mu wannan dajin inda muka hadu da jinsin zuriar fataken fulani mu kayi zaunen mu a cikin su muna rayuwa.

Gashi har Yau shekara ta goma sha hudu bamu bar nan ba.

A shekaran daya gabata ciwon daji yayi sanadiyar mutuwar Ammuh kuma tun mutuwar ammun Abbu ya kamo da mummun ciwon zuciya wanda nikaina na rasa gane wata irin tsaninin so da shakuwa ne ke tsakanin su,my dad cannot live without my mum

shakuwar su tasha banban da irin shakuwar masoyan zamanin yanzu.

A da chan,Allah ya bama abbu na baiwar magance cututtuka da sanin warakan ciwo ko da sanadiyar mutum ne koko na aljani.

Abbu na yana da baiwar shiga jeji yayi farauta kuma ya tsinko ganyayyaki,itacuwa da saiwa kala kala,yana kuma iya sarrafa su ta yadda yake so domin a samu sauki,da waraka akan kusan ko wani irin cuta.

Tsawon shekaru yana taimakawa amma yau Sai gashi har Abbu na yakasa gano itace ko wani ganyen da zai masa maganin Ciwon son ammu na dake damun zuciyar sa.

Mutuwar Ammuh kamar faduwar wata danga ce agare mu gashi abbu yasa abun aransa sosai fiye ma dani.

"Sai Gaba daya ya dena fita ko ina,tun lokacin ya tsayar da duk wani harkan sa ta siyar da magani gashi har ciwon zuciyar yayi tsanani ya kama shi ta inda bazai ma ji maganin gargajiya akan lokaci ba.

A Yanzu Buri na na sami taikamakon da zai wadatar dani har na kaishi ganin likitar bature a chan yankin kasar egypts inda nake karatu

dan naga suma suna shigowa kasuwanci a yankin mu kuma bamu da wani nisa sosai.

Ko da nayi yunkuri sai naga Jikin abbu yaki sam,A kullum tsoro na kar abbu shima ya mutu ya barni dan bansan ina zanje ba.

..........

A haka Ina zaune gaban murhun,idanuna
sun yi lufu lufu da hayakin danyen karar dake ci Da kyar wutar murhun ta kama tana ci bal bal tashi nayi na jawo kwaryan dake gefe na,don kafin nan na dan tsaftace wajen danake zaune,sai kawai na dora sauran gasashen namar rago da muka ci jiya domin shima ya turara musamu na sawa a bakin salati.

Asali dai Bamu cika cin abincin da ya shafi ganye ko itacuwa ba,,dani da iyaye na gaba daya We are not much of vegetarians.

Dana zo daga baya ma na san asalin tarihin ammu sai na dena bata lokaci na wajen nazarin yanayin cin abincin mu.

Ammuh tace min a chan somalia haka nan suka saba iyaye da kakanni,suna nomar turmeric wato(kurkurm) curry da kuma corriander,abincin su kuma daga namar rago,
namar shanu kaza da tinkiya,
Sai basmati rice.

Hakan ya dada bayyana min tasirin halin talaucin da kasar somaliar take ciki,amma tunda muka dawo nan alhamdullhi zamu ce,duk dama munsaban amma Abbu wata rana yakan sa muci zallan yayan itacuwa ko ganyen alaihu,tufa,cerely,gurji,karas,ibini da dabino da kuma ganyen lettuce.

Mukuma mukan bashi hadin kai ne A matsayin sa na masanin kariyar cuta sai muke biye mashi mafi akasarin lokuta muke sauya abinci.

"Ina zaune gaban murhun,Daga baya na na Ji karar sautin takun sa,mikewa nayi na juyo ta inda zan ganshi da kyau as usuall tsaye yake cikin dakakkiyar rigar jumfa wacce take suluk babu shape,rigar ya dan tsuufa amma fari ne tass wandon kuma kalar kasa ne,he is looking neat babu lifo,don a duk dama ni karama ce bai hanani tsaftace abbu na ba.

Tsaye yayi hannun sa rike da buta ya tsura min hasken fararen idanun shi yana kakalo murmushi kamar bashi bane mai sani kukan tausayin kaina ko wani dare.

Domin son yaga nayi murmushi sai ya yabani da kalman larabci yana mai cewa Saiiqah...yah noori...!

Nikuwa Yadda ya furta kalaman nan naga kuma yana kallo na yana murmushi sai ya sani naji wani tsananin kaunar sa da tausayin sa ya tsuma ni...a take na mike tsaye ina kallon shi

Hannun shi naga ya ware duka biyu ya buda min,ni kaina Bansan sanda na taho kusa da shi na rungume sa ba..gam ya dada matso ni tamlar wanda zai maidani cikin sa"wani sanyin hawaye mai shiga rai shi ya kufce min ayayin dana kankame sa nima jiki na dik yayi weak a haka na furta ABBUH ban karasa ba....sai naji ya shafa kai na,A hankali na kuma furta ABBUH NA, HAMMAM dina,

Wano Dada kankame ni yayi jikin sa sai rawa yake alaman shi kadai yasan meya keji ajikin nasa,a haka ya dago fuska ta zuwa nashi yana min murmushi mai taba zuciya da sa sanyin rai...

Yace yata shin waya koya miki kalmar "hammam" bacin nasan ke baki iya larabci ba?..hakika kalman tayi min dadi...bayan matata zaynah,a duniya ke kadaice zaki iya gayamin wannan kalma mai dadi kuma naji dadin shi.

Share guntun hawaye na nayi ina murmushi sai Na sunkuyar da kaina na seconds biyu..

Cikin farin cikin da bansan na meye bane na furta.
"Abbu,ranar a kasuwar kofar gidan modibbo naji wani balabaren egypts yana fada ma sarki 'hammam" shikuma sarki yaji dadi sosai har ya masa kyautar azurfa.

Shine Sai na tambaye shi ma'anan kalman shine yake cemin kalma ce ta girma kuma ba'a cewa kowa hammam sai mutumin da ya cika abun Alfahari,abun koyi,abun kauna kuma abun tinkaho..

Hannun shi na kama fiska ta na sake wasu irin disasshun murmushi:

nace Abbbu..kai ne abun alfahari na Allah ya baka lpya abbu na.

Dan Shiru abbu yayi,Sai Na lura tsaban farincikin abun da nace yanzun yasa abbu na baice komai ba.

Nidai karamar ajiyan zuciya nayi

Hannun shi dake famar sacewa da tsaninin sanyin dake busowa na riko cikin idonshi na furta
...wai shin yaushe zaka warke muje jeji ne,..?abbu na
Ina so na raka ka deban magani kaga kwana biyu kudin mu duk sun kare..ko ka mance lokacin da kake dauko ni akafada muna tsintar ganyen mu?ko dan ammu ta barmu shikenan kai zaka dena rayuwan ka dani?.

Kokarin Sake kiran sunan shin zanyi amma ban ko karasa kalmar ba ya rufe min baki na da yatsun sa..cike da sanyin jiki ya jawo ni jikin shi Tsam sai naji ya sake rungume ni..

Wani Ajiyan zuciya na sauke Nima sai na lafe ina mai sauke ajiyayyan numfashi.

Wani shiru ne ya ratsa tsakanin mu Tsawon lokaci sannan abbu ya dago ni yana mai kallon fuskata,nima kallon sa na tsaya yi dan daga ka ganshi kasan maganar dana furta ne yayi tasiri a zuciyar sa sosai.

But Maybe am too young to understand what love is shiyasa bazan fahimce rashin dauriyar sa akan soyayyar sa da ammuh ba.

Anma kuma Ba sai an fada min ba nasan abbu yana nadaman sakani cikin halin da nake ciki yanzu sosai.

Sai da ya kure ni da ido Kafin ya numfasa da dai Kamar wani magana zai min
sai naga ya sake min hannu na da sauri ya juya dubar sa kan abunda na daura akan murhu..

Ashe namar dana daura a wutar ne ke famar babbakewa nikuwa tsaban shaukin kasancewa tare da abbu na yasa ban ma ji ba,da azaman sa ya sauke namar yana yarfa hannu...

Da sauri na matso,ina cewa mugani...tafin hannun shin na riko inda ya kone ina furawa da iskan baki na inai masa sannu cike da so da kulawa..

Ina Cikin haka Kwasam sai naga dison Hawayen shi ya digo akan hannu na daya ke cikin nashi,sai dai bai ma bari na daga ido na kalle shi ba ya goge idanun shi da sauri ya kuma zaunar da ni kan dutsin dake wajen baice uffan ba ya juya abunshi

Nidai Ina ta kallon shi Har ya gama tsatsame naman ya aje agabana,sai ya dauki kwara guda
Yace yi bisimillahi

Inayi kuwa ya kaimin namar bakina.

Mahaifi na kkyawar mutum ne sosai duk dama wahala ya tsufar dashi amma kuma farin fata,bakin gashi da manyan dim eyes dinsa su suke yawan sani Lumshe ido a hankali ina kuma sake budewa
Cikin sauki Yake sakamin ina taunawa a tsanake.

Sai da nakai kusan sau hudu kafin nima na yanka bari guda na kai mashi bakin sa..

Ya na kan ci..sai na kirashi nace "Abbu cikin son na sa shi dariya..sai kuwa ya amsa ni da na'am noor!

Sai nace wai Meyasa ka daina kira na da asalin suna na?ko ya dena maka dadi ne..

Faffadan Murmushi kawai yayi yace,ai ko bayan raina ne, nasan kuwa akwai mutane dayawa a doron kasa da zasu kira ki da asalin sunan ki BAHIYYAH ta.

Amma kinga ni? Dole na girmama ki da sunayi da yawa..

Dariya mai sanyi kawai nayi ganin murmushin karfin halin da yake min yana kuma maganan cikin raha pretending to be ok bayan nasan ba yajin dadin.


Sai ya dafe tsakar kaina with much serious tone kamar wanda zai yimin wata muhimmin addua..Yace bahiyyah kincancaci a kira ki saiiqa..sabida ke alheri ce kuma akan hanyar alheri zaki dawwama har abada.

Kece ..noor wato haske,hasken rayuwar iyayen ta...sai yayi murmushi..

Hawayen dake hargowa a idanu na na tare cikin karfin hali nayi murmushi nace
..abbu dayan fa?

Baice min komai ba Hannun shi ya sauke kawai yana murmushin sa,sai da ya sake yankar namar zai kai min baki kafi yace

Almass?(diamond)kar ki damu dashi.

Nidai Kiyi hakuri bahiyya tah,nasan Abbu sam baya kyautawa yar sa.

"Ina kan tauna na baki na, sai nace hakuri akan me kuma abbuh na?bai amsa ni ba sai yace min nayi miki Alkwari bazan sake sakaki cikin wani hali ba.
Kisani nafi kowa son ki rayu cikin farin ciki ba kunci ba.
Tirrr da mahaifin da zai jefa yarsa cikin kunci..dan juya kansa yayi dan da wani irin remorseful feeling ya karashe kalman.

...atake sai naga yanayin sa ya fara sauyawa.

Hankali na adan tashe nace abbuh?wai akan me kake furta irin wayannan kalaman,nayi maka wani abu ne?

Yace ah,a Bahiyya...ai ko kin min laifi ma na yafe miki har abada,dada riko hanu na yayi yace min
Amma bansan ko ke zaki yafe min ba,bar ganin ina cikin zafin ciwo a jiya ina sane dake araina,kina wahala dani sosai naga har firgita kikeyi cikin dare kina kirayen sunana....ina tausaya miki sosai.

Kuma Tin A lokacin na fara jin dole na na rayu ko dan farin cikin ki bahiyyah kinyafe min...?

"Dan Shiru nayi dan banma san me zance masa ba Cikin farin cikin da bansan dashi ba na gyada kai ina goge idanuna da suka dan sauya kalar su

Yauce rana ta farko danaji abbuh ya furta min hakan kai tsaye..,har abbu ne yau ya iya mance jimamin mutuwar ammuh yake cewa zai rayu dani?wani Murna ne ya mamaye kirji na sosai wanda babu misalin shi.


******

Tun daga wannan rana har cikin makon,a gaba dayan ta a haka rayuwa ta sauya mana, duk dama abbu baya fita ko ina amma bai taba kwanciya ciwo ba tun wannan rana.


Muna cikin wannan yanayi Wata ranar Alhamis na fito nayi wanka na fes,ganin abbu ya warware yana kwance shiru sai na nemi izinin sa na bar shi a gidan shikadai,ni kuma na Fito cikin garin kallon wasa a chan yankin sarkin fulani domin ziyartar babban kawata wanda ake kira da JUNNUT..

Junnut ma marainiya ce,sai dai ta rasa uwa da uba ne baki daya,ayanzu a hannun yar uwan mahaifin ta wato ummah Surbajo take zama.

Mahaifin junnut da sister sa ummah surbajo asalin jinsin zuriar fulanin yankin ne.

Don haka junnut asalin bafulata ne maiji da kyau baiwa da kuma buri mai kyau na rayuwa.

Kawancen mu da ita ya samu nasaba ne tun daga kan iyayen mu,Don kuwa mahaifiya ta itace babban kawar mahaifiyar junnut

Ammuh tace min da ada chan damu ka shigo garin bamu san kowa ba
mahaifiyar junnut su ne jinsin fulanina farko da suka bada iyayen nawa mafaka acikin wannan yanki har aka karbe mu..

Iyayen junnut duka sun rasu tun kafin ammuh na ta bar duniya

Sam rasuwar sun baiyi mana dadi ba,gashi sun tafi sun bar dukiya mai tarin yawa

da shike su masu arzikin dabbobi da kudin hadadan kasuwanci da larabawan egytps da china ne toh bayan mutuwar su sai ya kasance yarsu da suka bari wato junnut bata cikin irin halin maraicin danake ciki.

...gashi a duk tsaunin wajen ummah surbajo ce kawai tayi karatu mai zurfi,tun asali ma ta dalilin ta iyayen mu suka yarda muke zuwa makarantar bature a chan kusa da egypt dama da yankin ethiopia har muka sami ilimin bature nida junnut yanzu munkai matakin ss1..

Wanda a yanzun Mutuwar ammu na da ciwon abbu ya dan dakatar da ni daga halarta kwana biyu banje ba.


Ummah surbajo tana matikar kula da junnut dan haka Ko meye junnut take so ana mata shi.
Rayuwar ta take yi cike da buri da son kawo mana cigaba...

Tun Muna yan Shekaru 4 shakuwar mu ya wuce yadda hankali zai iya dauka,ayanzu duk wani sirrin ta na sani haka itama kuma tasan nawa.

tsaban yadda muke da ita wani bin ko ciwon kai nakeyi zaka ga itama ta fara yinshi kuma bata samun sauki har sai na samu


Gashi kusan siffar fatar jikin mu da tsarin jikin mu daya, duk wani halayen mu na yaranta ma iri daya ne,banbacin mu shine ita tafi ni iya magana da mutane sabida awani wajen ni shiru shiru ne.

GAshi har munkai shekaru sha hudu,Da shike al'adan fulanin su muma muke bi,mutuwar ammu ne ya hana ayi min aure,ita kuma junnut burin ta na rayuwa ya hana ayi mata musamman data samu goyon baya daga antyn ta ummah surbajo.

Junnut tana matukar kaunar rayuwa,mace ce maison taga ta yi ilimin bature mai zurfi tayi kudi tana kwalliya tayi kyau,tana tuka motoci.

Above all babban burin junnut ne ta ga tayi aure nan gaba kuma ta auri Babban soja ko wani iri ne kuwa bata damu ba.

A hanyar mu na kasuwa Yau ma hirar data zo min da shi kenan.

Sai dariya muke fuskokin mu dauke da annuri Hannun mu sarkafe da juna.

Chan sai Tace min baahi?batare da na dago ba
Nace naam

"Daga Gobe Buri na zai iya cikawa amma kwata kwata bana jin farin ciki sabida nasan kwanan nan zamu rabu.

Nace ko?..wanne daga cikin burin naki ne zai raba mu junnut..

Tayi dariya tace min buri na koyan turanci.

Kinsan ko wanda anty surbajo take dan koya mana bazai ishe ni na wanku har na auro soja na ba ko?

Murmushi kawai nayi cikin nuna mata rashin fahimta nace To wanne kenan?ai Nima sai inbiki ko?
Junnut idan kika tafi kika barni bansan ya zanyi ba..


Dan Kallo na junnut tayi,dan Salon danayi maganan ya sata taji wani iri. jawo ni tayi muka koma gefe muka jingina da bayan mu.

Wani Ajiyan zuciya tayi,Tace ashe babu dadi?
...,bahiyyah kinsan me naji kuwa a lokacin da abbu yake ciwo kika daina fitowa muje karatu kwata kwata ma na daina ganin ki?

To Walhy ji nayi kamar nikadai ce a duniyan nan..

Ni Gashi ina nan Bansan wani halin kuke ciki ba gashi umma surbajo ta hanani zuwa yankin ku...wai its too far"cikin rigimammen gurgun turancin ta takarashe maganan Duk dama Damuwa ne sosai akan fuskarta.

Sai nayi Murmushi nace ai babu komai junnut,nasan bazaki barni cikin wani hali ba,ba gashi abbun ma ya warware ba

Dan karamin Nishi junnut ta sauke tace eh,Mungode ma Allah..

Amma kinsan me?nace mata a'ah..

Tace "inada yaqinin cewa bazamu taba rabuwa ba bahiyya, nidake shakuwa ce na har abada na
Amana,soyayya na rai da rai..ina matukar kaunar ki kawata.

Anan muka juyo duka muna fuskan tar juna cikin shauki mai nuna kaunar gaskiya dake tafe da kalaman zuciyar mu

Nidai Bance komai ba don tausayin ta da nake ji,junnut is kind of emotional don ko ni nasan nafita karfin xuciya da jarumta.

Cikin sanyin murya tace bahiyyya
.
Na dube ta nace naam junnut

Tace dama naji umma surbajo ne tana cewa gobe zasu zo su dauke ni..

Hannun ta na sake garan gatsau Cikin tashin hankali Nace su waye kuma junnut?wai Ina za kije ne?
Ita ma shiru tayi ta kure ni da idon don kuwa a
Ba zata naji kirji na ya buga.

Nan ta fara min bayani a tsanake don kuwa yau babu fuskan wasa a tattare da ita.

Tace"Yan uwan mama na ne daga chan wata kasar zasu zo,ummah surbajo tace awajen su zan koma zama na har abada,
bahiyyah ance suna da dukiya da duk wani abunda zaisa buri na na rayuwa ya cika kinga bama sai na tafi da gado na ba,wai dama jira suke na kai sha hudu ko sha biyar sai suzo su tafi dani..

Ruwan daya taru min a idanuna na sake cikin sanyin jiki nace dagaske kike yi junnut? Gyada min kai kawai tayi Wasu zafafan hawayen Junnut ta fashe dashi ta rungumeni, sai gashi jikin ta duk yasaki yana neman fara rawa nima Bansan sanda na kankame ta na fashe da kuka ba.

Rungume da juna Sai da mukayi mai isar mu kafin muka rarrashe juna,nan junnut tayi min alkwari cewa ko ta tafi bazata taba mancewa da rayuwar da muka gina tare ba

Don sanadiyar burirrika irin na junnut nima naji ina son nayi karatun baturen nan ko dan na taimaki abbu na, a duk dama bani da buri masu yawa irin na junnut,Nima Alkawari nayi mata cewa bazan mance ta ba,haka ma nace ni zan zamto mata mafaka na farko wajen ganin ta cimma burin ta duk rintsi duk wuya.

Tsananin amintar dake tsakanin mu yasa nake jin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On AHUMAGGAH
avatar
humaira-2

5 months ago

Reply

Tnx alot

Please Login or Register in order to submit comment