Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

tunani, shidai wani malaminsa ya tab'a Maganin matsala irin Wannan a shekarun baya, nan cikin sauri ya kira malamin nasa wani sheyi haka, ya tsufa sosai, mutuwa yau ko gobe jiranta yake
Haka Baba Alhaji ya kwashe matsalar HEESHAM tsaf ya gaya masa, aiko nan ya gaya masa me zaiyi masa a samu warakar wannan matsala, ya kuma tabbatar mai asiri ne, Sannan NUWAIRAN tadage da Addu'ar.

Aiko nan Baba Alhaji ya tada kan HEESHAM daga kan ciyarsa, ya d'auki allo da tawada ya rubuta wasu addu'o'i ya wanke yaba HEESHAM d'in yace yakaima NUWAIRA tasha rubutun, bayan sallar Isha'i zai mata Addu'a sosai insha Allah sun rabu da wannan matsalar Saidai idan wata kuma, Sannan ya gaya mata tadinga dagewa da Addu'a sosai..

Rungumarsa HEESHAM yayi da cewa "I luv u my Kakah, idan na rasaka nayi Babban rashi, Baba Alhaji murmushi kawai yayi masa, dayi masa nasiha akan ya dena barin matsala haka tana dad'ewa ba tare daya fad'a ba.. Toh HEESHAM yace masa da barin gidan.

Aiko yana yin parking bayan ya fitto daga motar tasa NUWAIRAN ya gani cikin kyakkyawar shiga, shigar da take matuƙar kwantar mai da hankali, nan ya rungumeta yana me cewa, "Subhanallah my Auntii, kinyi min kyau sosai, tace "Nasani ai, nasan zan maka kyau, danna gane kana san wankan qananun Kaya fiye da kowace shiga a jikina, yace "Dts gud my lovely Sweet Auntii... Ya faɗi hakan da d'aukarta kamar yanda a yanzu ya sabar mata, bai direta a ko ina ba sai'a dining, kana yaci gaba da cewa, kinsan miye, tace "No saika fad'a, yace "Da fari dai ga wannan ruwan rubutun shanye naga.. Ta karb'a da cewa, "Sweetheart mallakeni zakayi, yace "Aini na dad'e da mallakeki matar HEESHAM, kawai dai ina san gyaro matsalarmu ne da ikwan Allah, cikin farin ciki tace "Ina zuwa, nan ta b'ula ledar rubutun ta shanye tsaf da bismillah, tare da rungumesa, taci gaba da cewa, Allah yasa yau Ango kake, murmushi yayi da cewa ke kuma amarya ba, tace "Aini kullum a amarya nake, dan kakasa bambantani dasu..
Shafa fuskarta yahauyi cikin wani salo na masifar santa yace, "Da ban sameki matsayin Matata ba da nayi babbar asara, komai naki yayi daidai da yara yaran mata, masu aji daji da kansu, ina san ƴaƴa my Auntii zaki bani su..
Wani yanayi ne taji yana shigarta, yana bin jininta tace "zan baka mana mijina, amma nayi imani zan fika sansu, danni san Yarana yafi naka, yace "da gaske, tace "Allah kuwa..
Yace "Wato zaki dinga bani su shekara shekara.. Tace "eh mana...
Nan ya rungumeta suka shiga wani yanayi me wahalar fassarawa..


Aiko yau HEESHAM yake ango, har a zuciyarsa ya yarda Allah ya karb'i addu'arsu, dan lokacin daya duba hanya a bud'e take.. Saidai kasancewarsu saban shiga hakan yasa gabaki d'aya suka fitta daga hankalinsu, gaskiya HEESHAM yayi b'arna sosai, dole kuma ya zauna zaman jinya...

Tsoransa ya kama NUWAIRA sosai, bata da aiki sai yimai kuka, kamar tasan hakan qarama mai santa da ƙaunarta yake..
Washe gari komai shi yake mata, sai kallanta yake cike da mamakinta yana mata murmushi, gaskiya tana da shagwaɓa over, gata da raki, jin daɗinsa d'aya tana da tsafta, komai nata a tsaftace yake...

Harara ta galla mai, da cewa, "Wai miye kake kallona, yace "Aunty komai naki kyau ne dashi, jiya kin kuncemin komai, gaskiya bazan iya rayuwa babu ke ba, tace "Hmm ni ba inda zani, yace d'aurewa zakiyi muje asibitin nan na dubaki, Allah da gaske nayi miki b'arna, tace "Ashe ka sa'ni, yace "Ni da abuna, ai dole na sa'ni, dan Allah karki qara cemin bazaki ba...
Shuru tamai, shiya tayata komai har tagyara kanta, suka nufi asibitin...

Bata mai musu ba ya gyarata sosai abin dai ya zamar musu ni dake mun zama abu d'aya, sun fitto ne tana tafiya a hankali wai dan kar a gane tafiyarta ta canja, sai suka had'u da AHMAD.. Bayan sun gaisa sai HEESHAM ya kallesa a kunyace yace dashi, "YAYAH zan d'an tafi Hutu na 1week, AHMAD yayi murmushi yace "Wato, na samu Babya ko, HEESHAM yace "Ina maka fatan hakan YAYAH, yace "Gud, babu damuwa amma idan ka qara kwana d'aya zan hukuntaka, kallan NUWAIRA HEESHAM yayi wacce tasaki baki tana jinsu, yace da ita, "ina bazaki barni na ƙara bako.. Kunyar AHMAD ta kama NUWAIRA kamar qasa ta tsage ta shige ciki, tace "Toh wai meyasa ma ka d'auki hutun... Da tasan amsar dazai bayar da bata tambayesa ba, dance mata yayi, "La harkin warke ne, wallahi Yaya jiya na zama Ango, kuma jinyarta zanyi..
NUWAIRA najin wannan tab'arar tasa tayi gaba abinta a hankali, batare datace ko qara ba..
AHMAD ya sakar mai murmushi dan yafi kowa sanin tab'ararsa, yace "wato tun tuni ka tsaya tsoranta ko, HEESHAM ya mirgina kai yace "Hmm umm kaidai YAYAH bari.. Yace "Na bari ƙanina, fatana dai ka kula da kanka, zan shiga wani aiki yanzu, naso dasa hannunka, amma ba damuwa, Saidai ka tabbatar bazaka qara kwanaki ba, HEESHAM yace "insha Allah YAYAH, Sannan ina maka fatan alkairi kan Allah yasa ayi aikin lafiya a gama lafiya...
Yace "Ameen brother,
Da haka suka rabu...

Amota sai harararsa take ya, shiko ya dinga mata murmushi dan yasan ya bata kunya...

Wannan sati d'ayan dukkansu su biyun bazasu manta dashi ba a rayuwarsu, dan Soyayyar gaskiya ce ta bayyana kanta garesu, HEESHAM yana da tabbacin NUWAIRA na d'auke da cikinsa, dan yana d'aya daga cikin waƴan nan doctor cin da ake kiransu kamar mayu, shidai yasan ya kulata da yawa ba kad'an bane, dan har Addu'a take kan Allah ya fitta shi zuwa office..










Toh yaudai zai fitta office d'in, Sai wani lallab'asa take kan ya fitta, dan taga alamar baya san fittan, Bata san ya gane taba, dan haka bayan kammala breakfast d'insu kasancewar tana kan cinyarsa, shafo gefan fuskarta yayi zuwa wiyanta cikin wani salo na yara yaran maza, yace "Auntii zanyi missing d'inki sosai yau a office d'ina, Allah yasa na iya aiki, dan kin kuncemin komai.
Tace "Hmm, Ai aikin lada ne, duk da zanyi missing d'inka amma wallahi Luv kana da fitina, Sam kaqi barina na huta.. Murmushi ya sakar mata da cewa "idan ana sallah ba'a magana Luv, Sannan bazaki gane bane, wallahi Luv sanki wata rana yawa zaiyi mun, tace, "idan yayi yawan zaika kawo min shi zan adana maka, yace "Toh ya zakiyi da naki, tace "haka shima nawan... Magana ta gaskiya idan ba Kai bazan iya rayuwa, ina so ka yarda da hakan luv, dan a kullum rokwan Allah nake kan duk cutar dazai jarabceni da ita yasa karna manta dakai adukkan al'amurana, ina sanka da yawa luv, takai ƙarshen zancen da rungumesa da sakar mai kiss a wiya, shikam sakar mata yayi a baki, sanda suka gaba b'ata tunanin juna Sannan ya tafi ya barta da kewarsa, amma taji daɗin fitar tasa dan tasamu sukuni sosai, nan takira Ramlat mutuniyarta dan susha hira abinsu..

Daidai lokacin AHMAD ya shiga part D'in HAIRANAH dan ba itace dashi ba, tana toilet d'inta taci qananun kaya sai aikin wanke toilet d'in take, wata singilet ce a jikinta da wani wando iyakarsa gwiwa, ta d'ane kan wata kujera tana wanko jikin bangwan toilet d'in, yanda take yin d'age dan kai hannunta inda tsayin nata bazai kai ba ya bama AHMAD tsoro😳, dan kuskure d'aya zatayi kujerar da take kai tagurd'e tayi jifa da ita Ya shiga uku, kai dole yau ya gaya mata cewar tana da ciki, danta kiyaye mai.. dan haka ji tayi kawai an sauketa qasa, tasan bameyi mata hakan sai mijin nata, suna had'a ido ya galla mata wata shegiyar harara da cewa, "Wai ke meyasa baki da tunani ne.. Turo baki tayi gaba tace "Toh kuma yanzu me nayi, yace "Kuskure d'aya zakiyi kujerar nan tayar dake kijamin asara, danni bata ke nake ba ta cikina nake, tunda bakya jin magana, nace miki ki rage wannan aikace aikacen da kike ga Y'ar aiki kinqi, toh bari kiji, ciki ne dake, kuma wallahi ina MASIFAR sanshi, bana san ki dinga yawan bashi wahala, dan haka dole a yanzu kikiyaye, zan iya d'aukar mataki akanki indai har akan wannan cikin ne,
B'ata rai tayi da wanke hannunta ta ficce daga toilet d'in wai a dole tayi fushi, dama jiya tana fushi dashi danya hanata shan ƙanƙara, shine data tuna ta had'a fushin dana yanzu.
Biyota yayi da rungumarta ta baya yana cewa "Toh kiyi hakuri, amma wallahi bana sanki da aiki, zan gyaleki akan komai amma banda wasa da lafiyarki dana Yara na, inasanki matata dan Allah kiji tausayina ki kulamin da cikin jikinki ina sanshi over, ina san yara sosai bana san naji wani abu ya faru da cikin nan, yakai ƙarshen zancen nasa yana me shafa cikin nata.
Dake a gaban madubi suke suna had'a ido ta hango masifar san da yake mata ita da cikin, dan har wani shock taji dayakai hannunsa kan cikin nata.
Tace "Insha Allah zan kula da kaina sosai my blood.
Yace "Allah yasa..


Tun daga wannan lokaci AHMAD ya d'an samu nutsuwa, ta d'an rage aiki sosai, dan Asiya sosai take da qoqari, bata gajiyawa akan aiki, sai yanzu HAIRANAH takejin dad'in Asiyan dan tana mata aikin daya dace, amma ko kusa bata yarda da gyalan bedroom nata, dama na AHMAD ko wacce a cikinsu itace take mai gyara, yace kadda su kuskura yaga Y'ar aiki a part d'insa, baya so, dan haka suna kiyayewa sosai..



Fatan HEESHAM ya tabbata dan yau watansa d'aya da sati biyu dacin amarci, b'aro b'aro laulayi yayi ram da NUWAIRA, nata me fitina ne, yace kaza yake so yace kaza yake so, amma Sam bai tab'a kwantar da ita ba, kuma bata amai.
HEESHAM abin nema ne ya samu, dan haka biye mata yakeyi sosai dan haka ta qara shagwaɓemai, idan kaje gidansu bazakaso ka fitta ba, dan yanda suke zuba Luv abin da tsayawa arai yake.. Dama sun canja sunansu zuwa Luv, daga kiji wannan yace Luv kaza sai kiji wannan yace Luv kaza..

Duk san jiki da rakin NUWAIRA tana qoqari sosai wajen tsaftace ko'ina a gidanta, dan HEESHAM ya buqaci ya kawo mata y'ar aiki amma taqi, dan da gaske zuciyarta d'aya ta yarda ta kumayi imani y'an aiki suna kwace miji, qiri qiri ta gaya mai dalilinta naqin Y'ar aikin, yace to zai kawo mata tsohuwa, tace idan tana da jika makirci a wajen tsofaffi ba wani Babban abu bane, tuni zata tunkud'e matar gida tasaka jikarta, dan haka ko aiki zai kasheta zatayi aikin gidanta, bazai dai mata kishiya akan qazanta ba, dan tana da tsaftarta daidai gwargwado..
Haushinta ya kama HEESHAM, dan shima ta cikinsa yakeyi, gaskiya tana da kishi sosai, ya fad'i aransa, dan haka saiya raba musu aikin gidan, shine me wanke toilet da wanke wanke, da d'an abun da baza'a rasa ba, ita kuma shara da girki da goge goge, ta wajen harabar gidan kuwa me bama fulawowi ruwa ne yake tsaftace su kullum, wanki ko kullum injin ne me aikinsa, hakan yama HEESHAM dad'i ya d'an rabata da aiki...

Bai gayama kowa tana da ciki ba, kuma yana da tabbacin itama ba wanda zata gayama, dama ya gaya mata sai tayi wata bakwai zai kaita gidansu momy, alokacin ta d'auki zancen nasa wasa, bai damu ba, shidai yana san kawai yama momy bazata ne..🙈


Ramlat ma tana kwanshe da nata cikin, ita kam kowa ya sani, dan kiransu tayi tadinga gaya musu tana da shi. Hannatu kam wai sai sunci amarci, fata suke suyi shekara d'aya ko biyu.
Khadijan Sadeeq ko dama ta rigasu samu zata rigasu saukewa insha Allah..




MEENATU yau ta gaji da b'oyema Asiya manufarta dan haka yau take san sanar da ita manufar tata..
K'arfe goma sha d'aya na safe bayan Asiyan ta gama aikinta ta zauna a part d'inta tana hutawa sai MEENATUN ta kirata.
Tana zaune akan kujera mecin mutum uku Asiya na zaune akan mecin mutum d'aya, tace "Asiya na kiraki ne danna gaya miki meyasa nasa a d'aukeki aiki anan gidan, Asiya taja numfashi tace "Toh ina jinki Hajjiya.
Gyara zama MEENATU tayi da cewa, "A duniya ba wacce na tsana kamar HAIRANAH, ta Aure min miji nace mata zan fidda ita daga gidana, dan nayima kaina alƙawari bani ba zama da kishiya, taci min fariyar ban isa fidda ita ba, kuma Soyayya ce tasa AHMAD Auro min ita, kuma zama a gidansa daram, shine nayi alƙawarin fara kwace wannan Soyayyar kafin na kuma fittar da ita daga gidan kuma a wulaƙance a kuma tagayyare.

Zan baki dukkan farin ciki, idan har zakiyi abin da nake so kiyi, ina san ya zama bakimmu d'aya ni dake, zan dinga baki magunguna kina saka mata a abin cinta ko abin Shanta idan ta kama ma na binnewa ne kije cikin wayanku na ƙauye ki binne min a part d'in nata..
Idan kika amince da hakan zan saka a qara miki albashi, zan dinga miki kyauta akai akai, zan kuma y'an taki kifi kowace bazawara a danginku cin ribar zawarki..
Asiya Jan numfashi tayi, ta zubama MEENATU ido, tace aranta Allah me iko, tayi mamakin a wayewa irinta MEENATU amma haka ta iya fitowa lokaci d'aya ta gaya mata ainihin gaskiyar manufarta akan HAIRANAH, bata tare da wani tsoro ko wani tunani ba, hmm gaskiya bata san kan duniya ba, kuma bata san wacece ita ba, dan haka d'auke idanta tayi daga kallanta ta sunkuyar dakai, tace "Allah ya temakeki uwar gida, me yasa kika gaya min ainiyin manufarki akan HAIRANAH, ba tare da jin wani tsoron abin dazaije ya dawo ba...
MEENATU tayi dariya tace, "Yanzu ke a tunanin ki danna gaya miki magana ta gaskiya akan cikar burina akan HAIRANAH sai kawai naji tsoran kar wata rana kizo ki juyamin baya ko.
Asiya tace "shine ai, kinsan mutum akowane lokaci ya kan iya canjawa, daga mugu ya koma mutum na gari, amma ko'a mafarki ban kawoma kaina tunanin zan iya juya miki baya ba, ko kuma na tona asirinki ba, yin hakan bazai zame min alkairi a rayuwata ba, musamman idan nayi duba da yanda nake Y'ar ƙauye ke kuma kike Y'ar birni...

MEENATU tace, "Hmm kawai kisa aranki duk ranar da kika juyamin baya ko kika tona asirina tsakanina dake kin kashe kanki, Dan zan wulaƙanta miki rayuwa Sannan nasa a kulleki kullewar da bazaki qara fittowa waje ba, Saidai kita aiki a gidan yari ba fittowa anan zaki mutu a kuma rufe gawarki ba wanda ya sani..

Asiya tad'anyi yak'e tace "Babu ni babu juya miki baya Hajjiya, Sannan bani ba tona asirinki, gaya min duk abin da kike so zan miki shi, ai baki da matsala dani..

MEENATU tayi murmushin cin nasara a ganinta, nan ta miqa ma Asiyan Maganin da malamin HASEENAH ya bata tace, "Duk iya wiya ina san ki saka mata shi a cikin abincinta, kuma ki tabbatar taci.
Asiya tace "Toh, amma shi wannan me zai jawo miki, sai yanzu naji takaicin yanda bake d'ayace me juya Yallab'ai ba, MEENATU tatashi cikin murmushi tace "Ana dai tafe zan zama ni kad'ai ce me juyasa Asiya, wannan Maganin da kike gani, shi zai d'auke dukkan Soyayyar da AHMAD d'in yake ma HAIRANAH ya dawo kaina, hakan shine samun galabata ta farko a kanta...
Asiya tace "Angama Hajjiya, baki kuma da matsala, tace "toh maza jeki ina jiran sakamako, tace "Baki da matsala ai, Asiya na faɗin mata hakan ta tashi tabar falan..
MEENATU ta sauke ajiyar zuciyar zata samu yanda take so.


Wai ance shege na Ƙauye, Asiya na zuwa part d'in HAIRANAH taganta a kitchen tana had'a kayan kwad'ayi, da a falo take tana kallo, amma da kwad'ayin ya ciyota zarub tatashi tayo kitchen d'in.
Madara tasaka a cup ta gari da zuba mata ruwan sanyi sosai, ta saka wasu dunk'ula dunk'ulan Milo aciki da shuga kad'an haka, tana gama had'awa ko dawowa falon batayi ba ta fara shan abinta.
Tana ganin Asiya ta sakar mata murmushi tace "Bakije kin zauna kin huta ba, tace "Hmm, wani abu ne ya dame ni Ranki ya yaɗe, ni kuma na kasa yarda naci amanarki..
HAIRANAH ta tsaya da shan kayan kwad'ayin nata tace, "Toh, wani abu ne haka dazai dame ki, har ki shiga tuninin baki san cin amana ta..
Tace "Eh toh, dama Hajjiya MEENATU ce ta dingaya min wasu sharad'od'i akanki, cewar idan har bam bi abin da take so ba zata Sa a kulleni a gidan yari, babu ni babu fittowa, acan zan mutu a kuma rufe gawata, Ranki ya dad'e ina cikin tashin hankali, ina san rayuwata tayi kyau, bani san zuwa hannun jami'an tsoro, Sannan ni abin da take so nayi mata ba zanyi mata shi ba, dan tun ina budurwa da Mahaifina ya Aurar dani, yace min na guji aikata sab'on Allah, Sannan na guri cin amana, Sannan naguji san abin duniya, yana gaya min hakan an kaini gidan mijina Washe gari ya rasu, kinga ko idan ni me lissafice bazan manta da kalmomin nan nasa ba har ƙarshen rayuwata, tunda nayi imani ba munana bane, akan hanya suke...
Nan Asiya ta kwashe komai da sukayi da MEENATU ta gayama HAIRANAH tana meci gaba da cewa, na gaya miki hakan ne badan cin amanar MEENATUN ba, na gaya miki ne kawai dan naga babu Allah a tafiyarta, kuma nayi imani Allah bazai kamani da lefin cin amanarta ba, dan haka saiki nema mana mafuta ni dake dan nagama nawa..
HAIRANAH tayi murmushi tace "Hmm, bani Maganin zan yardashi a shara, Asiya ta miqa mata maganin, Sai taci gaba da cewa, Sannan kije ki nuna mata kin saka min a abincin nawa kuma ki tabbatar mata naci, wannan itace mafutar, Sannan duk wani abu da zata qara saki kiyi a gaba ki qara duba Allah ki gaya min, ni kuma na baki wannan amanar, idan kikacita na barki da Allah, Sannan ni bazan je na tona mata asiri a ko'ina ba, amma dake yau da gobe tafi qarfin wasa idan ke kika tona mata asirin nata koda ta kulleki na miki alƙawarin fiddake da izinin Allah, Sannan kuma duk abin da tabaki na ladan aikinki ki karb'a kiyi sha'anin gabanki dashi, kadda kiji tsoran komai, kin dai ji na gaya miki..
Tace "Aiko na gode Allah ya saka ya kuma qara kareki, nagode sosai...
HAIRANAH tace "Ni'ce da godiya, ga kayan kwad'ayi na ko zakisha, tace "aa badani ba, Wannan ruwan sanyi idan nasha hancina toshewa zaiyi, HAIRANAH bata kula bata amsa ba danjin ringing na wayarta da tayi a can falan nata, nan ta wucce Asiyan tayo falan da d'aukar wayar tata tana karawa a kunne da cewa "welcome my blood, yace "Yauwa my Baby, tace "kayi aikin lafiya, yace "Yanzu na fitto shine nace Bari naji lafiyar Babyna, tace "ina lafiya lau, yace "Gud, me kike Shane naji kamar kina jin daɗinsa tace, kwad'ayi kawai na had'a, yace amma banda ruwan sanyi ko, tace "hmm nifa my blood idan har ban sha abu me sanyi ba bana jin daɗin bakina, yace "Allah my Babyna zaki nemi dukkan furijin d'akinki ki rasa a gidan nan, dan shan sanyinki yayi yawa over, ko ki dena ko ranki ya b'aci, tace "Nifa na lura tunda na samu cikin nan baka san duk wani abu wanda na nuna ina so in dinga ci, yace "Faɗi gaskiya dai, abu biyu ne na had'aki ci shine shan bumbita da shan ruwan sanyi, kuma da gaske bana sanki dasu, zasu kawoma Baby matsala, amma karki dena zanyin maganin ki ne ai, Allah ya dawo dani gidan lafiya
Tace "Toh nadena bazan sake ba, yace "kin d'au alƙawari, tace saika dawo zan d'aukar maka, yace "Hmm, mezaki dafa min ne yau, tace "Abun dad'i, kai dai gama komai ahankali, dan bayan tadanadar maka lafiyayyan abinci dazanyi, wanka zanyi maka cikin kyakkyawar shigata me kalar Skye blue da ratsin baki zan maka, Allah har a zahiri da bad'ili saika yaba komai batare daka shirya yabawa ba.
Yace "Allah my Baby, tace "Allah mijina, yace "toh ki kulamin da Kanki sosai da Babyna kinyi, ina san cikin nan a kula min dashi sosai, tace "insha Allah blood baka da matsala da hakan...


AHMAD kenan, har cikin qarqashin zuciyarsa wallahi san cikin HAIRANAH yake.
Ayanzu bashi da abin so kamarsa, ya yarda ya kumayi imani hakan baya rasa nasa ba da ƙaunar da yake mata ne...


Asiya taje ta gayama MEENATUN ta sakama HAIRANAH maganin a abinci kuma taci..
Ai nan take murna ta kama MEENATU, ta d'auki kud'i me yawa tabama Asiyan, dama ta gayama AHMAD zata gidansu duba momynta dan haka tana zuwa ta gayama momyn nasu ai HAIRANAH taci wannan maganin a abinci kamar yanda malamin yace, aiko nan Momy ta zari gyale tace duk da HASEENAH bata nan suje wajen malamin nata su gayamai anci nasara akan dukkan aikin daya basu.
Aiko nan babu b'ata lokaci suyi wajen malamin, bayan ya gama dubansa, ya kalli MEENATU yace "koda HAIRANAH taci wannan magani ayanzu bazaiyi wani tasiri akanta ba, saboda shi a dubansa na wannan ranar bai gane tana da ciki ba, kuma dama maganin zai mata amfani ne idan bata da ciki, amma yanzu koda taci bazai mata amfani ba
Hmmm kuma AHMAD yana MASIFAR san HAIRANAH da cikin, kuma idan kika bari ta haihu dashi kashinki ya bushe, dan qarara zai nuna yafi santa da ƙaunarta fiye dake, dan a yanzu ma inda zaki duba zuciyarsa ba qaramin razana zakiyi da ganin qaunar da yakema cikin jikin nata ba, wannan yana qara masa santa sosai a ZUCHIYA..

Gumi ne ya wanke fuskar MEENATU, tace "Dan Allah malam ka temakeni, kayi wani mugun aikin da cikin zai lalace, ya b'aci b'acin da ita da samun ciki har abada bama a gidan AHMAD d'in ba, Yace "Bazai yuhu ba, na gaya miki HAIRANAH tana da Addu'a, duk wani aikin da zakiyi a kanta na banza ne, dan koda yacita cin banza ne, lokaci qanqani zata lalata aikin, Sannan bafa irinsu bane muke matsa musu da aiki, dan idan muka matsa da sai mun cutar dasu nan take komai zai dawo kammu indai ba suna cikin jinin haila bane...

Tace "Yanzu dai kana nufin babu wata hanya kenan, yace "Hanya mafi sauki itace, kije ki kamata da kokuwa ki mata dukan tsiya har ki fitar da cikin nata, idan ta qara samu ki qara b'arar mata shine mafita, ko ki dinga samun maganin zubar da ciki kina saka mata a duk abin daza taci, amma aiki ne dai ni bazan mata ba, sai in tana haila, idan kikaci galaba akan zubar mata da cikin, kizo ki gaya min saina mata aiki akan tabar gidan naki, wanda shima sai taci zai kamata..
MEENATU shuru tayi masa kawai, momynsu ce dai ta sallamesa suka bar wajensa..

Akan hanyarsu ta dawowa ne MEENATUN tacema momyn nasun suje wajen wani bokan momyn nasu ita tafi yarda da aikinsa, momyn tayi Na'am da zancen nata, dan haka bata ja ba, suka nufi daji wajen bokan, suna zuwa ko suka samu ganinsa, dan ba layi sosai, da MEENATU ta gaya mai damuwarta yanka mata wasu shegen kud'ad'e yayi, sai d'ankunnanta ta cire ta basa na zinare, dan bata fitto da kud'i sosai ba, yako bata wani Magani yace tasakama HAIRANAH a abinci, idan taci cikin zai zube nan take, kuma ba ita ba samun wani har abada..
Murna awajen momynsu da ita ba'a magana.

Aiko tana dawowa gida ta kira Asiya tace taje ta saka mata maganin a abinci, Asiya ta karb'a ta kaima HAIRANAH, nan taje tayi Flowshing d'insa kamar yanda tayima na farko..

Shuru shuru MEENATU bataji HAIRANAH ba lafiya ba, sai ta kira Asiya tace "anya Asiya HAIRANAH taci maganin nan, Asiya ta juya kai tace "Hajjiya ai akan idona taci, Allah yasa an samu nasara, tace "Hmm jedai ki duba min ita, dan Maganin dana baki na zubar da ciki ne, wai tana da ciki, kuma idan taci an tabbatar min nan take cikin zai fitta, kuma ita da aihuwa har abada, Asiya tayi wayon serven d'in recording d'in data saka ma MEENATUN tun fara maganar tata, wanda tasa aranta duk abin da zasuyi ita da MEENATUN zata dinga yin recording nasa dan qara tabbatar da hujja.. Kana tace "aa, bara naje na duba miki ita, MEENATU tace "Yauwa yi maza..
Asiya na fitta taje ta labe zuwa can tadawo tace, "Hmm Hajjiya tana nan qalau d'inta,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment