Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

12/10/20, 7:39 AM - Messages and calls are end-to-end encrypted. No one outside of this chat, not even WhatsApp, can read or listen to them. Tap to learn more.
12/10/20, 7:40 AM - Naffy Aliyu Umar: HASKE writer's ASSO.


Da sunan Allah me rahma mejin k'ai.


Barkamu da kuma saduwa da juna cikin wannan labari me suna,JARUMA.
Wanda ni maman khadija zan kawomuku shi amatsayin tuni domin natabayin shigenshi saidai bacewar da yayi yasa zan dawo da shigenshi saidai har yanzu ina kuma sanar da ku cewa duk Wanda yaci karo da ainihin wancan din ya temakamin dashi me SUNA BURINA.

Nagode.


JARUMA.


1



"Wai hajiya haka zaki zuba ido akan wannan lamari haka kawai yaita d'aukarma kanshi zunubi hakkin rai na rataya akanshi anya kina ganin hakan daidaine kuwa?

Zubama kanwartata ido tayi kamin tace"Yanzu sabida Allah suwaiba ni zaki kalli tsabar idona ki gayama haka? Kenan kema kina cikin masu fadin cewa Ahmad shike kashe matanshi ko? Shikenan nagode gara da kika fito kema kika nunamin abinda zuciyarki ke ciki Amma inaso in gayamiki wata magana daya, Yarona ba maye bane ba d'anshan jini bane Sannan babu wani mugun laifi da zaisa ajingina wannan abun dashi k'addarace kuma tana kan kowa danhaka ki tashi ki ficemin daga nan insha Allah sai anyi walkiya wataran angano me wannan mugun aiki,Ta idasa maganar tana share hawayenta Dan sosai takejin wani irin d'aci na taso mata.

" Yaya ba nufina kenan ba wlh nida..... "Kinga dakatamin suwaiba maza tashi kibar nan kamin in kakkauramiki mari wallahi wawuya kawai,Hajiyar ta katse kanwar tata cikin tsananin fushi.


D'an kwalinta ta cire ta rufe fuskarta tana hawaye wannan wace irin jarabawace me matuk'ar nauyi akan yaronta Shin meke faruwane haka? Tambaya Mara amsa kenan.



***

Yana kallon yanda kiran keta shigowa ajere jere Amma ya kasa d'auka tsabar nauyin da jikinshi yaimishi wani irin shegen ciwon Kaine yake takurashi Wanda ya tabbata koda be auna kanshiba yasan cewa jininshi ya hau amatsayinshi na cikakken likita.
Jawo wayar yayi jin anki daina kiran yasa akunnrnshi batare da yayi maganaba.

Yanajin yanda ta sauke ajiyar zuciya kamin yafarajin saukar daddadar muryarta me matukar sanyi"" Haba Dr. Kumafa nasan yanzu haka kaga kirana Amma ka share wai meyasa kakemin haka Dan Allah?

"Fatima banda lafiya fa wallahi zazzabi nakeji shiyasa kikajini shiru Amma zan kiraki anjima kadan ko Akwai wata damuwa ne yanzu?

Da sautin damuwa tafara fadin" Innalillahi wayyo Allah sannu ka gayawa hajiya ko? Kasha magani? Sannu Dan Allah kasha magani saika kwanta zaka warware insha Allah dama ba wani Abu baneba kawai zan tambayeka yaushe zaka zone naga lokaci yanata k'urewa,Amma ka kwanta anjima zan kira insha Allah.

Ajiye wayar yayi tare dajan bargo ya rufe har kanshi wani irin tausayinta yakeji ya tabbata takusa mutuwa tunda har ta like sai shi.



Kano.
"Allah yagani kina kunyata mata aunty sabida Allah yanzu mene haka? Namijine fa kinwani nacemishi nasanko auran akayi Allah haka zai dinga yimiki wulakanci ina sane yanda kike kiranshi Allah shi be kiranki Amma kinwani nace haba!!!

Sauran dafe bakinta tayi idanunta na cikowa da hawaye, Sabida dukan da yayar ta sakarmata abaki.

"Tashi kiban waje konaimiki shegen duka wallahi,Dawani bakinta kamar gidan tsutsa.

Tashi nai bakina adane tsabar jin haushi Dan sosai raina ke baci idan naga yanda yayata ke nacewa wannan me shegen girman da d'agawa.



***

"Malam har yanzu bakace komaiba Dan Allah ka tsaya kayi bincike kamar yadda yadace kadda yarinyarnan ta rasa ranta abanza wallahi yanzu ko barci ban iyawa sosai.

Yajima yana kallonta kamar bazai tankaba Sannan yafara magana" Amma wallahi hadiza kin bani mamaki bantaba tunanin zaki iya tunkarata da wannan maganar ba dan ita tunanin tarin ilminki bazai taba bari wannan maganar tai tasiri cikin rankiba Ashe abun ba haka yakeba to bari inyimiki magana wadda zaki gane abinda nake nufi kinajina ko? To duk labarin da aka kawo gidannan haka yake matan Ahmad duk mutuwa suke yara biyu kawai ke gareshi yanzu suna hannun mahaifiyarshi Aure tsakaninshi da Fatima babu fashi insha Allah zan auramishi ita da izinin Allah sannan zanyimiki wani albishir na daban shine idan Fatima ta rasu zan k'aramishi da aysha kuma koda bayan babu rai na ban yarda da canza wannan maganarba..



Kuka tasaka tare da d'ora hannuwa akai tana kuma zubamishi ido,Hakika tasan dama mijinta me ra'ayin rikau ne Amma bata taba tunanin yakai hakaba shikenan zai kasheta da sauran kwananta.

"Kadubi girman Allah malam kadda kaimin haka inason yarinyata bazan iya jure rashintaba natuba malam kadda muyi haka dakai Dan Allah kabar maganar nan Allah zaibata wani.

" Kinga tashi kibar nan tun muna shedar juna wallahi.


Da kuka tabar falon nashi ta nufi d'akinta yayinda yaran sukabita da kallon tashin hankali Dan hakan betaba faruwa da iyayensuba.

Fatiman ce ta tsame hannunta daga wanke bra dinta da takeyi ta rufama mahaifiyarsu baya, Kirjinta sai bugawa yakeyi fatanta ace bawai sanadiyyar aurantane ya kawo wannan sabanin ba.

Cikin sanyin jiki ta zauna gefenta tana murzar hanunta sosai takejin bakinta yaimata nauyi"Mama Dan Allah ki daina wannan kukan hankalinmu na tashi bamu saba ganin wannan tashin hankalinba Dan Allah.

"Fati waye yajamana iye!Duk uban wa yajamana wannan masifar inba keba,Kina sane da Wanda zaki aura amma hankalinki akwance so kikeyi in rasaki? So kikeyi zuciyata ta buga sabida zullumi kin kosan ko mata nawa ya aura duk suka mutu? To wallahi badani za ayi wannan danyen aikinba kodai kije ki gayama abbanku kin fasa auren kokuma in tattara in barmuku gidan Dan ban shirya ganin gawarki ba.

Dafe kanta tayi tana hawaye sabida damuwa Amma batajin zata iya daina kaunar Ahmad ita mamakin inda mamansu takai tarin ilminta takeyi ma sabida wannan maganar Sam bata daceba.

Ni da ke tsaye daga bakin k'ofa na idasa shigowa cikin d'akin ina share kwallar idanuna domin najima tsaye wajan.
" Dan Allah mamanmu kiyi hakuri ki daina cewa zakitai ki barmu idan kikatafi mukuma mu zauna dawa? Kiyi hakuri.

Cikin Dan tsawa tace kutashi ku fita dallah haba!!

Hijab dinta ta d'auka sai safa data sakama k'afarta ta lek'a d'akin Abban batare data kalleshiba tace"Zanje gida"

Da kallon mamaki yabita Dan tuni ta fice shi lamarin natama yafara bashi tsoro kullun da kalar tashin hankalin da zata nuna yasadai bewucetace k'ararshi zatakai wajan mahaifinta Wanda yake shima ubane agareshi domin da mahaifinshi da mahaifinta wa da k'anine to ashirye yake da Duk inda zata kaishi Fatima dai diyarshi ce bawani yabashi itaba danhaka auranta da Ahmad babu fashi kuma tana mutuwa zai maye gurbinta da aysha zaiga k'aryar rashin yarda da k'addara.





Wannan littafi free ne gaba dayanshi😊
12/10/20, 7:41 AM - Naffy Aliyu Umar: JARUMA.
2

Na maman khadija.


Haske writer's asso.




"Subhanillahi dattijon ya furta ganin yanda tataho tana share idanunta da gefen hijab dinta " ikon Allah to shige ciki ina zuwa Allah yasa lafiya da girmanki da komai zaki taho kina kuka.

Koda tashiga gidan d'akinshi tashige tai zamanta har lokacin kuka takeyi jitake kamar ma yanzu zata rasa fatiman.

Saida ya daidaita zamanshi sannan yabita da kallo duk ma tafad'a,"Ke bansan shirme Dan Allah dubeki da girmanki da komai Amma kinbiyo hanya kina kuka meya faru?

"Baba akan maganar auran Fatima ne nasan dai zuwa yanzu kasan komai tunda zai gayamaka,Maganganu nata kumayin yawa Amma abbansu yai shiru saima shirye-shiryenshi da yaketayi nikuma gaskiya bazan yadda in mik'a yarinyata makasartaba.

Sadda kanta k'asa tayi ganin irin kallon da yakemata.

"Ah lallai khadija banyi mamakiba dankuwa kedin mace ce mata kuma idan suka Shiga damuwa babu kalar haukan da bazasu iyayiba,To bari kiji lawal dai yaronane Amma banine na haifeshiba danhaka ban isa in tilastashi kan wani daya shafeshiba musammanma akan yaranshi tunda nashine kin gane ko? Waima tsaya yaranki nawa ne khadija?

Da kallon mamaki ta kalleshi amma ganin babu wasa cikin idanunshi yasata furta su bakwai ne.

" oh to nawa kikabawa Allah yabaki su?

Sadda kanta k'asa tai tana share hawaye Dan tasan halin mahaifinta damacan haka yake da wani kalar ra ayi Dan idan baka sanibama zaka iya tunanin shine mahaifin mijin nata sabida yanda hali yazo daya.
"Ba tambayarki nakeba? Ya katsemata tunanin data lula.

" Kayi hakuri baba Dan Allah.

Ai tambayarki kawai nayi khadija banda hauka kalar naki yaushe zakiyima Allah shisshigi uhum? Nawa kika biya ya rayamikisu gashi harkin kai uku ma'aura, Shikenan saikikoma wata jahilar k'arfi da yaji INA wannantarin ilmin naki? To zangayamiki magana guda daya amatsayina na mahaifinki kinajina ko? To wallahi wallahi ina bayan lawal garama ki kwantar da hankalinki kibi yarinyarki da addua waye besan k'addaraba ? So kikeyi muyima Allah butulci khadija? Maza tashi ki koma gida kuma kibawa mijinki hakuri tun muna shaidar juna wallahi.

Godiya taimishi sannan tata shi jinta takeyi kamar taita kwala ihu amma ta d'auki alwashin daga ta daina kuka zatai hakuri tunda har Mahaifinta ya goyi baya to kuwa babu yanda za ai maganar nan ta fasu saiwani iko na Allah.



***

"Dr.inaga yakamata ka raba kanka da wannan damuwar wallahi wani na nan ta shi qaddarar tafi taka yakamata ka dage da addua kaji.

" Bazaka ganeba salim wallahi har ji nake inama ni mutuwa ta d'auka kona huta da wannan tashin hankalin d'azufa mama da kanta take kuma jamin kunne akan fatiman wai ko ina mafarkin inacin naman mutane in gayamata kaga kenan itama tafara d'aukar jita jitan mutane ko?

"Kai haba Ahmad ya zakaima mama wannan fahimtar kawaidai tanabin hanyoyine wajan yanda za agano matsalarka da wuri Amma itafa ta haifeka idanma kanada wata illa ai itace shaida kamabar wannan tunanin.

Huci me zafi ya fitar kamin yace Hakane salim nagode Dan Allah ka shirya zaka rakani in dubo Fatima nafi sati rabona da ita duk tatashi hankalinta narasa wane kalar so takemin Niko banjin komai game da ita wallahi kai bama itaba gabadaya wa inda na aura bantabajin komaiba game dasu bi bammaso inkamu da son kowacce kuma insha Allah indai Fatima ta rasa ranta ta dalilina to ina tabbatarmakada cewa bazankuma aureba kai k'asarma gaba daya zanbari.

Da wannan hirar sukai sallama da juna kowanne ya hade komatsanshi zuwa gida.



***

Hajiya nifa zuwa yanzu wallahi zuciyata tafara karaya da lamarin yaronnan wannan wace kalar masiface? Auranshi shidda amma babu mace ko daya kuma sanadin mutuwar duk kusan iri daya!!! Nima kullun cikin zullumin jin kiran iyayen yarinyarnan Fatima nake dannasan zasu iya hanashi aurenta akoda yaushe kindaisan gulma yanda tak e na tabbata za a iyayin takanas zuwa kano Dan kawai akai wannan maganar, Koda yakema nasan iyayenta dole sai sunyi bincike.

"Hummm alhaji kenan ka ganni nan kullun ban iya barci Amma dai na fawwalawa Allah komai hukuncinshi kawai muke jira Allah ya zabamishi mafi alkhairi kuma ya k'aramishi hakuri da juriyar wannan jarabawa.





Bayan kwana biyu.


" wai ina fatin takene tun d'azu baki na jiranta Amma tazo ta nacema kwalliya ko? Ke aysha kin kaimusu abincin?

Mikewa nai tsam bakina a tunzure danni wallahi bankoson ganin Wanda yaya fatin zata aura nafiso tasamu wani tai auranta.

Da sallama nashiga cikin d'akin,Kamshin turarensu har waje.


Saida na gaishesu sannan na ajiye kayan hannuna na mike abokin ke tsokanata da "kanwar amarya ya shirye shirye ai inaga da ke zamu wuce idan muntashi d'aukar amarya saiki zamanki tare damu ko?

Kallon cikin ido naima Dr. Ahmad din kamin ince" Allah ko? Ai ni ko zuwa akai dani saidai a kalleni Dan bazan ciwuba nama na dacine dashi wallahi.




Maman khadija
12/10/20, 7:42 AM - Naffy Aliyu Umar: JARUMA.
3

Na maman khadija.




Wani irin dumm yaji cikin kanshi kamin ya lumshe idanunshi tsabar yanda zuciyarshi ke bugawa kuwa har ana ganin hakan idan ka kalli kirjinshi.

Rikeshi salim yayi gam yanad'an tausar hannunshi musamman dayaga fuskarshi har wani ja tayi tsabar tashin hankali da damuwa.
"Ka gani ko salim? Nufinta fa ni maye ne,Meyasa mutane ba zasu gane cewa ba laifina bane? Meyasa wannan masifar sai ni meyake faruwa dani?

" Kaga Dr Dan Allah ka kwantar da hankalinka mubar garinnan lafiya Sannan wannan bawani Abu bane indai ka yadda da Allah Fatima na sonka kuma ta amince zata zauna dakai ahaka ai inaga babu matsala kaidai ka dage da addua muma zamu tayaka.

Qamshin turarenta yafara iso musu sannan sallamarta,Fuskarta cike da walwala suka gaisa sannan ta zubamusu lemo takoma gefe ta zauna tana d'an murzar hannunta sabida kunya.

"Amarya ya shirye-shirye?

" Alhamdulillah,Tace tana kuma sadda kanta k'asa.

Shiru d'akin yakuma d'auka tsawon lokaci kamin salim din ya mike ya fita Dan basu waje.

Dan matsawa tayi kusa dashi tana kallonshi"Dr. Meya farune naganka wani iri ko bakaso zuwa wajena bane?

Huci me zafi ya fitar kamin yace bawai haka bane Fatima kawaidai inaji araina ne kamar zaki rasa taki rayuwarne kamar saura Dan Allah muhakura da juna Fatima.

"A a Dan Allah Dr. Kadda kaimin haka inasonka wallahi kuma kadda ka manta komai na Allah shine ya halicceni kuma ya halicceka shi kanshi abinda ke bibiyar rayuwarka Allah yasan ko mene gashi mu bamu saniba kaga kenan gudu ba namu bane dole muyi hakuri da duk tsarin da Allah yaimana Dan Allah ka daina maganar rabuwarmu dukafa yau saura sati uku biki kuma kawai sai mu fasa?


Riko hannuwanta yayi ganin tana hawaye,Kinga ki daina wannan kukan ni bahaka nake nufiba Fatima ganinayi duk hankali ba kwanceba Wallahi inason auren Dan ina matukar buk'atarshi Amma qaddarar dakebina yakesani jin bansan auran na tabbata kema zaki rasa rankine kamar saura waima kinsan kallon da mutane sukemin kuwa?
To kallon maye kome tsafi sukemin sabida wannan abubuwan dake faruwa nasan kinsan komai Fatima wallahi ko sha'awar naman mutun bantabayiba banjin wata alama da zata nuna nine ke kashe matana Amma mutune sunkasa fahimta kinkosan yanzu a katsina aure wuya yaimin? Mama taso inyi aure tun shekaru biyu da suka wuce sabida bazan boyemikiba inada yawan sha'awa Wanda idan tatasomin batamin da dadi,,Amma auren yaimin wahala Dan kai tsaye ake gayamata cewa babu Wanda zaibada diyarshi inda za a kasheta kumafa har cikin dangin mahaifina da NATA amma kowa gudun hakan yakeyi.


"Hummmm kayi hakuri dan Allah komai lokacine wataran sai labari zakayi dariya wataran zaka zauna da iyalinka wataran kuma wannan qaddarar zata shafe daga labarin rayuwarka insha Allah kaidai ka dage da addua Allah ya bayyana abunda ke boye kuma ya daidaita komai insha Allah zakaga kamar ba ayi komaiba wataran.

Idanunshi ya zubamata har lokacin hannuwanta na cikin nashi musamman yakejin wani irin nutsuwa dan gaskiya Fatima mace CE data amsa sunanta,Na fahimceki Fatima kuma ina godiya sosai Allah ya sanya alkhairi tsakaninmu shiru kwana biyu banzoba shine nace yaya maganar shiri naga lokaci yanata kuratowa ko?


Eh hakane kam Amma gaskiya ni babu abinda zanyi dan akwai wasu dalilai kamar yadda kasani wa inda sukan iya zama matsala shiyasa banyi tunanin shirya komaiba,Saidai akwai wata magana danaji Abba yanayi idan har ta tabbata nasan zaimaka magana inaga mu jirashi tukunna ko me kagani?

" eh hakan yayi da fatan bawani laifi naima Abban ba?

Dariya tai gami da d'an matsawa dan sosai takejin jikinta wani iri sabida tsabar yanda sukai kusanci da juna sosai.

Murmushi yayi dan ya fahimci meyasa tai hakan to itama kenan balle shi da komai daurewa kawai yakeyi dan dai zina batacikin tsarinshi hakika daya jima da fadawa cikinta.

Shigowar salim d'akin yasasu kallonshi dankallo daya zakaimishi kasan yanada damuwa.
"Kazo Abba yana kiranmu ya shigo yanzu, Cewar salim yana jawo juriya dan kadda ya karya ma Ahmad din guiwa amma sosai yaji hankalinshi yatashi dajin kiran Abban.

Daga fatiman har Ahmad din saida fuskarsu ta nuna zullumin kiran Abban.

" dan Allah idan kundawo kuzo nan kuci abinci nasan babu abinda kuka taba, Cewar Fatima dan kawar da shirun da dakin ya d'auka, Koda yake zan bawa auta ta kawo muku abincin can falon Abban.


"Anya kuwa ba hanani auran Fatima zaiyi ba kuwa salim?

" Kai habadai ka kwantar da hankalinka kayi addua insha Allah babu komai sai alkhairi.

Daga karbar da yaimusu sukadan sami nutsuwa dan sosai yake jansu da hira dan Abba sosai yakejin tausayin qaddarar Ahmad din.

"Yauwa idan ban mance da lissafiba yau saura sati uku bikinku to inaso a maidoshi ranar juma'a insha Allah sabida wasu dalilai da suka faru ko suke kan faruwa inafatan ba matsala idan ka sanar da iyayenka ko?

Ganin duk sun zubama Abban ido alamun basu ganeba yasashi sakin murmushi" Karku damu nan da kwanaki shidda nakeso kuzo ayi bikin an jawoshi baya kenan sabida akwai wata matsala dana hangowa banso kuma ta kasance inafatan kun fahimta yanzu?

Godiya gamida addua sukaita mishi domin basuyi zaton hakance zata faruba.


"Karka damu Ahmad kaidai kaje ka dage da addua sannan ka rage barci ka nace azumi da sadaka ka rubanya biyayyarka ga iyayenka insha Allah wataran sai labari dama haka qaddara take kaidai ka daure ka kara hakuri da juriya insha Allah komai zai daidaita danhaka dakaje saikaima iyayenka bayani inafatan hakan ya kasance alkhairi garemu baki daya.
Shigowa ta cikin d'akin yasa duk sukai shiru daga godiyar da suketa jerama Abban.
Sanye nake cikin Riga da zani na atamfa sai safa dakuma dogon hijab Wanda ya kaimin har k'afafuna saikuma nikaf dan idanuna ne kawai waje sai hannuwa da ke waje sabida hijab din me hannune.


Duk idanu suka zubamin saida na ajiye kayan abincin dake hannuna sannan nace Abba zan wuce.

To aysha Allah ya tsare yau sunyi sa a kenan Allah ya temaka adawo lafiya.

Batare Dana kalli inda sukeba nace Ku sauka lafiya.

Abbanne ya i dariya kamin yace aysha kaya da yani kenan makaranta zataje da take koyawa matan aure domin tuni tai sauka to idan batai niyyaba saitace bata zuwa,Duk dariya sukai kamin salim yace ainaga daga gani zatai rikici Abba.

" Hakane tanada rikici kam Amma kyawawan halayrnta sun danne rikicinta shiyasa duk muke sonta bata da matsala gaskiya,Cewar Abban har lokacin yana dariya.





***

Salim yana ganku firgai firgai haka lafiya ko?

"Mama lafiya lau daga kano muke wajan Fatima saikuma muka tsaya wasu shirye shirye dan munsamu ganawa da Abban yakuma gayamana cewa ranar juma'a yakeso a d'aura auren amemakon sati uku masu zuwa.

Tuni fuskarta ta fadada da murmushi dan tuni ta fahimci inda maganar ta dosa" kai Ammadai Alhamdulillah gaskiya sun kyauta wlh ai tunda kukaga haka to inaga tsegungumane sukaimai yawa yaga gara ayi kawai awuce wajan aiko mun gode aiko banga ta zamaba bari su halima suzo afara shirin kai lefe gobe goben nan insha
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment