Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

da nayi magana ko hira da kowa ba saikace kurma dan Allah ayimin wannan alfarman badan halina ba ataimaka aduba tsufana wani kallo ya watsa masa tare dacewa Baza ayi din ba ni ina ruwana da tsufanka aikina kawai nake dole kabi duk dokar dana kafa maka inba hakaba kuma kayi danasani sanina shide baba bece mishi komai ba yarabu dashi har yagama sannan yace Allah baka hakuri da haka har suka qarasa inda zasu yabashi tare da qara jamishi kunne akan yakiyaye shi BABA yace mishi in Allah ya yarda ze kiyaye sannan yakarba ya juya yabar wajen

Sarki SALAHUDDEENI MUHAMMAD SAMEER da ga gimbiya maryama wacce ake kira da Fulani shi yakasance mutum me bin ra'ayin mahaifiyarsa da umarnin ta duk abun da tace shi yakeyi  baya taba yin abu shikadai saida saninta saboda tun yana yaro ta horeshi da hakan kuma yasaba ko muguntar da yake yiwa mutane shide akaran kansa tawani bangaren acikin zuciyarsa bayaso qarewa ma wataran bayasanin abun da yakeyi saidaga baya idan ya tuna sai yaji kwata kwata ransa baya mishi dadi yarasa dalilin yin hakan da yakeyi kuma yakasa denawa  dan wataran ma haka kawai zeji inba mugunta yayiba baya jin dadi sai yayi ta daga baya kuma yayi da nasani hakade yake ta rayuwar sa kamar shi kamar ba shiba yana da mata guda biyu yana da yara guda biyar maza uku mata biyu matar sa tafarko 'yar qananin babansa ce IBRAHIM autan su kenan inabazu kumnta ba su ukune awajen mamansu dayan kuma shine na biyu AlKASIM wanda a yanzu Alkasim shine waziri IBRAHIM kuma galadima duk haka sarki sameer ya nada su kafin yabar duniya

dayar matar ta shi kuma yar gidan qawar babarsa ce duk wannan zabanma fulani ce tayi mashi gaba dayansu ba wacce ya aura dan yana sonta sai dan bin umarnin mahaifiyar sa matarsa ta farko itace me da namiji sai mata biyu dayar matar kuma yayan ta biyu duk maza babban dansa befi shekara ashirin da biyar ba sunayen yayansa nafarko Muhammad aka sa sai na biyu kuma Ahmad na uku abubakar sai matan daya zainab dayar kuma fatima itace autar su sarki salahudden beda hayaniya kuma bayasonta bashida yawan yin magana dan zamu iya kiranshi ma da miskili dan inbega dama ba sai kayi mishi magana goma be baka amsa ba sai yagama jan aji sannan ze amsa maka daya ko biyu abun sai ya hadar masa ga miskilanci ga jinin mulki shiyasa kana ganin shi kasan ya cika sarkin dan baya magana biyu yana daya za a aiwatar masa da abun da yakeso yanzuma yana turakar sa shikade yana kwance saboda yana bukatar hutu matar shi ce me suna ABIDA ta shigo dakin ta same shi ahaka gefanshi ta zauna tana kallon shi sai can tace sarkina ya akayine meke faruwa ancemin yau baka fito ba kwata kwata ko bakajin dadine uhm mika mata hannu yayi sta ruqe sannan yamike zaune da kyar yace wlh ba abun da yake damuna kawai de jinake banason fita gashi jiya nayi wani mafarki da ya ban tsoro da maamaki yakarasa fada murya adan sanyaye rungumeshi tayi tace ayya sorry mafarki ai na gaskiya bane ka kwantar da hankalinka in Allah ya yarda ba abun da zesame ka yanzu katashi ka shirya kafita fada watakil mutane suna can suna jiranka kama ci abin kuwa ta tambaye shi tana kallonsa saboda ba adakin ta yake ba yau ba itace da girki ba shiyasa ta tambaye shi kai ya girgiza mata alamar a'a tace meyasa ko ba akawo maka bane yace ankawo min amma nace afita da shi banajin son cin komai tace habade ya za ayi kazauna haka tun safe kazauna da yunwa yanzu katashi intai makama kashiga kayi wanka kan kafito inje in karbo maka wani abun gun auntyn yara kishiyar ta kenan kuma amarya shiyasa yaran suke ce mata wanda Muhammad ne yasa akece mata aunty tun yana yaro sai kuma sunan ya bita ita kuma sai take cemata auntyn yara tana gama fada mishi haka ya yunqura da qyar yatashi ta tayashi cire kayan jikinshi tadakko mishi babban towel ya daura ta rakashi har bandakin sannan tafito ta fito masa da kayan dazesa da duk wani abu da tasan ze bukata sannan tafita dan hado mishi abun da zeci bata wani dadeba ta dawo hannuta dauke da tire da abubuwa da ta hado mishi da sallama tashigo amsa mata yayi tare da bata iznin shigowa lokacin da taahigo har ta kammal shiryawa yan daura rawanin sa ajiye qa tayi akan dan qaramin dinin din dake gaban wata chair acikin dakin sannan ta qaraso inda yake ta tayashi daurawa suka qarasa saida tabbatar komai is ok sannan suka koma ka kujerar da ta ajiye mishi abincin suka zauna zata bashi yace ya hutar da ita ai gatan sai yayi yawa tabarshi ya ci da kansa haka ta rabudashi yafara ci a tsanake tana zaune tana kallonsa har yagama sannan tattare gurin suka fito tare suna zuwa falo tayi mishi addu'a sannan yafita qofar wajen ita kuma tabi ta dayar qoafar da zata sada ta da na su sashen shikuma yana fito wa dogarai daketsaye agurin zaman jiran fito warsa yana fito suka fara zubewa qasa suna kwasar gaisuwa amma ba wanda yasamu damar aka amsa tashi gaisuwar dan ko hannu be daga musuba kawai gaba yayi sukuma suka mara mishi baya suna tafiya ana zubewa ana gaida sarki amma sarki ayau be da niyar amsa gaisuwa kowa suna dab da shiga fada saiga baba yayi saurin tsugunnawa agaban sa yana gaida shi da har ze wuce sai kuma yadaka ta ya zuba mishi ido sai kuma ya dauke bece komai ba ya wuce ganin haka yasa baba mikewa ya wuce yana tunanin shikuma haka yake ka gaida mutum amma saide yakalle ka yawu uhm to Allah ya kyautawa halinsa Allah yakawo musu sauyi cikin masarutar nan dan tana bukatar sauyi kwata bata da tsari kamar ba masarauta ba bega wani abu me amfani da akeyi acikin ta ba yashikadaide yake ta zancen sa azuci yana tafiya
Sarki na shiga kowa yashigo yana diban gaisuwa saide yanzu ba kamar dazuba yana daga wa wasu hannu harda wandanda ma yake cewa lfy kawai yayi shiru saida suka gama gaisawa da mutane 'ya'yan sa ma maza duk sunzo sun gaidashi bayan nan kuma yamike yabi ta kofar ciki inda ze sada shi da bagaren fulani tana yabi tare da dogare biyu suna zuwa bakin qafar shiga falon suka tsaya shikuma ya shiga ciki------

******************
*S.A.S SPECIAL HOSPITAL*
Tundaga bakin gate din Aka rubuta well com to The S.A.S SPECIAL HOSPITAL da manyan baki kana shiga zakaga Wani tafkeken building dogo sama da qasa ne gaban sa duka glasses ne tundaga saman har qasan filin wajen shimfide yake da inter luck gefe gefe kuma du fulawoyi ne ta ko ina masu kyau da daukar ido gurin abun burgewa yayi kyau iya kyau antsarashi sosai Kamar ba akasar nan yake ba tundaga waje kasan ba qaramin waje bane inba gaya maka akaiba ko kuma ka karanta baza ka taba cewa wajen asibiti bane saboda haduwara da yanayin da akayi ginin a tsare kana shiga ciki kuma ko ina tails ne kuma part part ne aciki bangaren tiater daban bangaren emergency bangare labor ,medicine,maternity, bari guda aka ware na kayayyakin aiki da ake ahigowa dasu daga qasar waje dan kayan asibitin ma ba na nan qasar bane kuma komai suna dashi kaifin wani yaqare an qara shigo da wasu inda za aduba mutum da inda zakaga likita da inda za a baka magani da dakin hutu idan angama dubaka da office office din likitoci harta nurses suma da nasu office din da bagaren meeting shima part dinshi daban harda masallacin mata da maza abun mamaki acan baya kuma harda kitchen inda ake girkawa patient da kuma masu aiki abunde a tsare gwanin burgewa kuma duk aciki saida nagana kalle kallen komai sake waje ba abin damar shiga cikin office ko dayaba can na hango Saleem zaune yake bayan gama wayarshi da dad kenan yazo yazauna kan kujerun da mutane ke zaune akai Ana layin shiga dan yau harma amfara yiwa wasu mutane kafin yazo layi yahau yana jiran azo kansa yana addu'a Allah yasa yasamu dan bayaso ya rasa aiki a wannan hospital din Yana zaune kwa yaji ankira sunan shi da addu'a abakin shi yashiga wow babba office ne ya hadu iya hadu kana shogowa zakai karo da wani irin table me haske ido sai two chairs da bako ze zauna gefe kuma normal kujerar zama ce tree seater gaban ta da dan qaramin teble kansa kuma da roses a tsakiya daga cen baya kuma wani madedecin frige kan table din mamallakin me office din kuma sestem ce sai telephone din office din gefe kuma wayarsa ce ta amfani gida sai gaban table din da aje wani dan abun me kyau ajiki an rubuta DR.SHETTIMA JAFAR ASSISTANT DIRECTOR office din de gwanin sha'awa bawani tarkace aciki amma yayi kyau yana kan kujerarsa yana jujjuyawa yana dan duduba wani files saleem ne da yashigo da sallama yasashi dago wa tare da amsawa saida nadan zabura saboda kallonsa masha Allah kyakkyawa ne ne sosai tundaga kana gashin kansa nafara kallonsa baya tara suma kansa da dan gashi amma kadan sai girar sa tana da dan cika kuma yana da manyan idanawa farare tas sai siririn hanci da yakara mishi kyau bakinshi yana da dan girma amma ba sosai ba hakoransa farare ajere sai kwantacci yar qasunmba da take zagaye da fuskar shi bakaramin kyau taimishiba dan ba qaramar gyara take shaba ana kashe mata kudi sosai saide shi ba fari bane kuma ba baki bane wata irin kalace dashi me kyau yana da faffadan qirji amma beda jiki kuma bazakace mishi siriri ba duk da ba atsaye yake ba amma baza mu kirashi da dogo ba kuma bazamuce gajereba dede yake komai de yayi 100% saleem ne yace morning sir dr shettima yace morning too daga nan kuma duk sukai shiru sai saleem ya mika mishi file dinshi karba yayi yaduba yagani yayi mishi signing yace good result irinku ake nema yana fadar haka yaciro wata takarda yamika mishi shima yayi signing sannan yamayar mishi saida yagama komai sannan yabashi wasu takaddun shikuma ya debi wanda ake bukata sannan yayi mishi tambayoyi akan yanda ake tiater shikuma yana bashi amsa qara jinjina kwazon saurayin yayi da alama ba ayi wahalar kudin makaran taba yasan me yake sai yaji ya burge shi bayan sungama ne yace mishi angama da shi ranar Monday ya dawo zasu fara practice tsawo one month anga komai dede an tabbatar da kware warsu kafin su fara aiki kamar sauran jinjina kai saleem yayi tare da godiya cike da farin ciki yayi mishi sallama sannan yafito yanajin ransa fari tass sai yanzu yasamu kqanciyar hankali kullum yana hanyar zuwa gurin nan saide yau Allah yayi yasamu yana fita be tsaya ko ina ba sai napep da ya hau ya nufi gida ya matsu yaje gida yabawa su mama labari yasan zasuji dadi haka yana ta tunani yanajin dadi har ya qaraso gida besan ma yabawa me napep din dari biyar ba da yayi mishi magan ya tsaya ya karbi canjin saikawai yace ya bar masa yaje kawai be jira amsar sa ba ya wuce cikin gida har zeshiga sai kuma ya tsaya wani tunani ya fado masa kawai sai ya canza yanayin sa daga farin ciki zuwa bakin ciki sannan ya shiga yana shiga kuwa yagan su zaune afalo dukan su mama na kallon labarai ita kuma Azeema tana duba wani littafinta na makaranta sallamar da yayi suka amsa gaba dayan su yana shigo wa ya samu guri yazauna kusa da Azeema yace mama barka da gida tace yauwa ya hanya yace hanya Alahamdulillah Azeema ce tace yaya yana ganka haka yauma ba adace ba ko kai yagirgiza mata alamar eh mama tace daman nasani tunda naga yanayin ka nasan yaumade kamar kullum ne ta qarasa fada fuskarta cike da damuwa sai kuma yaji dama be mata haka ba kawai sai ya fashe da dariya yace albishirin ku dukan su da mamaki suke kallon sa mutumin da ya shigo da damuwa afuskar shi amma wai shine kuma yanzu yake dariya basuce dashi komai ba suka hada baki gurin cewa goro yace fari ko ja suka ce fari yace to yaude qarshen tika tiki tik yaude Allah ya taimake ni nagama wahala andauke ni ranar Monday ma zamu fara zuwa in Allah yakai mu cike da murna har suna qara hada baki gurin cewa da gaske yace wlh dagske mama tace kai Alahamdulillah Alahamdulillah Alahamdulillah ta daga hannu sama tana addu'a Azeema kwa wani tsalle ta buga daga inda take ta rungume shi tana cewa amma yaya shine zaka wani zo ka hade fuska duk kasa jikin mu yayi sanyi rabata yayi da jikinshi sannan yace so nake nayi muku surprise ne tace aikwa ka mana inataya ka murna Allah ya taimake ka mama ce ta dora dacewa Allah nagode ma tafada tana kallonshi tace gaskiya naji dadi sosai ALLAH yasa kafara asa'a Allah ya tainakeka yace Amin salati sukayi ga annabi sanna mama ta dora musu da addu'a saida sukayi addu'a sosai sannan ta dora dayi musu nasiha gaba dayan su nasihar kwa ta shige su bayan nan kuma ya shiga yi musu bayanin yanda sukayi da dad yagaya musu komai nanma ba qaramin dadi sukaji ba yande jiran kirashi kawai suke jira atare suka kasance ba wanda yatashi suna zaune suna ta hira harda ta mahaifinsu basu suka tashi daga wajenba sai da aka kira sallar magrib sannan kowa ya tashi saleem ya wuce masallaci mama ta tafi dakinta itama dan gabatar da tata Azeema ma tashi tayi ta tafi nata dakin ta tunani gobe da wuri zataje gidan su bestyn ta tayi mata albishir samun aikin yayan nasu har ta matsu goben tayi kamar ta jawota haka take ji.......


*AMEESHA*
tun kiran asubar fari ta farka dan ita ce ma ta tashi dadda daga bacci dadda na tashi tayi mamaki ganin wai Ameesha ce ta tasheta daga bacci yau matar da kullum sai tayi mata da gaske take tashi tayi sallah wataran ma sai gari yafara haske takeyi amma yau itace ta rigata tashi ikon Allah Sai kallo amma saboda yanzu ta tashi daga bacci ba ta da bakin da zata iya yimata magana dan haka kawai mike wa tayi suka fito tare ita tafara shiga bandaki ta fito itama dadda ta shiga tafito sukayi alwala tare suka koma suka fara yin nafila sannan suka jira aka shiga sallah amasalatai sannan suma sukayi tasu suna idarwa sukayi azkar sannan suka tashi Ameesha tace dadda kinsan yaza ayi tace sai kinfada uwata dariya tayi tace kai dadda daga magana tace nima ai amsa nabaki tace to dadda yanda zamu fi saurin gama komai da wuri yanzu ni zanje in dora mana girki ke kuma ki fara hada mana kayan dan ina gamawa zan tafi gidan su Azeema muyi sallama da ita sai la 'asar zan dawo dadda kawai zuba mata ido tayi sai da tagama sannan tace to kin gama bani umarnin uwata to bazan yi yanda kike so din ba da ke kikeyi min girkin sai yanzu da bukatar ki ta taso ko tace to shikenan karkiyi din danma nace zan taimaka miki wlh sai inta fiyata in rabu dake kuma idan nadawo har yaya bossay yazo baki gama ba to binshi zanyi mubarki ke kadai dan bazan qara kwanan gidan nan ba dadda de bata kulata ba tai ficewar ta dan taga shirmen ta karuwa yake yi kullum bata tsoron gaya mata duk abun da yazo bakinta amma sai ta fita waje kuma bakin yake mutuwa daman ance ido waka rena yace wanda na saba gani tana ganin dadda ta fita kawai sai ta tashi ta dakko bakkon kayan ta ta zazzage ta tafara ware kayan ta da take so tana ware kayan da bata so kayan da ta dauka basufi kala shida ba sai wani sabon hijab dinta da dadda ta siya mata bata wani sashi da yawa ba tsaf ta hada duk wani abu da tasan nata ne kuma zata bukace shi sauran kuma takulle su daban ta ajiye agefe ta ware kayan da zata sa idan bossay yazo masu dan kyau dan kar yan gidan su raina mata hankali dan tasan wasu 'yan gidan masu kudin basu da mutunci saida ta tabbatar kamai is ready ko yanzu yazo sutafi bata da matsala tana gamawa tafito tace dadda dan Allah indan dora ruwan wanka kafin ki dora abun da zaki dafa hararar ta tayi tace ke bafa nason shirme me yake damunkine to wlh kishi ga hankalin ki naga alamar kan ki rawa yake to wlh ki kiyayeni ki fita da ga idona kafin ranki yabaci baki ta turo mata gaba sannan ta koma daki ta qara fito da mayafi a hannun ta dadda tabita da kallo tace gidan ubanwa zaki da farar safiyar nan tace yanzu zan dawo gurin aunty lami zani muyi sallama tana kaiwa nan ta kwasa aguje tafita dan kar dadda ta hanata fita dadda taringa kwala mata kira amma taki tsayawa ta tashi tabiyo ta amma kafin ta fito har ta bace daga qofar gidan komawa tayi ta dakko mayafi itama tabi bayanta tana mita ai wlh bazan barki kishiga gidan nan na fada tana tafiya kamar zata tashi sama har ta qaraso bakin gate din gidan na zuwa ta bubbuga me gadi ya bude ya leko kafin yayi magana ta rigashi tace shiga ciki ka fito min da yarinyar da ta shigo gidan yanzu nan da mamaki baba me gadi yake tambayar ta wace yarinyar shi ba yarinyar da tashigo yanzu tace kamar ya ni zaka renawa hankali yace baba wlh gaskiya nake gaya miki bata zoba tace Ameesha fa nake nufi yace ai nagane wacce kike nema amma wlh bata zo ba da mamaki dadda tace to yarinyar nan ina tayi tace nan zatazo amma shine tayi wani wajen zata zo tasameni wlh sai nayi maganin ta yau zatasan ta rainani dani take zance tana kaiwa nan tayi kwafa tayi gaba tana bambamin bala'i tana wucewa Ameesha dake labe gefen wani gida ta fito tana ta dariya harda kyakyatawa tana bin bayan dadda da gwalo tace ai nasan daman sai kin biyoni shiyasa na buya idan kin koma nashi gidan nasande yanzu baza ki taba dawowa ba dole kijira sai lokacin da naga damar dawowa tana magana ta kwankwasa gidan baba me gadi yazata dadda ce takara bugawa ya bude rai abace yace nafa gaya miki wlh yarinyar nan bat....tsayawa yayi da maganar da yakeyi ganin wacce ake neman ce tazo yace ke ina kika je yanzu kakarki tazo ne manki fa dariya ta kuma yi tace rabu da ita baba ai ina kallonku buya nayi yace meyasa to tace wai ita adole bazan qara zuwa gidan nan ba gashi kuma yau zamubar unguwar nan kuma ina so muyi sallama da aunty lami dama sauran 'yan gidan zaro ido yayi yace tashi kuma ina zaku koma tace ni wlh bansan sunan unguwar da zamu koma ba amma de yau zamu tashi yace Allah sarki shikenan yanzu mundena ganinki tace aa wataran idan bossay zezo zan biyo sa sa mugaisa yace to shikenan Allah yasa da gaske kike yafada yana matsa mata tashiga cikin gidan ta qofar brander kitchen tabi tana shiga bata ga kowaba sai ta tsaya tana rarraba ido tana tunanin to kode aunty lamin bata zoba tana tunani kode ta juya ta koma gida kar taje akamata a kitchen din har tajuya danufin fita sai taji anyi gyran murya kasa juyowa tayi saboda bata san dawa zatayi tozali ba har yanzu tana tsaye ita bata tafiba ita bata juyo ba lami dake tsaye abayan ta tana dariya qasa qasa tasan tsorone ya hanata juyowa dan haka sai tasake gyara murya ta kwaikwayi irin muryar matar gidan tace keee da yar tsawa hantar cikin Ameesha ce ta kada tana tunanin shikenan kashinta ya bushe ankamata watakil ma ace mata barauniya tazo sata zuciyar tace ta bata cewa wlh kar ta juya kawai ta kwasa aguje tabar gidan tasande ai baza su taba biyo ta har gida ba inma sunzo dadda zatai maganinsu tana gama ayyana hakan kuwa ta daga qafa zata gudun kawai taji an ruqeta ai kwa saura kadan tasaki fitsari awajen tsabar tsoron da tashiga..........


More comment more typing.....🖋
No comment no typing
Likes and share

Flow my wattpad account
&Arewa books.com
❤xeemat....love❤
[2/27, 11:22 PM] ~~~~writer~~~~:   💅SARKI SAMEER....💅
              by❤xeemat....love❤

               🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

Episode17

Tana gama ayyana hakan kuwa ta daga qafa zata gudun kawai taji an ruqeta saura kadan tasaki futsari tsabar tsoron da ta shiga jin anyi shiru ba taji saukar duka ba kuma ba ayi mara komai ba  yasata juyo wa ahankali ganin ko waye tana dagowa kwa idon ta ya sauka akan lami wata mahaukaciyar ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa kai aunty lami wai daman kece duk kikasa nabi na tsora ta dan wlh kinban tsoro sosai lami dake faman boye dariyar ta sai yanzu tasamu damar yi tace ai nasani shiyasa nayi miki haka tace aikwa kin dau alhakina wlh kinsande yanda nake tsoron mu hadu da masu gidan amma kikai min haka harda boye Murya yanda zanfi tsorata ko dariya ta qara yi tace wlh tsoranki yayi yawa tace ai tsoro wajibi ne saida tagama nutsuwa sannan  tace wai ke sai yau kika ga damar dawowa duk kinbar ni da aiki nikade yanzu komai na gidan nan ni nakeyi katseta tayi da cewa Allah sarki har na tausaya miki Allah yakawo miki dauki danni nan dakike ganina ma daga yau baza ki qara ganin qafata agidan nan ba yanzu ma gurinki nazo muyi sallama saboda barin unguwar nan zamuyi tashi zamuyi yau yau dinnan   lami hannu tadaga sama ta dora akai tace nashiga aljanna nayi tsudum tsudum naqi fitowa kuma bazan fito ba 😂yanzu dan Allah dagaske kike ko da wasa tace wlh da gaske nake tace yanzu bazan qara ganin ki ba ko zakirin ga kawo mana ziyara tace a'a wlh bazan zo ba saide ke kizo tace inda zaku kona yana da nisane da zakice bazaki zo ba ba amana wallahi tace wlh ba nisa mukai ba tace wacce unguwar zaku koma Ameesha tace mata nima bansan sunan unguwar  ba da mamaki lami tackalleta tace kamar ya baki sani ba wai tsaya ma me yafaru zaku tashi matsala kuka samune da gidan da kuke zaune ko wani abunne yafaru da har takai ku ga tashi wlh banji dadi ba Ameesha tace wlh lafiya qalau gidan su bossay zamu koma shida maman sane suka ce mukoma can da zama baki tasaki tana kallon ta saida tagama sannan tace ke dan Allah amma wane bossayn kike nufi tace bossay nawa kika sani tace daya ita kuma ta daga mata kai alamar tabbatar wa tafa hannu tayi tace amma na tayaki murna har yanzu nakasa yarda wai gidan su bossay zaku koma da zama amma fa na taya ki murna dan wlh kakar ki ta yanke saka Ameesha ta bude baki zatai magana kenan suka ji andaka musu wata mahaukaciyar tsawa da ta karade gidan gaba daya saboda safiya ce sai da gidan ya bada sauti
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment