Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

nagode sosai Allah yayi maka albarka kaima Allah yabiya maka bukatunka na alkhairi yanda ka taimakeni kaima Allah ya taimake ka yaron kirki yaron mutumin da yakira da yaro yace Ameen baba nizan tafi ka kula sosai sai anjima yace to Allah yakaimu ina qara godiya yace ba komai baba yana gama fadar haka yafice daga gurin shikuma baba yakoma ya zauna yana dan jin sanyi aranshi duk dade besan zuwa tsawon lokacin da ze daka ba kafin ya aika gidashi a sanar da iyalansa amma duk dahaka yadanji dadi yasande dole zasuji halin dayake ciki bakamar idan ba gaya musuba har mutuwarsa ta riske shi tunda ance ya zama bawan gidan yasan baze taba fitaba saide a fita da gawarshi amma yanzu Allahamdulillah ko ba komai yasan bazasu shiga damuwa ba sosai akan basu san inda yakeba gwara su sani inyaso ko aboye sakawo mishi  ziyara wataran yagansu suganshi shikadai hakan ba qaramin dadi yaji ba yana ta tunane tunanen shi sai yaji damuwar sa ta dan ragu.......
Wata datijuwa  da bazata wuce shekaru sittin da biyar ba nagani zaune kan daya daga cikin royal chairs din falon red and golding falone me girma sosai an qawatashi da sosai kamar ba a Nigeria yake ba dan  hadu iya haduwa tana zaune kan two-seater masu kyan gaske irin na gidan sarauta tayi dai dai ana wanke mata kafa  daya dayar kuma ana daddanna mata gabanta kuma cike da fruits an yanyanka mata tana sha hankalinta kwance kana ganin ta kasan tana jin dadin yanayin, gimbiya *MARYAMA* kenan tsohuwa meji da ga mulki  kyau da gayu da ado dan ita bata yarda ta tsufa ba tanaji da kanta sosai ba fara bace kuma ba baqa bace amma saboda tsabar hutu yazauna mata ajiki sai takasance tana da dan haske fatar tana da kyau sosai sai sheqe take Wani
Wani bafade ne yashigo ciki da sallama bayan anbashi izinin shigowa yaqaraso ciki kansa aqasa yace ranki yadade gimbiyar mu  me ran qarfe kici zamanin ki kici na yayan ki kici kici na jikokin ki kici tattaba kunan ki kici na um hum um din ki matar sarki uwar sarki kuma kakar sarki jinjina gareki duk wannan uban kirarin da yake mata ko kallon inda yake batai ba sai da taji yagama sannan batare da ta kalle saba tace inajin ka junaidu meke tafe dakai yana durqushe aganba ta shima cike da ladabi kai aqasa yace daman sarki ne yace inzo ingaya miki cewa ansamu sabon bawa amma yanzu haka munkai shi dakin qasa zeyi kwana uku daga nan sai afito dashi  saivakawo shi gurin ki sai kibashi aikin da ya dace dashi saida tayi jimm sannan tace to amma wane irine mutum ne yace ranki yadade tsoho ne tace to zaka iya tafiya yatashi  ya fita yana cewa nabarki lafiya yana fita ta maida kanta ta kwantar asaman kujerar  tana dan tunane tunane bata wani dade ba hannu ta daga wa bayin dake gabanta suna aikin gaban su alamun ya isa haka amma basu lura saboda qasa suke kallo data ga haka sai tadan yi gyaran murya atare suka dago suna kallon ta sai tasake daga musu hannu dasuka ga haka sai suka sakar mata qafafun sannan tadan jasu ahankali cike da izza da kasaita ta mike ta nufi wata kwana suku ma suka tashi suka fita falmata ce tafara cewa Ramatu hmm wai yau munga takan mu Allah de yatai make mu bamu yi wani kuskuren ba da mun sha masifa dan naga yau yan muskilancinne akan matar nan kuma akusa take shiyasa ma bata son  yin magana dan idan tayi baza tafadi abu me dadi ba itama Ramatu tace uhm nima de abun da na lura kenan daman Allah Allah nake muyi mugama ta sallame mu tafi kar abun ya rutsa damu tace aikam de Allah sarki wlh har na tausayawa wannan tsohon da akace ansamo ze zama bawa shiko ko wane irin tsautsayi ne yasa ya fada hannu wadannan azaluman muta nan gashi ance tsoho tabb dayar ce tace wlh nima da naji na tausaya mishi sosai ahaka de suke ta suru tansu har suka bar part din gaba daya suka nufi nasu bangaren........................

Abangaran gimbiya mama Fulani tana shiga corridor din ta nufi wata qofa me kyau tashiga batare da ta qwanqwasa ba saida tashiga ciki sannan tayi sallama aciki amma duk da haka ta dan fito wani dattijo ne dake zaune kan bed da wani littafi ahannun sa yana dubawa bansan meye ba daga gani de kamar ma album ne na hotuna ajiye littafin yayi yana kallon ta batare da ya amsa mata sallamar ba saida tazauna akusa dashi sanan tace barka da hutawa yace barkan kide me yasame kine naga kamar ranki a bace yake tace ba komai fa kawai jikina ne baya min dadi narasa dalili bata bari ya bata saba taci gaba da cewa  yauwa yanzu ake gaya min wai ansamu sabon bawa ze fara aiki nan da kwana uku yayi jim sannan yace shiyazo neman aikin da kanshi ko siyansa kukayi ko kuma halin naku kuka yi niban san a masarautar da ake yin haka ba yanzu fa bada bane ace dole sai kasa mutum yazama bawanka ta qarfi da yaji yakama ta kucanza tsari a masarautar nan wlh kuma meyasa Zak....wani uban kallon da ta zuba mishine yasashi hadiye maganar da yake sai kuma yayi qasa da murya yace kiyi hakuri Allah ya huci zuciyar ki nayi shiru wlh kuma ni daman bada wata manufa na fadi hakan ba. ceke da masifa sai kace dan cikin ta kamar ba mijinta ba kuma sarki me murabus ba haka take mai maifada tace wai ban hanaka samana baki akan tsarin masarautar nan ba ina ruwanka damu ne ko dan kaga nace mishi duk abun da yayi a masarautar nan yasanar dani nikuma inzo ingaya maka shine zaka fara yimana shishshigi to daga yau ba abun da zaka kara ji daga cikin abun da yake wakana game da masarautar mu yace nacefa kiyi hakuri ko nadena daga yau duk abun da za kuyi kuje kwitayi yafada yana gyara kwanciyar shi tare da juya mata baya itama bata qara ce mishi komai ba ta tashi fuuuu tashige bathroom shikuma yabita da kallo yafara tunanin wai me yasa yazama haka ace matar shi ce zata na mishi fada haka kamar ma shine qasa da ita ba itace qasa dashiba shi abun yana bashi mammaki ganin yakasa daukan mataki akai saide duk abun da tace shi za ayi to kode tayi mishi yana cikin tunanin yaji kansahi yana mishi wani irin juyi kamar ze bar jikinshi haka yasa hannu biyu yana dafe kan yana ambaton duk addu'ar datazo bakinshi  daman yasaba duk lokacin da irin haka tafaru yafara tunanin faruwar irin wadan nan matsalolin domin yasamo solution to atake a lokacin yake jin irin wannan matsanan cin ciwon kan daga nan kuma bacci ya daukeshi idan yatashi kuma ya manta duk abun da yafaru to yanzu ma hakance tafaru yana cikin addu'o in kwa bacci ya dauke shi bayan kwanciyar shi da befi minti uku ba ita kuma tafito jikin ta sanye da rigar wanka tana fitowa ta tsaya tana binshi da wani shegen kallo sannan tasaki wani irin mumushi me cike da abubu wa masu wuyar fassarawa aranta kuma tace hmmm dani kake zancen kaci gaba kar kafasa   nima kuma bazan fasaba muzuba mugani shege kafasa ni da kai aga waye winner a fili kuma tace asha bacci lafiya ta wuce gaban dressing mirror tana shafe jikinta da mayuka da tura ruka saida taga ma tsaf sannan ta nufi wajen wardrobe tadakko wasu bakaken kaya tasaka tare da dakko wata baqar hula kallart ja tasaka sannan ta nufi wani waje ta bude labule sai ga wata yar qaramar qofa dan in ba agaya maka akai ba zaka rantsa babu komai awajen saida ta tsaya tayi wasu surutai sannan tasa hannu ta bude qofar tasa kai ta shiga nide tsoro ya hanani shiga bare indakko muku rahoto dan haka na tsaya awaje ina jiran fito warta saida ta dauki wajen thirty minutes sannan ta fito nagan ta sai faman zufa take tana goge zufar da hannun ta directe bathroom din ta kara koma wa amma bata dadeba tafi to taqara cire kayan jikin nata tasa wata atamfa yellow collar riga da zani ne sai ta dakko dan kwalinta ahannu bata daura ba ta dawo kan gadon tazaun agefen gadon kusa dashi  tana kallon mijin nata tana cewa kadena min taurin kai ka dena min shishshigi a lamura na sai mu zauna lafiya batare da ka wahala ba saida ta gama sannan ta kai hannu saman fuskar shi tashafasa tana shafawa kwa yabude idon sa sai tasakar masa murmushi  shima murmushin ya mayar mata dashi tace ya da bacci yanzu kasande ba kyau bacci dab da magariba ko yace eh nima wlh bansan ya akai na fara baccin ba kinsman bacci barawo ne shi yazo ya sace ni yar qaramar dariya tayi tace lalle yayi qoqari da ya sace sarki guda gaskiya yakama ta a hukun tashi dan yayi babba laifi shima dariyar yayi yace baccin za a hukunta ko tace eh mana yace to ayi saurin inkuma ya hada da me hukuncin shima yasace shi kinga shikenan tafaru ta qare kenan batace komai sai dariya datayi wace iyakacin ta baki dan bata kai zuci ba shima ita yayi yana tashi zaune haka de suka ci gaba da hirar su kamar basu san wani abuba wai shi tsufa ba kiran sallar da akeyine ya katse musu hirar tasu yatashi ya nufi bandaki yayo alwalla ya fito yace to kema kije kiyi kafin na dawo muci gaba hirar mu ko tace to shikuma yafita zuwa masallaci yana fita tabi lafiyar gado tai kwanciyar ta alamun bazatai  sallar ba kenan.......... har yaje yayi sallar yadawo bata tashi ba amma yana tambayar ta hartayi sai tace mishi eh tayi be yarda ba amma bashi da damar yin magana saboda sanin halinta dan yasan bata son yin sallah kwatakwata bata dame taba bece mata komai ba har zan zauna sai kuma yafasa yace mata zanje palace (fada) tace kayi me fa yace zan dan duba wani abune tace wane abu ne shi ko bashida suna yace to zanyi maganane da sarki akan batun sabon bawan da kikace ansamu inji aikin da za abashi tace bana bukatar zuwan naka nizan bashi aiki dakaina kazauna kawai anjima ni zanje mutattauna dashi basai kaje ba Allah sarki bawan Allah sarki me murabus  haka jiki babu kwari yace da ita to sannan yasamu gefanta yazaun tare da zabga uban tagumi da ta lura da hakan tasan yanzu ze fara tunanin nashi da yasaba sai kawai tace yallabai be dago ba yace mata uhm tace waini kam ya batun waziri ne da matar sa tadawo ne yace mata a'a yace min wai iyayen ta sunce bazata dawo ba wai har sai an amince da qudirin su sannan zata dawo tace lalle zata mutu a gida kenan ko kuma ta auri wani yace hakan ma baza ta faruba zade ayi tunani akai za asamu masalaha tace to Allah yasa yace Ameen.......

*******************
*AMEESHA*
bayan ta maida hankalinta gareshi yace yauwa kinsan me nakeso dake tace a a inaso kidawo gidan mu dazama zan fadawa ammi na halin dakike ciki nasan zata yarda ni kuma nadau nayin karatunki daga nan harkiga karshen biro da takarda kuma ba ruwanki da wani aiki muna da masu aiki yanzu zankai ki wajen daddar ki sai ki gaya mata nasan itama zataji dadin hakan ko ya kikace saida tayi shiru na dan wajen wani lokacin har saida yadan taba ta sannan tace sauke ajiyar zuciya tace bawai naqi taimakonka ba amma bazan iya zuwa gidan kuba da zama saide idan aiki za adauke ni inyi abiya ni danni nafiso innemi abu da gumina saboda gudun wulakanci ko gori shiya sa kaga ina jure duk wani cin da suke min watarana sai labari nafiso inyi karatu da kudin da na nema halak malak dina kayi hakuri idan bakaji dadin rejecting tayin dakai min kuma koda ina so ma dadda bazata taba barina in koma gidan Ku ba tafiso taganni akusa da ita bata son abun da zesa muyi nisa da juna nima kuma banaso inyi nisa da ita dan Allah ka fahimce ni kaji tagama fadar haka tare da kallon fuskar sa da taga yacan za gaba daya tace kayi hakuri dan Allah kace wani abu ba wai kayi min shiru ba kana kallona duk da haka be cemata komai ba saida yaga dama dan kansa sannan yace ok nagode zaki iya tafiya duk laifina ne bansan haka kike ba amma ba komai wai harni zakicewa zan miki gori zan wulakan taki ko da sauri tace dan Allah ka dena fadar haka wlh ni bada wata manufa ba nafada na fadi kawai abun da yake raina ne bawai kai nake nufi zakayi min haka ba yace ok Ammi na kike nufi kenan ko kuma 'yan gidan mu ko nan ma girgiza kai tayi tana dan dafe kanta da hannun ta alamar tarasa tayaza tai mishi bayani ya gane tace wlh duk bahaka nake nufi ba haba dan Allah me yasa ka kasa fahimta ta yace inkina so in fahimce ki shine ki amin ce da magana ta shiru tayi tace to shikenan naji inde ta bangarena nayarda saide kuma babbar matsalar itace dadda wannan kuma saide kaje da kanka ka shawo kanta ta amince dan kasan inde bata yarda ba bani da ikon zuwa dole saida umarnin ta yace kar kidamu da ita nidamn amincewar ki nake nema yanzu muje tare sai in tambaye ta din ko tace to muje Allah yasa adace yace Ameen yana fita daga ciki ya koma mazaunin driver yazauna yajuyo yana kallon ta yace to ai sai kidawo gaba ko tace to itama ta fito ta koma gaba ta zaune tare da rufo qofar shikuma yayi wa motar key suka nufi gidan kowa da abun da yake sakawa aranshi daman yanasane yayi mata haka yasan idan bahaka yayi mataba bazata amince ba ita kuma anata bangaren tayi mishi hakane dan ta wanke kanta daga gurin shi karya yi fushi da ita saboda tasan dadda bazata taba yarda ba shiyasa tace mishi ta amince tayanda in dadda tace mishi bata yarda ba bazega laifin ta ba saide yaga na dadda har suka qarasa gaban gidan ba wanda yasake cewa komai yayi parking din motar sannan suka fita gaba daya suka shiga cikin motar suna shiga da sallama abakinsu dadda dake kokarin shiga daki ta tsa ya tare da amsa sallamar tasu tana kallon su sannan tace a a bossay kaine da kanka har cikin gidan mu yace wlh dadda nine tace sannu da zuwa bari na dakko maka tabarma ko yace to yana ta zulumin tayanda ze gaya mata dan sai da yazo sai kuma yaga tayi mishi kwarjin hartafito be dena tunanin ba saida tace to zauna kaji yace to sannu da kokari saida yazauna yacewa Ameesha itama ta zauna dadda kuma ta jawo kujerar zaman tsakar gida ta zauna tace ina sauraron ku danna san da magana abakin ku sai kuma suka shiga kallon kallo kowa ya kasa magana harshi me cika bakin yakasa fadar komai saima cewa da yayi Ameesha kifada mata mana tace kafada mata de bakai kace zaka fada mata ba wlh nima bazan iya ba dadda de ta zuba musu ido tana jiran jin tabakin su har yanzu ba wanda yace komai sai tace inbaza kufada ba intashi intafi kunyi shiru kuna sa insa ni ina da abunyi inku baku da shi da sauri yace yi hakuri dadda daman wai....in wai in hmm daman ina son Ameesha tadawo ummm ...........
yakasa fada sai inda inda yake nima kuma nagaji da jira dan haka nake cewa sai gobe idan Allah yakaimu maji yanda zasu qare muji zata amince ko baza ta Amince ba .......
********************
daga sabuwar marubuciyar ku🖋
by
❤xeemat.....love❤



Don't forget pls comment and share it

My WhatsApp number 08124226526
Pls banda kira
[2/21, 10:40 PM] ~~~~writer~~~~: 💅SARKI SAMEER....💅
by❤xeemat....love❤

Allah yajikan magabatan mu da suka riga mu gidan gaskiya muma intamu tazo Allah yasa mucika da imani Allah ya kyautata qarshen mu Allah kasa gaban mu tafi bayan mu kyau Ameen....
Bismilah...............
Episode11🖋

***********************
Dadda dataga abun nasu kamarma raina mata hankali suke ta buga tsaki cike da masifa tace kunga wlh bana son iskancin banza fa ya inataimuku magana amma kun tsaya kuna raina min hankali BOSSAY ne yayi saurin cewa dan Allah dadda kiyi hakuri kitsaya ki saurare mu wlh yanzu zan gaya miki tace to inaji fadi saida yadan sosa qeya tare da sunkuyar da kansa sannan yafara bayani a hankali yace daman dadda dan Allah wata alfarma nake nema awajen ki nasan ma zaki min ko daddar mu hararar wasa ta watsa masa tace ai bazan ma yiba din tafadi haka cikin wasa yar qaramar dariya yayi yace haba dadda ai nasan fade kike zama kiyi kodan wannan jikar taki guda daya tace kai ni ka isheni da surutu kafadi abun da yakawo ka ko intashi yace to daman alfarmar danake nema itace dan Allah kitaimaka kiban Ameesha ta koma gidan mu daza ma wajen Ammi na saboda yanayin halin da take ciki kinga acan ma zata fi samun damar karatu batare da tasha wahala ba ni dakaina zan dau nauyinta har ta kammala makarantar ta gaba daya zan tsaya kuma nasan Ammi na zata riqeta kamar yar cikin ta har zuwa lokacin da Allah ze fito mata da miji tayi aure sannan zata bar gidan mu dan Allah dadda kar kice a'a dan Allah ki amince dani wlh zan kula miki da ita fiye da yarda kike kula da ita in Allah ya yarda baza ki taba da nasani ba akan ruqon da zakiban bazan taba cutar da ita ba kuma bazata ta ba neman abu ta rasa ba matuqar ina raye wannan alakawari na daukar wa kaina ni wlh ko kullumma kike so kiringa ganinta zan ringa kawo miki ita kuna gaisawa kinji daddar mu har waya zan siya miki kuringa gaisawa duk sanda kikeso namiki alkawari yana fadar haka sai yayi shiru yana jiran me zatace har wani tsawon lokaci amma beji tace komai ba hakanne yasashi dagowa yana kallon ta amma ga mamakinshi me ze gani kamar hawaye a idon dadda da sauri yace subhanallahi dadda lafiya me yafaru ko na fadi wani abun da ya bata miki rai har kike kuka haka amma still bace da shi komai ba sai ya maida dubansa ga Ameesha da tayi shiru kamar bata san me suke daman tasan hakan zata faru tasan halin abarta shiyasa tace mishi ta amince yanzu yasan yanda zeyi da ita tunda shi ya tsokanota besan halin ta bane da beyi gigin tambayarta wannan babbbar alafarmar dan tasan ko aure ta tashi yi wani ikon Allah ne kawai ze rabasu da ita shi ya katse mata tunaninta da cewa Ameesha kinga fa dadda kuka take bansan me akai mata ba tana dan boye dariyar da takeson kwace mata ganin duk yawani bi yatada hankalinsa amma saita danne ta wani maze tace to nimade abun yaban mammaki ganin hakan yakaqara juyawa gurin dadda yace dadda Dan Allah idan ni nabata miki rai har kike kuka to naroqeki dan Allah kiyi hakuri saida dadda tadan sace kallon sa ta gefen ido taga yanda duk yabi yadamu sai kuma tadan ji tausayin sa amma hakan fa bazesa ta taba amincewa da qudirin sa ba dan abune wanda bazai taba yiyuwa Ameesha ce tace dadda wai meye hakanne kiyi mana magana mana amma kintsaya kinayi mana kuka sai kace wata qaramar yarinya dadda cikin kukan da take ti kuma bata dena ba tace au hakama zakice hakafa yace ze rabani dake kin amince kenan kinyarda kibishi kibarni ni kadai ko to shikenan tafada tana qoqarin tashi tabar wajen wai ita adole tayi fushi dasu shiko Bossay abun yabashi mamaki dan haka kawai yabisu da ido yana kallon ikon Allah Ameesha ce tace dan Allah dadda kitsaya mugama maganar mana sai lokacin Bossay yace yanzu dadda duk wannan bayanin danai miki abanza baki yarda dani ba kenan tace eh ban yarda dakai dinba sai me ko zakai min wani abunne wlh tun muna sheda juna kafita daga idon in rufe in kuma kaqi zan nuna maka asalin kalata bakasanni ba ko to wlh daga yauma kar inkara ganin ka aqofar gidanan ma bare har kashogo min gida karabu da jikata bakai ba ita kar ka sake yi mata magan ko hanya ka ganta baruwan ka da ita kuma katashi kabar min gida dan bana son ganinka wai harda wani cewa saboda halin da take ciki wane irin hali take ciki ko kaga tarasa ci ko sha ko kaganta tana bara ahanya ko kuma talla kaga tanayi ko gayamin wani mawuya cin halin da kaga tashiga kabar min abata ahaka a yanda ka ganta ba ason tai makon naka inde ta haka zaka tai maketa idan taimakon naka na gaskiya ne kai mata mana tana nan duk abun da take buka ai zaka iya yimata bade kudi bane ko dolle sai tadawo gidan ku kanaso kenan ka lalata min yarinya ko kuma kasiyar da ita to ta Allah bata ka ba jikata tafi qarfinka kurwarta nesa dakai saide kaje kasamo wata amma bada gudan jinin Hadizatu ba tafada tana ta faman hararar sa kamar idonta ze fado qasa Ameesha tace haba dadda wai wane irin maganganu kikeyi ne haka shifa taimako na yace zeyi bawai cutar dani ba ke meyasa baki da yarda ne arayuwar ka ki rage wannan halin naki dan Allah dan wlh ba inda ze kaiki saide ma yakaiki yabaro ki kizo kina da nasani kinsande kuma danasani qeyace kije kici gaba kar kifasa tana gama fadar haka tajuya gurin Bossay da yayi mutuwar tsaye tunda yake arayuwar sa ba ataba cimasa mutunci ba irin nayau daga taimako kuma sai reshe yajuye da mujiya wannan wace iriyar tsohuwa ce da bata da fahimta kwata kwata jifa irin abubuwan datake gaya mishi duk dan yace ze taimaki jikarta tabbb babbar magana yau ya kawo kanshi yajawa kanshi masifa abanza a wofi da yasan haka take wlh da be zoba gwara yabar Ameeahan ta tambaya da kanta inyaso duk yanda sukai tagaya mishi da duk haka bata faru ba wata boyayyiyar ajiyar zuciya ya sauke sannan cikin sanyin murya da kanajin kasan dan dole aka fito da zance yace Nina jawa kaina ni na shigo gonarki da har kike jifana da irin wadannan munanan maganganun kiyi amma kiyi hakuri bansan tahaka zakiyiwa magana ta fassara ba da banzo ba yakarasa fada ranshi ba qaramin baci yayi ba da idonsa har ya canza kala daga fari zuwa jaja jaja yana kaiwa nan yajuya daniyar fita daga gidan sai yaji anruqe mishi hannu gam tsayawa yayi batare da yajuyo ba ahankali ta taka ta koma ta gaban sa suna fuskantar juna ta qura masa ido shima ita ya tsaya yana kallo ko
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment