Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kawai tare da zuro qafafun ta da niyar sauka daga kan gadon saide kuma abun da bata saniba shine qafafun ta baza su iya daukar taba dole saida taimakon wani aikwa tana takawa tasaki wata razananiyar qara tare da tafiya luuuuu zata fadi dan har tagama bayarwa tafadin saide bata kai ga faduwar ba dukan su sukayi kanta zasu taro ta saide shikadai ne yafisu zafin naman da yayi nasarar tarota shima kuma garin sauri be ankara ba yana tarota suka fada kan gadon atare tana rungume a kirjin sa haduwar qirjinsa da nata hakan ya haddasa musu wata irin mummunar faduwar gaba gabadayan su bawanda beyi mamakin jin irin wannan faduwar gaban ba wanda har kowa na iya jiyo bugawar ta dan uwansa saboda tsurewa da tayi ne yasa ta qara cukuikuye shi tare da kwantar da kanta a gefen fuskar sa batare da tasan me takeyi ba saboda ba a cikin hayyacin ta take ba..........,
[4/1, 10:45 PM] ~~~~writer~~~~: 💅SARKI SAMEER....💅
           by❤xeemat.....love❤

             🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

                🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
                             ﷽

                    Bismillah........ ✍
Episode 64-65

         """"""""""""""""""""""""""""""""""

Ganin tayi lamo ajikinsa sai abun yaqara bashi haushi janye fuskar shi yayi da ta dora kanta sannan yasa hannu biyu ze janyeta sai yaga ta qara riqeshi tsaki yayi tare da cewa useless girl ita kadai tajishi amma bawanda kuma hakan besa tasakeshi ba shettima mane yakai hannun sa da niyar yajanyeta ganin yanda tabi ta rurriqeshi  amma sai sam yadaga masa hannu alamar ya barta kar yataba dakatawa yayi sannan yace baby uhm tace mishi shi kuma sai yace mata  kitashi mana ko bazaki iyaba ahankali muryarta cike da shagwaba kamar zatayi kuka tace kainane yake juyamin idan natashi ze iya fashewa wayyo dadda ta taqarasa fada da dan qarfi sakamakon jin kannata yaqara sara mata hannu wanta tasa duka biyun  tariqe kan nata dan dagaske ciwo yake mata hankalin shettima ba qaramin tashi yaayi ba jin abun da take cewa bashi kadai bama har saleem yaji tausayin ta shettima mane akaro nabiyu yaqara kai hadubatapa ze riqe mata kan saide yanzu ma kamar dazun sam yadakatar dashi aqufale yake kallon sa sannan yace kanajin fa abun da take cewa kar azo wata babbar matsalar takara faruwa yakamata ka qara dubata fa da kyau wani irin kallo ya watsa masa da yasashi jan bakinshi yayi shiru dan yasan halin abokin nasa kamar yunwar cikin sa saboda haka yasan ma'anar kallon da yayi mishi hannu yadaga tare da nuna musu qofa alamar su fita subashi guri saleem ne yafara fita amma shettima sai ya tsaya yaqi ko motsawa kawai kallon su yake dan shi hakan da sukayi beyi mashi dadi ba ya matsu yaga yasake ta sunraba jikin su hakanna yake jin zuciyarsa nayi masa quna da be san dalilin jin hakanba (Allah sarki to kode kishi kakeyi ne bamusani ba)  sam ne yaqara kollon sa irin kallon baka ji me nace bane dauke kansa yayi daga garesa duk da yaga kallon da yake mishi kuma yagane abun da yake nufi amma hakan besa shi fitar ba saima juyar da kansa yayi gefe ganin hakan yasa sam kufula cikin farajin haushin shi yace wai bacewa nayi kafita bane ko innabarka da ita zaka iya duba tane duk wanna shirmen naku dakuke yi ku da ita ba dole kanta yayi ciwo ba idan kukace gabama nan gaba fashewa zeyi ya tarwatse bashike nan ba jin an ambaci kanta ze fashe yasata fashewa da kuka tare da cewa wayyo Allah na dadda kizo zan mutu wayyo wayyo kaina yar tsawa yadaka mata saboda ya tsani kuka gashi kuma tanayi masa a saitin kunnen sa dan ji yake da lafiyar ta qalau ba abun da ze hanashi ya canza mata kamanni da maruka dan abun da yafitsana kenan kaf rayuwar sa shiru tayi tana dan shashsheqar kukan tare da fara qoqarin tashi daga kansa saide kuma yasa hannun da ya dakatar da ita shettima da yagama cika famm kamaer ya fashe yasashi barin dakin a kufale ya fita tare da janyo qofar da qarfi da har saida Ameesha ta dan zabura dan ta tsorata da jin qarar girgiza kai sam yayi yanajin haushin abun da abokin nasa yakeyi da be gane kansa ba miqewa yayi tare da ita ajikinsa sai ya riqeta sosai yanda bazataji zafin kannata ba sosai kwantar da yayi akan gadon yana ajiyeta ta qara dafe kannata da hannuwanta shima sai ya dora nasa hannun akan nata sai daga baya kuma yajanye nata hannun ya dora iya nasa addu'a yashiga yi mata yana tofawa lokaci guda kuwa tafara jin sassauci haka yaci gaba da yimata harsaida ya tabbatar da yadena yimata ciwon sannan yajen ye hannun sa yana qoqarin meqewa budar bakin ta sai kawai tasaki dan qaramin tsaki tare da cewa kawai anzo an tofe mutum da yawu sai kazo ka goge min duk kabata min fuska da shi kamata ma yayi inyi wanka wallahi asukwane yajiyo jin abun da take cewa ga mamakinsa kuma sai yaga bakin ta a rufe idonta ma a rufe kamar ma ba ita tayi maganar ba jiyayi kamar ya kwasheta da maruka Allah yatai maketa a gadon asibiti take akwance kuma idan yatabata za a iya samun matsala shiyasa kawai yake daga mata qafa amma badan hakaba tun harararsa datayi tun farko da tuni yayi maganinta  ta kusa bakuntar lahira,
yana mamakin qarfin hali irin nata watakon ita duk halin datake ciki bakinta baya mutuwa bata da kunya ko kadan yanda ya karanceta a iya haduwar sa da ita yagane tana da tsiwa batajin magana aikwa da rabon kagi tabar asibitin nan sai ya gyara mata halayen ta saboda shi baya daukan irin wadannan shirmen,

bude idon datayine ya katse masa tunanin da yakeyi wata hararar taqara yimasa lokacin da suka hada ido tunani me zeyi mata kawai yake,

aikwa tana rufe ido taji saukar abu akan fusakarta  me dan dumi bude idon ta tayi tana kallon sa da tabbatar da abun da take zargi bata gama tunanin ba taqara jin ya tofa mata wani yawun a fuska zaro manyan idanuwanta tayi takaici ya isheta watakon de da gaske yawu ya tofa mata a fuska dan tsabar wulakancin da rashin sanin darajar dan adam kuka tafashe dashi kawai sai kuma ta yunqura da niyar tashi ta rama dan bazata hakura ba wlh saide kuma tana tashi taqara jin wani ciwon saurin komawa tayi ta kwanta tare da ruqe kan wani kallon ya watsa mata ganin abun da tayi niyar yi da yatsa ya nunata tare da cewa da kwa kin tafka babban kuskure a rayuwar ki dan sai nasakaki kinyi nadama ganin tana ta qara bata mishi rai da kuma lokaci yasashi dauko allaurar baccin da yazo da ita tofa anan akeyinta domin arayuwar ta ta tsani allura tana tsoron ta sosai tuni ido ya raina fata girgiza kai ta shigayi tanacewa dan Allah karkamin allura wlh na tsani ta dan Allah na roqeka dan darajar iyayen ka karkamin karkamin wlh idan kamin mutuwa zanyi kar ka kasheni da allura duk wannan surutan da takeyi be kulata ba cigaba yayi da hada ta aranshi kwa haka yake cewa ashe rashin kunyar ta ban zace, bakya da tsoran  mutane amma kina tsoron allura  mtswww ya kuma jan wani tsakin a bangaren ta kuma sai Allah yasa take jera mishi tunkan yayi mata ma allurar saida yagama hadawa tsaf ya nufuto ganin de da gaske inta zauna sai ya tsira mata yasa ta tashi da sauri tana niyar sauka daga kan gadon mayar da ita yayi da hannunsa kana yace mata juya qin juyawa tayi tare da make mashi kafada ido kawai ya zuba mata yana kallon ikon Allah wannan yarinyar yar qarama da ita amma tana neman saka mishi ciwon kai yana ganin qarfin halinta dan a iya kiyasin shi yasan su Hamna zasu girme mata amma sai faman wahalar dashi take akan abun da be taka kara yakarya ba sa'ar ta daya bata da lafiya amma da shikadai yasan kalar hukun cin da zemata,

yunqurawa ta qara yi zata tashi yasa hannu yadagata tare da zama akan gadon yajawota ya hada ta da jikinshi yariqeta gam yanda bazata iya kwacewa ba sannan yadaga rigarta ya saita daidai bombom dinta inda ake allura ya tsiramata yana tsikara mata kwa tasaki wata qara adaidai kunnen sa lokaci guda kuma sai ta dauke wuta dufff jin hakan yasashi dagota ya kwantar da ita ganin yayi bata motsi jikin ta ya mutu da alamade sumewa tayi saboda zafin allura, tashi yayi ya gyara mata kwanciyar tare da rufar ta a hankali ya furta marar kunya kawai idan kingama suman kin farfado sai ki koma bacci ko ruwa da yake gefe a gora yadauko ya shafa mata ta farfado saide dishi dishi take gani idonta har rufewa sukeyi saboda allurar da tafara yimata aiki,
kallonta yayi kana yace  allura kawai tasa kin suma amma kin iya yiwa mutane rashin mutunci maganin me tsiwa kenan anjima ma kika tashi kiyima wani rashin kunya sai namiki goma oho ita bata masan yanayi ba dan tuni bacci yayi awan gaba da ita saida yadan qara duddubata ahaka sannan yafice daga dakin yana fita yatarar da shettima abakin qofar sai safa da marwa yake yaqi zaune yaqi tsaye harde hannunwansa yayi yana kallonsa shima shi yake kallo sai yace malam lafiya kake kallona sam yace bansani ba wai meye matsalar kane da yarinyar nan naga duk kabi ka damu kanka akanta harar wasa ya watsa masa sannan yace ina ruwanka da ni kawai kazo zaka tsorata yar mutane gaya min me kayi mata nasan baka da imani wlh yanzu baza ka duba rashin lafiyarta ba zaka iyayi mata duk abun da yazo ranka kallonsa yayi yace dake ga mahaukaci ko to zaneta nayi kamar yanda kake tunani nafasa mata baki ma yanzu haka ta suma zaka iya zuwa kabata taimakon gaggawa kar tarasa ranta inkuma ta rasa saika bita ku tafi tare yana kaiwa nan yabashi hanya tare da nuna masa qofar da hannun sa sannan yawuce yabarsa agun, kamar mutum mutumi haka ya tsaya agun yakasa ko motsawa dan duk atunanin sa dagaske yake saboda yasan kadan daga cikin halayen sa kenan tsaf ze aikata abun da yace din sai can kuma kamar an tsikare sa da sauri yabude dakin yashiga har yana hadawa da dan gudu gudu yana zuwa kuma yaja burki ya tsaya ganin bawata alamar wahala atattare da ita dan dubata yaqara yi tare da sauke ajiyar zuciya,  a fili yace dan rainin hankali ashe qarya kake hmm da kwa yau kagane waye ni saina nuna maka bacin raina akan yarinyar nan wallahi saide komai ze faru ya faru abun rufarta ya gyara nata sannan yafita daga dakin zuwa office din sameer yana zuwa ya tarar dashi zaune kan kujerar sa yana duba wani file ko sallama beyi ba ya shiga ciki yaji shigowar mutum amma bedago yakallesaba saboda yasan ba wanda ze mishi haka inba shettima man ba shiyasa ya shareshi zama yayi akan kujera yana fuskantar shi sannan yace Allah yataimake ka wlh naganta lafiya qalau amma badan haka ba ko hmmm sai yanzu ya dago ya kalleshi sannan yace badan haka ba me zefaru zaka rama matane yace what ever de yanzu de duk ba wannan ba me yake damun ta yanzu wani irin kallon banza ya watsa masa sannan yaci gaba da aikin gabansa batare da ya bashi amsa ba duk nacinsa nason ya kulashi kin kulashi yayi daga qarshe ma sai yatashi yabashi waje yayi shigewar sa ciki zama yayi agun yana mamakin wannan halin na abokin shi yanzu inde yanaso yaji halin da take ciki dole saide yabishi ta lallami da limana sannan inyaga dama yagaya masa beyi qasa agwiwa ba yaqara tashi yabishi cikin cikin lallami yashiga roqonsa saida yaga dama sannan yagaya masa duk yanda sukayi da ita kuma ya dora masa da cewa ya gargadeta idan ta farka karta kuskura taqara yimasa wani abun makamancin haka inkuma bahaka ze riqeta ne har sai tasamu lafiya sosai ya hukuntata sannan ze sallame ta shide kawai to yake cewa bashida bakin ja inja dashi tundade yanzu masalaha yake nema gwara yabishi a hankali su rabu lfy,
tambayar sa yayi zuwa yaushe zata farka yace masa nan da awa biyu ma zata iya farkawa saboda bame qarfi yayi mata ba godiya yayi masa kawai ya tashi yafita yana fita yakira number bossay bayan sungama gaisawa yasanar dashi suzo anjima amma kar yagaya musu cike dajin dadi da haryana jiyo irin farin cikin dayakeyi sai faman godiya yake zabga masa kamar yayi mishi albishir da aljanna sallama sukayi sannan yakashe wayar ya nufi dakin da takede dan baya gajiya da kallon ta beqi ace kullum yana gabanta yana kallonta ba...........,


*Bossay*
fadawa yayi kan gadon sa tare yana tafaman sakin murmushi yaji dadin wannan albishir din daman fitowar sa daga wanka kennan dan haka yatashi da sauri yashiga shafa mayika tare da feshe jikin sa da turaruka wajen jerin kayansa yaje ya tsaya yana binkayan da kallo yarasa wanda ze saka kayan da yasaka ranar da zeje dauko ta yaje saikuma Allah beyiba zata gani dan haka da sauri yazarosu yasaka shaf shaf yashirya yafito har yana hada step bibbiyu gurin saukowa daga benen bakowa afalon dakin dadda yafara nufa yana zuwa bewani tsaya tabashi izinin shiga ba kawai yadanna kai ya shiga yana shiga yatarar da ita akan gado jin anbanko qofa yasa ta saurin boye abun da takeyi kallo daya zakai mata gane bata da gaskiya amma saboda halin farin cikin da yake ciki besa yagane hakan ba qarasawa yayi inda take yace tsohiwa kishrya zamuje asibiti muji ya ake ciki kinga tun ranar da sukace zasu kira har yanzu basu jiraba yakamata muje muji ko lfy tana gurin azaune takasa motsawa kawai sai kai datake daga masa alamar to be tsaya bitakanta ba yanufi dakin Ammi dan yanzu shi bakomai bane agabansa face yaje yaganta dan ji yake kamar yayi tsuntsu yangashi agabanta itana Ammi yanda yagayawa dadda itama haka yace mata sannan yace suyi sauri ba bata lokaci kuwa kowannen su yashirya suka fito falo suna shirin fita saiga faruq tanbayar inda zasu yayi dadda ce ta bashi amsa dan haka shima yace sai yaje bawanda ya hanasa gabadayansu suka fita amota daya suka hau bossay da faruq agaba say dadda da Ammi abaya gudu kawai yake da saida kowa yayi mamakin irin gudun da yakeyi saboda ba halinsa bane inde bawani abu bane emergency yataso baya gudu a mota da suka tambayeshi dalilin gudun sai yace musu anajiran sane agurin aiki shiyasa yakeso yaje ya dawo da wuri,

adan qanqanen lokaci suka qaraso asibitin yana gama parking suka fito tare da nufar cikin asibitin wayar sa ya dauko yakira shettima yasanar dasu zuwansu shi kuma yayi masa kwatancen inda suke,

gurin da yakwatan ta mishi yanufa sukuma suna mara masa baya ahaka har suka qaraso bakin qofar dakin nocking yafara yi daga ciki shettima yace ku shigo mana tura qofar yayi ahankali yasaka kai yashiga ciki sannan suma suka shigo,
gaba dayansu mutuwar tsaye sukayi da ganinta dan zuwa yanzu har ta farfado tana zaune shettima nabata tea abaki..........
[4/2, 8:13 PM] ~~~~writer~~~~: 💅SARKI SAMEER....💅
           by❤xeemat.....love❤

             🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

                🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
                             ﷽

                    Bismillah........ ✍
Episode 66-67-68

         """"""""""""""""""""""""""""""""""

shettima ne yacewa Ameesha da yaga bata kula dasu ba yayi mata nuni da hannu dagowa tayi ta dubi inda yake nuna matan akan bossay idon ta yafara sauka kuri tayi tana kallonsa kamar meson gano wani abun ko kiftawa batayi shima itan yake kallo sun qurawa junansu ido saidaga bisani ahankali yafara takawa zuwa inda take kuma be dauke idon sa akanta ba har yaqaraso bakin gadon sai kuma yaja burki yatsaya saida yagama qare mata kallo sannan yace baby meesha na da gaske kece ba gizo bane bata tanka masaba illa ido da ta zuba masa tana kallonsa dasauri yadan raunkwafa zeyi hugging din ta amma sai ta matsa baya dakata wa yayi sai yakuma qoqarin ruqo hannun ta amma sai ta qara janyewa jikinshi a sanyayye yace meesha nine fa tace nifa bansanka ba bazan bari ka taba niba kaidin waye suwaye ku dan Allah kufita wlh banason ganin ku taqarasa fada harda dan guntun hawayenta tana qara matsawa daga kusa dashi tsaye yayi ya kasa motsawa kamat mutum mutumi (gunki),

Dadda de suman tsaye tayi dan bata taba tsammanin ganin jikar tata ba ahalin yanzu dan ita zuciyarta bata takeyi tamutu kawai zasuzo suga gawarta ne kawai bossay na boyewa ne be gaya musuba sai kuma taga akasin haka bata san lokacin da kwalla ta fara zubo mata ba, ashede da rabon zata qara ganin gudan jinin ta jikar ta tilo aduniya,

faruq ne yaqarasa shigoa ciki tunda daman tunda suka shigo yana baya beganta kuma daman besantaba ganin de yarinya akan gado yasashi tabbatar wa akan itace Ameeshan da ake nufi bakin shi a washe har kana ganin fararen haqoran sa yace wannan ce Ameeshan taki dadda yatambaya yana kallon dadda datayi tsaye sai faman zubar da hawaye take rabuwa yayi da ita ganin bata da niyar bashi amsa, "sai kawai ya maida dubansa wajen Ameesha da itama zuwa yanzu ta maido dubanta garesa ganin hakan yasashi qara washe baki tare da qaraswa inda take hannu yadaga mata kana yace hy beauty girl dina yajiki kasake tayi tana kallonsa kallon da kana gani kasan kallon rashin sani take mishi batare da tace komai ba tacigaba da kallon su daya bayan daya,

Ammi ce ta katse musu shirun nasu da cewa dadda kiqarsa mana kin tsaya anan ko bakiyi  farin ciki da ganin jikar taki ba taho mutafi tafada tana ruqo hannun ta suka qarasa bakin gadon tsayawa sukayi agabanta

Dadda ce tabude bakin ta da qyar tace shalelena dagaske kece a zaune ba mafarkin da nasaba yi bane matsawa tayi kusa da ita tana niyar rungumota amma sai tajanye jikin da mamaki dadda ta tsaya tana kallon ta wasu hawayen nen suka qara tarar mata tace shalele nice fa daddar ki baki gane ni ba budar bakinta sai cewa tayi ni bansan kiba bantaba ganin ki ba kuma ni ba shalelan kibace tafada tare da murguda baki sannan ta karbi cup din shayin dake hannu shettima taci gaba da sha kamar ma bata san da halittar su agun ba sau biyu ta kurba sannan tace dan Allah kun isheni da kallo dan Allah kufita banason ganin ku anan,

gaba dayansu ba wanda beyi mamakin jin furucin ta ba musamman shettima da yanzu suka gama magana da ita take cemishi ya kira mata daddar ta shiyasa yayi mata wayo yace inbata sha tea din ba baze kira mata ita ba saboda jin hakan yasatake sha,
Amma kuma yanzu tace bata sansuba to kode kwakwal warta ta dan tabu wajen yin aikin jin sautin kuka ya katse masa tunanin sa,

dadda ce ta fashe musu da kuka tana cewa shikenan yanzu shikenan anrabani da jikata nashiga uku gudan jinina ta manta dani kunjifa me take cewa wai bata son ganin na tama ki yarda intaba ta dan Allah ku ganar da ita ko ni wacece wlh bazan iya rayuwa idan babu itaba kar ki gujeni dan Allah tafada tana kallon Ameesa da ta toshe kunnen ta bama jin surutun ta take ba bossay ne yashiga rarrashinta da shima kawai dauriya yake dan jinsa yake kamar ya fashe da kukan shima karde ace Ameesha tayi losing memory din ta idan kwa hakan yazasuyi gashi taki yarda da ko wannen su,

Ammi ce ta kallesu tace kunga dan Allah mubi komai a hankali wannan ai ba abun tashin hankali bane daman inde akace abu tashafi brain to dole za a iya samun irin wannan matsalar ko doctor tafada tana kallon shettima da yakasa magana daga mata kai yayi tace kayi musu bayani yanda zasu fahimta magana yagamsu da maganar ta shiyasa yafara yi musu bayani a nitse yake cewa yanzu daman ba lalle ta iya gane komai ba saboda yanayin matsalar ta tana iya taba kwakwalwa ta manta da wasu abubuwan amma in akai sa'a ana tuna mata da wasu abubuwan da kuma da kuma abun da tafiso naci ko nasha da komai de data ke rayuwa dashi da to zata iya tuna baya adan qanqanen lokaci batare da anja lokaci me tsawo ba kun fahimta,

cike da gamsuwa suka amsa masa itade dadda ba haka taso ba amma yazatayi tunda ahaka abun yazo,

Ammi ce ta zauna kusa da Ameesha tare da ruqo hannun ta yanzu bayi musuba kuma bata kwace hannun ta daga ruqon da Ammi tayi mata cikin nutsuwa Ammi tafara yimata bayani tace 'yata ki kwantar da hankalin ki munan da kika ganmu mune danginki tanuna kanta tace nice mahaifiyar ki ta nuna dadda tace wannan kuma sunanta dadda itace kakarki wadannan yayyankine tanuna bossay da faruq sannan tace kina dawasu yayan mata harma da qanne su suna gida munbarosu agida duk kinmata damune saka makon rashin lafiya da kikayi har aka kwantar dake anan kindade a kwance yau wajen satinki biyu akwance sai yau muka samu damar zuwa ganin ki kuma munzo da murnar gashi kinmanta damu amma dan Allah kide na furta bakya son ganin mu in baki san ganin mu to suwa zaki gani dole mune naki kinji 'yata ko kinaso kiga hawayen mahaifiyar ki kai ta girgiza mata alamar a'a tace to yanzu kin yarda zaki zauna damu tare,
kai ta daga mata sannan ammi tace yauwa yar albarka yanzu kibawa kakarki hakuri kice ta dena kuka kinga sai kuka take saboda duk cikin ku tafisonki shiyasa kiga tana zubar da hawaye akan abun da kikai mata bataji dadiba,

cikin sanyin murya tace dadda kiyi hakuri yanzu nasanki wani irin farin ciki dadda taji ya lullubeta jin shalelanta ta ambaci sunan ta hakan ba qaramin dadi yayi mataba batasan lokacin da ta saki murmushi ba tare da rungume ta tace ni daman banji komai ba kawai tashin hankalina kice bazaki zauna dani ba amma yanzu tunda kin amince shikenan hankalina yakwanta idan kina tare da mu zaki tuna komai zaki gane ko ni wacece zaki tunani ahankali taqarasa fada tare da raba jikin ta da nata kallon ta ta mayar kan bossay dataga ya kafeta da ido murmushi tasakar masa sannan tace kaine yayana ko kai yadaga mata sannan tace ya sunan ka da qyar ya iya cemata bossay jin jina kai tayi tare da nanata sunan kafin ta kuma duban faruq tace kaifa ya sunanka yace ni sunana Ameesha tace ashe sunan mu daya tunda nima haka naji suna kirana dashi yar dariya yayi dukansu saida suka dan murmusa jin shirmen da take yi ,
"dadda ce tace Allah sarki jikalle Allah yabaki lafiya wai yanzu dan Allah ita iya gaskiyarta ta zata sunan su daya batasan sunan namiji daban ba na mace ma daban Ammi ce tayi murmushi tace ai komai sai an nunamata an koya mata yanzu ba komai akanta duk abun da aka dorata ahaka zata taso dadda tace rayuwa kenan yau kaine yau ba kaibane gata de itadin ce komai nata amma kuma ba abun da tasani kamar 'yar qaramar yarinya Allah yaqara miki lafiya me amfani gabadayan su suka masa mata da ameen daga nan kuma faruq yace beauty girl ni ba sunana Ameesha ba da wasa nake miki wannan sunan mata ne ba a kiran namiji dashi nikuma sunana umar amma anace min faruq ke kuma yaya faruq zaki ringa cemin kinji kai ta daga masa kawai bossay ne ya doke mishi qeya yace bazata fada din ba ke faruqu zakina ce mishi inma kika ga dama kice mishi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment