Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

wayar sa yabawa Azeema yace intaje tabawa yayan ta sai ya kira shi su tattauna akan batun karba tayi tana masa godiya yace ba komai yiwa kaine daga nan kuma ya koma mota ya tayar yakaqara danna horn me gadi ya wangale masa qaton gate din shikuma yadanna kan motar yashiga ciki ajiyar zuciya dadda ta sauke tace to Allahamdulillah komai yazo mana da sauki batare da wata matsala ba suma duk hamdala sukayi sake da godewa Allah sannan suka kama hanyar komawa gida suna tafiya dadda na qara jimamin yanda akai hakan tafaru babban mutum ace yaba ta abun da mamaki wlh kowade da abun da yake saqawa aransa har suka qarasa gidan basu wani dadeba Azeema tacewa Ameesha to besty godiya nake bari in wuce gida inje insanar da mama nasan tana can tana jiran dawowata tace to bari muci abin ci saiki tafi ko tace a'a besty na qoshi Ameesha tace wlh sai kinci kinji ma na rantse Azeema tace to ina ruwana da rantsuwar ki nide bazan ciba Ameesha ta hade rai tace to karkici din alaraka taki gona tafada nakara hade rai alamun taji haushi Azeema data ga haka sai tace kai besty meye kuma najin haushi to naji zanci amma kadan kuma kiyi sauri dan banaso inkai magariba a hanya tace to sannan ta mike tanacewa yar rainin hankali ai da bakiciba wlh da kinga rashin mutuncin da zan miki dariya Azeema tayi tace to nide naji kiyi sauri malama Ameesha tace anqi ayi din tafada tana ficewa daga dakin bata dade ba ta dawo da kwanon abincin a hannunta ta ajiye agaban ta tace sai muci Azeema tace la wai daman dan wake ne ai da kinga ya min da bazan miki musu ba kinsan ina sonshi sosai gashi mama bataso tana yimana shi saboda ita be dame taba Ameesha tace ai daman dan hakan nace kizauna muci ama kike wani nannoqewa kina so kina kaiwa kasuwa da muna furci wani ni wlh naqoshi ni sauri nake yen yen yen dariya Azeema tayi tace au abun jarda cin fuska to wlh saima na tashi na tafi tace bismillah ai ban daure kiba qofa abude take bata qara ce mata komai ba kawai tayi shiru tacigaba da cin abincin ta dan ta lura idan tabiyewa bestyn tata sai sukai dare basu dena ba itama Ameeshan shiru tayi suka ci gaba daci har suka cinye tass sanna tafita da kwanon ta debo musu ruwa suka sha itakuma Azeema ta tashi ta shirya tace muje ki rakani ko tace muje itama hijab dinta tasaka sannan suka fito waje atare suna fitowa tace to ina daddan take tace oho watakil ta fita ko kuma tana bayi muje kawai inna dawo nagaya mata kin tafi tace shikenan muje suka fito suna ta yar hirar su har suka zo inda suka saba raka juna sannan sukayi sallama kowa yayi nasa wajen Ameesha na komawa ta duba ko ina taga da gaske de dadda bata nan to ita ko ina taje haka bata gaya mata ba haka ta koma daki tayi zaman jiran da wowarta amma shiru bata dawo ba har aka idar da sallar magariba sai lokacin kuma tafara jin tsoron gidan da kuma tsoron ina dadda taje haka hartakai dare bata dawo ba dataga de bazata iya zaman cikin gidan ba kawai sai tafito waje dake gurin da hasken fitilar wani gida dake kusa da nasu ta haska har qofar gidan su dan haka tasamu waje tare da zabga tagumi tana hawaye saida tayi wajen minti talatin itakadai dan har tafara kuka wiwi kuma tana tunanin ko taje gidan su Rasheeda kawai tagaya musu bata ga daddar ta tana miqewa saiga wani me keke napep yashigo layin kuma kamar gidan su yake nufowa dan haka ta tsaya taga waye aciki adaidai tar tana tsayawa saiga dadda tafito dasauri dan har ta manta ma bata bawa me adaidaitar kudin ba saida yace hajiya kudin sannan tace yi hakuri yaro namanta wlh yace ba komai tana bashi tawuce gurin Ameesha datayi tsaye takasa motsawa daga gurin dadda na qarasowa tace wayyo Allah na dan Allah kiyi hakuri wlh bansan zankai dare ba matsala akasamu a hanya cikin shashsheqar kukan da taci ta qoshi tace kuma dadda fisabilillahi sai kifita baki gaya minba yanzu da wani abun yazo yasameni fa ko andauke ni tace Allah ma yakiyaye ba abun da ze sameki ma wlh nayi tunanin kan qawarta ki ta tafi nadawo shiyasa ma ban muku magana ba nafita kuma nayi tunanin ma zasu kawo wuta Ashe basu kawo ba yanzu de kiyi hakuri muje ciki ko gaba tayi ita kuma tabita abaya suka shiga cikin gidan............

************************
daga sabuwar marubuciyar ku🖋
By❤xeemat....love❤

comment and share

**************************
[2/24, 10:12 PM] ~~~~writer~~~~: 💅SARKI SAMEER.....💅
               by❤xeemat.....love❤

               🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

Allah ya shiryemu shirin addinin muslunci Allah yasa mugama da duniya lafiya Allah yasa gaban mu tafi bayan mu kyau Ameen...............

                  Bismillah........
Episode14🖋

           **************************
Azeema nakoma wa gida da murna tagayawa mamanta duk yanda sukayi aikwa mama taji dadi sosai tace Allah yasa adace bari saleem din yadawo sai yakira muji yanda zasuyi Azeema tace mama wai har yanzu kina nufin kice yaya be dawo tace wlh har yanzu bedawo ba nima jiran sa nake yadawo inji yanda sukai Allah yasa yasamu aikin nan Azeema tace Ameen de inji ma ajikina yasamu tunda kikaga har yakai wannan lokaci in sha Allahu yasamu mama tace Allah yasa haka de suka cigaba da tattaunawa har bayan sallar magariba sai dab da sallar isha 'i Saleem ya shigo gidan amatuqar gajiye yadawo gida mama naganin sa tunda ga yanayin fuskar sa tagane yaumade ba sa'a dan haka bata tambaye shi komai kawai tace kashiga ciki ka watsa ruwa sai kafito kaci abin ci ka huta naga alamar agajiye kake yace mata eh wlh shima da yaji bata tambaye shiba sai bece mata komai ba kawai ya wuce bedroom dinsa yana tafiya ta bishi da kallon tausayi tana mishi fatan Allah yakawo qarshen wannan neman aikin da kullum ake abu daya ankasa samu inkuma ba alkhairi bane Allah ya musanya masa da mafi alkhairin sa bayan yayi wankan yafito da jallabiya ajikin shi sannan ya leka dakin maman tasa yaga bata nan amma yaji alamun tana bandaki dan haka sai ya dan daga murya yace mama ni  na wuce masalla ci be jira amsar taba kawai yafice yatafi masallaci tanajiyo shi daga cikin bathroom din amma bata amsa ba saboda wanka take shiyasa bata amsaba bayan tafito tashirya itama tayi tata sallar tare da yiwa mijinta da 'ya'yanta addu'a me tsayi tare da shafawa sannan ta mike ta fito falo tazauna akan kujera sannan ta kwalawa Azeema kira Azeema dake daki tun dazu bata fito ba ta amsa tare da fitowa tace mama gani tace wai bakisan Saleem yadawo ba ko tace yaushe yashigo banji shigowarsa ba tace tundazu yadade har yayi wanka ma yafita masallaci Azeema tayi saurin cewa mama meyace miki yasamu ko yauma de ba sa'a mama tace to bisa ga dukkan alamude babu saboda naga fuskarshi ba walwala shiyasama ban tambaye shi komai ba nace yaje ya yi wanka bayan yayi kuma ya wuce masjid yanzu de kije kicin kifito mashi da abincin shi kishirya masa kafin yashigo inyaso idan yaci sai muji ta bakin sa ko tace to bari inyi sauri nasan yakusa shigowa tana fada ta wuce cikin kitchen domin hado mishi batajima ba ta gama hada komai akan faranti danbun cuscus ne dayaji zogale da kayan hadi sai lemo da ta dora mishi akai da ruwa me sanyi sai cup din daze sha lemon duk de tahada mishi sai ruwan wanke hannu dan shi qa idarsace baya cin abinci da cokali inde dare yayi saide yasa hannu yaci koma menene bayan tafito ko ajiyewa batayi ba shima ya shigo cikin falon da sallama dukan su suka amsa masa yashiga ya zauna akan kujera  sannan Azeema tayi mishi sannu ya amsa mata tare da cewa sannunki ya zaman gida tace zaman gida gashinan mana tafaman yi ni wlh nama matsu akoma makaranta zaman gidan ya isheni yace sai yaushe zaku koma tace sai nan da sati daya yace ok ai ba yawa ma kamar yaune yanzu zakiga har taqare tace aikamde mama ce dataji hirar tasu ba qarewa zatai ba tace to suru tun ya isa haka kasakko kaci abin ci da to ya amsa mata sannan yasauka qasa kan carpet din yazauna tare yin zaman musulunci yakawo farantin abincin ya zubawa kansa a flat sannan yashiga ci anutse cikin nutsuwa dan Saleem akwai nutsuwa komai in yanayi baya gaggawa alamuran sa komai a tsanake yi yanzu ma ahaka yake cin abinsa Azeema  ce tace mama kefa baza kici ba tace zobo min dan kadan ta tashi tashiga kitchen ta zubo mata itama ta kawo mata saida karba sannan tace kefa baza kici ba girgiza mata kai tayi tace naci abinci agidan su besty kafin infito tace kuma baza ki karaba tace eh idan nakara ai cikina sai ya fashe ita kuma haka Allah yayi ta kwata kwanta bada ci karewa ma abinci be da meta ba idan taci abin sau daya ma arana zata iya kaiwa gobe wataran sai mama ko kuma taci sau biyu shima wataran sa mama tayi mata jan ido take ci.mama batace mata komai ba tahau cin abinta dan tasan ta tunda tace bazata Ciba to bacin zatai ba shiyasa ta rabu da ita kowa shiru yayi su suna cin abin cinsu ita kuma tayi shiru sai can kuma  takatse shirun nasu da cewa yaya saleem jifa yanda kake cin abinci kamar wata mace sai wani yanga kake bafa agaban budurwar ka kake ba dariya yayi har hakoran sa na fitowa yace lalle ma yarinyar nan nikike gayawa haka tace to ai gaskiya nafada yace to zo ki koya min yanda ake ci ni ahaka nasaba cin abinci na sai kace yau kika fara gani itama daman tsokana ce tasa ta yi dan tasani ahaka yake kawai sai tace ai naga na yau yafi na kullum kodan ba tsaywa nake ba ina kallon sosai ba sai yau yace daman sa min ido kike ko tace a'a mama tace Azeema wai meye hakane abincifa yake ci amma kinbi sai faman cikashi da surutu kike ko yaune ranar farko da kika fara gani bana son sha shanci banza kai kuma ka tsaya sai faman biye mata kake murmushi yayi kawai be ce mata komai ba ya ci gaba da cin abin cin sa falon tsit yayi babu wanda ya qara magana acikin su har ya kammala itama mama already takammala nata dan tama rigashi gamawa Azeema ce ta tashi ta tattare kwanukan dasuka gama takai kitchen ta dawo ta zauna saida mama tadanja lokaci kafin tayi gayaran murya tana fuskantar saleem tace to muna sauraron ka ya kukayi agurin aikin saida yaja dogon numfashi sannan yace wlh mama duk wannan sammakon danayi saida naje akace bezo ba sai wajen qarfe goma da indawo gwara kawai intsaya nanma de saida goman tayi akace still muyi hakuri wai wani uzuri yataso masa mukara hakuri mujira shi haka mukai tazama harwajen qarfe uku muka tambaya ko baze zo ba aka qara cemana ai yana ma hanya be qaraso ba sai wajen qarfe biyar da rabi  yana zuwa ya shiga cikin office din amma be bada damar shiga ba har sai wajen shida shima kuma befi mutane biyar ba yayiwa interview yace ayi hakuri lokacin ya quri mubari gobe mu dawo   haka kowa yatafi gida rai ba dadi yaqara sa fada ayanayin najin rashin dadin hakan duk uwar wagalar dasuka sha ace be samu ganawa da shiba wannan ai wulakanci ne Azeema  ce tace Allah sarki gaskiya kasha wahala suma basu kyauta ba da sun sani sun sallameku amma suka bari har kukayi wannan dadewar kuma ace saigobe gaskiya abun ba tausayi mama ce tace to Allah yasa hakan ce tafi Alkhairi saika qara jarrabawa goben ka koma daman duk abun da za ayi nasara akai sai asha wuya ba afiya samun nasara cikin sauqi ba kayi hakuri Allah yana tare da kai wataran sai labari jinjina mata kai yayi kawai saida tagama yimasa nasiha sannan tafada mishi abun da yake faruwa game da maganar neman baba da Azeema taje tafadawa su dad yaji dadin hakan shima sosai sannan yace Azeema taje ta dakko mishi katin number aikam dasauri taje ta dakko mishi ta dawo ta mika mika mishi yakarba yasa number awayar shi sai lokacin kuma sukaga dare yayi da har goma takusa sai mama tace kawai yabari gobe sai yakira duk suakyi na'am da hakan suka bari sai goben daga nan de suka ci gaba da tattau nawa har wajen sha daya sannan kowa yatashi yatafi ya kwanta sai da safe kuma idan Allah yakaimu......................
        
            ************************
                  ***AMEESHA***
Suna shiga cikin gidan bayan sun shiga daki Ameesha tasa dadda agaba wai lalle sai taga yamata inda taje ita kuma dadda tanacewa ina ruwan ta ko dole duk inda taje sai ta gayamata to baza ta fada mata ba din tayi duk abun da zatayi Ameesha kaku ta kqara sawa dadda harda buga kafafu tace wlh dadda in baki fadan ba zanbar miki gidan nan kigaya min wa kika sani agarin nan dakike zuwa wajen sa kuma ba kyaso insani bayan kince min bamu da kowa anan to wlh zan rabuda ke danni nagaji da halin da kike min sai ki tafaman boyen abubuwa daman duk sanda kika fita a mota na tambaye ki sai kice ina  ruwana bazaki fadan ba kuma kinki gaya min inda dangin na suke danni nama fara zarginki wlh kode da gaske ne tsinto ni kikai ki fadan gaskyi dan Allah tafada tana qara fashewa da wani kukan dadda data ga abun daga qarami yana neman ya koma babba dan ita bata so taji yarinyar nan nayimata zancen danginsu kuma ita wacece saboda batasan me zatace mata ba dan haka sai ta sassauta murya tajawo Ameesha jikin ta tace yi hakuri yarinyar kirki ki yafewa daddar ki da take saki hawaye nadena daga yau kuma zan gaya miki inda nake zuwa amma ba yanzu ba sai kin kwantar da hankalinki kin nutsu zuwa gobe sai muyi maganar kinji shalele na kai Ameesha ta daga mata alamar ta yarda kenan ita kuma dadda tanasane tayi mata haka amma ba abun da zata gaya mata tasan halinta kafin zuwa giben ta manta bazatayi mata maganar ba ,dago ta tayi tana share mata hawayen ta sannan tace yauwa haka nake so shalelena idan nagaya miki magana kiringa ji bakina jayayya dani yanzu kije kidauki ruwa ki wanke fuskarki da kika bata ta da hawaye nan ba tai mata musuba ta dauki fitila taje ta wanko fuskar ta dawo dadda tace kije kizubo abinci kici ki kwanta sai tace mata naqoshi sallah kawai zanyi inkwanta tace to shikenan haka akeso jekiyi ki kwanta bari ni inje inzuba inci  kafin ki idar da sallar nagama sai nima inyi sallar  mukwanta tace to sannan suka fito daga dakin dadda tayi wajen girkin nasu don zuba abincin itakuma ta dauki buta tashiga ta kama ruwa tafita tayi alwalla suka koma dakin tare har ta idar da sallar dadda batagama cin abinci ba dan haka kawai data gama addu'arta sai tajuya tayi  kwanciyar ta dadda naganin ta batace mata komai itama har tagama tafita da kwanon tashiga banda ki tafito tayi alwalla itama sannan tadawo dakin tayi sallar tare da addu'o'i saida ta dau lokaci me tsayi tanayi sannan ta shafa tayi shimfida akasa da wani  bargo da yaji jiki sosai ta shimfida akasa kamar yanda ta saba saboda batare suke kwana ba da Ameesha katifar bata da wani girma  shiya sa tabar mata ita kuma take kwana aqasa tana gama wa ta kwanta tare da yin addu'ar bacci ta lulluba da wani zane tafara tunanin abubuwa da dama da suka faru a rayuwarsu kasa bacci tayi sai da kyar baccin ya salallabo yasace ta......
             ********************
Washegari su Bossay suka tashi dashirin zuwa gidan su Ameesha da wuri kamar yanda yagaya wa qanini sa faruq cewa zasu fita hakan kwa sukai da wuri suka fita yace wa Ammin sa ta shirya kafin yadawo yana dawo wa zasu wuce dan ko shigowa ma cikin gida baze yiba zata fito sutafi tace mishi to sai sun dawo tunda suka fita kuma basu suka dawo ba sai wajen sallar isha yana dawowa yace wa Ammi tafito sutafi Ammi kwa tace ita wlh ba inda zata a dare nan tunda yaje yadade ta ringa jiranshi be dawo ba dan haka sai yabari sai gobe fitowa yayi daga motar yarufe ya shiga cikin gidan yana shiga yaga Ammin tashi bata falo sai furaira da tana ganin shi tamike tana mishi sannu da zuwa da mamakinta saitaga ya amsa mata fuska ba yabo ba fallasa ba hade ran da yasaba yimata mamakine yaqara kasheta jin yace furaira ina Ammi ko tana daki tunda take bata taba jin sunan ta abakin shi ba sai yau lalle wannan rana babbar ranace agareta tana cikin tunanin yakara cemata kabaki ji bane da in ina tayi saurin ce wa yaya tana kitchen bari inkirawo maka ita tafada ta shirin tafiya ya dakatar da ita yace bashshi zanje da kaina yana fadan haka be qara cemata komai yanu fi kitchen din yabarta tsaye da mamaki tana tunanin kode wani abun yasha da yasa ya manta dawa yake magana amma tunda take dashi bata taba jin ance gashi yau yasha wani abun ba to me yake damunshi dayasa ya canza mata haka lokaci guda bata da me bata amsa dan haka tazauna tana ta tunani shiko bema san tanayiba yana shiga kitchen din ya gano Ammin tasa tana juya abinci bata san da shigowar saba sai jin mutum tayi abayan ta ya ruqaota bata tsorata ba saboda tasan bawanda ze mata irin wannan abun sai shi san haka tace wai kai yaushe zakai hankali baka san ka girmaba kaine babba amma kamar wani qaramin yaro ni sakanni nasan me yakawo ka kuma ba inda zani adaren nan duk nacin ka qara rungumeta yayi yace haba Ammi dan Allah kar kimin haka wlh inbanje ba akwai matsala kitai maka kizo muje bafa wani nisane da gidan ba sosai befi muyi minti talatinba idan nayi guduma baza mukai hakan ba kuma kinga daman magana da daddare tafi dadi dan kizo muje kinji my lovely mom uwa tagari da babu kamarta uwata tafi kowace uwa nasan bazaki qi abun da danki yake so ba ko nasan zaki taimake ni wlh nasa ran zuwa kawai kiyi hakuri muje tace masa ai ko kai maye ne saide ka cinyeni amma bazanje ba sakinta yayi yadawo ta gabanta tare da ruqo hannu ta ya marairaice mata yace plsssss Ammi kitaimaka dan Allah nanmade qinyarda tayi saida qyar da sidin goshi yashawo kanta ta amince zataje wata rungumar yaqara yimata yace shiyasa kullum nake qara sonki ke tadabance acikin iyaye Allah yabar mana ke Allah yabaki tsawon rai tace Ameen kuma ya isa haka zakazo kana min da dadin baki sai ma infasa wlh yace meyayi zafi Ammi na yi hakuri bata kara kulashi ba ganini hakan shikuma sai yajata suka fito falo  sai tacewa furairah taje ta qarasa girkin kafin su dawo tace to sannan ta tashi tashiga kitchen din Ammi batai wani ja lokaciba mayafin abayar dake jikinta ta dakko tayi rolling sai tafito das da ita inka kalleta ma inba agaya maka akayiba bazaka taba cewa ita ta haifi ALIYU (Bossay) ba haka suka jera  abun sha'awa duk wanda ya kallesu sai sun burgesa dakanshi yabude mata mota tashiga shima yaza gaya mazaunin driver yazauna tare da yiwa motar key yaja ta zuwa bakin gate me gadi ya bude musu suka fita  tun a hanya yake ta washe baki yau zega Ameesha sannan ya bata hakuri akan abun da yayi mata be kyauta ba  yasan tana ta zuba ido taganshi amma yaki zuwa yanzu shikenan zata dauke shi makaryaci Ammi ce ta katse mishi tunanin sa da cewa kai wai har yanzu bamuzo ba kace ba nisa yace munkusa zuwa  fa Ammi.........
Washh wlh nagaji kuyi manage da wannan sai zuwa gobe kuma idan Allah yakaimu....🖋
                                  Bisalam.....
daga sabuwar marubuciyar ku...🖋
    
                          
            ❤xeemat.......love❤

Comment and share plsssssss
[2/25, 9:09 PM] ~~~~writer~~~~:    💅SARKI SAMEER.....💅
               by❤xeemat.....love❤
   
               🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

Ya Allah duk abun da ba ma gani👀 Allah kagane mana duk abun da bamaji👂 Allah kajiye mana duk abun da yafi qarfinmu💪 Allah kafi qarfinsa ya Allah duk abun da baza mu iyaba👌 Allah ka iya mana Allah kashige mana gaba adukkanin Al'amuranmu Allah kar kabarmun da kanmu tai makonka murke nema duniya da lahira........

                   Bismillah.......
Episode 15🖋

               ********************
Basu wani qara dadewa ba suka qarasa qofar gidan lokacin da sukaje gidan tara saura befi minti shabiyar ba yana gama dedeta parking din motar yajuya yana kallon Ammi nasa yace Ammi ga gidan fa yanzu yaza ayi zakifara shiga din dan Allah inyaso inkinshiga sai kituro min Ameesha sai mushigo da ita wata uwar hara ra ta maka mishi tace haka muaki da kai daman kaga nifa kar kabata min lokacin ina da abunyi kasani dole na fito adaren nan inbaka shirya shigaba ai sai kajuya mukoma gida takarasa fada tana hararar sa  da sauri yabude qofar yafita yana zagayowa itama yabude mata yace ranki yadade hajajun mu mushiga ni na isa yanzu ince mukoma gida tace ai naga alama baka shirya bane shiyasa nace haka tanafada tafito daga motar shikuma ya rufe Sannan ya tsaya wai yanaso tai gaba yabita abaya itama ta tsaya tace wai kai me yake damun kane bafa nason shashanci ni kakeso inyi gaba kenan dan sosa kyayarsa yayi sannan yace sorry Ammi muje yafada yana yin gaba ita kuma tana biye dashi abaya har suka shiga gidan da sallama abakin su saida sukai wajen sau uku sannan dadda ta amsa su tanace wa wai suwaye ne a tsohon daren nan suke damun mutane ya akai me yakawo ku me kuke nema gurin wa kuka zo sai faman jera musu tambayoyi take batare da tajira amsar dayaba kuma tanacikin dakin bata fito ba bossay ai tuni hantar cikin shi tabashi wata irin qara jikake qurrrrr ahankali yadago yana kallon Ammi itama shi take kallo aranta tana jinjina masifar wannan matar daga sallama ko lekowa batai ba amma sai faman zuba take sai yanzu taga ashe bossay bashi da lefi da yake cewa baze kara zuwa ba tamaga kokarin sa yanzu da ya iya zuwa duk da yana jin tsoro amma ya yarda ta shigo dadda ce ta katse mata tunani ta dacewa wai bamaga na nake bane anyi shiru ko barayine inma kune ta saide kusace ni dan banda abun da zaku sata acikin gidan nan😂kuji tafa taya za ayi barayi suyi sallama inbanda abun dadda Ammi ce tayi qasa da murya tana yar dariya tace wlh kazo mukoma tundade kanajin abun da take cewa alahalin ko lekowa batai ba kar muje muna shiga ta buge mu da wani abun shima qasa yayi da murya yana cewa Ammi plss wlh ba abun da zatai mana ke kifara shiga inta ga macece baza tace miki komai ba tace naqidin saida ya qara roqonta sannan ta dan daga murya sama tace baba bakine kifito ki ganmu mu
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment