Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta idar da sallar la'asr ta amsa musu sallamar suna shiga basu je ga shiga dakin ba Ameesha ta wuce ta dauko roba da wuqa da zasu yanka salad din sannan suka shiga dakin suna shiga dadda tace sai yanzu Sai kace an aiki bawa garinsu ina kuka tsaya kukuwa Azeema mace tace wlh dadda wani dan rainin hankali ne yatare mu yaci min mutun ci kuma yatafi Allah zesaka min takara sa maganar da kunbura fuska sai kace dadda ce tayi mata laifin dadda da mamaki take kallon su tare da son qarin bayani dan bata fahimci komai ba Ameesha ce ta gayra zama ta bata labarin duk abun da yafaru dadda kwa ita abun ma dariya yabata amma sai tayi qoqarin riqe abarta bata bari ta fito ba saboda yanda taga Azeema tasan ranta yabaci idan kuma tayi mata dariya zata fi jin haushi ma sai kawai tace ayya Allah sarki gaskya be kyauta ba kiyi hakuri Allah ze saka miki kuyi sauri ku gama kuci danni har na ci nawa danaga shiru tunda mungama komai idan kuci sai kuje can gidan din saikiyiwa maman tasu sallama da to Ameesha ta amsa sannan taci gaba da yanka salad din da suka suyo bawanda yaqara cewa komai har tagama taje ta wanko ta dawo sannan taqara komawa ta zubo musu ta kawo komai da zasu bukata harda ruwan sha sannan takalli Azeema tace mata bismillah kai ta girgiza mata alamar baza taci ba hararar ta tayi tace wai ke baza kicire wannan abun aranki ba shi yana can yana uzurin gabansa ya manta dake amma ke zaki tsaya kina sawa kanki damuwa abanza a wofi shiru tayi mata bata ce mata komai ba kuma bata sa hannu a abincin ba
Saida dadda tasa baki sannan ta fara cin abincin bawanda yayi magana har suka gama ita kuma dadda nata faman gyangyadi alamar bacci take ji sai Ameesha ta gama kimtsa wajen sannan tayo alwala tacewa Azeema taje tayo tazo suyi Sallah bayan sun idar da sallar ne Ameesha ta sake shirya wa tasa doguwar rigar atamfa da dinki yayi mata das kamar ajikin ta aka dinka shi sai ta dora mayafi akai Azeema de na zaune tayi tagumi tana kallon ta har ta gama sannan ta tashi sukayi wa dadda sallama suka fita ahanya made bawan da yace komai saboda Azeema taqicewa komai shiyasa itama taja bakinta tayi shiru suka ci gaba da tafiya sunqun sunqun kamar
raquma har suka qarasa gidan dasuka shiga nan made Azeema taqi sakin jikin ta har saida mama tagane bayan sungama gaisawa da Ameesha sai ta tambayeta me yafaru da Azeema ne nanma de labarin abun da yafaru tabawa mama

Mama tace maganinki kenan ke meyasa zaki zageshi bayan kinsande ya girme ki gwara da yayi miki hakan ni wlh yayi min daidai Azeema jin hakan yasa ta tashi daga gurin ta koma daki dariya mama tabita da ita tana cewa Allah ya shiryeki sai da tayi shiru sannan Ameesha ta sanar da ita cewa dadda tana gaida ita kuma tace tana tayaki murna Allah yasanya alkhairi da Ameen mama ta amsa mata sai Ameesha ta dora dagaya mata zasu tashi itama mama batajin dadi ba dajin tashin nasu haka tayi musu fatan alkhari bayan sungama kuma itana ta tashi tabi bayan Azeema tana shiga kuma taganta kwance ta kifa kanta tana ta faman kuka da sauri ta qarasa inda take tare da dago ta ta rungumeta tace haba besty wai meye haka ne kikeyi sokike kisawa kanki cuta akan abun da be taka kara ya kar ba Azeema tace dole kice haka mana tunda bake aka zaga ba tafada tana kwace jikinta daga jikinta Ameesha itade taga takanta dan ita wlh abun harma yafara bata haushi daman ita Azeema haka take kwata kwata bata iya fushiba zata dade batayi ba amma idan tayi anshiga uku kullum cikin mita take

Dan haka kawai sai tacewa Azeema ke ni wlh nagaji bari inzo intafi gida tunda abunnan yafaru sadi baki hakuri nake amma kinki hakura bansan kuma me zan miki ba tana gama fadar haka ta miqe zata fita sai kuma Azeemar tayi saurin ruqeta daka tawa tayi da tafiyar sannan ta juyo tana kallon ta tace wlh inde bazaki dena ba tafiya zanyi
Daka tar da kukan da take yi tayi sannan tasa hannu tana goge hawayen tace nadena wlh abunne sai nayi qoqarin in manta sai kuma inqara tuna wata maganar tasa maganganun sa sai yawo sukeyi min narasa dalili Ameesha tace ki manta kawai gyada mata kai tayi sannan tashiga bathroom ta wanko fuskarta sai ta zauna ta goge fuskar itama Ameeshan zama tayi suna fuskan tar juna tace ko kefa dan Allah wlh har kinyi kyan gani bakya kyau da danuwa bare kuma kuka murmushin dole ta qaqaro ta aza a fuskarta sannan tace ai baza kigane bane amma de yanzu in sha Allah komai ya wuce tace yauwa koke fa..........
nande da wasa da wasa Ameesha ta shawo kanta sai kuma suka barke da hira kamar ba gobe kiran sallah ne ya katsesu suka ankare wai har lokaci yaja haka dasauri Ameesha ta miqe tana cewa kai besty wai har lokaci yaja haka nayi magariba awaje Allah yasa dadda kar tamin fada Azeema ma tace wlh nima nayi mamaki muyi sallah to sai inrakaki tace shaf shaf suka idar da sallar sannan suka fito falo mama bata nan daki suka leqa Ameesha tayi mata sallama sannan suka qara fito wa sukayi waje Ameesha tace laa nikam kinga har zantafi bamu hadu da yaya saleem ba Azeema tace wlh kuwa saide ingaya masa idan yadawo niban ma san me yazaunar dashi awaje ba har yakai wannan lokacin tace to shikenan kya gaya masa haka sukai ta hira har suka zo inda zasu rabu sannan sukayi sallama kowa ya nufi hanyar sa Ameesha sai sauri takeyi kamar zata tashi sama abu biyu ne suka sata saurin na farko tana tunanin kar dadda tayi mata fada na biyu kuma kar yaya bossay yazo bata nan aikwa adan mintina kadan ta qaraso gida da sallama ta shiga cikin gidan dadda bata waje dan haka kawai tashiga dakin tana shiga taga dadda na lazumi guri ta samu tazauna har dadda tagama sannan Ameesha tace dadda kinga nayi dare ko wlh muna daki bamu lura da lokaciba sai da mukaji kiran sallah dadda tace to ai shikenan tundade kindawo gida lafya sai a kiyaye gaba kuma tace in sha Allahu dadda daganan dadda ta dora mata da nasiha akan zaman rayuwa sosai kwa nasihar ta shige ta har aka kira sallar isha'i sanna ta tsaya dayi mata alawala Ameesha ta qara yowa tazo tayi sallah itama.....
Abude kamar wasa har goma ta wuce amma shiru kake ji ba labarin zuwan bossay tun Ameesha na hakuri har takasa tace dadda kinga fa har yanzu yaya bossay bezoba anya kuwa zezo tafada fuskarta cike da damuwa

Dadda tace tunda kikaga haka watakil wani uzurin ne ya riqeshi ya hana shi zuwa kije ki kwanta kawai sai gobe idan Allah yakaimu tunda yanzu kinga har shadaya ta kusa bazuwa zeyiba kije ki kwanta da to ta amsa mata jikin ta asanyaye ta ta jawo katifar da suka daga dazu
ta sauke ta ta dauko zanin ta shimfida da filo sanna ta kwanta tayi luf kamar me bacci ita kadai tasan yanda takeji aranta saboda ta kwallafa rai akan yau zata bar gidan amma sai gashi Allah beyiba haka ta kwanta ta ringa tunani dan bata jin zata iyayin bacci yau................





#comment
and
#Share
More comment more typing.....
No comment no typing.................
Pls likes more


by❤xeemat.....love❤
[3/3, 9:51 PM] ~~~~writer~~~~: 💅SARKI SAMEER......💅
          by ❤xeemat....love❤

           🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

            🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
                                       ﷽
                Bismillah.......🖋
Episode21&22
                    ****************
da wuri saleem yatashi yafara  shirin zuwa wajen aikin da zeje yama gama shiryawa yafito ya gaida mama tana yimishi magana ma akam ya tsaya ya fara karyawa amma yace mata aa baya so yayi late da addu'a ta rakasa har bakin ƙofa Azeema ce ta fito da gudu tana cewa yaya wai fita zakayi ina ya qoqari ingma hada maka abun da zakaci dan Allah ka tsaya ya kusafa just give me a few minits dan Allah kaji dan murmushi yayi yace haba auta sokike infara laifi daga zuwa na nafiso inriga kowa zuwa kibari namiki alƙawari koma me kike min ki ajiye min idan nadawo zanci koda ya wuce bata rai tayi tace nifa wlh bazan bari ka zauna da yunwa ba ko ka tsaya ko kuma kaban address din wajen inzo in kawo maka gurin aikin buda baki yayi yace ke rufamin asiri in mutu maza sukaine ba mata ba daga fara zuwa ne sai kawai aga ankawo min abinci kinsan kwa yanda gurin yake da tsaro kiyi hakuri mama ce tace wai ke meye haka din wani sabon kinibibin ne da saunawa yana fita beci abincin ba sai yau zakisashi agaba da shirme kai kuma ka tsaya da tunima ka kusa zuwa,  hakan ma da kayi ai ƙara bata loƙacin kake yi ka wuce katafi dan murmushi yaqara yi sannan yace mama ai da sauran loƙaci yanzufa ko bakwai batayi ba zumudine irin nawa kawai amma yanzu tunda tanaso bari injirata ta qarasa idan kuma takai qarfe  bakwai da minti goma zan yafi da sauri Azeema tace nayarda wlh  mama tace au biye mata din zakayi  to nide ba ruwana idan kaje kasamu matsala sai hankalinku ya kwanta ko girgiza kai yayi yace mama in Allah yayarda ma bazamu samu matsalar komai ba  in sha Allah kada kai tayi ta koma tazauna tace ai sai kuyi tayi jinjina kai yayi kawai sannan yabi bayan Azeema da tunda taji yace zejirata ta koma kitchen din yana shiga yaganta a tsaye sai faman aiki take da sauri gyaran murya yayi ta dan juyo ta kalle sa tace laa wai biyo ni kayi ai nama kusa kaje ka jirani a falo kaji yace to sannan yajuya yana ce mata sauran ki minti goma tace kafin lokacin ma ai nagama yace Allah yasa tace amin sannan tadan zuba ƙullin dake gabanta dan tabbatar da man yayi zafi yana zubawa kuwa yayi ƙara cuuwwi nan da nan tafara sakin ƙosai da Sauri da sauri  tana gama daidai yanda tasan ze isheshi sai ta kashe gas din ta zuba masa a plate sannan ta dauko cup tazuba mishi kunun gyadar da hadashi tundazu tazuba a flax sau yanzu ta tsiyaya mishi daidai yanda tasan ze isheshi sannan ta dora akan faranti tare da cokali sai yar ƙaramar robar sugar ta dora masa duk wannan abun adan ƙanƙanan lokaci tagama komai tafito tace gashi har nagama aide lokacin be cika ba ko daga mata kai yayi sannan yace gsky kinyi sauri me kika yiminne haka akeso sai naci tace idonka yagane maka tunda gashi yanzu zaka gani tana gama fadar haka ta ajiye masa waro ido yayi yace wow gaskiya auta godiya nake kinmin suprise wlh rabona duk son da nakeyi wa abunnan na dade banci ba bansan meyasa ba kwason yinshi tace wlh nima ina so mama da baba basa sonshi shiyasa bamufiya yinshi ba tace yauwa yaya wai har yanzu basu ƙara kiranka  yace wlh basu kiraba tace to anjima idan ka dawo sai ka ƙara gwada kiran su kaji me ake ciki yace nima tunanin danakeyi kenan bari idan nadawo din sai inkida tace hakan yayi tace bari inbarka kaci inje in ƙarasa wancan dan kai kadai nayiwa yanzu yace to sannan yaci gaba da cin abunshi hankali kwance duk saurin da yakeyi hakan besa shi cin abincin da sauri ba ci yake kamar yanda ya saba lokacin da yagama bakwai da rabi daidai sannan yatashi ya ƙara  gyara jikin shi sannan ya nufi dakin mama da tun dazu tabar falon yana zuwa yayi sallama ta amsa masa sannan ya shiga daga bakin ƙofa yace mama ni nagama zan wuce tace Allah ya kiyaye hanya ALLAH ya tsare hanya yace amin sannan yajuya ya fita da sauri ya dan leƙa kitchen yace wa azeema shi ya wuce itama da addu'a tabishi sannan ta rakasa har bakin hanya saida taga ya hau napep sannan ta juya ta koma ..............

*S.A.S SPATIAL HOSPITAL*
lokacin da ya qaraso gurin ƙarfe takwas saura minti  biyar Allah ya soshi be makara ba  inda suka saba zama idan sunzo shi da sauran jama'ar wajen basu dade ba kwa sai ga Dr.shettima  ya iso wajen suna ganinshi kowa yafara gaida shi yana amsawa sannan aka bude masa office dinshi ya shiga ciki yazauna bayan wasu yan mintina kuma ya bukaci su fara shiga
daya bayan daya suka ringa shiga suna fitowa duk wanda yafito kuma sai ya wuce inda zeyi nashi trainning  ahaka har akazo kan saleem  da fara'a a fuskar shi ya shiga ciki  yana shiga kuma ya tsugunna har ƙasa ya gaida shi da mamaki dr...shettima yace haba abokina  da girman ka zaka tsugunna min ina jinma fa ka girme ni amma ka tsugunna min tashi dan Allah kar wani yazo yaganka ai yama dariya yanzu a wannan zamani ko manyama idan za agaidasu ai ba a tsugunnawa yaƙarasa fada yana yar dariya tare da miƙawa saleem hannu alamun suyi musabaha da farko da ƙnyarda yayi saida yaga dr shettima ya dan yi masa hararar wasa yace kai nifa ba ayimin irin wadannan abubuwan ni kowama nawane inzaka saki jikinka ma kasaki dan atare dani zakayi trainning dinka tun jiya ma na riga nagama da file dinka aiki kawai zamu fara idan nagama sallamar mutane akwai wata patient da za a cire mata appendix dan haka sai ka shirya zaka fara ganin yanda ake farke mutum ko antaba yi agaban ka
yace a'a yaude zan fara gani jinjina kai dr shettima yayi sannan yace zaka gani yau kuma atsarin aikina saudaya nake koyawa mutum abu saboda bana san wasa idan akan harkar aikine dan haka na dauke ka dan naga alama kammar bazakayi wasa  ba kuma na yaba da kwazonka  shiyasa dan haka to be a careful ka maida hankali sosai kayi aiki kar kasa wasa aciki saleem yace in sha Allahu zan maida hankali nagode da shawarar ka yace ba komai ka dauke ni amatsayin yayan ka duk wani abu da baka ganeba ko ya shige maka duhu kasanar dani karkaji komai ni kuma zanyi maka bayani in Allah ya yarda
Saleem ba ƙaramin dadi yaji ba yace nagode nagode Allah yabiya maka bukatunka yanda ka min kaima Allah yayi maka yace bakomai ai duk yiwa kaine ring din wayar dr shettima ne ya katse musu hirar su duba screen din wayar yayi dan ganin me kiran nashi SAM naga anyi saving dashi akan screen din wani killer smile yasaki tare da saurin dagawa saboda kar wayar ta katse yana dagawa ya kara wayar akunne yana cewa shegen gari sai yau aka tuna dani kullum sai nakiraka amma dan rashin mutunci baka daga wa kuma baza ka kira ni ba ko shiru akayi daga dayan bangaren jin hakan yasashi cewa kaifa matsalata dakai kenan ka kirani kaqi magana kuma nima nayi maka magana amma kayi min shiru wlh baka da kirki ko kadan nide banji me akace daga can bangaren ba kawai de naji yace wai da gaske ko da wasa kai amma naji dadin hakan Allah yadawo mana dakai lafiya kace muyi babban shiri yauwa daman inaso muyi magana kan batun sabbin ma aikata acikin mutane hamsin da wani abun gasky wadanda muka dauka basufi ashirin da biyar ba saboda yawancin su duk basu cancanci adauke suba shiru yayi yana sauraron abun da dayan yake gaya masa sai can kuma yace ok ba matsala ammafa inaganin basai an ragesuba saboda muna bukatar mutane da yawa saboda dayan bangaren da aka bude kuma babu wasu ma aikata sosai aciki inaga kawai abarsu baza arasa abun da zasuyi ba amma inkana ganin arage din sai yafi sai murage din ko yakace sake yin shiru yayi yana sauraron sa
Sannan yace ok zan qara bincikawa badamuwa yauwa sai kuma....
Begama fadar abun da yakeso yace ba yaji wayar tayi ƙara ƙit alamun ankashe wayar kenan bin wayar yayi da kallo sannan yasaki murmushi yace hmmm baza ka taɓa canzawa ba Allah yashirye ka ace mutum baze taba jiran kagama magana ba shi inya gama tashi maganar shikenan sai ya katsewa mutum waya yana magana yana kallon saleem da yayi shiru yana sauraronsu sai can kuma yace kayi hakirifa ina ta waya nabarka da kai kadai saleem yace bakomai wlh naga alamar kamar ma baka ji dadin kashe wayar dayayi ba dr shettima yace wlh banji dadi ba ban gama magana ba yakashe kuma daman halin sane yasaba yiwa mutane haka bashida mutunci wlh ko kadan gashima kuma nan da two weeks zedawo shikenan mun shiga uku sai ya takurawa kowa da masifa kaima wlh kayi hankali dashi dan abu kadan zakai mishi ya koreka daga aiki any mistake game over saikabi a hankali jinjina kai saleem yayi sannan yace shine me asibitin kenan
Yace eh shine wlh amma wlh yaba da wuyar sha'ani sai ka koyi zama dashi zaku zauna lfy
Saleem yadanyi murmushi tare da jinjima kai sannan yace to Allah yabamu ikon iyawa dashi Allah yasa muhadu dashi lfy mu rabu lfy ƴar ƙaramar dariya yayi sannan yace aikwa da ƙyar ace kuhad ku rabu batare da wani abu yahadaku kawai de kayi addi'a Allah yasa matsalar tazo da sauƙi danshi mutum ne wanda ba a iya mishi haka de sukai ta tattaunawa akansa kafin daga bisani dr shettima yacewa saleem kaga muata batawa mutane lokaci kaje ka jirani a waje kafin infito sai muwace yace to sannan yatashi yana ƙara yi mishi godiya sannan yafita yana fita mutane suka ci gaba da zuwa har yagama dasu gaba daya sannan yatashi yafara shirin fita teaiter din da zasuyi ƙarar waya yaji akan table dinahi da mamaki yajuyo tare da ƙarasowa kusa da wayar sai kuma ya tsaya yana kallon wayar to waye yabarta anan begama tunani ba yaji anyi noking yace come in dasallama saleem yayi sannan ya ƙaraso inda yaji wayar tashi na ringing yace afuwan dan Allah wayata namanta yafada yana ƙoƙarin daukar wayar sai kuma ta katse girgiza mishi kai dr shettima yayi tare da dan matsawa dan yabashi damar daukar wayar aikwa saleem na dago da wayar idon dr shettima ya sauka akan hoton wellpaper din da yake kan wayar saleem ƙara zaro idon yayi domin tabbatar da abun da yagani gaskiya ne ko kuma gizo ne amma da maida idonsa kai saleem har yasa wayar a luck yajuya ze fita da har ze tsayar dashi amma ba halin yin hakan saboda saleem har yariga da ya ƙarasa fita tunani ya shiga yi inbe manta ba hoton da yagani kamar fuskar yarinyar da suka hadu jiya tazage shi.........


#comment
and
#share
#likes
More comment more typing.....
No comment no typing.................

❤xeemat.....love❤
[3/4, 8:12 PM] ~~~~writer~~~~: 💅SARKI SAMEER.....💅
               by❤xeemat.....love❤

                🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
                             ﷽

                Bismillah..........🖋
Episode 22&23
                  ******************
Dr.. Shettima Girgiza kai yashiga yi a fili yace kai ba ita bace kawaide gizo ne mema ze hadata da wannan yaron wata zuciyar ce ta bashi amsa da cewa inkuma budurwarsa ce tunda har yadora pic dinta amatsayin wallpaper sa wata zuciyar tace kode qawar sace nanma de girgiza kai yayi yace ai basa kama da qawarsace tun ajiyan zangane hakan in kuma budurwar sace nanma yaron baze kulata ba tunda shi yana da hankali daga ganinsa baze kula irin wadannan matan ba yarinyar daga ganin tama kasan ba abata tarbiya ba agidan su tunda har take iya cin mutunci nagaba da ita shi sai yanzo ma yake tajin wani bacin ran na taso masa wai shi zatacewa dan iska me bin mata alhalin ko ganinshi batayi ba amma take dorarwa waya sani ma ko itace me bin mazan daman ance duk abun da kakeyi gani kake kowama na aikata irinshi arayuwarsa shiyasa ta fadi haka shikadai sai faman saqa da warwara yake yi sai can kuma yasaki wani irin murmushi kamar bashine yake bacin rai yanzu ba ,ba komai yasashi wannan murmushin ba face tunawa da yayi da dayar yarinyar da loqacin da ta ruqe mishi hannu tana ce mishi dan Allah bawan Allah kayi hakuri karabu da ita na roqeka kaji plssss harga Allah hakan da yarinyar tayi ba qaramin tafiya yayi dashiba gashide yarinya ce batafi qanwar qanwar sa ba amma ta burge shi tun ganin farko dayayi mata yaji ta burgeshi shi tunda yake be taba jin yanaso yayiwa wata mace magana ba da nufin wai ta burgeshi sai akan yarinyar nan yar qarama abun har mammaki yake bashi wai shi ya aika yaro yace ayi mishi magana da mace lalle yarinyar nan taciri tuta ta karya mishi record  saide bemasamu maganar da ita ba waccen kucakar yarinyar tazo ta bata mishi rai da harma yafasa maganar da yayi niya
gemunshi yadan shafa tare dayin wani murmushin yace Allahn da yahada ni da ita jiya shi zeqara hadani da ita nan gaba in Allah ya yarda zamu qara haduwa dake small girl sunan daya samata kenan tundade besan sunan taba nocking din office din da akayine yakatse mishi tunani iznin shigowa yabayar
wata nurse ce tashigo tace sir we are ready ok I'm coming juyawa tayi tafita shi sai yanzuma ya tuna ashefa zasuyi aiki amma yazauna yana tunanin abun da bashida amfani a halin yanzu agashi har goman ta kusa ma shaf shaf ya gama shiryawa sannan yafito
yana fitowa ba kowa agun sa saleem da yake ta faman jiran fitowar tashi yana ganinshi yatashi da sauri ya miqa hannu dan ruqe mishi lap code din da yaruqo be hanashiba ya miqa mishi sannan yayi gaba shikuma yamara masa baya wani dogon corridor suka mika sai da sukayi gaba kadan suka yi kwana suka shiga wani daki wanda dagani daman kasan titer room ne nurse biyu ne adakin kowa yayi shigar fara aiki cikin kayan aikin su sky blue sai farar hula da farin face marks suna shiga dr shettima ya karbi rigar hannun saleem ya shiga wani daki da yake acikin dakin da suke anware shine daman sboda shiga canza kaya ko wani uzurin privacy sai ka shiga kayi har da toilet aciki bayan ya shiga yagama shirya wa yace wa saleem ma yaje ya shiryo
shiga yayi be jimaba ya fito shima cikin shigar kayan aikwa ba qaramin amsar sa kayan sukaiba yayi matuqar kyau acikin su yana fitowa kuma ya tsaya daga baya saboda shi ba abun da ze taba kawai kallonsu zeyi sai wata yar joter da pen da dr shettima yabashi yace yaringa recognize din duk abun da ya fahimta abun da yake da tambaya idan angama sai yayi yace to sannan yafara aikin dan shine zaiyi aikin sauran dan tai maka masa zasuyi da wani abun cikin kwarewa da kwazo irin nashi yafara gaba tar da aikin saleem ya tattara duka hankalinsa da nutsuwarsa kan abun da akeyi yana yi yana rubutawa kamar yanda akace kuma yana fahimta Yanda ya kamata...........

Yau nashiga busy da yawa kuyi maleji da wannan da babu gwanda ba dadi
_________________®___________________
Announcement

DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment