Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

karabu da ita kawai yau daya de naga ai ko gurin qawar tata ma bata shiga ba kuma zece ta koma gida hakan ai be dace ba kabarta yanzu muje dukan mu nima inaso inga marar lafiyar yafada tare da miqewa,
Saleem beyi masa musuba yace to sannan itama ta miqe suka fito a tare saida suka fara zuwa wajen dr jamil suka taho tare dashi sannan sukaje wajen Ameesha suka duba ta sannan suka fito Azeema sai faman matsar kwalla takeyi da ta tausayawa bestyn tata addu'a tayi mata Allah yabata lafiya office din shi sika qara komawa dukan su bayan shigarsu ne saleem yace sir bari inje kan aikina anajirana ke kuma saura ki qara yin wani wajen kiga yanda zanyi dake anan yana gama fadar haka ya fice daga ciki dan har yanzu haushinta yake ji,haka ta qari zaman ta shiru ba magana dan har yanzu be kulata ba ko kallonta ma beyi ba har aka kira sallah ya miqe yana niyar fita yace kishiga ciki akwai toilet aciki zamuje masallaci yana gama fada be jira amsar taba ya fice ajiyar zuciya ta sauke da daman duk atakure take dashi zaman da sukayi waje daya sai taji duk ta qosa tabar wajen amma ba dama,miqewa tayi taje tayo alwala bata tsaya duba sallaya ba ta curo dan kwalinta ta shimfida tayi tayar da sallah bayan tagama tayi addu'a ta nike ta koma inda take bata dade da zama ba suka shigo shi da saleem shiya fara shigowa yazauna a mazaunin sa sanna saleem ma yasamu kusa da ita ya zauna tare da mika mata ledar hannun sa da ya karbo mata abinci acikin hospital din takeaway ce aciki sai drink da water saida ya bude mata sannan ya miqa mata yana bata yace bari inkoma kici abincin sosai sannan idan da akwai wani abun da kike so saiki gaya wa yayanki ko kice yakirani yagaya min da ba yanzu zan dawo ba tace to nagode adawo lafiya yace Ameen sanna yajuya yace sir sai anjima, "ok" yace mishi kawai sannan yacigaba da abun da yakeyi shikuma ya fita,
da farko da kinci tayi amma ganin tana jin yunwa gashi kuma ba kallonta yake ba yasa tafara ci a hankali sai kace wacce akace sai taci ta dole har tagama kwa be kalle taba ahaka har aka qara kiran sallah yaje yayi ya dawo lokacin itama ta idar da tata,saleem ba dawo ba sai daf da magari ba yana shigowa yace ta taso su tafi sallama sukayiwa dr. Shettima sannan suka fita.......


*BOSSAY*

yau tunwajen la'asar ake neman dadda amma ba aganta ba hankalinsu duk yabi ya tashi ko ina sundu ba amma basu ganta ba abunde yafara basu tsoro dan yanzu sallar isha'i ake kira amma bata dawo ba haka kowa ya wuce dan gabatar da sallah kafin adorable daga inda aka tsaya bayan sun idar da sallah a masallaci bossay yafito yabiyo hanyar da wowa gida yana ta faman sauri yazo daf da gate din gidan sai yaga kamar gibtawar mutum ta gefen shi da har ya share ze tafi sai kuma yafasa yabi inda yaga anyi yana zuwa kwa yaga dadda ta rabe ajikin garu da mamaki ya tsaya yana kallon ta yama kasa magana ganin yaganta yasa ta harare sa sannan tace to uban sa ido ashe ka ganni ni wlh banason ganin ka shiyasa ma na buya inbari sai ka fara shiga sannan inshigo amma saida idon ka ya hango ni,
da qyar ya iya budar bakinsa yace I na kika je sai yanzu kika dawo duk kinbi kintayar wa mutane da hankali kallon sa tayi sannan tace to ubana shaqeni ingaya maka tunda kaine ka haifeni ko kuma mijina sukadai ne ne nasan zasuyi min irin wannan tambayar to bazan fada ba ta gama maganar tana ratsawa ta gefen shi zata wuce hannu yasa ya ruqota sannan yace dadda baki da gaskiya gashinan nagani a idonki kuma tunba yauba na fahimci baki da gaskiya akwai wani abun da kike boyewa dadda yau inason sanin ko ke wacece kuma a ina kika samo Ameesha daga gani ba jininki bace ita saboda ko kadan bakwa kama kigaya min gaskiyar wacece ke in bahakaba kuma wlh zandau mataki akanki ko in hadaki da 'yan sanda watakil su zaki gaya musu gaskiya idan nu baki gaya mana ba ya qasa fada tare da dawo wa gabanta yana qara cewa ke nake saurare yanzu nake sonji kuma dole kigaya min inba hakaba daga nan sai police station dan ko gidan nan bazaki shiga ba in kuma kina ganin qarya ne gwada kiga aiki da cika wa.............✍


*yauwa naji wasu suna ta tambayata wane group za sushiga a page din baya ai na fada nace duk wanda yake a facebook yayi searching din group din sarki SAMEER sannan yayi join anan zanringa yin posting....
Yan WhatsApp kuma suyi min magana ta number ta insaka su a group din whatsapp 08124226526*


Kar kumanta da comment ko like da share..
[3/15, 11:04 PM] ~~~~writer~~~~: 💅SARKI SAMEER....💅
           by❤xeemat.....love❤

             🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

                🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
                             ﷽

                    Bismillah........ ✍
Episode40-41

         """"""""""""""""""""""""""""""""""

Tunda yafara maganar dadda take binshi da kallon mamaki dan ba qaramin mamaki yabata ba saida taji yayi shiru sannan ta kallesa tun daga sama har qasa ga mamakinsa saiga kawai tasaki murmushi be gama mamakin ba saida yaji ta tace to bismillah mutafi ko ance maka ina tsoron 'yan sanda ne ni bana tsoron kowa sai ubangijin da ya halicceni dan haka ka kaini gaba da wajen 'yan sanda ma inyaso su kasheni bashikenan ba tana gama fadar haka fusge hannun ta daga  ruqon da yayi mata sannan tace muje mana ya ka tsaya shi harga Allah tsoro ma tabashi sai yaga kamar ma ba itaba to kode mutanen boye sun shafeta ne inbahaka ba kalli fa ba alamar tsoro a tattare da ita kuma shi yayi hakane dan ya tsoratata sai gashi kuma taqi tsoratan katse mishi tunani tayi dacewa kaga kana batan lokaci nikazo mutafi amma still de yakasa tanka mata koda kalma dayace suna cikin haka faruq ya qaraso gurin da saurin sa yana zuwa ya rungume dadda yana cewa sweet heart ❤ ina kika shigane duk kinbi kintayar min da hankali bakiga har na rame yafada yana raba jikinsa da nata kallon shi tayi tace nibanga alama ba gakanan bulbul dakai harma qiba ka qara a iya yau daman kafiso intafi ko fuska yadan bata yace kefa wlh matsalace dake duk ba wannan bama gaya min inda kikashiga aka nemeki aka rasa har nafara tunanin zuwa gidan radio da gidan tv a fara cigiyar ki koda gawar kice muka samu hankalin mu ze kwanta amma fa da sai nafi kowa shiga damuwa idan naga gawarki kin mutu kinbarni hannu tasa ta talle mishi qeyar sa tace saide kai ka mutu amma baniba kawai saikai ta jamin mutuwa tode gashi na dawo da raina kuma mutuwa sai ka mutu kabarni dan sa naga tattaba kunnen jikata katseta yayi da cewa to kin manta dani zata samomi ki tattaba kunnen idan kuma na mutu to taya zaki samesu daquwa ta cila masa tace kaifa dadina da kai baka da ta ido wlh kuma nama fasa baka itadin wani zanbawa dariya yayi yace to baga kiba inkika hanani ita ai sai kiban kanki ko daman tunda nace ina sonta kike kishi da ita kinga dan sawal wali zaki liqe min ko to ni bake nakeso ba nafison kamar ni yafada yana kallon jikinsa sai kuma yakalleta tare da daga gira daya banza tayi dashi sai daga baya kuma tace kai ni banda lokacin shashancin ka yanzu katafi kabani guri yar dariya ya qara yi sannan yace intafi ke kuma fa ai qafata qafarki kizo mushiga daga ciki kigaya mana inda kikaje juyawa tayi ta kalli bossay da yayi tsaye agun ya hade hannuwan sa a kirji ya zuba musu ido kawai kamar wanda aka dasa agun abun duk yabi ya isheshi yarasa ma mezeyi mata,
tana maida dubanta ga bossay sannan tace ko kafasa ne mutafi mana sauke hannun sa yayi bece mata komaiba yabi ta gefenta yayi wucewar sa dariya tayi aranta tace yo ni yaro wane darene jemage be ganiba har ni zaka dagawa hankali to uwarka ma kar nake kallonta bare kuma kai haihuwar yanzu yanzu mtsw taja tsaki da qarfi faruq ne gakalleta yace ke kuma ke dawa kike tsaki ko maganar da na fada ce take miki ciwo to kiyi hakuri zan aureki amma sai lokacin da jaki yayi tsawo falwaya tai ganye hararar sa tayi tace naga alamar kafara shaye shaye ni wuce mutafi gaba yayi tana binshi ahaka har suka shiga cikin gidan suna zuwa falo suka tarar da Ammi nafaman yiwa bossay fada wai tana yi mishi magana yayi mata banza ya shigo gida ko sallama babu sai faman hade rai yakeyi shigowar sune yadaka tar da ita da sauri ta qarasa kusa da dadda tare da rungume ta tana cewa faruq a ina kasamo ta dadda ina kika shiga duk kintayar mana da hankali tafada tana raba jikinta da nata tana jiran amsar ta dadda ta dan saki murmushi tace ayya kuyi hakuri dan Allah wlh gidan wata qawata naje lokacin da na fito kuma kina bacci shiyasa kawai na tafi ban sanar dake ba gashi kuma hira tayi dadi bansam lokaci yaja haka tana gama fada ta samu kan kujera ta zauna Ammi binta tayi da kallo amma bawai dan ta yarda da abun da tafada mata ba kawai de zata rabu da ita tunda de bataso ta fadi gaskiya to sai su rabu da ita dan haka kawai saitace to ai shikenan tunda kindawo lafiya amma daga yanzu duk sanda kikaji kina son zuwa guri kisanr dani tuk lokacin fitar taki tayi sai faruq yakaiki ko kuma Aliyu ko basa nan ma ai aysher zata iya kaiki amma dan Allah karki qara fita bada sanin kowa ba tafada ayayin da take nufar kitchen dadda to kawai tace mata sannan ta ja bakinta tayi shiru faruq ne yace mata to kinji de dan haka sai kiringa fada ni kuma kullum zankaiki ai kece kedin ta dabance dole ko me nakeyi inbarsa inzo inkai amarya ta ko ina takeso amma wlh kidena fita ke kadai dan a unguwar nan akwai 'yan yankan kai zasu daukeki suje subawa aljanun su ke shikenan kin tafi kenan yafada yana qumahe dariyar sa dan yasan yanzu zata fara yi mishi bala'i ........
Ilai kuwa yana gama fadar haka ta haushi da duka waikai dan Allah yaushe zaka dena jawa mutane bala'i suna zaman lafiyar su baka da zance kullum sai yiwa wani mummunan fata to koma mekake yi ya koma kanka sannan tace kaini dan Allah ma daga yau karka qara zuwa inda nake tunda baka da halin kirki dan kaga ina wasa dakai shiyasa ka rainani to zan dena ka kusa dena ganin dariyata suna cikin wannan abun nasu,   
su Ammi suka fara fito da abinci ita da sannan suka jere akan dinning faruq ne yafara miqewa sannan yamikawa dadda hannu wai ta tariqe ya tasheta amma sai taqi harda juya masa kai irin gayawa qeya dankwali yabaka amsa dariya yayi yace kinsan de daukar ki ba wahala zata minba dan haka gwara kitaso inkuma ba hakaba hmmm kinsan sauran tana jin hakan tasan kuma bata ido ce dashiba tsaf ze iya aikata hakan dan haka ta miqe tace kaide wlh kafiya takura jan hannunta yayi yace naji koma me zakice saida yaja mata kujera   sannan yasake ta ta zauna bajimawa sauran yan matan gidan ma duk suka fita kowade ya hallara "amma banda bossay da tun shigowar su da yaganta ya yashi daga wajen yatafi part dinshi dan acewar sa yana son kasancewa shikadai san yasamu damar tunani dayawa ko ze gano wani abun"
Ammece tace wa mimi zekikira yayanku yafito shi muke jira da gudun ta kwa ta tashi ta nufi hanyar dakin shi bata dade ba ta dawo tace yace wai yaqoshi baya jin yunwa "ok"Ammi tace sannan furairah ta fara yin sarving dinsu nande kowa yafara cin nasa bamai magana acikin gurin yayi shiru sai qarar cokula kawai daya bayan daya suka fara tashi daga nan wasu suka wuce domin su kwanta wasu kuma suka zauna a falo suma kuma bayan wani dan lokaci kowa yatafi ya kwanta,......

      "Washe gari bayan sun kammala breakfast suna falo dukan su dadda tacewa faruq to dan albarka qyande alqawari cikawa sai kazo mutafi ko kallonta yayi sannan yace to je kishirya kifito nutafi Ammi ce tace ina kuma zaku yace asibiti zankaita ance yau doctor din ze dawo shiyasa tace inkaita ta gani,

Ammi tace to kuna da tabbacin ayu ze dawo kuma ayau zefara yi mata aikin ni inaganin da kun hakura da zuwan nan kubarwa gobe koma jibi lokacin komai yafara daidaita kinga sai kije hankali kwance ko yakika ce ai hakan yafi ko tafada tana kallon ta dan jin abunda za tace dadda hade rai tayi tace nifa komai zaki fada sai de kifada dan koda 'assayada dita sai naje Ammi shiru tayi sannan tace to Allah ya kiyaye hanya Allah yabata lfy sai kundawo faruq idan akwai wata matsala sai kayi gaggawar sanar damu yace to Ammi yana fada yace to ai sai kitashi mutafi ko tashi tayi ta gyara mayafinta da ta ruqoahi ahannu  tun lokacin data fito daga daki tana gama gyarawa faruq yace bari indauko mukulkin motar tace to sannan ya haura sama da gudu yana shiga ba jimawa yadawo riqe da mukullin motar "ba bata lokaci suka fice daga falon suna fita suka shiga mota faruq ya tayar da motar sannan yajata da gudu suka  bar gidan gudu yafara yi kamar yanda yasaba saida dadda ta dakatar dashi sanan yadan rage gudun yana tafiya daidai shi ba guduba shi ba ahankali ba ahaka har suka qarasa.....
tundaga baking gate suka ga anata share share daza sushiga kwa saida aka tsaidasu aka bincika su sannan suka shiga ciki kuwa jama'ane ta ko ina kowa da abun da yakeyi ana ta gyare gyare sude sunga ikon Allah basu san neyake faruwa ba komai za ayi oho basu da me basu amsa parking yayi sannan suka fito suka nufi ciki bayan sun shiga kuma sai suka rasa inda zasu dosa da qyar de suka iya kai kansu wajen da suka tsaya ranar nan dadda tace to kaje kakira mana shi mana muji ya ake ciki ko shiru yayi sannan yace nifa dadda wlh ba inda nasani kawai mu tsaya anan idan Allah ya kawo mana wani sai mu tambaye shi tace in kuma  bawanda yazo fa sai muyi ta zama kenan yace in Allah ya yarda ma baza murasa ba "yana gama rufe baki kwa sai ga dr.shettima kamar anjefoshi sai faman sauri yake harze gotasu ze wuce dadda tayi saurin dakatar dashi tace bawan Allah dan Allah tambaya muke ganin ita tsohuwace yasa shi dakatawa duk da irin saurin da yakeyi ahankali yace inajinki tace dan Allah daman mune wadanda muka kawo wata yarinya da za ayi mata aiki akace sai babban likita yadawo kuma ance yau ze dawo shine muka zo muji ko ya akciki dan dawowa yayi kusa da ita sannan yace ok to kujira yanzu haka ma da kuka ganni sauri nake zanje na dauko shi a airport dan ko gida ma basu san da saukar shiba yace nan ze fara zuwa idan ya dubata sai yaje gida dan haka ku kwantar da hanjalinku yanzu zamu dawo tare kujirani hamdallah dadda tayi sannan tace to shikenan Allah ya dawo daku lfy gsky naji dadi sosai kayi sauri kaje dan Allah dan na matsu inga anyi mata aikin nan tadawo gareni jinjina kai yayi sannan yajuya ya fita yana fita ya afka mota yajata a sukwane yayi waje yana zuwa ya doka horn da sauri gate man ya wangale mishi gate din shikuma yadanna hancin motar ya kwasheta a guje ya fice gudu kawai yake ba qaqqautawa cikin yan mintina kadan ya qaraso airport ✈yana zuwa kwa yaci sa'a be makaraba domin lokacin da yazo lokacin jirgin yagama sauka Hamdalah yayi dan duk azatonsa idan yazo ze tadda shi yana jiran sa shiyasa yake ta gudu saigashi kuma yazo akan lokaci fita yayi daga motar ya tsaya agaban motar yana jiran fitowar sa sabda already jirgin yagama sauka dan har wasuma sun fara fitowa saida yadade agun dan yana tunanin ma mutanen ciki sungama fitowa gaba daya amma begansa ba to kode be tahoba sai kuma yatuna ai baya magana biyu tunda harya kira yace yataho yadauke sa to kwa yasan dole yataho din kuma watakil abun nasane ya motsa yanzu haka yana cikin jirgin sai yaga damar fitowa sannan ze fito gajiya yayi da jiransa dan haka yafara takawa zuwa gaban jirgin da niyar ya leqa yaga ko yana nan din dagaske tunkan yaqarasa ma yaga ansako qafa daya dakatawa yayi saboda yana da tabbacin shine dayar qafar aka sako ahankali kamar ba a so ake ajiyeta sannan yafara saukowa gaba dayansa har ganganr jikin sa ta bayyana tundaga qasa nafara kallonsa har zuwa sama bansan lokacin da na sume ba na dawo saboda tsabar tsorata danayi bazan iya kwatan ta muku abun da nagani ba yanzu dole sai nabari na kwakwalo jarumta zuwa gobe sai in bayyana muku........✍



*tode daga yau nagama posting kamar yanda nagaya muku sai a group biyu kacal zan ringa yi saide kuma ko wani ze iya yin share to another group*

Follow me all👇

wattpad@xeemat
Arewabooks@Azeemadahiru
Facebook @Azeemadahiru(xee
Whatsapp@~~~~~writer~~~~~
My WhatsApp number is 08124226526
💅SARKI SAMEER....💅
           by❤xeemat.....love❤

             🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

                🌹الحَمْدُ ِلله سبحان الله الله أكبر🌹
                             ﷽

                    Bismillah........ ✍
Episode42-43

         """"""""""""""""""""""""""""""""""

tundaga qasa nafara binsa da kallo har zuwa sama masha Allah dogone amma bacan ba sosai yana da dan budewa da faffadan qirji gashi da cikar haiba kallo daya zakai mishi kagane wannan ba irin sauran maza bane shidin na dabanne ya shabam bam da sauran danni tunda nake bantaba ganin mutum me irin zubin halittar shi ba domin abar kallo ce koda ita kadai akabarka akace kai ta kallo kar ka kalli fuskar shi to hakan ma ba qaramin dadi zemaka ba domin zakai ta kallane batare da kagaji ba tunda nayi mishi kallo daya jiya haryau bandawo daidai ba sai tunanin shi nake jikin shi sanye yake da jens ne yellow sai rigar ma yellow ce sai wacce ya dora akai kamar ta sanya me gashi gashi ita kuma baqace  kuma ta sauko mishi qasa har wajen gwiwa kuma tana da huciki mma besaka hular ba ahankali nafara bin fuskar shi da kallo fari ne sosai har wani jaja yake kamar idan kasa yatsa katabashi jini ne ze fito  tundaga kan lips dinshi nafara bi da kallo dana kasa gane wane irin kalane ko kuma abun yashafa oho ammade gashi nan kamar red kamar pink kalar tayi kyau sosai kuma ba babba bane dan qarami ne amma ba sosaiba sai dogon hancin shi sai idanun sa dara dara gasu farare tas dasu sannan sexy ne sai eyelashes din sa dogaye ga cika kamar na mata sai eye brown dinsa da ta wani fidda shap kamar anyi shaving dinta asaite take gata baqa kamar ansaka mata kwali sai gashin kansa da yake akwance luf yasha gyara dan harya zubo kan goshin anyi masa wata kanan nada yayi kamar macaroni sai Bluetooth da ya maqala akunnen shi guda daya hannunshi daya  a cikin aljihun rigar jikin shi dayan kuma yana ruqe da trolley ahankali yake tafiya kamar bayaso da sauri dr.shettima yaqarasa gurin sa tare da yin hugging dinshi tare da cewa you are well come my man I'm so happy to see you I wanna miss You too much duk wannan abun da yake besamu arzikin anyi mishi magana ba kuma yana tsaye ko motsi beyi ba bare kuma yamayar masa da hugging din dayayi masa saida yagaji dan kansa sannan yataba jikin shi danashi yana ta faman sakin murmushi da gaske de yaji dadin dawowar tasa  kuma qin kulasan dayayi be damesa ba hannu yasa yakarbi trolley din hannun sa sanna ya ruqe hannun sa suka fara tafiya har suka qarasa wajen motar sannan ya bude mishi ya shiga sai ya bude back seat yasaka trolley din sannan ya zagaya ya shiga mazaunin driver yazauna tare da yiwa motar key tare da yin reverse yasai ta kan mota sannan yafara tafiya a tsanake dan juyawa yayi ya kalle sa saiga ya kwanatar da kansa jikin hannun kujera ya lunshe idon sa kamar me bacci ganin hakan yasa shi yin shiru shima dan yasan tunda yaganshi haka to ko meze ce mishi ba amsa ze samu ba dan haka gwara kawai yayi shiru shima,,

ahaka bawanda yayi magana har suka qaraso hospital din yana gama parking yaqara kallonshi tare da kiran sunan shi yace SAM muqaraso fa shiru ba amsa kuma har yanzu be bude idonsa ba saida yagama shan qamshin shi sannan ya bude idon sa yadan kallishi batate da yace komai ba kuma yabude motar yafita da shima budewa yayi ya fito yarufe qofar yazagayo ya koma kusa dashi yace ka tsaya ko sai na dauke kane sai yanzu ya bashi amsa shima ba bude baki yayi ba kwai uhm yace mishi dr. shettima sai yadanyi murmushi yace ai zan iyane kar ka ganka wani qato dakai ba wahalar dauka zakamin ba jinjina mishi kai yayi sannan yafara tafiya ba tare da yabashi amsa shima bayansa yabi dake kowa yasan da dawowar sa yasa ba kowa awaje kowa yakama aikin gabansa gudun jawa kai matsala any mistake game over qaramin abu zakayi yayi firing dinka dan haka kowa yake taka tsantsan idan yazo dan surabu lafiya tunda ba dadewa yakeyi ba idan yazo,

yana tafiya yana kallon asibitin har suka shiga ciki nanma kalla yaringayi office dinshi asama yake dan haka direct suka nufi sama saide suna dab da fara hawa benen saiga dadda tsudum abayansu tan cewa to yaza kutafi bayan kasan tundazu muke jiran ku tsayawa dr.Shettima yayi saboda yagane muryarta amma banda dayan dan har ya qarawa motarsa mai be tsaya sauraron taba duk da yasan dasu ake magana dr.shettima ne yace kiyi hakuri baiwar Allah yanzu yadawo kinga dole sai yadan huta tukunna ze samu damar fitowa kuqara hakuri tunda saboda aikin nata nema yazo nan da baze zo bama kujira kinji baba jiki asanyaye dadda tace to aishikenan yafito lafiya munade jiransa yace to karkidamu bawani dadewa zamuyi ba yana fada ya wuce shima dadda komawa tayi kusa da faruq, faruq na ganinta yace dadda yanaganki haka me ya sukace miki tace bansani ba din ni wlh banma san neye amfanin ka ba kazo kayi zaune nida nake mace ni nake qoqrin jin ba asi kaide anyi malalacin namiji ni kakiramin wancan yaron duk wulakancin shi yafika wayewa da shine da tuni yayi abun da yadace amma kai sai wani noqewa kakeyi saikace dan qauye kwata kwata baka wayeba sai iya shiganta ka anan kafi kauri dariya yayi sosai yace lalle dadda yanzu nidin ne ban waye ba ki kallenifa kina ganina kinga wayayye dan zamani yafada yana wani kada kai harda juya ido saikace mace kasake dadda tayi tana kallonsa tace ikon Allah kai abun naka kullum gaba yake ji yanda kake abu saikace mace wannan ce wayewar da ancuci wayewa wlh da ka waye ai baza ka tsaya anan ba ni wlh nama yi danasinin tahowa dakai daman wancan yaron na lallaba muka taho yace au yanzu dadda hakan ma danayi miki bazaki gode min ba saide ki ta kusheni kina yabon wani to bari intafi gida sai kikirashi yazo din yana gama fada ya tashi yana niyar fita daga wajen da sauri
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment