Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta fad'a a duniya,

Dikko yace tou yanzu me kake so nayi maka ne ? Alhaji yace ranka ya dad'e so nake kayi min maganinta, dariya Dikko yayi sannan yace nima so kake ta d'aukeni ? Cikin biyayya Alhaji yace haba ranka ya dad'e kada Allah ya had'aka shegiyar yarinyar nan.....

Dikko yace aini ko ta had'u dani bata da yadda zatayi dani, nidai bana neman mata kuma bana sabgarsu bana shiga huruminsu gudun raini, kayi hak'uri insha Allah zanzo katsina jibi idan Allah ya kaimu zata goge vidion dan wahala, ranka ya dad'e ai tace ta turawa k'awarta ne, Dikko yace k'arya take kadai jira zuwana .....

Godiya Alhaji yayi sannan sukayi sallama da Dikko,

Murmushi nayi a daidai wannan lokacin sannan nace duk mai niyar yin magani na nice zanyi maganin d'an banza, zomon bana shike maganin karen bana, maganin d'an iska kuma karen maguzawa, dani dakai dashi mu zuba duk wanda ya fasa yaci k'aniyarshi.......

Sallamar Hafsa ce da wasu zugar tantiran mata, a ciki kuwa harda Amisty, kila sunzo ne suci min uwa tunda nace uwar d'akinsu k'atuwar jahila ce, oho koma dai miye su shigo ina jiran isowarsu wurina inji su kuma da wace suka zo................???




22/08/2019


Taku a kullum mai san farin cikinku wato .

*MEELAT MUSA*

⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*



🅿 ------ 16


*_Bandai ji komai ba , 71 , 29 babu damuwa zamu rama muma..._*



_____```^^=°°--- Basarwa nayi tare da d'auke fuska ta daga dubansu, mutum dai bai isa yazo har gidana ya dakeni ba, kallon banza ko maganar banza mutum yamin wadda batamin ba wallahi ina da Lamba3 d c o zaici k'aniyar mata....

A daidai lokacin da suka iso gabana maganar zuci ya k'are, Amisty ce tace wurinki fa muka zo kina yi kamar baki ganmu ba, saida na gama kallesu tsaf sannan nace sannunku da zuwa tare da mik'ewa zan shiga d'aki dan d'auko musu tabarma...

Gaba d'ayansu rufa min baya sukayi suma suna k'ok'arin shigamin d'aki, ja nayi na tsaya tare da tambayarsu ina zasu je ? Amisty tace ciki zamu shiga ? Murmushi nayi tare da cewa kuyi hak'uri ku jirani ni bana kai mata cikin d'akina...

Hafsa zatayi magana Amisty ta dakatar da ita, kallonsu nayi tare da cewa barta ta fad'i cikinta, Amisty tace barta kawai d'auko mana kedai, munafikin murmushi nayi tare da juyawa na shige cikin ɗaki, domin ita Amisty tasan wace ce ni, tabarma na d'auko nazo na shimfiɗawa banza nace su zauna...

Dukansu zama sukayi lokaci ɗaya, su A ` i da Saude Nana da Karima duk suka taso suka dawo ƙofar ɗakina, nima zama nayi tare da cewa meke tafe daku ne ? Na ƙarasa maganar tare da kauda kaina gefe ɗaya....

Amisty tace Sultana ke kikace mu sameki gida ! Kallonta nayi tare da cewa sai akayi ya ya ? Amisty tace ai shine muka zo ! Kallon tantiran mata nayi sannan na maida hankalina wurin Amisty nace da Allah daga yau idan zaki zo wurina kidai min kwashe kwashe , da sauri Amisty ta kalleni sannan tace haba Sultana mi yasa haka kuma ?

Kai tsaye nace kinsan bana san munafirci kuma ban tare da munafikai, waccan bak'ar yarinyar da kika gani na nuna Hafsa budurwar Dikko sannan naci gaba da cewa gaskiya aminci take da mak'iya na saidai ta zab'a ni take so ko su A ` i , murmushi Hafsa tayi tare da kallona sosai ni kuma na d'an gyara zama yanda zan d'aukar mata hankali sosai, saboda ina so na rabata tarayya dasu A ` i idan ina tare da Hafsa suma suna tare da ita riƙa zugamin ita zasuyi har su hanani na cimma buruni tunda na lura ita Hafsa doluwa ce kuɗinne kawai ba wayau sai tsabar neman matan bala'e. Kwazzaba tasa har bata iya tantance kifi bata gane kwad'o,

Cikin ruɗewa Hafsa ta fara magana irin ta "ya "yan masu kuɗi, kin gane Sultana nifa ba abokaina bane kawai gaisawa mukeyi sai kuma wata huɗɗa tamu data haɗamu amma ba komai tsakaninmu gaskiya,

Ɗaure rai nayi tare da cewa nifa ba abinda ya haɗaku nake so na sani ba cewa nayi kawai ki faɗa ni zakiyi abokiya dani kibar su A ` i ko kuwa su A ` i kika zaɓa, Hafsa tace haba aike tawa ce kuma ina tare dake, murmushi nayi tare da cewa magana ta ƙare mata tacewa mijinta shege...

A ` i zatayi magana nace dakata malama ta bakin gulbi, ki taka sannu da lafiya kafin insa a ɓatarmin dake cikin garin nan, nuna yawan su Amisty nayi tare da cewa nan da kika gansu duk dalibai na ne, zan fara basu karatu daga jibi idan Allah ya kaimu, na kafa ƙungiya ta mai take *kwarata* duk wacce kika gani anan mabuƙaciya ce, zan haɗa ne zanba mace namiji idan an sallami mace zata fiddani, zan haɗa mata da mata amma a tafiyata ban tafiya da taron banza, sabbin ɗalibai ku na ɗaukeku kyauta basai kunyi register ba, amma daga ba yanzu ba duk wacce zata shigo cikinmu saita ajiye dubu talatin kuɗin register haƙƙina neman maza da mata masu abun hannunsu....

Miƙa hannuna nayi tare da cewa duk wanda yake tare dani ya ɗora hannunsa a saman nawa, kowa ɗora hannunshi yayi harsu Nana matan aure ba'a barsu a baya ba, ku ɗauki alƙawari babu cin amana , gaba ɗaya suka amsa munyi alƙawari bazamu ci amana ba, nace kuyi alƙawari zaku zama ɗalibai masu biyayya, munyi alƙawari zamu zama ɗalibai masu biyya nace idan kun samu ina nan ko bana nan zaku ajiyemin nawa kason, shima suka maimaita, sannan nayi addu'a tare da neman Allah yasa albarka a cikin wannan ƙungiya tamu mai albarka wanda nayi ma laƙabi da *KWARATA* saboda dukanmu lalatacci ne ,

Bayan an gama nace tou kowa ya tashi ya tafi nima zan fita inda fuskar jama'a take na samu gida na siya idan kuɗina yakai, idan basu kai ba kuma zamu kama shago, wannan shago zai zama nan ne kowa zataci gayu da safe taje ta zauna, yayin da zamu kafa ƙaton allonmu ya kalli al'umma, za'a rubuta a gaban shagon ko gidan tambarin *KWARATA* idan ma baka iya ba kazo za'a koya maka.

Zamu rubuta a jikin takarda mukai kuma a buga mana su da yawa, ni zanbi manya ofisoshi da kasuwa da kuma kamfaninika da inda "yan siyasa ke zama saina zabo mana manyan alhazawa sai mu raba musu, duk wanda ya gani ya karanta dama ga number wayata nan a jiki, ku kuma kuna shago kunsha wanka kunayi kuna ƙara powder da jagira ina binku ina muku wanka da turare, da mutum yace zaizo zance ya iso akawai kaya a ƙasa, yana shigowa ya ganku wayyo shikenan labari zai canja salo, ni kuma ina da wata dabara ɗaya amma bazan faɗa muku ba saboda karuwa bata da amana,

Nana tace tou mu da muke da aure fa ? Kallon ta nayi ƙasa da sama sannan nace duk iskanci da kukeyi keda A ` i sai yanzu kika tuna Allah ? Tsoki nayi tare da cewa tunda na lura kema kinasan duniyar sai in ɗaukeki aiki ki riƙa sharewa kina gogewa, ke kuma Karima idan mijinki ya barki zan zuba miki kayan mata da maza na gyaran harka duk wata zan baki dubu biyar ko anyi ciniki ko ba'ayi ba, amma idan mijinki ya barki fa.

Tun kafin in rufe bakina Karima tace koma bai barni sai naje wallahi, dubu biyar fa ? Ina nan kullum zaune gida naira hamsin ma wahala take min , kuma Sultana ki rubuta a jikin takarda duk wanda zaizo ya taho da kaza kinga idan anci an rage ai muma zamu maida miyanmu.....

Kallon Karima nayi sannan nace kazar Lbura'uba, an faɗa miki *kwartancin* wahala zamuyi ? Kudai kuyi ta addu'a a samu bakin titi, addu'a sukayi tayi Allah ya taimaka ya bada sa'a, daga ƙarshe dai kowa ya kama gabanshi, nima na kulle ɗakina na fantsa ma cikin gari...

Ina bakin titi tsaye naji wayata tana ta kururuwa dan haka dole na dakata, fiddota nayi na duba dan ganin mai kirana, Lamba 2 wato Bello kenan, ɗauka nayi tare dayin sallama, bayan ya ansa na gaishe shi, bai ansa gaisuwar ba yace ke Uwar masu gida hotuna na gani ?

Amma ai ka gane ko waye a jikin hotunan ko ? Eh nine , tou kuɗi zaka bani naira budu ɗari biyar nan da gobe idan Allah ya kaimu idan kuma kace babu sai ina watsa su duniya kowa ya kalla kyauta.... Ɗanka da matarka da abokanka duk suna kwance a saman gado zasusha kallo abunsu...

Sirikinka da surukarka zasusha kallon siriki tsirara... Tou nabarka lafiya, ina faɗin haka na katse kiranshi, ina duba yanayin samun mutum kafin na yanka mishi haraji, Bello baida ko sisi kuma baida wata sana'a data wuce caca, kuma caca ba kullum akeyinta ba, gashi kuma na sace kuɗaɗanshi kaff da na gani a mota ba damuwa na bane nidai kuɗi kawai, ina gama waya da Bello na kira lamba3 wato d c o, mai girma ɗan sanda yarinyar jiya ce, Maryam Sultana Aliyu Binna, ya garin ? Haka nayi masa bayani bayan ya ɗauki wayata....

Hajiya ya kike ? Lafiya qalau kana ta ina haka ne ? Yace naje ganin gida ne baby, cikin salon cuta na kwantar da murya ƙasa ƙasa nace kuma "yar laɓai maimakon ka kirani inyi rakiya ? Murmushi yayi sannan yace wallahi nima tafiyar bazata ce wife ina ce bata lafiya, tou lallai wannan kuwa da sa'a take wace ce ita, dan bansan abinda wife in take nufi ba, dana dangantata da mace saboda naji yayi magana da sunan jinsin mace ne, yace wife itace ba lafiya,

D c o yace matata nace, danshi yanda yake kallon wayewa ta ya ɗauka wata shegiyar baturiya ce, danaji yace mata nace ai shine nace wannan tana da sa'a, da kaji kuma nace wace ce ita ina tambayarka amarya ne ko uwar gida ?

D c o yace ai mata ta ɗaya ce, nace tou yayi kyau yaushe zaka dawo ne ? Zan dawo amma sai ta samu sauƙi, to Allah ya sawaƙe ya bata lafiya, d c o ya amsa da amin mukayi sallama.....

Lallai duk yanda akayi wannan matar tashi tasan damarta ne, idan ta riƙe d c o sosai taya zamu samu wani abu a wurinshi ne to ? Wato ita munafika nufinta ita ɗaya zataci ? Taci gidansu bari dai d c o in ya dawo bata ƙara ganinshi dan ubanta ba rashin lafiya ba ko mutuwa tayi sai anyi jana'izarta baije ba....

Napep na hau na nufi gidan Alhaji marenin wayau na, tsoho ya tsufa amma zuciyar bata mutu ba, buɗe na samu gidan dan haka na banka kaina tsaye na shiga, babu dawakuna ko guda ɗaya duk an fitar dasu an share gidan ƙwal gwanin burgewa, sai cire yana akeyi ana wani kakkaɓe kakkaɓe get in gida sai wanke shi akeyi ana goge duk inda yayi ƙura....

Cikin masu sharar na tamabaya lafiya ko Alhaji ya tashi ne ? Yace lafiya qalau bai tashi ba ubangidan shi ne zai dawo gobe, tsoki nayi tare da cewa shine ake ta wani share share ? Yace Eh , Dikko ko ? Na tambayi yaron yace Eh ai ance ma ya iso yana Abuja ko zasuyi me ne ne ? Amma dai naji ance jirgin safe zaibi yaje kano akwai abinda zasuyi sannan zai shigo katsina....

Jinjina kai nayi sannan nace tou shi ina Alhajin ne ? Ai sun tafi kano taroshi, daga nan har kano suka tafi su taho dashi saboda tsabar basu da aikinyi ? Yaron yace ai ba rashin aikinyi bane ba hajiya duk abinda kika ga sunayi dan sun san zasu samu, Alhaji fa baya saida fari baya saida baƙi kiwon dokuna yake amma kiji irin dukiyar dake gareshi, sun san suna samu da D ---K ɗin ne shi yasa suke laƙafe dashi, da yana nan da baya nan kuɗi suke samu kamar tashin hankali...

Tou zan tafi kawai mayi waya dashi, jakata na buɗe nayi ma yaron alheri godiya yayi tayi tare da cewa Allah ya kareki ya ƙara arziƙi hajiya ubangiji yasa kifi haka Allah ya ƙara lilka darajarki ngode sosai. Ban saurareshi ba nayi waje abu na,

Gida na koma saida nayi sallah isha'e sannan na fara nazari akan Alhaji abinda zance masa kawai ya bani mota da gida sai in fita daga harkarshi, dan ni duk inda zanji ƙamshi ko labarin sunan D ---K na tsani wurin tsakani da Allah bana san Dikko na tsani rayuwarshi wallahi, amma idan har Allah yayi min cikakken arziƙi saina wulaƙanta ma Dikko rayuwa,

Wani irin baƙin ciki naji yana tasomin hawaye ya cikamin ido na abinda ya faru tsaƙanina da Dikko ya dawomin sabo fil a zuciyata, zuciya ta tace min ƙaryane baza a fita daga harkar Dikko ba sai na halakashi, kamar mai aljannu lokaci guda na burkuce nayi nayi na saita kaina amma na kasa wuƙa na ɗauko tare da kwarara wani irin ihu nace wallahi saina kashe ka........ Na ƙarasa maganar cikin kururuwa.

Duk wanda ke gidan nan babu wanda baiji ihuna ba, da gudu Nana da Karima sukayo ɗakina amma banda su A ` i saboda yau da wuri suka tafi gida. Lokacin da su Nana suka shigo duk na yanyanki wasu wurare na jikina da wuƙa, abin ya tada musu hankali dakel suka riƙeni suna tambayata waye Sultana kallon Nana nayi cikin kuka nace wallahi saina kashe shi gobe zai shigo katsina bana ko ƙaunar jin irin sunanshi a rayuwata....

Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, shine abinda Dikko ya faɗa a daidai wannan lokacin tare da janye ruwan dake gabanshi, hankalin kowa yayo kanshi tare da tambayar lafiya ranka ya daɗe ? Dafa ƙirjishi yayi tare da cewa gabana ke faɗuwa babu gaira babu dalili.

Duk kusa dashi suka matsa suna mishi sannu, kallon babban yaronshi yayi sannan yace maza kiramin gida, ɗaukar waya yayi ya kiro dadyn dikko, babu ɓata lokaci dady ya ɗauka D --- K babu ko gaisuwa yace Dady lafiyanka qalau kuwa ? Murmushi Dady yayi tare da cewa mi kuwa zai sameni ? Bayan ina nan zaune cikin iyalina muna farin ciki saboda zuwanka ! Dikko yace Dady karka ɓoyemin dan Allah miye ? Dady yace tsaya ma kaji, saida ya haɗa Dikko da kowa yayi magana sannan yace kaji ko ?

Ajiyar zuciya Dikko yayi kamar wanda yasha kuka ya ƙoshi sannan yace kawai haka nan naji gabana yana faɗuwa, Dady yace saboda zaka ga ganni ne, kayi ta addu'a Allaah ya tsare kuma kayi bacci da wuri, jinjina kai Dikko yayi tare dayi ma Dady sallama suka ajiye waya....

Dakel su Nana suka lallasheni nayi shiru, Karima tace inyi ta addu'a don Allah sharrin shaiɗan ne, nace tou amma har yanzu ban daina baƙin ciki ba, saida suka tabbar hankalina ya kwanta sannan suka tafi bayan sunsha fama na faɗa musu ko waye naƙi faɗa musu...

Suna fita na rufe ɗakina nayi addu'a na kwanta bacci,

Da safe kuwa misalin 12:45pm na fara gwagwaɗawa Alhaji kira, bawan Allah banda zufa babu abinda yake haɗawa, idanuwanshi sunyi jajir saboda tsabar tashin hankali duk wanda ke wurin saida Alhaji ya bashi tausayi duk da babu wanda yasan abinda yake damunshi, amma banda Dikko dakeyin kyakkyawan murmushin dake fito masa da tsananin kyawunshi, da yasan yanda yakeyin kyau idan yanayin murmushi daya dawwama yanayin fara'a, duk da ko baiyi murmushi ba yana da kyau sosai gaskiya, taunar rainin hankali yake ma cingom in bakinshi sannan yace wai har yanzu ta hanaka ka huta ne ?

Kamar Alhaji yana jira yace Eh ranka yadaɗe, Dikko yace bani ita, Alhaji yace ai kiran ya tsinki, ɗaure fuska Dikko yayi sannan yace kirawo min ita...............




23/08/2019



*JAMILA MUSA* 🤙🏻


Ina mana barka da juma'a,


⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*



🅿 ------ 17


_Don Allah kuyi haƙuri mu dukanmu mubi labarin nan a hankali, wannan labari na faɗa muku yanda yake, an rage wasu abubuwa ne wasu kuma an gyara su, labarin yana da yawa sosai ba'ayi komai ba yanzun muka fara wasan , kuyi haƙuri muje a hankali, ni jamila musa nake cewa asha karatu lafiya...._


Gajiya nayi da kira ba'a ɗauka ba dan haka na haƙura banyi yunƙurin sake kira ba, ina ƙoƙarin ajiye wayata kira ya shigo a cikin wayata mamaki ya kamani sosai ganin kiran Alhaji, taya zai kirani bayan ni na kirashi da kaina bai ɗauka ba ?

Haka nan naji tsikar jikina ta tashi zuciyata namin wasi wasi lallai akwai wata ƙullallah da ake son ɗaura min, duk yanda akayi wani baƙon lamari zai faru tou amma bansan ko miye ba, kashedi zuciyata tamin tare da hanani ɗaukar wayar, sau biyu aka kira ban ɗauka ba dan haka suka haƙura basu sake kira ba...

Kallon Alhaji Dikko yayi sannan yace yarinyar nan zata kai shekaru nawa ? Saida Alhaji ya kwantar da kai cikin biyayya sannan yace baza ta wuce sha shidda zuwa sha bakwai ba, D --- K yace tou wallahi wannan yarinya tasan abinda takeyi kila shekarunta ya wuce yanda kake tunaninta tana abunta da lissafi, amma baka taɓa kiranta a waya ba ko ... ?

Alhaji yace Eh gaskiya chat kaɗai mukeyi da ita, sai ranar da ta turomin vidion nan shine na kirata, amma daga ranar ban sake kiranta ba saidai ta kirani, Dikko yace tou jikinta ya bata ba kaine kake kiranta ba shi yasa bata ɗauka waya ba, amma nasan zata kiraka zuwa anjima zatayi tunanin wayar ta koma hannunka, ajiye wayar yayi a gefenshi suka ci gaba da abinda sukeyi..

Ina ajiye wayar kiran Bello yana shigowa, ɗauka nayi bayan mun gaisa yace min Uwar masu gida nifa har yanzu ban samu kuɗin da kike magana ba, jinjina kaina nayi tare da murmushi nace kanajin wasa bazan iya tura hotunan ka ba a yanar giza gizo ko ? Tou wai babu zan baki ne ? Cikin faɗa yace tou banda su ko satowa zanyi in baki saboda inajin tsoronki to ki turawa uwar yanar giza gizo dan kutumar ubanki ko an faɗa miki tsoronki nakeji ko inajin tsoron a ganni tsirara, idan baki sani ba har gasar fitowa tsirara nayi daga ƙofar gida na har bakin masallacin juma'a naje ranar juma'a babu kaya a jikina na dawo, ni zaki ɗauka hoto kimin hauka ? Tou bake ba ubanki ma nafi ƙarfinshi ki riƙe kiyi ta kallo mtsw ya kashe wayatshi....

Murmushi nayi tare dabin wayar da kallo, har zan haƙura wata zuciyar tace wallahi ƙarya yakeyi bai wani fita tsirara ba idan kika fahimci maganar shi ta farko a sadudance yayi miki magana, karki sauƙaƙa mishi number wayar matarshi zaki fita ki samo ki tura mata zata bashi labari, idan kin tura mata ni na sani sai ya kiraki, idan ya kiraki sai kice kin turawa ɗanshi ma, shi kuma ɗan ba hoton za'a tura mishi ba voice note za'ayi mishi da wasu maganganu masu zafi zuciya zata tunzurashi yayi ma baban magana, tashi dai ki fita duk ki samo numbobinsu ki dawo sannan musan abunyi...

Bello kuma shida abokinshi suka kashe sannan yace na faɗa mata, abokin yace tou yanzu zata shafa maka lafiya kaga kun rabu lafiya zata gaji da ajiyar hotunan ta gogesu, Bello yace ni tsoro na ɗaya tace ta turawa wata ƙawarta hotunan fa, karka damu sun gaji su goge dan ubansu, dariya sukayi tare da ƙara kashe wa cikin duniyanci....

Ina fitowa daga wanka nace ba'asan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, zakayi dana sanin hanani kuɗin nan, kila kuma rabona ne yake da yawa kuɗin zasu sake yawa.

Har na gama shiri da abinda nake saƙawa nake warwarewa, Nana na kwaɗawa kira ta kwararo da gudunta tazo, kallonta nayi sannan nace Nana aiki yamin yawa zan fita neman wurin zama sannan kuma zanje wurin wani Alhaji dake tamin rainin hankali, ai kinsan majalissar babana ko ? Nana tace Eh na sani, nace ai kinma san Bello abokinshi ko ? Nana tace sosai ma, tou lambar wayar matarshi da babban ɗanshi zaki kawo number wayoyinsu zan baki dubu ɗaya...

Yashe baki Nana tayi sannan tace godiya nake Sultana, wani sauran biredi da naman da naci jiya na rage na miƙa mata ansa tayi taita kwarara godiya harta fita, tana fita nima na tattara nawa ya nawa na fita nabar gidan...

A ƙofar gidan Alhaji napep ya sauke ni, wasu irin zuƙa zuƙa motoci tun daga ƙofar gida har cikin get in gidan, kuma yauma get ɗin a buɗe yake daga inda nake tsaye ina hango komai na gidan !

Matashin jiya daya faɗa min cewa Alhaji yayi tafiya shine yazo wurina da sauri ya gaisheni cikin girmamawa ansawa nayi cikin sakin fuska sannan nace gidan naku lafiya naga taron motoci ?

Lafiya qalau ubangidan nasu ne ya dawo ko gida ma baije
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On KWARATA
avatar
muhd-habu

6 months ago

Reply

Nice

Please Login or Register in order to submit comment