Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta saki baki ga wacce bata sani ba taci gaba da buɗemin sirrin mijinta wanda haka ba daidai bane ga duk macen data san abinda takeyi , ɗakinta da tsore inta babu inda bata kaini ba dan in gani da idona tana da komai na rayuwa tsaftarce da haƙƙin Alaji bazata bayar ba , tunzura ta nayi tare da cewa Eyy ki barshi gaskiya gaki ma yadda kike kyakkyawarki ko kun rabu sai kin samu wanda yafi shi , murmushin jin daɗi tayi tare da cewa ai cewa ma akeyi nafi ƙarfin shi , kallonta nayi tare da cewa gaskiya keɗin duniya ce da matsayin gidan sarauta...

Sallama mukayi da ita tayomin rakiya har ƙofar gida inda nayi parking in motana , saida na fara tafiya sannan nasa Wane Yaro ya kiramin wayar Alaji , bayan ya ɗauka nace masa ina san ganinshi amma ya faɗamin sirrintaccen wurin da zamu haɗu , bayani yamin sannan nace masa na gode tare da kashe wayata...

Kai tsaye gida muka nufa a bakin hanya na ajiye Wane Yaro ni kuma na wuce gida , a ƙofar gida nayi parking in mota ta na shige ciki , sallama nayi kamar yadda na saba na wuce ɗakina , ruwa na zubo a boket naje na watsa sannan na dawo ɗaki nayi kwanciyata dan hutama rayuwata....

Bayan sati biyu , abubuwa da dama sun faru , ga lamarin iskanci na kuma yanzu na zuƙa hannu na , Babana kuma ya samu mage kamar yadda malam yace kuma ya aiwatar da aikin kamar yadda akace yayi ,

Na samu Alaji munyi magana dashi kuma ya faɗamin cewa yana san wayayyar mace "yar gayu wacce zata biya masa buƙatarshi a duk lokacin daya so , ba laifi yana da wanka kuma yana gayu kuɗinshi a sake yake ga mata , dan haka na ɗaura dashi cewa ya saurareni ina san na haɗa gidanmu sannan naci gaba da harkar bariki na,

Da alkairi na nake shiga cikin ahalinmu , nakan basu kwance kaya , in siya musu kayan kwalliya idan na samu kuɗi , ina aika musu da kayan abinci kuma ina zuwa lokaci ² ina basu sha'awa kuma cikin hikima na fara musu tallar bariki ,

Duk wata hidimata yanzu Alaji shike ɗauke da ita , babu abinda na nema na rasa fanni abinci kuɗin kashewa da kuma suturu ya kwacemin duk wani abinda zaizo ya dameni , yauma ƙaton rago ya kawomin dan haka na sakashi a napep na tura Wane Yaro yakai gidan Baba ƙarani da 100k nace ya sayi icce...

Babana kenan , ɗan duniya abin alfahirin uwar ɗakin kwarata , cikakken namiji mai dogon zamani , namijin duniya gatan mata , ka gansu ka ƙyasa ko ba sisinka su bika , baka gada ba haye kayi Sultana tai gado ɗan gado kuma saiya zarta.....

Uhum Baba kenan , Amisty ce kwance a saman Baban Sultana suna ɓalgacewa bayan sun gama ɓalɓalewa yake tambayarta ya Uwar masu gida ? Tace tana nan cikin ƙoshin lafiya , Amisty itace take kaiwa Baban Sultana labarin halin da Sultana take ciki , kuma shine ya tirsasawa Amisty ta kwashe kayanta ta dawo zamani dan kawai ya riƙa jin halin da nake ciki , abin kunya Baba ka rasa macen da zaka huta da ita sai abokiyar "yar ka , dakai da Amisty duk ranar da Sultana ta gano ku zaku fuskanci babbar matsala....

Lokacin da Baba ƙarami yaga rago abun ba ƙaramin burgeshi yayi ba dan babu biki ba suna kuma ba sallah kawai an bashi kyautar rago , yaji daɗi sosai a lokacin da Wane Yaro yaje kai rago ya samu Zainab da Farida a gidan dan haka daya tashi zai dawo suka biyoshi zuwa wurina...

Nayi farin ciki da ganin "yan uwana , muka rungume juna cikin soyayya irin ta "yan uwan da suka daɗe basu haɗu ba , sannan muka shiga jajantawa juna yaushe rabo ? Bayan an gama suka tambayeni ko na fara kasuwanci ne ? Dariya nayi tare da ce musu sosai ma , me kike siyarwa ne ? Suka tambayeni kai tsaye nace *Karuwanci* shine sana'ar da nakeyi...

Zasu fara wani mamaki nace karku wani damu kuma kar kuyi mamaki nayi amfani da huɗubar da Baba yake baku ku tashi ku nemi kuɗi domin ku kare mutunci kanku , huɗubar ce na ɗauka kuma da ita zanyi amfani kuma ma babu laifi an samu nasara tunda na siya gida ga mota kuma ina da "yan canjina , ku kun samu gida da mota ne ? Na tambayesu , shiru sukayi , murmushi nayi tare da cewa karku damu ƙanwarku ta kasa kuma ta samu masu siya nayi ciniki sosai dan haka kawai ku dawo nan muci gaba da zama dan tunda na siyi gidan na fitar da ɗakunan matan Baba shima Baban zan dawo dashi dan kasuwa bata yuwuwa babu shugaban ƙungiya....

Gaba ɗaya wutarsu ta ɗauke musu basu da zaɓin daya wuce su dawo zama tare dani tunda inda suke a raɓe suke , koda suka tashi tafiya na basu kuɗi na basu kayan sakawa , sunyi godiya sosai tare dacemin insha Allah zuwa jibi zasu dawo , rakiya nayi musu suka tafi...

Baba ƙarami da jama'ar dake da sauran mutunci a idon Babana sune suka sameshi suka bashi magana cewa ƙauracemin bashi ne zaisa nayi halayen kirki ba , ya dawo kusa dani wani abun ma a gaban idonshi bazanyi ba , Baba yace shi ba wani abu yakeji ba kawai kunyata yakeji ya zama sokon uban daya kasa ceton "yarshi daga shiga wata baƙuwar rayuwa !

Magana suka ba Baba harya amince zai dawo gidana , kuma yaje wurin Maman Fa'iza suka ce zasu dawo suma jibi idan Allah ya kaimu dan haka gida zai dawo kamar yanda yake da , su Nana Karima da suke zaune a gidan kuma bazan tada su ba saidai idan sune suka tashi da kansu...

Da marece ina kwance Amisty ta shigo ɗaki babu sallama , jakarta ta ajiye ta ɗauki buta ta nufi bayan gida , tana fita na tashi da sauri naje na ɗauko jakarta na buɗe , kuɗine masu yawan gaske a ciki dan haka na tattarasu gaba ɗaya na kwashe su na ɓoye sannan na koma saman katifa nayi kwanciyata kamar yanda nake daga farko...

Ban daɗe da kwanciya ba ta shigo tare da cewa tashi gidansu Hafsa zamuje bata da lafiya , subahanallah na faɗa tare da tashi zaune nace meya sameta haka ?

Ƙonewa tayi ta faɗi maganar tare da ɗaukar jakarta , nima tashi nayi banko ɗauki gyale ba makullin mota kawai na ɗauka tare da cewa muje , tunda nake ban taɓa zuwa gidansu Hafsa ba sai yau zan fara , a tsakar gida nayiwa su Nana saina dawo sannan mukayi waje dani da Amisty...

Daga ni sai Amisty muka tafi ni naja motar har muka isa gidansu Hafsa , har zanyi parking a waje Amisty tace inyi horn za'a buɗe , banyi musu ba na dannan horn mai gadi ya kwashe mana get muka shige , kusa da motar Hafsa anan nayi parking in mota ta sannan muka shige ciki...

Har muka isa ɗakin Hafsa bamu haɗu da kowa ba , palon ɗakinta ma ba kowa dan haka bedroom muka shiga kai tsaye , Hafsa tana kwance a saman gado an naɗe ƙafarta da farin bandeji , idonta a rufe kila tanayin bacci ne , zanyi mata magana Amisty tace karki tasheta bacci takeyi , banyi magana ba na samu gefen gado na zauna , palo Amisty ta koma babu jimawa ta dawo ɗauke da wata ƙatuwar roba bansan ko miye a ciki ba , wurin ƙoƙarin ta hawo saman gado ta ɓareminshi kaf a jikina , tsakiyar idonta kaɗai na kalla na gane wannan abun shiri ne ,

Kallon kokon data makomin a jiki nayi sannan na sake kallonta , kiyi haƙuri Amisty ta faɗa , ba koma nace cikin sanyi jiki dan Amisty tsoro take bani , cikin sigar lallashi tace ki shiga toilet saiki wanke , banyi magana ba na miƙe na nufi inda Amisty ta nunamin da ɗan yatsanta , kokon gaskiya baya wankuwa gefe² dole sai na cire kayan nayi wanka gaba ɗaya dan babu inda bai kai ba ,

Cire kayana nayi nai wanka , bayan na gama na wanke kayana na ɗauro towel na fito da kayan a hannuna da niyar ince a ina zan shanya ? Ina fitowa naga Hafsa tana rufe ƙofa da makulli bayan ta gama ta tillashi can saman waldrop , bayan ta tilla ta warware bandejin sannan tace hausawa sunce mai haƙuri mawadaci nasha haƙuri kuma na daɗe ina dakon yunwa da ƙishirwa , yau zanci insha zan kore duk wata tsohuwar yunwar dake cikin hanjina... Dariya sukayi tare da tafawa ita da Amisty....

Amisty ta ansa da cewa lallai zamuga wasan kura ga uwar kwarata gata lesbian , Hafsa tace tabbas yau zan koya mata irin namu salon tunda muma ta koya mana irin nata , a'uziyya naja tare da ƙara riƙe towel in jikina gam , murmushi Hafsa tayi tare da cire rigar jikinta tace kinga sheɗan baya tafiya gashi ma ya fara cire rigar jikina , kin gani ta faɗa yayin da ta ɓalle bireziyarta , ja baya na farayi da niyar komawa toilet ina ihu a kawo min ɗauki *kwarata* sun rufeni a ɗaki ,

Dariya Hafsa tayi tare da shan gabana tace ina zakije ne ? Kuma babu mai cetonki dan gidan ma babu kowa , shi yasa nace Amisty ta kawomin ke kwana biyu zakiyi kawai kafin nan nasan kema kin zama "yar hannu...

A saman bedsite naga kwalbar mai mai gurguwa dan haka da sauri na yada kayana na ɗauka na kwaɗawa Hafsa a kai harsai da jini ya fita , ajiyar zuciya ta sauke tare da fizgoni tace nagode ta ƙarasa maganar tana ƙoƙarin haɗa bakina da nata , da ƙarfi na tureta naci gaba daba da ihu ina kai mata duka , kwata ² bataji dan haka ta janye towel in jikina , ita da Amisty suka kamani mukaci gaba da kokowa da ƙarfin bala'e suka ɗorani saman gado.....









11/09/2019




💅🏻 *MEELAT MUSA NE....*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*



🅿 ------ 30


*_Ina miƙa saƙon ta'aziyya ga "yar uwar aikinmu Halima Yahya 20 Allah ya bada haƙurin rashi ubangiji yasa ta huta Allah ya kyautata namu ƙarshen idan ajaliyyarmu tazo...._*


Amisty ta danneni da ƙarfin tsiya Hafsa ta sauka dan ɗauko igiyar da zasu ɗaureni da ita , murmushi nayi tare da kallon Amisty sannan na nunata da yatsa na juya na kalli Hafsa itama na nunata da yatsa sannan na gaggaɓe da wata irin dariyar dani kaina bansan na iyata ba ,

Lokaci guda kuma na ɗaure fuska kamar bani nayi dariyar ba , da sauri Amisty ta kalli Hafsa suka kalloni a lokaci ɗaya , hawo saman gadon Hafsa tayi tana ƙoƙarin riƙe hannuna ta ɗaure , kallonta nayi kamar wata sakara sannan nace dake da Amina ku tabbata idan har kuka min wani abu kasheni shine kawai mafita a rayuwarku , amma na rantse da girman Allah wanda ya halicceni ya halicceku dani daku dukanmu shi muke bautama , mutuwa ta ko taku zata iya zuwa ko wane lokaci yanzu ko anjima , ko kuyi ko ku bari yanda kuka buɗemin sirri saina buɗe sirrin uban kowa a cikinki ,

Bayan buɗewa saina tona musu asirin da ku kanku sai kunsha fiya² kun mutu saboda baƙin ciki , kar wacce ta ɗauremin hannu ko ƙafa kuyi duk iyakar iskanci da kuka iya , bashi ne kuma bazaiyi kyau ba a lokacin da zan biyashi akan iyayenku ,

Muni , baƙin ciki , firgici , tashin hankali gaba ɗayanku zaku fuskance su yayin dana shigo rayuwarku , ina da illa kuma ina da bala'en haɗari haka nake dasa baƙin cikin da baya mantuwa a zuciyar duk wanda ya nemi ya dasa baƙin ciki a rayuwata , ciwo gareni haka nake da ɗaci kuka akemin kamar mutuwa yayin da na shigo gida dan ruguza farin ciki zuri'a ɗaya , ku lasa ku maida miyanku tunda kun buɗa ni kuma nayi alƙawari daga yanzu rayuwar farin ciki ta ƙare gareku ,

Kallan kallo suka tsaya yi kowa da abinda take saƙawa a zuciyarta , tsoki nayi tare da cewa kuna ɓatamin lokaci domin ni ruwan ƙorama ce zuwa nake da ƙarfi na tafi idan kuma na tashi tafiya nakan tafi da abu mafi soyuwa ga al'ummar gari za'ayi ta tunani na har shekara ta zagayo ba'a gama wani kukan ba zan sake caɓar wani abun inyi gaba dashi haka mutane zasuyi ta kuka dani har ranar da mutuwarsu zata riskesu , dake da dake duk wanda na bari a cikinku ya huta ban yafewa kaina ba...

Dukan ƙofa akayi da ƙarfi tare da cewa Hafsa me kukeyi kuma ? A shagwaɓa tace Mom ya akayi kuka dawo ne ? Ƙara dukan ƙofar tayi tare da cewa ni banje ba tunda na shigo nakeji ana ihu *kwarata* wai me ke faruwa ne ...?

Dukansu shiru sukayi , ci gaba tayi da dukan ƙofar tana cewa wallahi idan kika bari na buɗe ƙofar nan da kaina zaki ci ubanki.... Cikin yanayin ɗacin rai Hafsa ta kalleni sannan ta sauka ta fara ƙoƙarin saka rigarta a lokacin har Mom inta ta zuro makulli ta waje ta fara buɗe ƙofa...

Murmushi nayi da gefen bakina nima na sauka daga saman gadon na ɗauka towel in na ɗaura , ban gama ɗaurawa ba ta shigo ɗakin , kayana na ɗauka da makullin motar na raɓa ta gefenta zan fita , riƙoni tayi tare da cewa ke daga gidan ubanwa kika zo nan ke kuma....?

Ko kallonta banyi ba da nace mata daga gidan ubanta nake , bakiji ina miki magana ? Kema nan dako haihuwarki ba'a gama ba har kin iya iskanci haka ? Kallonta nayi sannan na faɗa mata kaf abinda ya faru na ɗaura da cewa kuma na rantse da girman Allah saina rama ,

Haƙuri ta fara bani , niko nace dama kin adana kalmomin haƙurinki kila zasuyi tasiri a lokacin da "yarki ta fara halbe²n mutuwa , ina faɗin haka nayi gaba , a palo naga wata ƙatuwar hijabi dan haka na ɗauketa nayi gaba , a ƙofar palo na saka sannan na wuce inda na ajiye mota ta , ina zuwa na shiga naja cikin gudun tashin hankali nabar gidan kamar babu rai a cikin motar...

Tuƙi nake bansan inda nake bi ba , domin idona cike yake da hawaye yayin da hankalina da zuciyata suka tafi tunanin hanyar da zan samo iyayensu Amisty dan babu hanya mafi muni da zan saka musu inba inyi iskanci da iyayensu ba kuma in ɗauka vidio in tura musu...

Wani irin wawan burki na taka dan ban lura ba traffic ta riƙeni , tsayawa nayi tare da sauke gilashin mota ta ina kallon wata mace data bugawa wata mota itama dai masiffiyace itace take da laifi amma sai rashin kunya takeyi ,

Kyawawan motoci ne masu tsada kuma ta kashe musu fitilar baya kuma sai zagi takeyi tana cewa idan sunajin su wasu shegune itace maganin "yan iska sai an biyata motar ta data goge , tunda sune sukayo baya , duk wanda ya bata haƙuri sai tace batayin haƙuri uban waye ma ake tuƙawa a motar ?

Daga ciki aka sauke gilashin motar ya sauka a hankali , Dikko na faɗa tare da ƙarasa sauƙe gilashin mota ta dukanshi , matsawa matar tayi taci gaba da zazzagawa Dikko rashin mutunci , kuma ya hana kowa yayi mata magana , murmushi nayi tare da ɗaga kaina na kalli danja har yanzu ba'a sakemu ba , amma waccan wawiya ce da tasan Dikko da bata shiga rayuwarshi ba Allah dai yasa ba a gidan haya suke zama ba suma...

Ina tunani naga ta juyo tana kuka kome Dikko yace mata Oho su kuma an sakesu sun wuce , ɗaga gilashin motar nayi nima ana sakinmu nabi bayan motar matar da gudu dan ina so inji abinda Dikko yace mata take kuka ,

Itama gudu takeyi sosai nima na take tawa sosai , muna samun sarari na shiga gabanta , dole ta tsaya har yanzu tana cikin ɓacin rai , fitowa nayi daga cikin mota ta ko takalmi ban tsaya sakawa ba , na nufo motar matar har yanzu kuka takeyi , gidan gaba na buɗe na zauna , kallona tayi tare da cewa lafiya ?

Cikin yanayin damuwa nace abinda aka miki ne baimin daɗi ba shi yasa na biyoki in baki haƙuri me ya haɗaki dashi ne ? Cikin ɓacin rai tace ɗan iskan yaro ne gashi da siffar mutanen kirki amma baida mutunci , kuma baida kunya ko kaɗan , driver inshi ne yayo baya ya gogi motana ni kuma na kasa haƙuri na fita nayi musu magana shine duk sukamin shiru , ni kuma nace uban waye ma ake tuƙawa a motar ashe yana ji yana sauke gilashi ni kuma naje wurinshi da niyar ce masa bai kyauta ba shine yace min...

Wai kar inmi mishi rashin kunya bayan yasan komai , cukwui da nonon raƙumi nasha aka bani kyautar motar na taho kan titi ina ma mutane ganganci ko an faɗa min titi ɗakin mijina ne ? Ban tsaya naji sauran bayanin shi ba na taho saboda yaci min mutunci da yawa...

Lallai Dikko cikakken ɗan iska ne , haƙuri na bata tare da fita daga cikin motarta na nufi mota ta , wato ya yazo gari kuma hali na nan bai canja ba , mota na koma na shiga naja nayi gida ,

Tun kafin inyi parking naga Nana zaune a saman dakali sai kuka takeyi , ko inda take ban kalla ba na wuce cikin gida , dan har Nana haushinta nakeji saboda abinda su Amisty sukamin....

Wanka nayi tare da sake wanke kayana na bazasu a saman igiya , ɗaki na koma na shirya bayan na gama abinda nake na ɗauko kuɗin Amisty dana sace na fara irgawa , ban gama irgawa ba naji A ` i tana kwalamin kiran cewa kizo ana kiranki a ƙofar gida ,

Abinda raina ya bani Babana ne dan haka na ajiye kuɗin na fito , a tsakar gida Karima ke ƙyanƙyasa min cewa an saki Nana , idanuwa na zaro tare da cewa innalillahi garin ya ? Nayi maganar a sirrance tare da natsawa kusa da Karima ! Karima tace ai labarin sai kin dawo kije kiji kiran da ake miki , har ga Allah banji daɗin mutuwar auren Nana ba kuma na lashi takobin gyara aurenta da gaskiya ,

A ` i ta ƙara cewa jiranki akeyi , cema Karima nayi ki jirani ina dawowa , bayan na fito ƙofar gida nacewa A ` i waye yake nema na ? Filin da aka rushe gidaje ta nunamin kallon motar da akayi parking nayi sannan na kalli A ` i nace waye ? A ` i tace wani dattijo ne , wane kala ne ? Fari ne ! Ya yanayinshi yake ? A ` i tace wallahi ban lura dashi sosai ba yaro dai ya turo yace Sultana taje...

Kai tsaye na nufi wurin , tunda mu "yan kasuwa ne ina zuwa na buɗe mota na shige naja na rufe garam , shi kuma ya sanyawa motar lock , ko faɗuwa gabana baiyi ba domin dama raina ya bani za'ayi haka ,

Waye kai ? Na tambayashi domin duhu ya shiga , ni ne , ya bani amsa , kaine wa ? Na sake tambayarshi , *Shekara biyu...* ne ya bani amsa , dama ana ganin shekaru ? Umm idan bakya ganinsu zaki wuce su ? Ɗan gajeran tsoki yayi tare da cewa yanzu ba wannan ba me yasa kike san yawan yin kuka ? Ni banda isashiyar lafiya sai kiyi ta kuka kina taramin damuwa ! Me akayi miki ɗazu ne ?

Tou sai yanzu na gane ko waye , murya nabi na ganoshi , me kuma ya sake dawo dakai cikin rayuwata ? Na tambayeshi , bai bani amsa ba ya fara gangarawa da motar yana saukowa , riƙe sitiyarin nayi nace ina zaka kaini ne kuma ? Janye hannuna yayi daga saman sitiyarin baiyi magana ba a daidai lokacin daya sauko ya juya kan mota ta kalli titi...

Haba wai ina zakaje dani ne haka ? Ba tare daya kalleni ba yace yi haƙuri An mata yanzu zan dawo dake bazan daɗe ba , shiru nayi , kinyi haƙurin ko ? Ya tambayeni cikin sigar lallashi murya mai kwantar da hankali dasa natsuwa , shiru nayi ban sake magana ba , a hankali yayi tuƙi har muka fita bakin hanya , yana hawa titi kuma ya fara falfala gudu kamar yanda ya saba.

Tafiya mai nisa mukayi , sannan Dikko ya sauka daga saman titi yaci gaba da gurzar burji , ganin ɓoyayyar hanya yasa na fara kuka , kallona yayi tare da cewa wai miye ne ? Kina tunanin zanyi miki wani abu ? Ɗan soɓaro baki yayi sannan yace wannan hanyar tafi sauri ne bara mu koma titi tunda kinajin tsoro..

Nidai bana so ka mayar dani gida, kwaikwayo na yayi tare da cewa idan naƙi mayar dake kuma fa ? Sai in barka da Allah.... , murmushi yace An mata kenan waike bakijin kunyar min rashin kunya ? Banaji kai har abunda za'aji ma kunya ne , murmushi yayi bai sake magana ba ,

Wayarshi ya fiddo yayi latse² sannan ya kara a kunne , bayan an ɗauka yace fito na iso , kashe wayar yayi ya faka motarshi gefen wani gida ,

Duk dani dashi babu wanda ya sake magana har mutumin ya fito daga gidanshi , saitin Dikko ya tsaya ya gaisheshi cikin girmamawa nima ya gaisheni cikin mutuntawa , ko kallonshi banyi ba ban kuma ansa ba , gyara zama Dikko yayi sannan ya kalleni fuska a ɗaure yace bakiji ana gaisheki , gabana ya faɗi yanayin kallon da yayi min nace ai nace lafiya lau bakaji
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On KWARATA
avatar
muhd-habu

6 months ago

Reply

Nice

Please Login or Register in order to submit comment