Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Cikin kuka nace shikenan kullum mai makon katifa tahau saman gado sai gado yai ta hawan katifa nidai na shiga 3 , Mamy tacemin da Allah ke banza ce ki kwantar da hankali babu abinda zai faru domin na sake kiran yarinyar nayi mata baraza na da zan saki vidion a social media idan Al ' Ameen ya sake magana kuma ta kama kanta sosai ,

Dakel dai Mamy ta lallashe ni ta kwantarmin da hankalina ta sake bani ƙwarin guiwa , a gidanta na yini saida nayi sallah isha'e ta kawo ni gida ,

Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya , yanzu tsawon watanni 3 kenan da kafa su Ummu Affan da Maman Sadiq a ƙungiya kuma tun daga ranar dana kaita bata sake bi takaina ba , yanzu tama ƙwace sosai wuta kawai takeyi abunta a cikin anguwa ,

Mijinta kuma tuni ta wanke ta bashi dan tunda ya taso ya fara hayagaga ta kwantar da banza da asiri , Maman Sadiq itama tuni an mata register amma bata ƙarƙashin ƙungiyata tana ƙarƙashin ƙungiyar su Amisty ne ,

Safiyya kuwa ɗiyar Baba ƙarami ciki gareta , gashi biki yazo Mamy ta hana talabijin bare labulaye , fitina sukayi ta rashin lissafi akan rashin talabijin da labulaye , ga rashin lafiya ya taso ta gaba tun Safiyya tana boyewa har abu ya fara damunta dan haka ta faɗawa Mamy cewa bata lafiya wata 3 bata ga jinin al'ada ba , kai tsaye Mamy tace ciki gareki sai kawai kije ki zago bedi ki saɓa kisha ,

Safiyya kuwa ta gaji da ɓoye ²ta rasa ina zata soka rayuwarta gashi Mamy bata , bata sahihiyar mafita ba , dan haka kawai ta haƙura ta faɗawa mahaifiyarta komai bata ɓoye mata ba , da Mamy da mahaifiyar Safiya akaci gaba da musayar harshe tsakanin Mamy da Uwar Safiyya , tashin hankali naƙin ƙari , ni ko kada Mamy ta faɗamin cewa nayi ai ba danneta akayi ta ƙarfi aka ƙwata ba lokacin da Alhaji yake bata tana ta tanɗewa tare da wa suka tanɗene ? Taje can taji da abunta sakaran banza tunda bata iya shan gishiri ba ,

Ƙarshen film in dai mahaifiyar Safiyya zama akayi aka sasanta suka fuskanci juna ita da Mamy daga ƙarshe dai a asibiti aka wanke cikin tass , ta tashi babu talabijin ba labulaye babu budurci kuma babu albashin kuɗin aikin da alhaji yayi , bayan wanke ciki da sati biyu aka ɗaurawa Safiyya aure , kwanata biyu a gidan miji ya korota tare dayi mata shegen duka rashin samunta da baiyi ba a matsayin budurwa , itama daga nan ta yanki nata tikitin na shiga sahun jerin *Kwarata...* kuma buƙata na ya biya.

Rayuwa mukeyi dai tsakanin ni dasu Amisty kowa naji haushin kowa , har yanzu ban sake ganinta da Babana ba , ta sake faɗaɗa ƙungiyarta da manyan mata masuji da duniya kuma duk matan aure sunfi yawa a cikinta domin yanzu kasuwar sutafi ja ba'a neman "yan mata kuma bata zawarawa akeyi ba matan auren dai ,

Ƙungiyar Amisty ta samu karɓuwa fiye da tunanin mai tunani ta samu kuɗi ta goge ta zama lafiyayyar hajiya , nima kuma inata bakin ƙoƙarina wurin ganin na kafa tawa ƙungiyar amma wallahi taƙiya daga ni sai Mamy a ƙungiyarmu , itama Ummu Affan ta kafa tata tana bada hayar matan aure ko a hanya ta ganni batamin magana saboda tana ganin tafi ƙarfina , al'amirin duniya ya fara bani mamaki dan haka na fara sanyi da rayuwata.

Mazan kuma nabi su² amma da an fara ciniki dai kalmar ɗaya ce 1k gani ni kuma haɗama gareni bana iya iba kaɗan sai in kantamo dubu ɗaruruwa , zuwa wannan lokaci kuma al'amura sunjamin baya sosai tun ba'ayi nisa ba duniyar ta ajiyeni bani ake yayi ba lokacin ba nawa bane na wasu ne , kenan tun kafin na ajiye bariki tana neman ta ajiyeni , dan har alaji su Amisty sunyi gaba dashi !

Ina cikin wannan tararrabi Allah ya kawomin wani zazzafan matashi maiji da kanshi ga kuɗi ga gayu amma matsala ɗaya wallahi mummuna ne ,

Naji daɗin zuwanshi kuma mun antaya soyayya shi ya wankoni daga talauci yayi ta yayyafin ya cidar hadarin naira da anyi tsawa saidai kiga yana ɓarin naira , cikin ƙanƙanin lokaci nima na farfaɗo na fara dawowa hajiyata ,

Naci gaba yanzu har hotel nake kwana amma matsalar ɗaya abunda na fuskata bayada alƙamin rubutu , kullum haka zanje in kwanta salaf in taso babu wani ɗan shafe² ko ɗan lashe ² ko ɗan tsotse² idan kuma na tashi tafiya haka zai bani kuɗi masu sa mutum ya kasa gano hanyar gidansu , abun a dameni dan haka na tambayeshi nace shin wai kai bakajin kanajin sha'awata ? Saidai yayi dariya yace yana da sha'awa in kwantar da hankali ranar hawa na zuwa ,

Ina kwance ina bacci a saman gadon hotel nayi guda² ina sararawa abuna idanuwana a rufe amma ba bacci nake ba , a tunaninshi nayi bacci dan haka ya tashi saf² ya fita daga bedroom in , wallahi haka nan naji tsikar jikina ta tashi jarr hankalina ta tashi ƙararrawa ta doka hayani ta riƙa tashi cikin kaina , da sauri na sauko daga saman gadon nayi bakin ƙofa ,

Da sanɗo na shiga palon ya bada baya yana waya cikin harshen turanci , hakanan na tsargu dan haka zuciyata tace kiyi masa vidio ko recording kamar yadda kika saba wannan da ganinshi baida gaskiya , da sauri na latso recording na fara ɗauka saida ya gama wayar tas sannan ya juyo da wata irin siffa mai ban tsoro dasa firgici tunda nake duniya ba taɓa ganin irin siffar ba , dakewa nayi banji tsoro ba kuma ban firgita ba naci gaba da addu'a nima na tsareshi da ido ,

A hankali siffarshi ta dawo siffarshi da nasanshi da ita , murmushi yayi yace ke matar aure ce ? Na girgiza kai da a , a , yace tou ki wuce daga yau karki sake dawomin matan aure muke nema , murmushi nayi tare da cewa ngode kuma na barka lafiya , ina faɗin haka nayi gaba abuna ko ciki ban koma ba bare na ɗauko gyalena , saida na fita daga ɗakin na ruɗe na firgice na kwarara wani irin ihu mai tada hankali ,



Hmmm

_Ƙalu bake gareku matan aure......_







04/10/2019





*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*



🅿 ------ 49


Gaba ɗaya na firgice na fita hayyacina kururuwar da nakeyi ta karaɗe kaf girman hotel in , hayagagata ya jawo hankalin mutane akayo wurina ana lafiya ? Duk wanda na gani sai inga fuskar mutumin nan gareshi wayyo Allahna na shiga 3 🙆🏻 na lalace shikenan mutuwa zanyi na bani ׳ na ƙarasa maganar tare da faɗuwa ƙasa ina burgima.

Baiwar Allah lafiya ? Meke damunki ? Shine tambayar da mutanen da suka zagaye ni sukemin amma maimakon naji maganarsu sai naji muryar mutumin cikin muryar tsoratarwa da firgitarwa yana cemin da hantarki da ƙodarki ko zuciyarki wanne kika bamu....

Da sauri na dafe cikina na tallabo saitin zuciyata amma har yanzu wayata na riƙe ram a hannuna , cikin kuka nace wallahi bazan bayar ba , nawa ne ni ɗaya , cikina ne da zuciyata hantana da ƙoda Allahna ya bani ba wani ba , kuma ubangiji bazai baku damar rabani da ko ɗaya ba , wata irin gigitacciyar dariya akayi tare da cewa kina nufin kinci kuɗinmu a banza ? Tou wannan kuɗin ki sani jinin wasu ne da wasu sassa na jikin ɗan adam dole ki bayar da naki kema domin a bawa dodo ya bamu kuɗi zuciyarki zata shiga kwarya , bankwana da duniya sai wata rana....

Gaggaɓewa akaci gaba dayi da dariya data gigitani a karo na biyu , addu'o'e naci gaba dayi da ƙarfi idan ina addu'a bana gama wata saina saketa na kamo wata , dai najin sautin muryar dariyar nayi sai sautin kuka har zuwa wannan lokacin ban daina addu'a ba , bayan wani lokaci kuma na dainajin sautin kukan gaba ɗaya...

Da sauri na miƙe ko jikina ban tsaya kakkaɓewa ba nayi gaba , mutane suka bini da kallo yayin da wasu ke tunanin ko ina da taɓin kwalwa ne , da gudu na fita daga hotel in , ina na fita na samu napep sai gidan Mamy amma har yanzu hankali na baya jikina gaba ɗaya a ruɗe nake , napep na tsayawa na fita da gudu nayi cikin gidan Mamy , bata nan sai yara na samu nace musu ina Mamarsu ? Sukacemin yanzun nan ta fita tace idan kinzo ki kirata ,

Jikina yana ƙyarma na fara laluben wayar Mamy babu ɓata lokaci ta ɗauka , gaisawa mukayi nace mata kina ta ina haka ne ? Sunan hotel in dana baro ta faɗamin tare da cewa wani sabon sauna ne na samu ki jirani na wankoshi cikin mintuna kaɗan zan dawo , kaina ya juya a gigice nace karki je , ki dawo hotel in nan akwai wani gahurtaccen matsafi daya bayyana karki shiga ɗaki ki dawo , Mamy tace wane ɗaki ? Nace ɗakin dana shiga wallahi matsafi ne karki shiga ki dawo akwai zama na musamman , Mamy tace tou lamba nawa ne ɗakin ,

Da sauri na dafe kaina duniyar ta riƙa juyamin kamar nahau shillo mai wanawa , gafa lambar ɗakin ina gani a idona bana iya faɗa dan na iya lissafin lambobi tunda dasu nake sarving numbobin mutane a cikin wayata , ganin na kasa faɗa kawai nace ....

Ki dawo........... Na faɗi ki dawo cikin wata irin murya hawaye suka gangaro daga cikin idona ina cewa nidai kawai ki dawo matan aure yake nema ko wane ɗaki bana so ki shiga ki dawo Auntyna bana san na rasa ki adaidai wannan lokacin ki dawo dan Allah na ƙarasa maganar ina durƙushewa ƙasa naci gaba da kuka , amma duk wannan maganar da nayi sam Mamy bata jini ta riƙa hello , hello idan kina jina kawai ki jirani , tana faɗin haka ta kashe wayarta ,

Da gudu na fita daga cikin gidan , mai napep in daya kawoni shi nace ya maidani inda ya ɗaukoni dan dama ban sallameshi ba , nace kayi gudun bala'e ka kaimin motar nan maleji karka tsaya kuma karka kauce ina so kawai na buɗe idona na ganni a hotel in nan kamar kyaftawar ido ,

Gudu mai napep yakeyi amma ce masa nake ya ƙara ina kiran wayar Mamy amma ba'a ɗauka , saidai na daki napep in nace wuta mai mota nace karka tsaya kaucewa ababen hawa muje kayi tuƙin nan kamar babu koma bisa titin nan saimu , gudu yake balbalawa na tashin hankali amma gani nake kamar baya tafiya , wayar Mamy kuwa saidai ta ƙari ringing inta ta tsinke amma ba'a ɗauka har muka isa hotel in ban daina kiran wayar Mamy ba kuma bata daina shiga ba haka kuma babu wanda ya ɗauka...

A harabar hotel in naga dandazon mutane , da gudu na tunkari inda suke kamar wata mahaukaciya na riƙa ture mutane , hasahsena ya zama gaskiya domin Mamy ce yashe a ƙasa mutane sun zagayeta ga "yan sanda har sun rigani hallara a wurin , jini ne kawai ke ɗiga daga cikin idon Mamy kamar babu ƙwayar idonta dan baka gani hasken idon ko sai jini dake ɗiga ɗis ² ,

A wurin mutane ke cewa yanzu wata ta fita itama tana ihu ita Allah yasa tana da sauran shan ruwa a gaba , goge hawaye nayi a zuciyata nace ba ni suke so ba matan aure , mutane sukaci gaba da cewe lallai akwai abinda yake faruwa , jiki a sanyaye na na isa gaban Mamy nace Aunty na ƙarasa maganar ina mai kamo hannuwanta , bata iya magana ma kwata² dan haka na rungumeta naci gaba da kuka , bayan "yan sanda sun gama bincikensu kuma basu samu wata sahihiyar sheda ba haka aka ɗauki Mamy da wayarta akayi asibiti da ita... Nima napep na koma nace masa mubi bayansu.

Bayan mun isa asibiti "yan sanda suka danƙamu a hannun likitoci babu ɓata lokaci aka shiga duba Mamy , tashin farko dai likitocin sun tabbatar da babu idon Mamy kuma har yanzu jini bai gama fita ba , ni kuma hankalina yafi karkata akan wayarta dan haka naje wurin ɗan sanda nace ranka ya daɗe wayar zaka bani na kira Babanmu ,

Kallona yayi sama da ƙasa sannan yace wace ce ke ? Nace ɗiyar mara lafiyarce ni , dan bana nan na dawo gida "yan uwana sukace Mama tace ta fita amma idan na dawo na kirata , bayan na dawo suka faɗamin na kirata mun fara magana da ita a waya daga baya kuma saita nunamin batajina , ka duba jerin kira kuma zaka gani dan daga baya nayi ta kiranta bata ɗauka ba ,

Miƙomin wayar yayi domin wayar Mamy ba'a buɗeta sai an zana pattern yace buɗeta tou tunda kince ta Mamanki ce , lafiya lau na zana na buɗe wayar domin kullum a gabana take zanawa kuma baida wahala , bayan na buɗe ya duba yaga kiran da nayi mata kamar dai yadda nayi masa bayani , yana cikin dubawa kira ya shigo dan haka ya ɗauka , bayan gaisuwa naji yace muna genaral , yana faɗin haka ya kashe ya miƙomin wayar ,

Babu wani daɗewa mijin Mamy ya iso asibitin , yasha kuka kamar ranshi zai fita duk iskancin da Mamy ke zubawa baya gani yana san matarshi , jikin gadon Mamy ya matsa cikin kuka yace Mamy Allah ya tsinemawa wanda yayi miki haka , Allah ya baki lafiya mata ta ubangiji yasa ki warke ,

A wahalce Mamy tayi murmushi ta lalabo hannun mijinta tace kayi haƙuri mutuwa zanyi amma ina roƙonka daka yafemin , cikin kuka ya rungume Mamy yace Hajiya baza ki mutu ba wallahi baki mutuwa , Mamy tace naji amma kawai kace ka yafemin , cikin in'inna yace na , na na ya.... Ya fe miki , godiya tayi masa tare da cewa naji muryar Sultana tana ina ? Yace gata nan hajiya ya kamo hannuna ya haɗa da nata ,

Umarni ta bashi cewa da Allah ya fita zatayi magana dani , cike da ladabi ya fice daga ɗakin , Sultana ta kira suna na , nace na'am tace dubamin babu kowa a kusa dani ? Babu Aunty na faɗa cikin girmamawa magana ta farayi bayan na tabbatar mata da babu kowa a wurin :•

Sultana ta kira suna na , nace na'am Aunty , tace tou ki saurareni dakyau , nace inajinki Aunty , Mamy tace kinga whatsapp in nan da kike ganinta ? Wallahi ba ƙaramin haukata mata takeyi ba , shiru nayi ban sake magana ba naci gaba da sauraren Mamy .

Aurena biyu a duniya , ina da shekara 39 akamin auren farko bayan nasha gwagwar mayar rayuwa , iyayena ba masu kuɗi bane suna dai da rufin asiri na ci da sha da sutura , mahaifina ba ɗan kasuwa bane kuma ba wani shahararen ɗan boko bane ba , yana aiki a ƙarƙashin kamfani wani attajiri ,

Matan Babana biyu daga mahaifiyata sai abiyar zamanta , muna da yawa sosai mu "ya "yan babanmu , cikin hukuncin Allah matan gidanmu suna auren mazaje masu rufin asiri , duka matan gidanmu saida aka aurar dasu kaf har ƙanne na ni ban samu mijin aure ba ,

Na tayar da hankalina sosai domin auren nake so ido rufe amma ban samu mai aurena ba , abin ya dameni sosai saina ma daina fita kwata ² kullum ina gida ko a familynmu daina shiga nayi domin na ganɗame sosai saina farajin kunyar shiga mutane ko baƙi akayi gidanmu sai in ɓoye ,

Ina wannan ɓoye ²n ne Allah ya kawomin Bello a rayuwata , Bello abokin Yayana ne duk duniya baida aminin daya wuce Bello shima Bello baida aminin daya wuce Yayana , kowa yana san kowa kuma kowa baya ɓoyewa kowa sirrin junansu , sun yadda da juna fiye da tunaninki domin dai Bello zai iya tarawa da matar Yayana shima Yayana zai iya tarawa da matan Bello ,

Tunda Allah yasa ya ƙyalla idonshi ya ganni ya liƙemin , nasan baƙin halin Bello sosai nasan illarshi kuma nasan miyagun halayyarshi dan haka koda ya furtamin kalmar so ban ansa ba nace bana sansa , shine ya faɗawa Yayana yana so na amma nace bana sansa , shine Yayan nawa yazo ya sameni yayi min kaca ² , nace ni bashi ne bana so ba halinshi ne bana so , kuma kaji tsoron Allah kai kanka baza ka iya bashi auren "yar uwarka da kuke ciki ɗaya , Yaya yace tou ko kinso ko kinƙi sai kin auri Bello idan baki aureshi don Allah ba zaki aureshi dan dole , saikin nemo Bello da kanki , yana faɗin haka yayi gaba abunshi ,

Tun daga wannan ranar sukayi ta kusatsamin asiri na firgice na fita hayyaci na da kaina nake nemo Bello , idan na fita ban ganshi ba ko zankai gobe ban dawo gida ba saina ganshi hankalina zai kwanta ,

A taƙaice dai Bello na aura aurena na farko , ranar da aka kawoni gidan Bello bayan mutane sun watse shima Bello ya shigo da abokanshi da suka rako ango ɗakin amarya kamar dai yadda akeyi ,

Kowa fatan alkairi yaimin da addu'ar zaman lafiya , bayan an gama Bello ya bayyanar min da abokanshi kowa ya faɗamin sunanshi , saida yazo kan *BINNA...* ya dafashi cike da soyayya yace kinga wannan nace Eh yace Binna kenan Bello baya rayuwa saida Binna kamar yadda mutum bai rayuwa saida lumfashi , ina san Binna fiye da yadda nake san kowa a duniya , Binna nawa ne nima nashi ne , murmushi Binna yayi cike da izza amma baiyi magana ba , gaskiya Binna ya shiga zuciyata kuma duk duniya ban taɓa ganin wanda nake so a daidai wannan lokacin ba kamar Binna ,

Sun ɗan daɗe dai suna fira amma har akayi firar aka tashi Binna bai saka baki ba har suka gama suka tafi , bayan Bello ya dawo daga rakiyar su yacemin na tsani Binna na nuna miki shi domin ki ganshi , hawaye ya cika a idon Bello yace tsinan Allah kawai ranar da zan zama ango Binna ya ɗauke budurci ya gudu , saboda kawai nayi ma yarinyar gidan da suka ɗaukoshi a bakin titi suna taimaka mishi ,

Nayi alƙawari saina ƙafa babban tarihi a zuciyar Binna saina tagayyara mishi rayuwa saina zama silar rushewar kaf ahalinsa wanda suka gabata da wanda basu zo ba , saina jefa ƙiyayya mara gogewa tsakaninshi da "yan uwanshi da suke uba ɗaya , nayi alƙawari kuma babu gudu babu ja da baya ko duniya zatashi saina cika muradina ,

Wani irin nishin wahala Mamy tayi har yanzu jinin bai daina ɗiga ba , a wahalce taci gaba da cewa....

Bayan Bello ya gama alkaba'inshi ya hawo gado babu wata sallar godiya ga Allah babu wani abunda ya shigo min dashi irin wanda ango yake zuwa ma amarya dashi a daren farkonsu , haka ya hayeni yaita sassaƙa kamar mai faskare ya samu babban bedi , haka kuma babu wata addu'ar tarawa da iyali ,

Sam banajin daɗin zaman aure da Bello dan na fahimta mugun atsabibi ne , babu sallah bare salati haka kuma bai yadda da ƙaddara ba komai dai malamin tsibbu , ina haƙuri dai ina zama amma sam bana sansa dauriya ce kawai ,

Tun daga ranar da aka kawoni ina amarya ban sake ganin Binna ba saida yazo faɗama Bello an haifeki ,

Duk ƙudirin da Bello yayi akan Sultana da burin mahaifinta akanshi ta faɗawa Sultana , tace wannan shine silar abinda ya rabani da Bello domin na nuna ban yadda ba ya aiwatar da ƙudirinshi akan Binna ba domin gaskiya ina sansa kuma bazan bari a cutar masa da rayuwa ba ,abun yayi ma Bello ciwo dan shine ya sakeni ,

Bayan mun rabu nayi ² Binna ya aureni yaƙiya ina sansa kuma ina sha'awarshi dan haka nayi masa tayin kaina kuma Allah ya taimakeni ya ansa , da sauri na runtse idanuwana , Mamy bata gani na dan haka taci gaba da cewa kullum ni nake isko Binna ko ya nunamin baida buƙata sai nayi yadda za'ayi ya kwanta dani danni kaɗai nasan yadda nakeji idan ina kwance dashi ,

Har na shekara 2 ina zawarci Binna fa ya kame akan bazai aureni ba , dole na haƙura na samu miji nayi aure , tunda nayi aure na daina zuwa wurin Binna , ina zaune da mijina lafiya babu abinda na nema na rasa , saidai zaman kaɗaici yana damuna , wannan dalili yasa na saya babbar waya na fara chating..

Banda friends sosai a whatsapp dan haka dana duba naga wanda ke online saina dameshi da surutu , idan nayi magana sai mutum ya ɗauki tsawon lokaci bai bani ansa ba , na gaji dai nacema wata ƙawata wai sai inyi magana kuyi kamar baku gani ba , dariya tayi sannan tacemin haba hajiyata yaushe rabon duniya da ayyaraye , ni bana cht da mutum prvt ina can group inmu na mata masu duniya , wayayyin mata masu aji masu faɗa a gidan aurensu aji ina ƙaruwa ina zan tsaya saurarenki.

Koda na tambayeta me ake koyawa a group in sai tacemin bara tayi adding ina gani ya kori ji , nace tou , bayan tayi adding ina ta gabatar dani tare da tura hotona , kowa dai yaimin fatan alkairi , a hankali dai nake rayuwa da "yan group in ina fuskantar su ,

Basu da aiki sai turo style na ɗinki , idan sabuwar atamfa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On KWARATA
avatar
muhd-habu

6 months ago

Reply

Nice

Please Login or Register in order to submit comment