Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

jibgegiyar mace a gefenka, amma a zahirance gwaram ce tunda har ka samu damar fitowa, saboda haka k'aranta ba matsala bace, abinda wata motar ta kasa sai kaga machine yayi.

Tabbas muna da masaukin ki, d'aki d'aya 5k ne a wata haka kowa yake biya sai kuma zaki bayar da kyautar dare d'aya ga mai gidan wannan shine tsarin wannan gida me kika ce ?

Wannan ba damuwa bace amma nima ina da nawa tsarin na basu amsa, muna saurarenki suka bani amsa, gyara tsayuwa nayi sannan naci gaba da cewa ina da ranakun aiki ina da na hutu, yau da gobe da jibi daga nan har zuwa k'arshen satin nan babu maganar kwanciya da ko wane na miji amma zai yadda daga nan zuwa sati na gaba.........? Nayi musu haka ne dan ni kwana ukku kad'ai zanyi na k'ara gaba abu d'aya zuwa biyu nazo koya kad'ai a gidan karuwai kuma a raina bazan biya kud'in hayar ba haka na yanke..

Na saman benan yace min mi yasa kike da wannan tsarin haka ne An mata.......? Wata irin fad'uwar gaba naji tare da kallonshi da sauri domin ya kirani da irin sunan da Dikko yake kirana dashi, janye zance Dikko nayi a raina sannan nace idan har ruwa ya kare a cikin tanki ko ka tara abun ibar ruwa baka samun komai haka nan zaka gaji da jira ka d'auke, amma idan aka bari ya taru kana tarawa zai cika ma duk abinda kake buk'ata, to nima haka take daga gareni karfina ya k'are dan na kwana ina aiki saboda haka a barni na huta na kwanakin dana iba,

Murmushi yayi tare da cewa gaskiya ku bata d'aki tabbas muna da masaukin ki a gidan nan, sakaran banza na fad'a a cikin raina nace otiho dakai baka tsan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, duk shelar da nayi na ce bariki tafini tabbas ka gagara ganewa da gaanin wannan sha ka tafi ne, fuska ta d'auke da mugunta nace mashi idan an bani d'akin kai ka biya kud'in sannan kuma ka bani rance dubu d'ari, tukuicin d'aki zaka kwana biyu kana morewa dani nima daga cikin irin baiwar da Allah ya bani, dubu d'arin ka kuma da kud'in d'aki duk zan baka su idan na fara kasuwa......

Ba damuwa a bata d'akin sama lamba 59 ya fad'a cikin zaguwa, ga *kwartuwar* shi gefe ya manta da labarinta, hawa sama nayi aka nunamin d'akin, makulli aka bani na bud'e na shiga ina shiga na kulle d'akin ta ciki.

Dudduba d'akin nayi bayan na shiga, falo ne sai d'akin bacci madafar abinci da bayi, d'akin bacci katifa ce irin ta "yan bodyn sch, falo tayils ne babu kujeru sai kafet, k'arewa d'akin kallo nayi sannan na koma jikin tagar d'akin na fara kallon yanda *karuwai* suke rayuwarsu.

Ina tsaye na fara tunanin fuskar da tacemin An mata, ina k'ok'arin tunoshi kwalwata ta fara jakkancin data saba, a bayyane nace ki saurara kar kimin haka don Allah rayuwa mai had'ari na kawo kaina ki tausamin ki sanar dani ko waye waccan, kwana biyu kad'ai zanyi nabar gidan nan amma ina so ki sanar dani ko waye shi d'in......

Bugawa zuciyata tayi tare da cewa abokin Dikko ne wallahi, shine ya raka abokin Babanki aka kaiki wurin Dikko....... Kamar kasuwa haka zuciyata da kwalwata suka fara gardama hayani ke tashi daga cikin kwalwata da zuciyata, yayin da kwalwata ke cewa bashi ne ba zuciyata tana cewa tabbas wallahi shine, kyarma jikina ya farayi gaba d'aya d'akin naji yana juyamin, kamar ana jijjiga ni naji anayi dan haka da sauri na dafa bango na zauna k'asa tare da fara karanto duk addu'ar data zo bakina......

Bayan na samu natsuwa ne, na dafa daidai saitin zuciyata da kwalwata sannan nace idan nayi muku wani laifi da Allah ku gafarceni amma ku daina dakushe wa ku barni nayi komai cikin hikima kamar yanda na tsara zanyi. Kuyi hakuri ku daure ku bani gudamwa.

Kwana na biyu a gidan karuwai ina koyon abinda yakaini, safe rana dare wannan d'an iskan yake kawomin abinci, a yanda nayi niya yaune zan tafi amma na fasa tafiya sai naga mai gidan bene....... Wato mai wannan gidan na karuwai.

Da daddare misalin 9:30pm na sauko k'asa na samu wuri daga gefe na zauna banma kowa magana ba haka kuma babu wanda na kalla amma hankalina gaba d'aya yana wurinsu,

Murmushi nayi a lokacin da naji wasu *kwarata* na ciniki, kallarni sama da k'asa kaga zubina ai kasan nafi k'arfin ka kwanta dani kace 1k zaka bani, yo wace kala gareki ni keda bakin masai baku da banbanci a wurina tunda kowa ma zuwa yakeyi ya hau ya kama gabanshi, ina ma laifina da zan baki 1k idan haka yayi miki in bayar idan baki yadda ba naje wurin Umma.

Mai makon naga taji haushi sai kawai tayi dariya tare da cewa shege kenan, to kawo dubu d'in, d'an sosa kansa yayi sannan yace kai nama manta dubun zan siya ma iyalina biredi wallahi kuma machine ina baida mai amma bari dai in bada dari biyar, batayi zuciya ba tace to kawo dari biyar in, bata yayi suka shiga cikin d'akin.....

Tsoki nayi tare da ganin wallan matan aure, kuna gida kwance mazajenku suna nan wurin sakarkarin matan da basu kaiku komai ba, kuna can kuna girman kai da kunyar banza da sakarci aje a yayo cuta a cusa muku babu gari babu dalili.

Me Allah ya rageku dashi ? Me karuwa take dashi wanda Allah bai baki ba ? Naki ma yafi nasu daraja tunda ke ta hanyar bautar Allah zaki mik'ashi kuma Allah ya baki lada, amma matar malam bahaushe tanajin kanta yai mata girma ji takeyi idan ta nunawa mijinta tana buk'atarshi kamar zai rainata, wata ma macen idan bashi ya nemeta ba saidai ayi ta zama a haka, to ya nemiki jiya shekaran jiya kullum har "yar basirar dake gareshi ta kare, ko kuma sai yazo kwanciya dake ki tashi hankalinshi ki tado fitar da kila anyi sati ko wata da yin abu saboda ke kawai za'a kwanta dake, kin b'ata mishi rai yaji gaba d'aya abun ya fita a kanshi ko kuma yayi shi ba cikin natsuwa ba, da kanki kike jefa kanki halakar da babu mai iya fitar dake sai Allah , daga haka sai shedan ya fara doka masa gangar sa ya barki yaje ya nemi na banza, dan babu zuciyat wanda shed'an baya wasa da ita.

Idan kika had'u da muguwar mace sai ta rabaki da mijin fafur ki kasa gane kanshi, daga nan sai ki fara tattara kaya ke a dole kinyi yaji. Idan an tambayeki abinda ya had'aku ki fara cewa baya dawowa gida da wuri, idan kin kawo abinci baya ci, idan kinyi kwalliya baya yabawa, bayan duk kece babban da kika jawo ma kanki wannan damuwar........... Mudai je zuwa zamu gano masu laifin tsakanin matan da mazan su waye masu matsala......

Ina zaune a wurin har 12:30am bai fito ba, tou me akeyi haka har yanzu wanda ba'a gama shi ba ? Duk gorin da yayi mata na had'a mata k'addarar ta da bakin masai batayi zuciya ba.

Lallai bariki bariki ce, mutanen cikinta suma sun barikantu kodai taji haushin abun bata wani nuna mishi damuwa ba, ina nan zaune a wurin har mutumin da nake tunanin mutumin da nake tunanin yana tare da Dikko ya shigo,

Da fito ya shigo babu sallama sai gyara wando yakeyi kamar wani sabon shigar *kwartanci* kallona yayi tare da cewa har yanzu baki bacci ba ? Nima irin yanda naga *karuwai* sunayi idan zasuyi magana nayi, d'an kashe idanuwa nayi cikin sigar bariki sannan nace banyi ba, to me kike jirane ? Kud'in da zaka bani ina so na shiga kasuwa gobe zanyo siyayya kasan jibi nake komawa bakin aiki na......

Murmushi yayi saboda yasan shine farkon layi idan na fara iskanci, kina da account ne ? Ya tambayeni ?Banda shi, to da safen zan baki idan naje wurin mai gida na, Allah ya kaimu nace tare da mik'ewa na fara tafiya cikin *kwartanci* sakaran banza ya bini da kallo, zakaci ubanka idan na gano ku, jibi kamar yanzu kana nan zakayi baccin bak'in ciki dan zan b'ace muku b'at kamar jirgi a cikin gizagizan sararin samani............









07/08/2019


⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*


*_Ku nemi naku fitowa ta farko daga shahararriyar kungiya mai san farin cikin makaranta wato BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION, sabon salo ne daga shahararrin marubuta biyu, MAI JIDDA daga alkalamin MARYAM MUHAMMAD HASSAN, MAFARKIN NANAH, sabon sauyi na SA'ADATU LAWAL maman ilu, kar ku sake ku bari a baku labari......_*

*_ZAINAB ATTAHIRU B ' K sakonki yazo gareni ngode sosai ina miki fatan alkairi, ki kasance cikin farin ciki da kwanciyar hankali har a busa kaho............_*


🅿 ------ 8


Tafiya mukeyi daga ni harshi babu wanda yayi ma wani magana, saini da a zuciyata nake ta addu'a, Allah na rok'eka ka bani farin jini ka zubamin kwar jini kasa na rik'a bud'ewa mutane ido duk wanda yayi ido dani, Allah kasa wannan kyawun nawa ya zamar min babban jari, kasa nayi suna sosai a harkar karuwanci.

Tafiya mai nisa mukayi har muka iso k'ofar gidan, sai yanzu yayi magana cewa ranki ya dad'e anzo, ba tare dana fito ba nace masa, malam ya sunan anguwar nan ne ...... ?

Sanin da nayi ma anguwar a da yanzu karuwai sun canja mata suna, gidan na sani ba sunan wurin ba, ki sauka ki bani kud'ina sauri nakeyi.

Ina k'ok'arin fitowa nace kasan kana sauri ka bari aka haife ka ? Ka iya tafiya domin dai ni d'abi'ata idan nahau abin hawa gaskiya bana iya biyan kud'i, amma Allah ya taimaka sauka lafiya !

Fitowa yayi daga cikin napep in ya fara ke bansan rashin kunya bani kud'i na ko in wulak'anta ki a wurin nan, d'an gajeran murmushi nayi tare da cewa banda haukar ka wanda ya fito bariki ai baya tsoron wulak'anta, ai ta wulakanta ta kare tunda har na fito daga gidanmu na taho yawon karuwanci........!

Shiru yayi ya rasa abin cewa, dan haka nace ko kana da sauran magana ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa jeki kya gani...... Dariya nayi sosai irin ta cikakkin "yan duniya na kashe dariyar da rangad'a gud'a, sannan nace shege kaji uwar bari ko ?

Tou babu uwar da zan gani dan duk wani gagararren d'an iska dake fad'in garin katsina nice uwarshi nice ubanshi, duk wani kangararren dan iska da "yar iska da iyayensu sukace jeku kun gani, to wallahi idan suka taho ni zasu gani.....

Sauk'i ya nemar min sannan ya koma cikin napep inshi, yana k'ok'arin tashin ta nace malam dakata, tsayawa yayi yana kallona, kana da waya ne ? Rik'e waya ai sai ke da kika fito neman haramun, to naji ba komai, kadai ganni sosai ko ? Kuma zaka iya ganeni gobe idan mun had'u, tsoki yayi sannan yace taya zan manta da fuskarki azzaluma kawai, yawwa ina so dama ka gane ni gobe idan ka ganni, ni suna na Sultana idan kayi gaba ka bada labarina dan ina san cikin d'an k'ank'anin lokaci suna na ya zagaya kaf fad'in garinnan, sauka lafiya.......... ! Ina fad'in haka na shige gidan karuwai,

Tun a zauren gidan na farajin kuruwar wata karuwa, karuwinta ne yake dukanta da belt kamar uba yana hukunta d'iyar sa, babu ji babu gani yana dukanta yana cewa dan ubanki sai kin bar gidan nan, wallahi na gama zama dake, d'an murmushi nayi a bayyane nace Allah sarki duniya yayin da wasu ke shigowa yayin wasu ke fita,

A hankali nabi gidan da kallo ga mutane nan iri iri, yayin da wasu ke caca, wasu na lido, wasu na shan sigari yayin da wasu ke kwance saman jikin maza babu kunyar Allah bare tsoranshi, wato abinda dai na lura duk abinda kake so shi kakeyi babu mai ce maka dan mine ne ......?

K'arewa gidan kallo nayi sosai, d'akuna ne k'asa da sama, bene ya zageye k'asan gidan yayi masa rumfa sai yanayin gidan ya tabbata kamar irin hadari ya taso. Wani irin ihu na zabgaga tare da kashe ihun da gud'a, wanda haka yayi sanadiyyar jawo hankalin duk wanda ke cikin gidan na waje da wanda ke d'aki babu wanda aka bari kowa saida ya fito....... Kirari na fara kwararwa bari ba tare dana kalli dandazon mutanen dake kallona ba.

Bariki ba'ayi miki tilas babu wanda ya rako wani kowa da k'afarshi yazo kuma in yaji wuya shi zai koma, baki duba mai kyau ko mummuna, haka kuma babu ruwanki da maye ko mayya mai lafiya da mai cuta duk wanda yazo kina da masaukinshi, baki san inda kowa yake ba amma kowa yasan inda kike, gani nazo ki sakamin albarka, baki da tabbas bariki haka nima bani da tabbas, matsalar ubace ta kawoni amma ina tare da had'ari guda d'aya, bana san shiga sabgar kowa karki sake ki bari wani ya shigo rayuwata, ilimi nazo d'auka a cikinki amma ni nafiki rashin tabbas, ina da masaukin kowa amma banda na mata.....duk namijin da uwarshi ko ubanshi yace jeka ka gani tabbas idan yazo ina da masaukin shi nima,

Kija da'irarki ki bani tawa, bana shan sigari bana cin goro, abu d'aya ya kawoni shi zanyi na koma, bansan bincike haka kuma bana san bin kwakwaf, kar ku sake naji bakin wani nan, idan ba amsa zai bani ba, kuma magana d'aya nake so ta fito bakinku akwai ko babu, itace amsar da nake so a bani, tambayata itace kawai d'akin zama ko nayi gaba.........?

Wani daga can saman bene yace ke "yar cakulkula dake har kin san dad'in namiji ? 'Daga kaina nayi sama na kalleshi sannan nace daga ganinka gidan haya aka haife ka, kaine matsala da kanka bakaji abinda nace ba ? Akwai ko babu kawai nake so naji.

Daga bayana wani yace ki bashi amsar tambayar shi mana sai mubaki taki, murmushi nayi sannan na d'aga kaina sama na kalleshi tare da cewa, duk tayar abun hawa sunanta taya, amma kaga tayar daf tafi ta jirgi girma amma abinda jirgi zai d'auka daf bata iya d'auka, jirgi ya d'auke ka kuma ya d'au kayan ka, kamar dai kai kaga ga jibgegiyar mace a gefenka, amma a zahirance gwaram ce tunda har ka samu damar fitowa, saboda haka k'aranta ba matsala bace, abinda wata motar ta kasa sai kaga machine yayi.

Tabbas muna da masaukin ki, d'aki d'aya 5k ne a wata haka kowa yake biya sai kuma zaki bayar da kyautar dare d'aya ga mai gidan wannan shine tsarin wannan gida me kika ce ?

Wannan ba damuwa bace amma nima ina da nawa tsarin na basu amsa, muna saurarenki suka bani amsa, gyara tsayuwa nayi sannan naci gaba da cewa ina da ranakun aiki ina da na hutu, yau da gobe da jibi daga nan har zuwa k'arshen satin nan babu maganar kwanciya da ko wane na miji amma zai yadda daga nan zuwa sati na gaba.........? Nayi musu haka ne dan ni kwana ukku kad'ai zanyi na k'ara gaba abu d'aya zuwa biyu nazo koya kad'ai a gidan karuwai kuma a raina bazan biya kud'in hayar ba haka na yanke..

Na saman benan yace min mi yasa kike da wannan tsarin haka ne An mata.......? Wata irin fad'uwar gaba naji tare da kallonshi da sauri domin ya kirani da irin sunan da Dikko yake kirana dashi, janye zance Dikko nayi a raina sannan nace idan har ruwa ya kare a cikin tanki ko ka tara abun ibar ruwa baka samun komai haka nan zaka gaji da jira ka d'auke, amma idan aka bari ya taru kana tarawa zai cika ma duk abinda kake buk'ata, to nima haka take daga gareni karfina ya k'are dan na kwana ina aiki saboda haka a barni na huta na kwanakin dana iba,

Murmushi yayi tare da cewa gaskiya ku bata d'aki tabbas muna da masaukin ki a gidan nan, sakaran banza na fad'a a cikin raina nace otiho dakai baka tsan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, duk shelar da nayi na ce bariki tafini tabbas ka gagara ganewa da gaanin wannan sha ka tafi ne, fuska ta d'auke da mugunta nace mashi idan an bani d'akin kai ka biya kud'in sannan kuma ka bani rance dubu d'ari, tukuicin d'aki zaka kwana biyu kana morewa dani nima daga cikin irin baiwar da Allah ya bani, dubu d'arin ka kuma da kud'in d'aki duk zan baka su idan na fara kasuwa......

Ba damuwa a bata d'akin sama lamba 59 ya fad'a cikin zaguwa, ga *kwartuwar* shi gefe ya manta da labarinta, hawa sama nayi aka nunamin d'akin, makulli aka bani na bud'e na shiga ina shiga na kulle d'akin ta ciki.

Dudduba d'akin nayi bayan na shiga, falo ne sai d'akin bacci madafar abinci da bayi, d'akin bacci katifa ce irin ta "yan bodyn sch, falo tayils ne babu kujeru sai kafet, k'arewa d'akin kallo nayi sannan na koma jikin tagar d'akin na fara kallon yanda *karuwai* suke rayuwarsu.

Ina tsaye na fara tunanin fuskar da tacemin An mata, ina k'ok'arin tunoshi kwalwata ta fara jakkancin data saba, a bayyane nace ki saurara kar kimin haka don Allah rayuwa mai had'ari na kawo kaina ki tausamin ki sanar dani ko waye waccan, kwana biyu kad'ai zanyi nabar gidan nan amma ina so ki sanar dani ko waye shi d'in......

Bugawa zuciyata tayi tare da cewa abokin Dikko ne wallahi, shine ya raka abokin Babanki aka kaiki wurin Dikko....... Kamar kasuwa haka zuciyata da kwalwata suka fara gardama hayani ke tashi daga cikin kwalwata da zuciyata, yayin da kwalwata ke cewa bashi ne ba zuciyata tana cewa tabbas wallahi shine, kyarma jikina ya farayi gaba d'aya d'akin naji yana juyamin, kamar ana jijjiga ni naji anayi dan haka da sauri na dafa bango na zauna k'asa tare da fara karanto duk addu'ar data zo bakina......

Bayan na samu natsuwa ne, na dafa daidai saitin zuciyata da kwalwata sannan nace idan nayi muku wani laifi da Allah ku gafarceni amma ku daina dakushe wa ku barni nayi komai cikin hikima kamar yanda na tsara zanyi. Kuyi hakuri ku daure ku bani gudamwa.

Kwana na biyu a gidan karuwai ina koyon abinda yakaini, safe rana dare wannan d'an iskan yake kawomin abinci, a yanda nayi niya yaune zan tafi amma na fasa tafiya sai naga mai gidan bene....... Wato mai wannan gidan na karuwai.

Da daddare misalin 9:30pm na sauko k'asa na samu wuri daga gefe na zauna banma kowa magana ba haka kuma babu wanda na kalla amma hankalina gaba d'aya yana wurinsu,

Murmushi nayi a lokacin da naji wasu *kwarata* na ciniki, kallarni sama da k'asa kaga zubina ai kasan nafi k'arfin ka kwanta dani kace 1k zaka bani, yo wace kala gareki ni keda bakin masai baku da banbanci a wurina tunda kowa ma zuwa yakeyi ya hau ya kama gabanshi, ina ma laifina da zan baki 1k idan haka yayi miki in bayar idan baki yadda ba naje wurin Umma.

Mai makon naga taji haushi sai kawai tayi dariya tare da cewa shege kenan, to kawo dubu d'in, d'an sosa kansa yayi sannan yace kai nama manta dubun zan siya ma iyalina biredi wallahi kuma machine ina baida mai amma bari dai in bada dari biyar, batayi zuciya ba tace to kawo dari biyar in, bata yayi suka shiga cikin d'akin.....

Tsoki nayi tare da ganin wallan matan aure, kuna gida kwance mazajenku suna nan wurin sakarkarin matan da basu kaiku komai ba, kuna can kuna girman kai da kunyar banza da sakarci aje a yayo cuta a cusa muku babu gari babu dalili.

Me Allah ya rageku dashi ? Me karuwa take dashi wanda Allah bai baki ba ? Naki ma yafi nasu daraja tunda ke ta hanyar bautar Allah zaki mik'ashi kuma Allah ya baki lada, amma matar malam bahaushe tanajin kanta yai mata girma ji takeyi idan ta nunawa mijinta tana buk'atarshi kamar zai rainata, wata ma macen idan bashi ya nemeta ba saidai ayi ta zama a haka, to ya nemiki jiya shekaran jiya kullum har "yar basirar dake gareshi ta kare, ko kuma sai yazo kwanciya dake ki tashi hankalinshi ki tado fitar da kila anyi sati ko wata da yin abu saboda ke kawai za'a kwanta dake, kin b'ata mishi rai yaji gaba d'aya abun ya fita a kanshi ko kuma yayi shi ba cikin natsuwa ba, da kanki kike jefa kanki halakar da babu mai iya fitar dake sai Allah , daga haka sai shedan ya fara doka masa gangar sa ya barki yaje ya nemi na banza, dan babu zuciyat wanda shed'an baya wasa da ita.

Idan kika had'u da muguwar mace sai ta rabaki da mijin fafur ki kasa gane kanshi, daga nan sai ki fara tattara kaya ke a dole kinyi yaji. Idan an tambayeki abinda ya had'aku ki fara cewa baya dawowa gida da wuri, idan kin kawo abinci baya ci, idan kinyi kwalliya baya yabawa, bayan duk kece babban da kika jawo ma kanki wannan damuwar........... Mudai je zuwa zamu gano masu laifin tsakanin matan da mazan su waye masu matsala......

Ina zaune a wurin har 12:30am bai fito ba, tou me akeyi haka har yanzu wanda ba'a gama shi ba ? Duk gorin da yayi mata na had'a mata k'addarar ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On KWARATA
avatar
muhd-habu

6 months ago

Reply

Nice

Please Login or Register in order to submit comment