Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

toshewa , na sake tashi wata kidahuma ta karfi da yaji.....

Gaba ɗaya saina manta maganar da nayi da Mamy nayi ² na tuno amma sai zuciyata tacemin bamuyi wata magana ba , duk yanda naso na tuno wallahi gaba ɗaya komai ya goce daga cikin kaina , amma ban manta na fitar da Babana waje ba kuma na riƙe nabar su Amisty kuma na tuna nayi waya da Dikko amma sauran maganganun sun ɓacemin ,

Ina ƙofar ɗaki tsaye Mamy ta miƙomin waya cewa ana kiranki , da sauri na ansa na ɗauka , An mata Dikko ya kirani a cikin wata irin murya yace meke damunki ne ? Ba komai na bashi ansa , yace karki min ƙarya meke damunki ne ? Tunani na fara yi , sassauta murya yayi yace me kikeyi yanzu ? Ba komai , kina yanayin tsayuwa ko zama ? Nace tsaye nake , An mata zaki iya faɗamin ko wane iri ne Dikko ? Shiru nayi ina tunani , yace tuna ² An matana , har yanzu kaina juyawa yakeyi , yace kin tuno ko wane iri ne Dikko ko ?

Wallahi Dikkon ma ya ɓacemin , An mata tsaya kiji kin tuna nine mukayi fada dake har kika mareni , kin tuna ? Eh na ganeka , amma me yasa kamin wannan bayanin ne ? Murmushi yayi tare da cewa kawai mafarki nayi wai kin manta dani shine nayi sauri na tashi a baccin na kiraki dan Allah kimin adalici karki manta dani kinji An mata , nace tou yawwa An matana..... Muah yai sumbata , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya na kashe wayar....

Ɗaki na shiga na ɗauko wayar budurwar Dikko ina zama kusa da Mamy nace ciro layin ciki ki saka a wayar nan.....






27/09/2019




*JAMILA MUSA....* 💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*



🅿 ------ 43


*_Ina miƙo saƙon ta'aziyya gareki HALIMATU SADIYYA MUHAMMAD { Leema } Allah ya bada haƙuri ya jiƙanta yasa ta huta mu kuma ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo..._*

*_Don Allah dan Annabin rahma kuyi haƙuri yadda labarin yazo min kenan haka nake rubuta shi_*


Me za'ayi da layin idan an ciroshi ne ? Shine tambayar da Mamy tayimin , kallo nabi Mamy dashi yayin da nima nake tambayarta wane irin layi kuma...? Mamy tace kina miƙomin waya ne kince na cire layin ciki na saka a wannan wayar shine nace meye ?

A ni ban wani faɗa ba ko dai kin fara ƙarya ne Mamy ? Nifa bana san ƙarya da kika ganni ƙatuwa dake bakyajin kunyar Allah bare kunya na kike nema kijamin sharri ko ? Tou tashi fitar min ɗaki , kamar sakara haka Mamy ta tsaya tana kallona , a hayagagance nace fita....... Da Allah malama , na faɗi maganar ina nuna mata hanyar fita , kallona Mamy tayi sosai tace ke Sultana anya kina da lissafi kuwa ?

A , a banda shi sai ke kika iya malamar lissafi , kila ma kece makarantar boko gaba ɗaga ko ? Murmushi Mamy tayi tabi Sultana da kallo cikin yanayin tausayawa , shi yasa ramuwa ga ramuwar abinda akayi maka babu kyau ka rama sharri ga sharri , Binna kuma idan har na faɗa mishi komai tabbas rayuwar yarinyar nan zata ƙare a gariri ne kawai , tun farko da bai anshi buduricin matar Bello a daren farko ba duk da haka bata faru da tilon "yar shi da ya ɗauki soyayyar duniya da ƙauna ya ɗora mata , dogon tunani Mamy ta tafi , tunanin abinda ya wuce shekaru da yawa shine wani sashe na daban yazo mata a kanta...

_Cikin farin ciki Binna ya shigo gidansu , dan dashi da Bello kowa baya ma kowa iyaka da shiga gidan kowa , kowa kai tsaye yake shiga..._

_Bello yana zaune tsakar gida Binna ya rungume shi cikin farin ciki da in ina yace kai banzan abokina an haifomin balarabiya yanzu na aihu a duniya duk na gaba hoton banza ne , kaga yarinyar kuwa ? Kyakkyawa da ita gata fara , burina akan ta zai sauka , itace Uwar masu gida dama nace sai an haifomin mai kyau zansa sunan mahaifiyata , zan gina mata rayuwa mai kyau dan ina so inyi alfahari da ita..._

_Murmushin yaƙe Bello yayi tare da cewa wane irin farin ciki kake ji a yau ɗin nan ? Binna yace baya musultuwa , Bello yace yanzu alal misali yarinyar nan sai kawai ayi mata fyaɗ...... Ai bai gama faɗa ba Binna yakai mishi wani irin duka harsai da Bello ya suma , duka ɗayan da Binna yayi masa yasashi tafiya duniyar suma , da gudu Mamy ta ɗauko ruwa ta yayyafawa Bello ya dawo , kallon Binna yayi tare da cewa alal misali fa kawai nace ! 👌🏻 Binna baiyi magana ba sai huci yakeyi kamar ɗan matashin zaki , jinjina kai Bello yayi tare da cewe hakan ya nunamin irin soyayyar da kake yi wa yarinyar nan , tsoki Binna yayi ya fice daga gidan..._

_Fitar Binna Bello yayi dariya tare da kallon Mamy yace wallahi tabon da Binna yamin yana nan bazai taɓa gogewa ba , shi a tunaninshi yaci banza , ya amshe min budurci mata a daren farko kuma yake tunanin zai gujeni , kyaleshi nayi kawai ni da kaina naje na bashi haƙuri duk da ni yayi ma laifi , na lallashe shi muka dawo muka koma ɗaya , tun kafin Binna yai aure yake bada labari akan zuwan Uwar masu gida , yau tazo kuma ta faɗo a dai² lokacin da Bello ke jiranta , ɗaukar fansa ba'a kan "ya "yanshi yake ba akan zuciyarshi yake wato Uwar masu gida mu tafi wasan daga yanzu Binna dani dakai wanda ya fasa shi ba ɗan iyayenshi bane ba..._

_Mamy tace haba dan Allah wai harsai yaushe zaku daina wannan ɗauke ²n fansar naku ne ? Ya kamata abu ya riƙa wucewa a wurinku don Allah , kayi haƙuri don Allah karka cutar da yarinyar ku daina jefe² da tsafe²n nan Bello , Bello yace na rantse da ubangiji daya aiko annabi da gaskiya sai yarinyar nan tayi karuwanci , shine abinda ya tsana tayi , kuma sai tayishi wallahi , namiji ɗaya ne zai buɗe mata ƙofa daga nan zata firgice ,kuma yaci buri akan sai ta zama malamar asibiti wallahi har a busa ƙaho ita da ilimin zamani , zan cuɗanya "yan uwa su halaka zan ɓata zumuncin su ,.... !_

Murmushi Mamy tayi tare da kallon Sultana tace tou zan wuce , kallonta nayi nace kai tun yanzu ? Haba dan Allah karki tafi ki zauna muyi magana , Mamy tace ba komai zan dawo zuwa asabar in Allah ya yadda , ansar wayata tayi ta sakamin numberta , tace kinga number na nan , idan kika tuna abinda zaki faɗamin to ki kirani kinji ko ? Jinjina kaina nayi alamar gasuwa , zan wuce ta sake faɗa , miƙewa nayi dan in mata rakiya...

Har ƙofar gida tayi sallama da Baba tahau motar ta tayi tafiyarta , wurin Baba naje na zauna dan Amisty bata nan kila tana gidan Asma'u , kallon Hafsa nayi dake muguwar matsoraciya ce kamar ni , nace da Allah ba mutane wuri zasuyi magana da Babansu , babu gaddama ta miƙe itama ta wuce gidan Asma'u...

Kusa da Babana na matsa sosai ina kallonshi nace Babana , yace Mamana ya akayi ne ? Runtse idanuwana nayi kwalwata tanamin wani irin zafi kamar zata fita daga cikin ƙoƙon kaina , hawaye ya cikamin idona cikin kuka na sake cewa Baba , riƙeni yayi tare da cewa wai miye ne Mamana ?

Buɗe idona nayi tare da cewa zaka iya misulta irin soyayyar da kakemin ? Murmushi yayi tare da kafeni da idanuwanshi , faɗamin Baba , hannunwashi ya buɗe kamar zai rumgumi wani abu , kallon yanda ya buɗe hannuwan nayi nace ɗan haka Babana ? Ƙara buɗewa yayi na sake cewa wannan kaɗai ? Murmushi ya sakeyi tare da buɗe ko wane hannu saida ya taɓa bango iyakar buɗewa sannan yace ina miki soyayyar da bata da farko bata da ƙarshe ,

Murmushi nayi tare da kamo hannayenshi na riƙe nace nima ina sanka , ina kuma tausawa rayuwata ranar da za'a waye gari babu ɗaya a cikin wa'annan masoya , idan na rasa ka zanyi kuka Babana harsai na haukace , idan kuma na rigaka mutuwa nasan kaima zaka zare kamar dai yadda zanyi idan baka duniyar nan ....

Murmushi yayi tare da cewa haba Mamana idan har na mutu karki sake kimin kuka kimin addu'a itace kawai zata tabbatarmin da irin soyayyar da kikemin , tou mudaina maganar mutuwar nan Babana...

Yace tou an daina , nace to wai Babana ina kasan Mamy ? Yace tsohuwar matar Bello ce , murmushi nayi tare da kallonshi nace kaima ka zagaya zawarci ba .... ? Na ƙarasa maganar ina nunashi ina dariya , dariya yayi shima cewa ita dai tayi zawarci na , tou mi yasa baka aureta ba ? Ba tsari na bace ba , ya bani amsa , murmushi nayi nace to wai kuma da gaske tana da aure ? Eh mana tana da aure hada yaranta amma bata aihu da Bello ba , tou Baba amma kuma naga kamar karuwa ce ! Yace Eh me yasa kika ce haka ? Shiru nayi dan dai babu dama na bashi labarin abinda ya faru tsakani na da ita akan iyayensu Amisty ,

Share maganar nayi da son nayi mishi maganar su Amisty amma sai kawai zufa taci gaba da kwararomin , kaina ya ci gaba da tafasa zuciyata tanamin wani irin zafi , lokaci guda kuma ɗimuwar tunani ta sake zuwa min , kallona Baba yai yace ya akayi kuma kinyi shiru ? Saboda hijabi ne jikina da yaga irin zufar da nakeyi...

Miƙewa nayi kawai na koma cikin gida , ina shiga Nana ta nufoni tana magana ko saurarenta banyi ba bare insan abinda take cewa , ina zuwa ɗaki na faɗa saman katifa na dafe kaina wai meke faruwa dani ne......?

Gaskiya Bello baka da mutunci kuma kaci amanar amintaka Allah bazai barka ba , Mamy ke faɗawa Bello magana dan daga gidansu Sultana wurinshi ta nufa kai tsaye , dariya Bello yayi yace umm dama nasan sai kin hallara ai mayya , wai me yasa kike san Binna da yawa haka ne ?

Murmushi Mamy tayi tace duk abinda yasa ma nake maitar tashi ka sani kuma maitarshi yanzu na fara , dariya yayi yace iska na wahar da mai kayan kara kuma wallahi kika sake dawomin da hannun agogo baya saina shafe babinki a saman doron ƙasa ... Dariya Mamy tayi sannan tace ina jiranka , tana faɗin haka taja motar ta tayi gaba...

Ranar juma'a da daddare bayan na gama sallar isha'e na fito da makullin mota ina sauri dan jirana Baba yakeyi sai kira yake kwalamin , ina fitowa Nana tace Alaji yazo nemanki bansan kina nan ba aka ce masa bakya nan , ko inda take ban kalla ba , muka fita daga gidan dani da Baba majalisarsu zan ajiye shi yacemin yanajin sauƙi naje na kaishi yaga abinda ake ciki ,

Ina ajiyeshi na dawo gida ban biya ko ina ba , ko parking ban gama gyarawa ba na hango wata mota a gabana kamar ana kokowa a ciki sakamakon haskasu da nayi da fitilar mota ta , da sauri na fita daga cikin mota ta na tun karesu ina zuwa na buɗe motar wai in rabasu , me zan gani.... Haka ?

Ƙanwata na gani ana iskanci da ita a cikin motar watanni biyar na bata da aihuwa , kallon saurayin nayi sannan na kalleta nace me kukeyi haka ne ? Babu damuwa ko fargaba a tare da ita sukaci gaba da abinda sukeyi , jiki a sanyaye na rufe musu ƙofar na koma motata na zauna ina jiran su gama ,

Hawaye naji ya cikamin ido nasan duk yadda akayi kila ta nemi wani abu ta rasa kuma ta tambayi Baba kawai zaice taje saurayinta ya bata , kwantar da kaina nayi saman sitiyarin mota ina goge hawaye , zata fito zan mata faɗa nace duk abinda take so ta faɗamin zan riƙa bata ,

Ai ban gama tunanin ba kaina ya juye , zuciyata tace karki wani yi mata nasiha kinga kin samu ƙarin fasinja daga nan zaki samu tayo miki yaƙi da "ya "yan gidan Baba ƙarami kawai kuci gaba da sha'aninku tunda kun rabu dasu Amisty , murmushi nayi tare da cewa tabbas haka za'ayi...

Dama ranar dana dawo naga kowa sai janye ɗanshi yakeyi karna gurɓatashi , zuciyata tacemin Eh kiyi ƙoƙari ki yaƙi duk wanda ya kyamaceki kinga idan kowa ya zama ɗan iska abun zai miki sauƙi wurin gori ,

Haka ne fa , ina ƙoƙarin fita a mota shima yayi parking in tashi daga bayana ya riƙa wasa da fitilar motarshi , ta kashe ta kunna , rufe mota ta nayi na nufi saman dakali inda zan jira fitowar "yar uwata ,

Ina zuwa dai² motar zan wuce ya buɗe murfin motar ƙamshin shi da sanyi a c suka lulluɓemin kaf ilahir ɓargon jikina , a kasalance na tsaya tare cewa ashe kaine ? Ey mana nine nazo gaishe shi , murmushi nayi na kunna fitilar wayata dan idanuwana sun ƙagara suga fuskar Dikko , haskashi nayi yaɗan shanye idanushi saboda hasken fitilar...

Sai ya ɗan rufesu ya buɗe su yayi haka yakai sau biyar sannan yace kinasan ki ganni ne ko ? Bara na kunna miki fitila ki ganni sosai , da sauri na kashe fitilar wayata na taɓe baki nace wa ni ? Tirr Allah ya sawaƙemin me zan kalla fuskarka , a dai² lokacin daya kunna fitilar motarshi yana cewa kinfi kowa sanin abinda kike kallo....

Murmushi yayi tare dayimin wani irin kallo yace ya kika gannin ne ? Ya ƙarasa maganar yana kashemin ido ɗaya , juya mishi baya nayi ina murmushi cikin jin kunya , gyara zamanshi yayi yana cewa bari in tafi zuwana kenan nace saina fara ganinki yakai hannunshi ya kashe fitilar daya kunna ,

Harararshi nayi tare da cewa kuma bakai kyau ba , dama banda abinki meya haɗa namiji da kyau ? Kece dai mai kyau kuma daga yanzu idan na kiraki saima na riƙa cewa ya kyau ? Zan tafi yayi maganar yana rufe motar , shiru nayi banyi magana ba dan bana san ya tafi kuma shima ya gane haka ,

Sauke gilashin motar yayi ya kwatar da kanshi saman murfin motar yana kallona ta sama yace ko kar in tafi ne ? A , a , a , a kawai kaje abunka , cikin sigar zaula yace kedai....... In tsaya ki ƙara gani na ko ? Matsawa nayi ina cewa wuce , murmushi yayi tare da cewa to na wuce sai Allah ya kaimu , nace amin , ɗage gilashin motarshi yayi ya fice da rubos tun daga ƙofar gidanmu har bakin titi , yana fita yaci taya ya ɓace abunshi , murmushi nayi komai na Dikko burgeni yakeyi ,

Cike da soyayyarshi na isa bakin dakali na zauna , ban daɗe da zama ba ta fito zata shige gida nace yaki Hamida , zuwa tayi tace gani , cikin tausayawa na kalleta dan itama babu uwarta a gidan , nace Hamida kin tambayi Baba wani abu bai baki ba ko ?

Shiru tayi tana kallon ƙasa , nace kimin magana kinyi shiru , yanayin ta ya nuna bata san ta faɗamin abinda ya faru dan sunsan bana san laifi Babana , tou tun yaushe kika fara wannan harkar ne ? Tace an daɗe gaskiya , nace yanzu har kinsan daɗin namiji kenan ko ? Daga gefenmu naji maganar Fa'iza na cewa wai na cikin masai ke cewa na waje ya taka kashi , nawa kike Sultana ? Kema kinsan daɗin namiji bare ita ko an faɗa miki ita dutse ce ba mutum ba ? Duk yadda kikeji itama irin abun takeji , ko nufin ki kiyi mata nasiha ? Keji Sultana da buƙulu zatama yarinya baƙin ciki ,

Ba tare dana kalleta ba nace ke kuma ina ruwanki da firarmu ? Da ruwana mana idan bata samo kuɗinta ba kece zaki riƙa cida ita ne ? Fita sabgar Fa'iza nayi nace nawa ya baki ne ? 150 zaro idanuwa nayi nace 150 sai kaci yaci yaɗi ? Fa'iza tace waike Sultana ina ruwanki da rayuwarta ne ? Ko ke wani ya shiga taki sabgar ne ? Banma Fa'iza magana ba naci gaba da cewa aiko kina karuwanci wahala gaskiya , janyeta Fa'iza tayi tana cewa kyaleta idan kika biye mata sai yinwa ta kamaki a gidan nan , tunda Allah ya baki kin samu na kalacin safe...

Suna gaf da shiga gida nace Hamida idan zaki iya huɗɗa dani kizo zan kaiki inda zaki samu kuɗi karki kuskura ki bari a koya miki toya awara a ƙofar gida hayaƙi ya kashe miki ido , kizo in haɗa da wani Alhaji ki biya buƙatarki kuma ga tulin kuɗi , Fa'iza tace naje na toya awarar dan uwarki , dama habaici ne nake mata kuma taji haushi tunda ta tanka , Fa'iza taci gaba da cewa kuma ita bata bin manyan Alhazawa ta bar miki kije kija , nace kece shedar inaja tunda kinga motar da nake hawa , danni ba sakara bace bana barin namiji ya hauni ya a banza ya sauka ni kuma in tashi a 150 ko doki namiji zai hau sai bada kuɗi da yawa bare kuma mace mai daraja....

Idan dai ka murza tou tabbas nima saina murje aljihunka fess , janta tayi sukayi shige gida , dariya nayi nima nabi bayansu , ina cewa 100k idan kin shirya ki sameni ɗakina...





29/09/2019





*JAMILA MUSA....*💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*



🅿 ------ 44


Ina ƙoƙarin shiga ɗaki Nana ta taho wurina a firgice jikinta yana kyarma tace Uwar room zo kiji wani abun tashin hankali , a firgice na kalleta nace kai miye haka har kin bani tsoro wallahi , magana ƙasa² tace zo muje ƙofar gida tayi maganar tana jan hannuna har muka fito waje...

Muna fita ta fara waige² irin yanda magulmata keyi idan zasuyi kilbibi , bayan ta tabbatar babu kowa tace da Amisty da Hafsa suna asibiti , a nutse nace meya samesu ne ? Ƙara matsowa kusa dani Nana tayi kamar zata koma cikin cikina tace gidan matar da suke zuwa...

Meya faru a gidan ? Nana tace mijinta yazo ya samesu suna maɗigo , { Lesbian } Asma'un tana ganinshi ta fara kuka ashe sun manta basu rufe ƙofa ba ya rutsasu duk sun haye mishi mata , Asma'u tace ya rufa mata asiri tana cewa ita wallahi ba halinta bane cutarta kawai akayi tana bashi haƙuri ,

Bai mata magana ba ya koma ya kulle ƙofa , bayan ya kullo ya dawo yace kiyi haƙuri my wife ba wani abu da zai faru sukadai yi miki haka ko ? Tace Eh yace tou koma gefe yanzun nan zan rama miki abinda sukayi miki , wayarshi ya ciro daga aljihu ya fara kiran abokanshi yana cewa suzo gidanshi yanzu akwai babban aiki kuma kowa ya shawo ta dubo ya taho dan yau a gidanshi za'ayi kwana ana wasan *DANBE...* shagon mada da shagon gwaggo zasu buga babbar lamba...

Bayan ya gama waya ya hunce tare da jawo ƙarfar Hafsa yace kece kika sha mata nan ko ? Ya ƙarasa maganar tare da taɓa inda yaga tana ma matarshi , cikin kuka Hafsa tace dan Allah kayi haƙuri tsautsayi ne , mijin Asma'u yace ai nima tsautsauyin zan nuna miki , Hafsa zata sake magana ya haɗe bakinshi da nata , wata irin ƙara Asma'u tayi ba tare daya kalleta ba yace Swry madam rama miki zanyi....

Cikin kuka Asma'u tace dan Allah kar kayi , har yanzu bai kalleta ba yace tou ni banza ne inzo in samu wasu na ƙwaƙulemin mata in barsu su tafi a haka ai wallahi ko waccensu saina bata tukwuici , kowa a cikinsu sai taji nauhi na , ihu Asma'u takeyi tana ba mijinta haƙuri baya ji kuma baya gani , kusa dashi ta matsa ta riƙoshi wani irin mari yayi mata wanda yasa tayi zaman dirshen dole a katsa ,

Haka ya farke Hafsa tas kuma bashi ne farko ba shima akan hanyar wani yabi ya wuce , bayan ya gama ya jawo Amisty itama ya kaita , yana gamawa da Amisty ya sake jawo Hafsa saidai ya zagaya ko waccen su so 3 sannan abokanshi suka shigo suma sukaji yanda kowa keji , bayan sun gama yace itama Asma'u suyi mata , ke a gidan dai haka aka kwana bala'e ana zagaye ² har gari ya waye , da safe kuma ya bawa Asma'u saki 3 gaba ɗaya , kai naga cikakkin *KWARATA...*

Wato a gabanki akayi komai kenan ko ? Na tambayi Nana , tace a , a ina ni ayi a gabana ? Ita Amisty tamin waya na taro musu mai napep , dani dasu Zalifa mukaje dan har muka isa asibiti Hafsa bata farko ba , itama Asma'u taji jiki sosai dake Amisty jar wuya ce ita bata wani damu ba ,

Shiru nayi ina kallon Nana zuwa wani lokaci nace mata miye wasan *DANBE... ?* Nana tace wani sabon iskanci ne maza ke zuwa su saka kuɗi a jera musu layin mata , ko wane namiji zaibi mace goma wanda yakai ba tare daya gajiya ba kuma ya gamsar da ko wace a cikinsu tou dama kuɗi ake zubawa , idan ko wace ta samu biyan buƙata kuma namiji
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On KWARATA
avatar
muhd-habu

6 months ago

Reply

Nice

Please Login or Register in order to submit comment