Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ba , kauda kanshi yayi sannan yace ya kukayi dashi ne ? Yake tambayar mutumin , Eh babu damuwa amma sai an koma hutu ,

Dikko yace har yaushe ne hutun zai ƙare ? Mutumin yace saura sati biyar , tsoki Dikko yayi yace ko na barta yanzu ? Cikin girmamawa yace ai matan gidan dukansu basa nan idan dai sun dawo zan kiraka insha Allah ,

Ba komai sai ka kira ɗin , inji Dikko godiya mutumin yayi sosai cewa yaga saƙo yafa gode sannan ya matsa , Dikko yaja mota muka dawo gida ,

A ƙofar gida yayi parking sannan yace ki kiyayi dawowa ta iskanci da rashin kunya cike da kai amma babu ilimi ni bana san zama wuri ɗaya da jahili kina ɗawainiya da fankon kai a haka kike tunanin zaki hareni shakaru biyu masu zuwa ? Dan dai zan fita katsina a daren nan amma wallahi dana zaune dake har tsawon sati biyar saina koya miki hankali bakauya dake kina fitowa ko hijabi babu ke ba ɗiyar kafirawa ba , zama saman dakali yawon banza fira da maza rashin kunya da tara "yan daba duk ranar dana waiwayoki jikinki zai baki labari fice ki ban wuri kafin in fara miki rashin mutunci , ya ƙarasa maganar tare da buɗemin motar na fice...

Fita nayi daga cikin motar jiki a sanyaye dan duk duniya babu abinda na tsana irin inji an danganta ni da kalmar jahila , kuma ba ƙarya bane jahilarce ni , fita katsina kuma da zaiyi yanzu zaije jigawa saboda an fara shagalin bikinshi ne naji ana ta faɗa ,

Banda tsoki babu abinda Dikko keyi da ana canja hali daya canjawa Sultana hali , duk duniya babu abinda baya so irin mutumin da baya ganewa , wallahi idan har Allah yasa ya dawo lafiya sai an nemi An mata an rasa idan zata shekara dubu saita ta wadata da ilimi , baida inda zai ajiyeta daya tafi da ita , kuma yana so kusanci mai girma da shaƙuwa ta shiga tsakaninshi da ita ,

Rayuwarshi da ita ya fara kuma yana so ya kulle da ita , farin ciki da duk wani jin daɗin shi yana hannun Sultana bai taɓa tunani zaiji soyayyarta ko kaɗan ba a zuciyarshi , daya san wannan ranar zata zo da baiyi mata abinda yayi mata a baya ba ,

Bai ɗauki mace komai ba amma ƙaramar yarinya ta hana mishi sukuni , da girmanshi waishi soyayya zata zo ta dama , kamarshi soyayya zata hana bacci abubuwa suyi ta masa yawo a zuciya , idan An mata tayi fushi ko kuka duk yanaji wannan bala'e kamar asiri.....

A ƙofar gida na samu Nana har yanzu bata daina kuka ba da takardar sakinta a hannu , wurinta na nufa dan jajanta ma......

Dikko kuwa yana komawa gida ya ɗauki abinda zai ɗauka suka kama hanyar jigawa......




12/09/2019



Jamila Musa....
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*



🅿 ------ 31

*_Gaisuwa ta musamman gareki "yar uwa ta gari fatan alkairi da addu'ar Allah ya ƙara zaman lafiya da ƙauna mai girma tsakaninki da mai gidan ki , RABI MUSA ..._*


A damuwance na zauna kusa da Nana dan ina tattare da ɓacin rai da damuwa , ansar takaddar nayi da cewa saki nawa akayi miki ne ? Cikin kuka Nana tace saki ɗaya , tou ina shi mijin naki yake ? Cikin shashshekar kuka tace yanzu ya shiga cikin gida...

Tsoki nayi nace tou me yayi zafi haka har ya sakeki ? Ƙara fashewa da kuka Nana tayi saida tasha kukanta har ta godewa Allah nidai ban bata haƙuri ba kuma bance tayi shiru ba saida ta gaji ta rufe bakinta da kanta na kuma sake tambayarta abinda ya haɗa har akayi mata saki !

Aure zaiyi ! Ba tare dana kalli Nana ba nace tou ke ina ruwanki da auren banzarshi da zaiyi ? Saida Nana ta ƙara goge hawaye sannan tace ba auren ya dameni ba matar da zai aura itace ciwona , wace alaƙace tsakaninki da ita da har bakyaso ta zama abokiyar zamanki ne ?

Rumtse ido Nana tayi tare da ƙara rurewa da kuka tace *A ` I* zai aura fa , ɗan gajeren tsoki nayi tare da miƙewa nace A ` in banza A ` in wofi ! Da saboda A ` i har kika kashe aurenki ? Kiyi haƙuri Nana gaskiya baki da wayau kuma lokacin dana so na farkar dake daga baccin asarar da kikayi dake dasu A ` i kuka haɗu kuka riƙa cimin mutunci , kin watsa mutuncin aurenki kin lalata rayuwarki kika biye musu suka koya miki maɗigo ,{ Lesbian } ta koya miki kika koya kuma kika iya , gashi yanzu zata aure miki mijin kinga zaki tashi a tutar babu , ba abokiyar iskanci babu mijin aure..

Idan kuma zawarcin kika fuskanta ga "yan mata tsalala sabbin zubi suna yawo a gari suma basu samu sun shige ba , idan maza suna kallon lutsa²n zawarawa wankakki "yan gayu masu ƙamshi da gogewar zaman takewar aure , Nana gaki muguwar ƙaza babu sallah babu salati babu biyayyar aure ki faɗamin wane sakaran namiji zai kalleki bare yayi tunanin jajibar ki ya kaiki gidanshi ,

Ke kanki baki wanke kanki ba bare namiji yayi tunanin idan ya aureki zaki wanke mishi gidanshi , mazan yanzu sunfi san kwankwashshin mata , masu gogewa wanda zasu gyara masu gida ba su kashe musu gidaje ba , dan mazan yanzu suna kashe kuɗaɗe su gina gida na fita idon duniya , tou yau dake da A ` i wa gari ya waya Nana ...? Kin san zawarci kuwa ? Kai lallai kin tafka babban kuskure aradu...

Juyawa nayi zan shige gida Nana ta riƙoni cikin kuka tace ki taimaki rayuwata wallahi ko naje gidanmu korata zasuyi Baba baya san *Zawarci* shi yasa ban tafi ba , tou idan kuma na bashi haƙuri ya mayar dake kika sake jawo matsala fa ? Bazan jawo ba Mother kuma zan ɗauki duk shawarar da kika bani bazan sake tsallakewa ba ,

Tou zan baki shawara idan har kika ɗauka ba A ` i ba ko uwar A ` i mijinki bazai sake kallo ba bare ya sha'awar aure tunda sun zama maciya amana , Nana tace ngode sosai....,

Muje cikin gidan , lokacin da muka shiga har mijin Nana ya gama tattara kayanshi ya fito zai bar gidan ,

Gabanshi nasha tare da cewa Audu ina so zamuyi magana dakai don Allah , kallona yayi ƙasa da sama yace idan har maganar Nana zaki min bana so , ko Nana autar matace duniya na haƙura da ita , cikin sigar lallashi nace don girman Allah kayi haƙuri ka saurareni , ka bani dama nayi magana dakai na minti biyar kaɗai dan Allah badan halina ba ,

Tsoki yayi ya koma da baya ya jingina da bango sai haɗe rai yakeyi shi mai gida , murmushi nayi sannan na matsa kusa dashi nace Audu meya haɗaka da Nana ka saketa ne ? Banza yayi ya ƙaleni , ban damu da shirunshi ba naci gaba da cewa tou nidai don girman Allah ina neman alfarma kuma wannan alfarmar ba kowa zaka ma ita ba saini , na roƙeka da girman Allahn daya halicceka ya baka aron numfashi da lafiya , ya baka ji ya baka gani yayi maka hankali , idan har kaji daɗin wannan ni'imomi da ubangiji yai maka kayi haƙuri ka mayar da Nana ...

Cikin damuwa Audu yace Sultana Nana bata da mutunci kwata² ina ce duk abinda Nana kemin a gaban idonki , Nana ta rainani itace dakamin tsawa fita ba izini na magana da mazan waje duk wanda nace bana so tanayin tarayya dashi sai ta kafe tayi , rabon da inyi kwanciyar aure da Nana tun muna tsohon gida , na rabata da A ` i taƙi ta rabu da ita , A ` i tana so na kuma tana tausayamin sai in aurota dan ta kwantarmin da hankali na , kuma nace zan auri A ` i sai tacemin bata yadda ba ? Bayan tana san A ` i ta kasa rabuwa da ita tou idan na auro ta ta zama abokiyar zamanta ai duk wata ƙauna ya kare ko ?

Duk cikin ɓacin rai yakeyin maganar har wata maganar ma bata fita , haƙuri na bashi saida na tabbatar ya sauka sannan nace tou aurenka da A ` i fa babu fashi kayi aurenka bama hanaka , amma kayi haƙuri ka mayar da Nana dan soyayyar da kake ma manzan rahma S. A. W ,

Jinjina kai yayi yace in zauna da ita da baƙin halin nata da ƙazantar da duk iskancin da takemin a haka ? Karka damu mayar da ita sauran gyaran duk nawa ne idan bata gyara ba ni da kaina zan ƙaro maka mata sadaki da lefe duk ni zan bayar kuma zan baka jari , tou shikenan na mayar da ita...

Godiya nayi mishi sannan nasa Nana ta anshi kayanshi ta mayar cikin ɗaki , nayi musu saida safe , na wuce ɗakina , ina shiga Karima ta shigo tana cewa wallahi banso kika sa aka maida ita ba , banza nayi bance da ita komai ba , ta ƙari kilbibinta naji babu ansa ta fice....

A ɓangaren su Amisty kuwa ina fita Momyn Hafsa ta cire wayar wuta taci gaba da dukansu babu ji babu gani , tana dukansu tana cewa wato na hanaki wannan iskancin bakya bari ko ? Tou wallahi yau saina kashe ki , dama tunda nabar gidan nan na kasa samun natsuwa zuciyata tana saƙamin tunda bana nan nan zaki kawo "yan iska su tarar min a gida , Amisty ganin hankalin Mom ya fita jikinta tana dukan Hafsa har ta daina motsi yasa ta biyo ta bayanta ta fice da gudun tashin hankali ,

A bakin get ta faɗawa mai gadi Momy ta kashe Hafsa , da gudu ya nufi ɗakin Hafsa , ita kuma ta fice daga gidan , saman Hafsa ya samu Momy tana dukanta tana yaginta duk tayi mata kaca² jini saibin jikinta yakeyi , da sauri ya ciro wayarshi ya kira Yayan Hafsa ya faɗa mishi duk abinda ake ciki dan babu yanda za,ayi ya ɗauke Momy , babu ɓata lokaci ya iso , dakel ya ɓanɓare Momy sannan mai gadi ya kama mishi Hafsa suka tafi asibiti da ita....

A asibiti kuwa likitoci sun tabbatar cewa Hafsa bata mutu ba , dan haka suka shiga bata taimakon gaggawa dan ceto rayuwarta....

Amisty kuwa a gidan Asma'u ta yada zango , tana zuwa wanka tayi Asma'u ta kawo mata abinci taci sannan suka ɗora iskancinsu daga inda suka tsaya !

Tunda safe almajirai suka fara kawo kayan "yan gidanmu a cikin baro , sahu ɗaya yaran sukayi nace idan sun koma suce a samu mota a zubo kayan zan bada kuɗin ,

Nana na kira ɗakina nayi mata nasiha , cewa ki rufawa kanki asiri ki gyara halayenki , ki zama mai tsabta ki fita daga harkar zaman majalisa kija mijinki jikinki , ki zama mai biyayya da haƙuri a rayuwarki , karki kuskura mijinki ya sake neman haƙƙinshi a wurinki ki hanashi , ko inuwar Audu kika gani ki bashi natsuwa ,

Tsafta a rayuwar aure itace jigo , kamar yanda baki shiga makaranta dole saida uniform , bazai fa yuwu ba ki gama duk wata fangila taki kisha yawo cikin rana ga kaurin zufa ga warin rana gana haƙi , zaninki na zarnin fitsarin yara ga ƙarnin tunbiɗi babu wanka babu wanke jiki ba sake kaya a haka zakije kice namiji ya kwanta dake ? Wace natsuwa zai samu ? Taya zai samun natsuwar da zai biya buƙatarshi....?

To idan zaki gyara ki gyara , ki nemi ruwa da turare sabulun wanka da man shafawa ki fara wanka , ki zama mai biyayyar aure kima mijinki sannu da zuwa idan ya dawo ki masa rakiya idan zai fita tare da addu'ar Allah ya bashi halal inshi , ki gode masa akan abinda ya kawo miki ki kuma yi haƙuri idan bai kawo miki ba , ba kullum ake nema a samu ba , dole wata rana a samu wata rana kuma a rasa , kin dai ga yanda rayuwar take tafiya dan haka ki tashi ki miƙe da gaske ki janye tunanin mijinki daga kan A ` i idan kuwa ba haka ba ta shigo to aradu sai tayi waje dake...

Jiki a sanyaye Nana tayi godiya tare da cewa bara in tashi nace da dai kin kyauta ki kuma zuƙe jikinki daga sabgar matan banza , insha Allah Mother ngode sosai , yayi kyau na faɗa tare da cewa zan fita saina dawo , addu'ar a dawo lafiya tamin , ni kuma na irga kuɗi 20K na bata idan an kawo kaya ta sallami masu motar , in an rage canji ta ajiyemin , insha Allah ta amsa min sannan ta fita , nima na shirya na fice !

Anguwar su Amisty na nufa , kafin inkai ƙofar gidansu nayi parking jikin wani shago , amma ina hangen gidansu Amisty , wayata na kallo da take kuka , lambar Amisty ce keta tsalle saman screen in wayata , kamar bazan ɗauka ba na ɗauka dan inje me zatace ! Ina ɗauka ta fara ,

Tauraruwa mai wutsiya ganinki ba alkairi ba , ciwon tsakar dare mai hana bacci , ance kinje anguwarmu bayan kin sacemin kuɗi me kuma kikaje yini ? Murmushi nayi tare da gyara zamana sannan nace tsauni da ƙaya da tsawon zango maibi da ƙafa sai ya daure , yaro bai ɗaukar yaro dan kansu matsa sai sun faɗi , guguwar tsakar dare ga tsoro ga ban al'ajabi , kura bata cin damisa saidai taci zaki , ki saurari kaidina zuwa gobe kamar yanzu , kashe wayata nayi dan ganin mahaifin Amisty ya fito ,

Yana wucewa da motarshi nima nabi bayanshi da tawa motar , a hankali yake tuƙi nima a hankali nake binsa saf da ƙafa har ya isa wurin aikinshi , inda yayi parking nima a wurin nayi yana fitowa nima na fita murmushi ɗauke da fuska na nufi wurinshi ,

Da sallama na isa wurinshi tare da cewa sannu , yawwa ya ansa yana kallona , murmushi nayi tare da cewa naga kamar baka ganeni ba ma ko ? Cikin muryar dattijantaka yace Eh ban gane ba gaskiya , ajiyar zuciya na sauke tare da cewa me yasa baka gane mutane haka ? Murmushi yayi sannan yace to bani sani mana , nace tou sakamin numberka mayi waya dai zuwa dare , babu musu ya ansa ya gwagwaɗamin lambar shi nayi ajiyeta da Lamba shidda , bayan na gama ajiyewa na kirashi yaga tawa sannan nayi masa sallama na wuce ,

Daga nan ban zame ko ina ba sai Office in Babansu Hafsa , suna da dokoki masu tsaurin gaske dan haka aka hanani shiga , nayi ² aka hanani , lambarshi na tambaya itama dai ban samu ba , dan haka na haƙura na nufi gidansu Hafsa ,

A wurin mai gadi na samu number bayan na bashi cin hancin 5K , ina ansa na nufi gida , cikin farin ciki nayi sallama dan har "yan gidanmu sun dawo dukansu , amma Inna bata dawo ba , Babana kuma saida dare zaizo ,

Cikin kulawa nake gaishesu amma kowa sai ya ansa min a wani dusasar , haka nan dai na haƙura na wuce ɗaki na , saida nayo wanka na fito Nana ta shigo ta bani cikon kuɗina tace ta bayar da kuɗin ta sallamesu , godiya nayi mata sannan tace bara ta sharemin ɗakina , nace babu damuwa ta share...

Satin "yan gidanmu ɗaya da dawowa amma Babana baizo ba kuma Inna bata dawo ba itama , Baban Amisty da Baban Hafsa munayin waya dasu , kowa ya damu yaushe zamu haɗu dan wayar babu abinda ke cikinta banda zallar sakin layi , har yanzu badai mu haɗu ba kuma sati biyar ya ragemin a lissafin satikan da Dikko yake lissafi....

Mijin Zalifa ma ya matso lamba mu haɗu amma yanzu bashi ne gabana ba , Alaji wato Abbu Afsar shi kuma yana min hidima sosai wacce ta wuce hankali ma , maganar wani abu har yanzu babu wani abu daya shiga tsakaninmu yadai cemin yana so muyi aure na zama abokiyar rayuwarshi niko ba auren ne gabana ba ,

Zalifa kuma tazo min da labarin mutuwar ƙawar Amisty wacce muka haɗu da ita a station Fadeela wacce tayi cikin shege da aurenta kuma itace ta kawomin Zalifa gidana , ta mutu sanadiyar rataye kanta da tayi bayan tasha gwagwar maya wurin zubar da ciki bai zubu ba , kuma sunje wurin bokaye anyi asiri anyi tsafin amma cikin bai fita ba , kuma anyi ƙoƙarin ɓatar da hankalin mijin dan ya yadda cikinsa ne shima ba'a samu nasara ba , dan haka ta kashe kanta , ...

A ɓangaren ango D K yau akayi walima amarya ta tare a gidan angonta Dikko dake G R A { karkara road } , an gina gida na faɗi a faɗin birnin garin katsina , an kashe kuɗi kuma anyi hidima ta kece raini , gida ya tsaru iyakar tsaruwa , iyayen amarya suma sun kashe kuɗi wurin ƙayata ɗakunan amarya da palukanta tunda kuɗi da kuɗi ne suka haɗu abindai sai wanda ya gani , duk inda ka nufa a gari maganar auren Dikko akeyi da gidanshi , gaskiya Dikko mai sa'a ne...

Cikin farin ciki ango ya shiga ɗakinshi danshi babu wani abokin daya rakoshi cewa yayi baya so , bayan yayi wanka ya saka jallabi ya nufi ɗakin amarya , itama tayi wanka ta shirya cikin shiga mai kyau da burgewa , a ɗakin amarya yayi alwalla suka gabatar da nafila raka'a biyu dan miƙa godiya ga mai duka ,

Bayan sun gama sukayi addu'o'in neman zaman lafiya da wanzuwar arziƙi mai ɗorewa tare da addu'ar Allah ya basu zuri'a masu albarka ya kuma kauda sharri da fitina a zaman aurensu , bayan sun gama ya dafa kanta yayi mata addu'a ,

Bayan ya gama ya koma palo dan ɗaukoma amarya ɗan abinda ya shigo mata dashi kamar dai yanda kowa ya sani anayi , sama ² Sadiyya taɗan lallasa tace ta ƙoshi , shine ya tattara sauran yaje ya zubarwa da karnuka , bayan ya dawo ya wanke hannunshi da bakinshi ɗakinshi ya koma ya sake ciwo ɗama dan shima ya nuna tashi jarumtar a daren farkonshi da matarshi...

Itama amarya fitar ango ta ƙara gyarawa ta cuscusa na cusawa ta shafa na shafawa ta kukƙurɓa na ƙurɓawa ta ɗaga katifa ta jera layunta , ango na dawowa itace ta taroshi dan a halin yanzu sha'awar Dikko ta rufe soyayyar da take mishi ,

Cike da bariki taja Dikko suka sauka saman gado , daga nan labari ya fara canja salo , kowa dai gwanine wurin ganin ya nuna shi wani shege ne , Dikko kuwa a zuciyarshi yake mamakin Sadiyya dan yasan duk macen da bata goge ba a harkar maza tana tsoron namiji bare kuma a daren farkon ta ,

Yayin da Sadiya kejin daɗin salon Dikko ta yaba mishi ko a haka aka tsaya tasan Dikko namijin duniya ne gaskiya Dikko ya karanci mace yasan duk wasu salo na burge da saka nishaɗi , ya iya sirrika masu tsayawa a zuciya , duk mazan da tayi mu'amula dasu tasan Dikko zakara ne a cikinsu ,

Soyayya tai nisa ango ya tunkari gidan sarauta , amma me zai samu ? Labari yasha banban domin dai wani ya rigashi hayewa saman kujerar mulki , la'ilaha illa anta sub'hanaka innee kuntu minazzalimeena , lahaula wala kquwwata illa billahi aliyyil azeem , Dikko ya faɗa tare ci gaba da cewa Allah na tuba , Allah ka yafemin , kukan makirci Sadiyya ta fara wani irin kallon tsana Dikko yabita dashi yayin da yake kallonta kamar an mata a daren daya kacaccala mata rayuwa ,

Yaya DK don Allah ka rufamin asiri yanda Allah ya rufa maka , ka rufe wannan sirrin don girman Allah karka tona min asiri.... Wani irin tashin hankali yazo a zuciyar Dikko ya tsaya yayi ² yayi control in zuciyarshi ya kasa yana ƙoƙarin sauka daga saman Sadiyya matsalarshi tazo , wani iri ihu yayi ya tafi gaba ɗayanshi kafin kace mi ? Tuni lumfashin shi ya tsaya cak..... Wannan itace babbar matsalar dake damunshi da ranshi ya ɓaci sai kawai numfashin shi ya ɗauke....

Cikin ruɗewa ta ɗauki wayarta ta fara kiran Momyn Dikko , babu ɓata lokaci ta ɗauka Sadiyya ta karanta mata halin da Dikko yake ciki , jikin Momy na ƙyarma ta miƙe "ya "yanta suka riƙeta saboda karta faɗi ta samu matsala , kuka ta farayi tana Allah ka tausawa rayuwata idan har Dikko ya samu matsala mijina ya shiga tashin hankali ubangiji ka dafamin a dukkan lamurarra na , meya faɗawa Dikko rai a wannan dare ....?

Kai ku sakeni ta faɗi maganar tare da kwacewa ta shiga ɗakinta ta nemo wani magani da ake mishi amfani dashi idan lalurarshi tazo , ko Dadyn bata faɗamawa ba driver ya ɗaukota tayo gidan Dikko dan tasan idan har Dady yaji to idan dai Dikkon bai mutu ba kilashi yana iya mutuwa...

Sadiya kuwa tana gama waya da Momy ta sakama Dikko gajeren wando dakel , sannan ta lulluɓeshi da bargo ,

Babu ɓata lokaci Momy ta iso , Sadiyya ta buɗe mata ƙofa kuma itace tayi mata jagora har zuwa ciki , a ɗakin Sadiyya ta samu ɗanta kwance cikin tausayawa tace meya haɗaku ne ? Sadiyya cikin daburcewa tace ba komai wallahi , Momy tace bazai yuwuwu ba me kikai masa ne ? Fashewa da kuka Sadiyya tayi tana cewa wallahi ba komai Momy , Hmm shine abinda Momy ta faɗa tare da matsawa kusa da Dikko ta buɗe bakinshi ta zuba mishi magani , kamar mai ciwon aljannu haka ya tashi kamar babu abinda ya taɓa faruwa dashi , kallon Momy yayi tare da cewa lafiya kika zo ? Ya ƙarasa maganar yana ma Sadiyya kallon tuhuma ,

Cikin so
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On KWARATA
avatar
muhd-habu

6 months ago

Reply

Nice

Please Login or Register in order to submit comment