Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

biki ko suna...

A lokacin da Mero ta samu cikin farko Sahura kuwa tace ina wuta ta jefata , nan ballin asiri ya fara tashi jefe² tahana mahaifiyarmu zaman lafiya , da ta samu ciki sai ya ɓare , ciwon yau daban na gobe daban , abun dai babu daɗi ,

Su kuwa malam ba abinda ya damesu da harkar da iyalinsu ke ciki burinsu kawai sudai a kawo musu , kullum matan malam basu da aiki sai wanke alluna , ana haka dai har Allah yasa Mero ta samu cikina , tunda Sahura ta lura Mero tana da ciki taci gaba da wurgago subbancinta , haba ina harta isa ? Allah yace saina zo asiri baya tasiri a wannan lokaci sai hukuncin Allah...

Har Mero ta haifeni cikin wahala take da musibar rayuwa , tunda na sako ƙafa duniya dama azababbena aka haifoni , da rana zansha baccina har in gode Allah , amma da zaran an kira sallah magrib na fara kwarara ihu har garin Allah ya waye babu wanda ya isa ya runtsa idonshi kona second a gidan nan saboda kuka na , a haka akayi suna Allah ya cidani da Aliyu , ina wannan masifafen kuka da an kira asubahi kuma zanyi bacci , malam kuwa saida ya rubuce yace abani insha maganin kuka duk ranar da aka bani rubutu kukana sai yafi na jiya , har malam ya haƙura ya daina rubutu ana bani...

Haka Mero ta haƙura taci gaba da rainona duk wanda ya ganta yasan tana tattare da damuwa , tabi ta soye tayi baƙiƙƙirin saboda tsabar rashin kwanciyar hankali , dana fara zama kuwa idan ta zaunar dani zan fashe da wani irin ihu mai firgici wanda dole saita ɗaukeni ta goyani , nadai zama fitinanne ta ko wane sashi ,

Dana fara rai rafe kuma ɓarna harta ƙeta , duk abinda yake na Mero bana ɓatawa amma daga ba ita ba duk abinda na gani saina tadashi aiki , Sahura tace iskanci kesa nakeyi ɓarnar tunda nasan abun uwata bana ɓatawa , da nayi mata ɓarna sai tayita dukana maimakon inyi kuka sai inyi ta dariya...

Abun fa ya fara tayar da kowa hankali , har aka yayeni a nono , iskancina kuma sai abinda yayi gaba , tun ina ɗan firiri na , na iya tsakalo fitina saidai idan ban fita ba , masu kawo ƙara kuwa haka zasu jero layi , wasu a biyasu wasu kuma a basu haƙuri...

Shekarata 3 Mero ta sake samun ciki , amma har ta haifeshi Allah bai sanar da Sahura ba , tashin hankali wanda tayi ba kaɗan ba , amma bata da yanda zatayi dan duk wanda yazo baya komawa sai idan Allah yaso...

Ranar suna data zagayo aka sakawa jariri suna Muhammad , wanda ake kiranshi da ƙarami , ku kuma kuna ce masa Baba ƙarami , haka dai akaci gaba da cakwakiyar rayuwa , har Allah ya kawo wata mace matar wani attajiri malam yayi mata aiki , bayan buƙata ta biya shine ta siyawa malam gida anan cikin garin birnin katsina , a anguwar ƙofan marusa , daga nan muka tattaro mukayo birni !

Shekarar mu biyu da dawowa birni Mero ta ansa kiran mahaliccinta babu jinya haka kuma babu ciwon kai bare na hannu , nasha kuka kamar zan mutu na rashin mahaifiyata , wanda Sahura ko a kwalar rigarta ,

Bayan anyi kwana 3 da rasuwar Mero Sahura ta samu malam ta kitsifa masa ita bata iya zama dani ga iskanci ga rashin kunya ta taɓani ace dan uwata bata raye take azabatar dani , saidai ya raba mana wurin zama ,

Ba tare da nazarin komai ko tunani ba , yace in bar mishi gidanshi dani da ƙarami , haƙuri na bawa malam akan ya bari saiya kamani da laifi , amma fur ya ƙeƙashe idanuwanshi saina bar mishi gida , ina ƙoƙarin barin ɗakin malam Sahura tace sai inzo in tafi da ɗan uwana dan so take gaba ɗaya fitina ta fitar masu daga gida , a lokacin shakarar ƙaramin 2 da wattanni , ni kuma ina da shekara biyar da "yan watanni , haka malam yayi mana korar karnuka , ina kuka na ɗauki ƙarami muka fita daga gidan ,

Ina ɗauke da ƙarami na shiga cikin gari , duk wanda ya ganni ɗauke dashi zaice na mayar da yaron nan bana iya ɗaukarshi , ko sauraron mutane banayi bare na basu ansa , tafiya nakeyi har aka kira magrib , ni kuma a lokacin na isa wata anguwa ita Gambarawa....

Bakin wani shago na zauna na sauke ƙarami dake ta zabgaga kukan gajiya da yunwa , bayan na zaunar dashi naje na ɗauko buta da wani ya gama alwallah ya ajiye na bashi sauran ruwan daya rage yasha , bayan yasha na matsa wurin mai shagon da yake ƙoƙarin buɗewa ya dawo daga sallah nace Baba da Allah ka taimakamin da sadaƙa zan siyawa yaro abinci yaci ,

Cikin hargowa yace ai sai ka buɗe ka ɗauka mishi ɗan barauniya , dama irinku ne masu sacewa mutane abu idan basa nan , wata irin kwanya yaimin tsakiyar kaina harsai da nayi tunanin kaina ya huje , dariya nayi tare ce masa ka nunamin inda zan ɗauka , kuɗi ya fiddo daga cikin aljihunshi kwaci ² shege ɓarawon banza , kallonshi nayi sannan na duma ma kuɗin wawa , kaf kuɗin na kwace na ruga na cicciɓi karami nabi lunguna ba tare da nasan gari ba ,

Biyoni yayi da gudu yana a tara ɓarowa , ƙarami kuma sai kuka yakeyi saboda ya wahala , ganin jama'a na ketowa daga hanyoyi da dama yasa na samu wani zauren gida na sake na rufe bakin ƙarami sautin kukanshi ya daina fita...

Dube ²n su sukayi basu sameni ba saboda haka suka hakura kowa ya kama gabanshi , saida na tabbatar babu kowa sannan na fito naje na samawa ƙarami abinci yaci muka bar anguwar Gambarawa a daren na dawo Qerau da zama....

Haka rayuwa taci gaba da tafiya , ni na saka kaina makarantar allo kuma na samu gidan aiki , gidan aikin suka sakani makarantar boko , haka dai na haɗa abu goma da ishirin , ga karatun allo ga boko ga gidan aiki ga rainon ƙarami ,

A daddafe dai nayi ta dafa rayuwar kuma ban sake zuwa wurin malam ba kuma daga Qerau zuwa Ƙofar marusa babu wani nisa ,

Shima ƙarami daya isa sakawa makaranta boko gidan aiki na suka sakashi , kuma tare dashi mukaci gaba da aikin gidan , daga baya ma suka bamu wurin zama a cikin gidan ,

Na gama secondry sch Bello ya shigo cikin rayuwata , gidan ƙawar matar da muke zaune gidanta itace take aikena gidan ƙawarta gidan kuma a maƙotan gidansu Bello ina zuwa idan aka aikeni nan ya ganni ya liƙemin , yana zuwa gidan da muke zaune yana yini wani lokaci ma har kwana yakeyi , ya shigeni sosai abota mai girma ,

Makarantar gaba da secondry tare da Bello muka fara nidai nayi karatu kuma na fito da sakamo mai kyau yayin da Bello ya faɗa harkar mata , a lokacin kuma ƙarami yana secondry sch aji biyar , bayan na gama degree aka fara neman min aiki , yayin da ni kuma nake neman ƙara faɗaɗa ilimin nawa...

Har wannan lokaci banje wurin malam ba , kuma malam bai nemeni ba ni kuma naƙi nemansa dan dama ni nasan inda yake , saida naci gaba da karatu na , na faɗa harkar wasan caca daga nan duk lissafi ya jagulemin , dan duk wannan kangarar da nayi a baya tana da dalilinta kuma a gaba zaki ji ta , dan bayan na baro gida naɗan samu natsuwa , amma shigowar Bello rayuwata yasa na ida ƙwacewa......







16/09/2019




Jamila Musa.....💅🏻
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_



*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_



*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_


_Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻

*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_

&

*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*



🅿 ------ 34


*_Fatan na samu kowa lafiya ? Kuyi haƙuri na jina shiru kwana biyu banajin daɗi ne amma na samu sauƙi alhamdulillah ngode da addu'o'in ku a gareni masoyana , gaskiya naga soyayya kuma ngode sosai , na warware zamu ɗaura daga inda muka tsaya , fatan alkairi a gareku masoyana kuyi farin ciki..._*


Shiru Babana yayi ya zubamin idanuwa yana min kallo mai tattare da bayaso ya faɗamin , nima ƙureshi nayi da idanuwa amma bance masa komai ba , shiru yayi yana nazari zuwa can ya ɗago ya kalleni , nima kallonshi nake har yanzu zuciyata dai ta bani kila zai ɓoyemin wani abu ne...

Gyara zama yayi yaci gaba da cewa , zuwan Bello rayuwata yazo min da al'ajabi mai girma , wanda ya kasance bana iya ƙetare maganarsa , idan yacemin inyi zanyi idan yace na bari zan bari ya rabani da ko wane aboki shi ɗaya ne abokina ,

Bello shi ɗayane iyayenshi suka aifa , kuma attajirai ne na gaske , soyayyar duniya sun ɗorawa Bello sun sangartashi yadda ya kamata , saidai ya kashe waccan mota ya ɗauka waccan , ba mazaunin gida bane ba , domin duk kayanshi na sakawa yana cikin motarshi , tafiya yake jira kawai yayi gaba , gashi cikakken ɓarawo domin duk ƙarfin arziƙi mahaifinshi saida ya duƙar dashi ƙasa.

Tun wancan lokacin Bello ya mallaki bantan baƙin biri , daya ɗaurashi duk inda ya shiga idan dai akwai kuɗi hayaƙi ne zai riƙa tashi , da yaga yahaƙi yasan kuɗi ne a wurin zai buɗe kawai ya kwashe yayi gaba ,

Bello mashayi ne , ɓarawo ne , ɗan caca ne sannan tantirin mazinaci ne , idan har ya zuƙawa mace masifa tou duk irin kamun kanta da natsuwarta sai Bello ya keta mata mutunci , baya neman zawara baya neman matar aure sai "yan yara ƙasa da shekarunki , shekaruna kenan ni Sultana , kuma daya biya buƙatarsa ya gama da ita wata zai nema...

Da nayima Bello magana sai yacemin sa'ar caca malaminshi ya bashi , gabana Bello ke zuƙewa kuma gabana yake kwalbewa , ma'ana a gabana yake shawuwa yasha sigarinshi yasha giya da sauran kayan shaye ²n shi...

Ni kuma a lokacin na koma makaranta naci gaba da karatu na , dan zurfafa ilimina dan na fahimci rayuwar idan baka da ilimin zamani mai zurfi tou ka zamo an maido wuta an ɗauke...

Banda isashshen lokaci bansan abinda gida yake ciki ba idan na tafi makaranta , gidan da ake riƙemu akwai ɗiyar mai gidan itama yarinya ce ƙarama lokacin tana js3 ashe itama Bello ya ɗora mata alƙalamin kudirinshi akanta wanda ya fake da soyayya ne ni kuma duk ban sani ba ,

Wallahi babu abinda na sani tunda bana nan , ƙarami ma baya zama gida shima makaranta , Bello idan yazo bama nan zai buɗe ɗaki kawai ya shiga babu mai hanashi tunda abokina ne ,

Wata rana kwatsam ina makaranta "yan sanda suka zo suka tafi dani , tambayarsu na farayi lafiya ? Babu mai lokacina , haka suka sarkafeni da sarƙa suka tafi dani ofishinsu...

Suna zuwa office sukaci gaba da dukana babu ji babu gani , sunma hanani nayi magana bare naji laifina ? Saida suka min lullusar fitar hayacci sannan aka wurgani cikin cell aka rufeni ,

Saida na dawo hayyacina naga Bello gefena yana kyalkyalamin dariya , ƙarami na gefe sai kuka yakeyi , goge hawaye nayi tare da cewa me mukayi haka abu babu mutunci ? Dariya Bello yaci gaba dayi yana shan lolypop inshi...

Ƙarami na kalla nace meye wai ? Cikin kuka yace wai rafe naji dai suna cewa , cikin ɓacin rai nace rafe me ? Miye rafe kuma ? Ƙarami yace nima ban sani ba kawai dai haka naji suna cewa , tsoki nayi zuwa can nace waye yayi rafe ɗin ? Cikin kuka yace mu duka naji suna cewa , har yanzu Bello dariya yakeyi yana shan lolypop , raina naji ya ɓaci na tashi nayi kan Bello naci gaba da dukanshi babu ji babu gani ina cewa me mukayi ne ...?

Dariya Bello yakeyi yana cewa wallahi hauka yasa suka kawoku , ni kaɗai nayi kuma yarinyar da kanta tacemin tana so in rantsar da ita , itama ta zama cikakkiyar mace kamar kowa , tou dan nayi abinda takeso sai azo a rufemu , ai godemin ma ya kamata suyi , shaƙe Bello nayi sosai tare da cewa itama ka zuƙe.......?

Bushewa yayi da dariya to me ake jira da abun kwaɗayi.... ? Yau taji abinda uwarta keji , da sauri na rumtse idanuwana dan naji kaushin maganar Bello a raina , murmushi yayi tare da cewa kaji babu daɗi ko ? Tou ai itama uwar ta tuni na bata alƙalamin daraja kuma yanzu nan zata zo ta fitar damu dan nace idan har ta bari muka kwana sirrinta a buɗe yake dan ina da babbar sheda ,

Kallon Bello nayi idona cike da hawaye nace hajiya ma .....? Murmushi Bello yayi yace harda tukwuici take bani ma , kuka naci gaba dayi dan banji daɗin abun ba , daga haka nayi shiru na samu wuri na natsu muna jiran tsammani...

Hajiya itace tayi cuku² dan Alhaji shine yasa aka kamo Bello kuma Bellon yace tare mukayi kowa saida ya zagaya sau biyu domin ya buɗe mutuntakar a yarinyar yadda ya kamata !

Saida Hajiya ta saki kuɗi sosai tare da ƙaryata zance mijinta cewa ba Bello ne yayi wannan aika ² ba wasu daban ne sukayi kuma suka gudu haka nan aka ɗaura alhakin tuhuma akansu yara marayu basuji suka gani ba sai Allah ya saka musu...

Saida aka kai ruwa rana sannan muka fito , Bello yace mena faɗa muku nace muku zamu fito babu ɓata lokaci , haushin sa kawai nakeji domin naji ciwon wulaƙantawar da yayiwa yarinyar da nake ma kallon ƙanwata , kuma naji ciwon keta mutunci mahaifiyata Hajiya da ta ɗaukeni matsayin ɗa , kuma nima daga wannan lokaci na ɗaura ɗamarar saina masa yaji idan da daɗi !

Alhaji kuwa korar kare yayi mana daga gidanshi bayan yayi maganganu masu zafi da ɓatanci akanmu , kayanmu muka kwashe daga gidan Bello ya bamu mazauni a gidansu...

Duk lokacin dana kalli Bello sai naji kamar in haɗiye zuciya in mutu saboda tsabar baƙin cikin abinda yayiwa mutane masu mutunci , koda zai fita da daddare binsa nayi domin na fara harin rayuwarsa ,

Gidan caca muka nufa dashi , shine zuwana na farko dan kallon wasan da Bello zai buga , bayan yayi "yan al'adunshi ya binne ya ɗaura , hankalina ya tashi ganin tulin kuɗi da aka zuba , cikin ƙanƙanin lokaci aka fara gabatar da wasa , an ɗauki lokaci mai tsayi ana gwabzawa bayan wasan yayi zafi Bello ya lashe wannan makudan kuɗaɗe ,

Bayan ya kwashe kuɗinshi aka fara shagali , kwalaben giya suka fara wali da dai duk wani mai ɓatar da hankali , ina cikin ɓacin rai dan haka bansha ba , amma Bello yace idan nasha zan rage damuwa , dan haka na ansa nasha cikin ƙanƙanin lokaci na nemi damuwa na rasa !

Uwar masu gida labarin dai bazai buɗu duka ba , dan wasu labaran bai kamata na faɗa miki ba , mu tsaya haka nan , domin nima na zama atsabibin matsafi dan ko magana nayi bata faɗuwa ƙasa na koma kamar wani mai kambun baka saboda tsabar neman asiri irin nawa !

Daga nan na shiga wasan caca nima , naci gaba da harkar mata , shaye² da duk wani abunda ya zama zunubi , nayi nisa banajin kira , sheɗan yaci gaba da busamin sarewar halaka na shi , ga Bello bashi da ƙanne ,

Bayan ƙarami ya gama secondry sch yacemin bazai ci gaba da karatu ba , nayi juyin duniya yacemin daga haka ya tsaya , to ni na bashi gidan zama wanda a caca na ciwoshi , kuma ni na bashi kuɗi yaci gaba da kasuwanci , kuma duk matan daya aura nine na kashe kuɗi nayi masa hidima ,

Ƙarami bai daɗe da aure ba Malam ya saki wasan , wato ya mutu , bayan yasha doguwar jinya an girbi abinda aka shuka domin aikin tsubbu ɓata ce , ya lalata maka zuri'arka ga dakon zunubi , wasu an ɓatar an raba an haɗa dan dole an talauta wasu an raba aure an raba uba da ɗa anyi an gama dai duk an tafi an iske Allah....

Bayan ƙarami yayi aure aka barni daga ni sai Bello mukaci gaba da gurza rayuwa , har Allah yasa ya samu yarinyar da yake mugun so , kyakkyawar yarinya mai hankali da biyayya Bello ya mutu akan yarinyar nan , sukaci gaba da soyayya , na tambayeshi ko itama dai kamar sauran ? Yacemin a , a wannan ta aurece gaskiya , naji daɗi sukaci gaba da zuba soyayya sun shaƙu sosai tarayyarsu abun burgewa ,

Basu wani daɗe suna soyayya ba sukayi aure , lumshe ido Babana yayi sannan yaci gaba da cewa ango na shirin shiga ya angonce Binna ya anshi budurcin matar Bello , Bello yayi kuka saida yayi jinya gashi kuma yana mata san da baya iya rabuwa da ita , uhum tafasha azaba yarinyar nan , bayan Bello ya samu sauƙi akaci gaba da abota ,

Nima yana nan zai rama ashe , to yanda kasar suri bata cuwuwa ga bakin duk wani bil'adama haka Uwar masu gida tafi ƙarfin Bello dan yasan idan yace akanki zai ɗauki fansa tabbas nima zan rama akan "yar sa , shi yasa ya matsamin na sakaki a caca , hawaye ya cikawa Babana ido ,

Yaci gaba da cewa yasan duk duniya ya cire soyayyar Allah da manzan sa babu wanda nake so a faɗin duniyar nan bayan ke , tabbas yasan zanci caca shine suka juyarmin da hankali ta hanyar bani asiri cikin abunsha , bayan sunyi galaba a kaina suka rasa abunyi , shawarar abokinmu ya nema shine yace yasan wani da yasan Dikko , yace idan aka kaiki a wurin bazan iya ja da hukuma ba , hankalina ya kwanta da naji wurinshi kike nasan babu abinda zai faru ,

Ashe shima sun shirya mishi gadar zare , ɗan masu aikin gidansu shine yayi jagoranci , cikin kuka Babana yace aka ciwa "ya ta mutunci , haka na gudu na ɓuya kamar ƙolo na boye saboda kunyarki , duk da nayi haƙuri ban ɗauki fansa akan abinda Bello yayi ba duk da haka bai faru ba ,

Amma dana biyewa sharrin zuciya gani takaini ta baro ni , murmushi nayi nace ba komai Babana na yafe maka , kuma wannan abun ka ƙaddara babu abinda ya faru , !

Amma me yasa ka bar iyalinka cikin wahala ? Tsoki yayi sannan yace nima haka aka barni a saman titi bansan mai kyau ba bansan mara kyau ba , banda mai nunamin kyakkyawa ko mummuna , babu wanda ya kula dani shi yasa nima na saki kowa yayi rayuwarshi ,

Baba Allah fa yana kallonka , ka karanta kuma kaji ka gani kuma kasan abinda Allah yace akan iyali , girgiza kai yayi tare da cewa kar muyi haka dake Mamana , banasan maganar su , tou Babana amma me yasa baka aiki ne ? Wannan ra'ayina ne , caca na zaɓa kuma zanci gaba bazan daina caca ba sai numfashina ya ƙare , cike da damuwa nace ko kana da dalili ne ? Uwar masu gida mubar maganar nan ,

Tou Babana ina Sahura ? Kuma me yasa kayi kangara kana ƙarami ? Murmushi Baba yayi tare da cewa wannan kangara wani aiki ne malam yayi akan wani yaro dan ya lalace , matar Babanshi tazo ayi mata aiki ne , sai abun ya dawo kaina ,

Matar ta dawo ta faɗawa malam buƙata bata biya ba , can wurin binci kenshi ya gano inda aiki ya sauka kuma ya warware komai , idan dai kayi mugunta tou ka daina saurin rufe ƙofa domin dawowa takeyi , Sahura kuma tana can gidanta bana dai zuwa gaskiya...

Tou ita Inna baza ta dawo ba ? Manta da ita gani nan na isheki taje can tayi ta zuciyarta , kallon agogon hannunshi yayi ya miƙe yana cewa bani makullin motarki , miƙa mishi nayi ya fita yana mita ba'a kawo mishi kuɗin wayoyinshi ba , gaskiya Babana bansan irin halinshi ba , dandai yaƙi yadda ya faɗamin komai duk haka ya bani labari nidai a duƙunƙune....

A ƙofar gida ya anshi kuɗin wayoyinshi yayi gaba , "yan gida kuma cewa sukeyi da wani yake da motar nan sai Baba ya siyar da ita amma da yake ta Sultana ce komai daren daɗewa zai dawo mata da abinta , saboda kar yamin faɗa raina ya baci shi yasa baiji a ina na samu mota ko yamin faɗa ina hawa mota ba ,

Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya , Babana yake amfani da mota ta , Bello ya fita harkata nima na fita harkashi , d c o babu ruwana dashi , Hafsa da Amisty banda labarinsu , su A ` i ma bana shiga sabgarsu , mijin Zalifa da Zalifar duk na daina jinsu , Alaji kaɗai yake zuwa fira danshi ya matsa aurena zaiyi...

Haka nan na tsira yin bedday babu gaira babu dalili , nayi i v nasa akaci gaba da rabawa , har a gidan radio nasa Alaji yakai sanarwa , manyan baƙi a wurin Baban Amisty mai yanka cake kuma Baban Hafsa , wurin taron kuma wani zuƙeƙen gidan Baban Hafsa , nayi gayya duk wani lungu da saƙo na zaƙulo manya ² karuwai nakai musu gayyata wanda duk ba ƙawaye na bane nasu Amisty ne ,

Al'amarin wannan taro ya karkato da hankalin jama'ar gari a kaina dan ban ibo abun da wasa ba , kowa da abinda yake faɗa akai na yayin da wasu mutane suka cewa taron iskanci ne ba wani taron birthday ba ,

Hafsa kuwa Amisty tayi mata waya ta faɗa mata cewa zanyi birthday amma taga venue gidan shaƙatawar Dady inta ne , yaushe ne ake taron Hafsa ta tambaya ? Amisty tace mata ranar laraba , Hafsa tace tou Allah ya kaimu zata ga yanda zan wulaƙanta ta ....

Nima da Nana ta bani labari dariya nayi tare da cewa Nana nima zan wulaƙanta ta yayin da taga Dad inta ya yanko cake ya rungumeni yana bani a baki na ,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On KWARATA
avatar
muhd-habu

6 months ago

Reply

Nice

Please Login or Register in order to submit comment