Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

☆“☆ª☆_☾`☆•`☆´-`☆´-
❉ *.¸¸.*♠*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ *.¸¸.*⚫.¸¸.*♠
*YA FARU AKAN KAI NA!!!*.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ ¸¸.*⚫¸*♠ *.¸¸.*⚫*.¸¸*❆ `☆´-`☆´-
Fasahar Rahma Muh'md Rufa'i Nalele
Wattpad @rahamanalele

*HASKE WRITE'S ASSOCIATION*💡

Zaki iya karanta littafi nawa idan ke matar Aure ce, idanko ke ba matar Aure bace bana buqatar ki karanta min novels..
Daga Marubuciyar...
1 *BIRNIN MASOYAH*
2 *Y'AR ƘAUYE KO Y'AR BIRNI*
3 *SADEEQ*
4 *AMAKIRCI NAH*
5 *HAYATUDDEN*
6 *MASIFAR SOOH*
7 *SAMARIN BANAH*
8 *LIKITAN ZUCHIYAH*
9 *HALIN WASU MUTANAN*
Ayanzu kuma ina a YA FARU AKAN KAI NAH...🙋🏼
Visit to Like my Page https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=745670445877015&id=675818692862191

” بسم الله الرحمن الرحيم
☆page 01☆


Kasancewar yana yin yana yin damuna, hakan yasa kasuwar cika maqel da mutane, kallo d'aya zakama kowa awajen kasan Allah Allah yake yayi yasai duk abin dazai siya yabar kasuwar, musamman idan kayi duba da yanda hadari ya hararo wanda shima kallo d'aya zaka mai kasan k'iris yake jira ya sauko da ruwa..

HAIRANAH tana d'aya daga cikin mutanan dake siye siye acikin kasuwar, sai siyan abubuwa take sauri-sauri gudu-gudu tana Allah Allah tagama siyan komai akan lokaci kan saukowan ruwan, dan tasan idan tagama siyan komai koda ruwan yasauko bata da matsala Dan tana d'auke da y'ar lemanta

Lokacin data gama siye siye hakan yayi daidai da shigowar HEESHAM cikin kasuwa.....
Kyakkyawan saurayi ne wanda ya had'u tako ta'ina, ya had'u irin sosai d'innan, fari ne tas irin wannan farin me tafe da cikakkiyar lafiya, me kyau ne na qarshe irin tsaftataccen kyau d'in nan me tsayawa arai, shekarunsa bazasu wacce Ashirin da huɗu ba, yana da jiki irin wannan jikin da ake kira da samun irinka sai an tona, ma'ana shidai baza'a kirasa dame jiki ba, sannan baza'a saka shi a sawun y'amushashshu ba sirara, yana dai tsaka tsaka, tsayinsa yayi daidai dana samari irin SAMARIN NANAH, kallo d'aya me hankali zaimai yasan yana da wayo sosai me tafe da karfin basira tare da wadatar ilimi zallah, dama tunaninka zai baka koda ace rainan nan qasar ne ba shakka yana samun kulawa sosai arayuwarsa, musamman idan kayi duba da tarin hutun dake tare da fatarsa..

Waige waige yake yi yana duba direbansu, daga kawai bara ya sai abu saiya shanyasu a mota kamar wasu kayan wanki...

Shaaaaa ruwan sama ya b'arke kamar da bakin kwarya, nan take mutane kowa ya fara shigewa shagunan mutanen kasuwan dan gudun kada ruwan yadakesu..
Arayuwar HAIRANAH tana San taga ana ruwa tana tafiya acikinsa da lema akanta, Dan haka nan take ta bud'e lemarta cikin murmushi dan haka kawai taji wani dad'i aranta, tasan hakan baya rasa nasaba da yanda tagama siyayyarta.

Saidai me😳 iska ce me qarfi ta figi lemar tata tayi gaba can da nisa zuwa wajen HEESHAM dake kici kicin gudu dan kar ruwan ya jiqasa shaqaf, ai nan take yaga lema gabansa, ya fara waigen daga inda tafito, shi dai anasa iya waigen baiga me ita ba, Dan haka ya d'auka da murna, baibar wajen ba dan yasan akwai me lemar anan kusa dashi..
Aiko kamar ya sani Dan karyowar kwanan HAIRANAH kenan ta hangi lemarta a hannunsa ya tare ruwan abinsa tare da kallan shagunan mutane yana Allah Allah yaga direban nasu ya jasa sutafi, dan yasan Shehu bashi da sauri akan komai na rayuwa.....

HAIRANAH takai hannunta daniyar kwace lemarta saidai hannun nata na tab'a na HEESHAM tayi saurin janyewa, sakamakwan wani shock da yayi ram da hannayen nasu, nan take HEESHAM ya zuba mata ido, ZUCiYARSA na bugawa kamar yanda tata take bugawa, tunda suke basu tab'a jin irin wannan shock haka ajikinsu dan sun tab'a wani ba... Wannan wata alamace tada'akwai wata alaƙa me girma a tsakaninsu..

HEESHAM ya galla mata harara yace, "malama ya zakizo da hannunki me kama da wayar lantarki ki tab'ani.
HAIRANAH itama ta gallamai harara tace, "ban gane ba, kana nufin haka kawai zanzo na kama hannunka dan rashin tarbiya, kawai nazo kwatar lemata ce arashin sani hannuna ya gogi naka, maza kabani lemata in qara gaba dan ina da abin yi.....
"Da gaske... HEESHAM ya katseta da fad'in hakan tare da wurga mata wani shegen kallo, kana yaci gaba da cewa, lemarki ko lemata, ta ina wannan lemar tazama taki, kinga malama qara gaba tunkan na yanke miki.
Jin hakan yasa ran HAIRANAH b'aci, nan take tasa hannu ta riqe lemarta qam tana cewa, " wallahi saika bani lemata tunda ba taka bace, wallahi saika bani kayata, takai qarshen zancen kamar zatayi kuka, dama ita bata raina abin kuka, tana matuƙar san lemarta over, dan agidansu ba wanda yake tab'a mata abinta dan kowa ya tab'a sai sunyi rikici, dan takanas ta kano abokin yayanta SABIR dayaje kwatono ya siyo mata dan sanin qaunar da takema lema...
HEESHAM yana ganin hakan ya kyalkyale da dariya, dan shi a rayuwarsa ba abin da yake so kamar yaga manya suna kuka🤣 koya saka mutum magana abin yana masa dad'i matuƙa azuciya, dan haka shima qara qanqame lemar yayi yace, "bazan baki lemar nan ba, dan ina tafiya naganta tazo gareni, kinga ko Allah ne ya turomin ita, dan haka saidai kiyi kukanki ki share hawayenki dan baki kam bazan baki ba..
HAIRANAH tagane yaran idansa qir yake, tayi imani idan batayi da gaske ba tafiyan mata da lema zaiyi, dan haka ajiye cefananta tayi a gefe tana jan lemar HEESHAM naja, nan fad'a ya kaure, jama'ar wajen sai kallansu suke cikin mamaki, masu magana nayi masu kallo nayi, gashi ruwa ake sosai yanda ruwan yake sauka a qasa haka ruwan yake sauna akansu, amma dan bala'i Sam d'aya yaqi barba d'aya wannan lema.

Shidai HEESHAM dama neman rikici da fad'a aikinsa ne, dan haka yayunsa suke fama dashi a gida🤣..
HAIRANAH bata San halinsa bane, dan haka dataga da gaske bazai bata lemarta ba dan kowa yayi masa magana cewa yake lemarsa ce qarya take masa ba tata bace, dan haka sai kawai tafashe mai da kuka wiwi..
HEESHAM mai zaiyi imba dariya ba, ya dinga kyakyatawa, mutan wajen suka dinga mamakinsa gashi yaqi sakin lemar, wani tsoho daga cikin wani shago yace, "haba kai ko yaro, maizai hana bazaka bar mata lemar ba, tunda ta kafe lemarta ce, kuma kaji wasu sunce tatace, maizai hana ka bar mata aiko takan ce ka bar mata tunda kaga ita mace ce..
HEESHAM yaci gaba da dariyarsa yana d'agama tsowan hannu alamar yaji, Sannan yaci gaba da kallan bakinta da yanda take kukun, wallahi tunda yake tsokanar yayunsa bai tab'a jin nishad'i irin na yau ba, shiya d'auka ƴan uwansa ne kawai zasu mai kuka idan ya tsokane su, amma itama kalleta sai wani kuka take mai, kallanta yake dakyau yana auna shekarunta, ba shakka sa'arsace, dan bazata girme masa ba, Saidai su zama sa'annin juna....😌

HAIRANAH ko kuka take tsakaninta da Allah, can dayaji d'an tausayinta saiya tsaida dariyar da yakeyi tare da d'an sakar mata lemar amma ba dukka ba, idansu cikin na juna yace da ita, "Zan sakar miki lemar dan ganin damana, amma saikin gaya min sunanki..
HAIRANAH ta gallamai harara cikin takaicinsa tace, "Bazan gaya ba, murmushin daya qara masa kyau yayi tare da d'an qanqame lemar cikin zaro ido yace, "Tunda bazaki fad'a ba, bara namiki me gabaki d'aya, ya kai qarshen zancen dasan funcike lemar DAGA hannunta...
Ganin hakan da HAIRANAH tayi, aiba shiri tayi saurin cewa "Sunana HAIRANAH🤣..
Murmushin dai ya qarayi, tare da sakar mata lemar yana cewa, "Sunanki dadad'i HAIRANAH, yana fad'in hakan ya juya yabar wajen tabishi da kallan harara, kana ta d'auki cefananta da kallan mutanan wajen tajuya itama tabi tata hanyar...

HEESHAM da murmushi akan fuskarsa ya bud'e motarsu ya shiga, Shehu direba ya kallesa yace dawowata kenan nake tambayar yallab'al INA kake yace min ka shiga ciki nemana.
Kallan Yayansa AHMAD HEESHAM yayi Wanda yake karanta jarida kana ya maida kallan nasa kan Shehu direban Wanda ayanzu yaja motar ya Bashi amsa da, "ina cikin nemanka na had'u da wata Yarinya futunanniya...
Da sauri yayansa AHMAD yace, "Dama akwai wanda zai kaika futuna HEESHAM...
Cikin jin kunyar yayan nasa HEESHAM ya sunkuyar da kansa bai qara cewa komai ba, Shehu direba murmushi kawai yayi, dan shima yasan futunar HEESHAM daqer asamu Wanda yafishi..




HAIRANAH ko tafiya take tana tuna HEESHAM, ita tunda take bata tab'a ganin mutum irinsa ba, ya ita da lemarta ya wani ce tasace, murmushi tayi kawai, irin yana da futuna matuƙa.
Saidai mezai faru😳.. Tana karyo kwanar layinsu taci karo da wani mutum.... Nan goshinsu ya haɗu yabada wani sauti guf, dajin zafi sosai mutumin yaja baya yana me dafe goshin nasa da cewa "sorry, Sannan ya durƙusa yabi cefanan nata dan kwashe mata kasancewar tunda sukaci karo suka sub'uce ahannunta suka zube.
Itama hannunta dafe da goshin nata ta durƙusa tana tayasa kwashewa.
Nan suka kalli junansu ai atare zuciyarsu tabuga kamar yanda kukasan ana buga ganga.
Nan HAIRANAH taja wani numfashi tare da saurin tashi ganin ya gama kwashe mata cefanan...
Ahankali cikin nutsuwa ya tashi shima da kallanta ya miƙa mata cefanan yana me qarema kayan jikinta kallo tare murmushi yace, "kiyi hakuri ƙanwata, bansan kin tawo ba daban shigo da sauri ba..
Jiki a sanyaye HAIRANAH ta karb'i cefanan nata zuciyarta bata dena bugawa ba, batace mishi komai ba taratsa ta gefensa ta wuccesa tana me juyowa tana kallansa, ahaka ahaka har ta isa gidansu.. Namma kafin ta shiga sanda ta juyo ta kallesa dakyau, yana nan tsaye inda ta barsa yana kallanta, sanda tagama ƙaremai kallo tsaf kana ta juya ta shige gidan nasu..

Da mamakinta shiko ya ɗauke idansa daga ƙofar gidan nasu, tare daci gaba da kallan Layin nasu daga sama har ƙasa, kana dai gani kasan wani abu yake nema, candai ya tsaida idan nasa akan wani gida, ganin da yayi kamar ana ƙoƙarin fitowa daga gidan ne yasashi saurin buɗe wata black motarsa me masifar kyau ya shige cikinta...
Yana kallo wasu maza biyu ne suka fitto daga cikin gidan daga ciki kuma yaga an kulle gidan, har mazan suka tafi idansa nakan gidan, haka a ƙalla ya b'ata sama da awa uku yana cikin motar tasa hankalinsa nakan wannan gida amma baiga wani ya qara fitowa ba, dan dole badan yaso ba haka ya kunna motar tasa yabar Layin...

HAIRANAH ko tana shiga gidan nasu taga Yayarta NUWAIRA tana karatun littafin hausa, bayan ta ajiye cefanan zama tayi a kusa da NUWAIRA ɗin kasancewar zuwa Lokacin anɗauke ruwan saman..
Haka ta zabga uban tagumi tana mamakin zuciyarta, gabanta na tsananta faɗuwa yayin da hankakinta yayi mummunan tashi, sakamakwan gane karatun zuciyar tata da tayi...
Nan take hawaye ya zubo mata cikin tashin hankali tadafe ƙirjinta jin wani yanayi daya farayi mata.
Ta fahimci rikicinta da HEESHAM da sukayi a kasuwa *WASA NE*
Cin karo da tayi da wannan mutumi rashin sani ne,
Kallansa da tsayawa da tayi jin kalamansa na bata haƙarin da yayi *GANGANCI NE*
Dan gashi yana san zame mata masifa a rayuwa..
Zuciyarta ba abin da ayanzu take hasko mata sai fuskarsa da murmushinsa, haka kawai taji tana sanshi tana ƙaunarsa tana san qara ganin fuskarsa tana san ta qara jin muryarsa..
Hawaye ya qara zubo mata...
Daidai lokacin NUWAIRA tadafa kafaɗarta batare data kalleta ba bare tasan Awane yanayi take, cikin sanyayyiyar muryarta tace da ita, "Hmmm, labarin nan yana ban takaici, gaskiya marubuciyar nan banza ce, waifa yarinyar wuccewa kawai tazoyi, sai ta haɗu da saurayin shikenan tafara sanshi da ƙaunarsa, yanzu gashi tazo gida wai tarasa sukuninta tana san zama kamar wata zararriya, kiji ƙarya fah..
Gaskiya marubutan nan suna raina mana hankali, nifa bazan tab'a yarda mace tana fad'awa soyayya me zafi haka ba, Sannan a lissafi irin nawa rashin hankali ne mace me mutunci da daraja taje tacema namiji tana sanshi.. Tana kawowa nan azancenta, taja tsaki daci gaba da cewa, ba wata Soyayyar dazan bari tayi tasiri cikin zuciyata har na barta ta haifarmin da wani tunani bare tasani shiga cikin wani hali halin dazai kaina ga fad'awa tashin hankali..

Kigafa wannan, daga kawai ganin mutum akan hanya sai tawani faɗa cikin Soyayyarsa, saboda tsabagen shashanci da toshewar basira da kuma ɗorama kai damuwa......

Hawayene ya qara zuboba HAIRANAH, cikin wani hali tace, "Aunty Ba kawai bane, ba shashanci bane, ba kuma toshewar basira bane, ba ɗorama kai damuwa, wallahi ƙaddarace, wallahi *YA FARU AKAN KAINA* yanzu yanzun nan..😭

Yanzu naganshi, Yanzu na sanshi, yanzu yayi min magana, kuma yanzu na fara sanshi, kuma san nashin qara shigata yake, bin jinina yake, ina jin shigarsa kamar yanda kika san yanda mutum yake shan ruwa, kamar yanda kike fad'a yanzu, Nima yana san hanali sukuni, wallahi nidai ina sanshi.....😭😭😭

Ahankali NUWAIRA ta sauke hannunta daga kafaɗarta, tare da zuba mata ido cikin mamakinta tace, "HAIRANAH? 😨 me kike cewa ne, kina magana nefa akan kin fad'a Soyayyar wani mutumin dabaki sanshi ba yanzu..
Cikin nuna mata tabbaci HAIRANAH ta goge hawayenta da bayan hannunta tace, "kwarai Aunty, ina sanshi kuma saina Auresa, zanje nayi sallah yanzu naroki Allah kan lamarin, idan nasamu nutsuwar zuciyata, sai naje na gaya masa tunkan mama tadawo taganni cikin wannan halin, kuma dan Allah wannan yazama magana tace nidake, bana san mama tasani dan Allah, HAIRANAH na faɗin hakan tatashi da barin tsakar gidan tayi cikin falansu zuwa shashinsu dan aiwatar da abin datace....

NUWAIRA tabita da kallo cikin matuƙar razana, dan hankalinta baqamin tashi yayi ba, dan haka itama tashi tayi tabi bayanta dan ta magance matsalar yanzu yanzu tunkan abin yayi nisa...

Aiko NUWAIRAN na zuwa bedroom nasun taga HAIRANAN har tashiga toilet, zama tayi gefan gado tana jiran fitowarta cikin mamakinta.
Aiko HAIRANAH na fitowa NUWAIRA tatashi tasha gabanta tana cewa, "Amma baki da hankali, ban tab'a sanin ke wawiya bace sai yau, ya za'ayi daga ganin mutum kiji kina sanshi har kina maganar zakije ki gaya masa kina sanshi, anya kina cikin hankalinki kuwa, anya kinsan abin da kike cewa kuwa..
Cikin jin haushinta HAIRANAH tace, "Toh aunty ni nayi kaina dazaki sha gabana kina tuhumata, Allah ne fa yayini yayiki yayi wanda ya had'ani dashi yanzu, lefine danna tsinci kaina cikin wannan halin bayan kinsan banice da zuciyata ba.
Allah ne fa da komai namu, Aunty ina iliminki yake, ina tunaninki yake, wallahi kamar saukar ruwan sama haka naki sanshi da ƙaunarsa ya mamaye zuciyata, idan bazakiji tausayi na ba kuma zaki gaya min magana me dad'i ba, dan Allah Aunty na rokeki Karki qara tarata da wannan zancen dan zanji tsanarki da gaske cikin zuciyata. Takai k'arshen zancen da had'e hannuwanta biyu alamar rok'o👏🏻
NUWAIRA tacije bakinta dan taji zafin kalamanta tace, "Haka kikace.
HAIRANAH ta sauke hannayenta da ratsawa ta gefanta tana cewa, "Aunty ai nace, Saidai kuma gaba..
NUWAIRA najin hakan taficce daga bedroom d'in taje tasakama kofar falan nasu key, tayi bedroom d'in Mamansu takwanta tana cewa "zanga ta'inda zaki fitta kije wajen nasa ki gaya masa kina sanshi wawiya kawai..

Sallar azahar HAIRANAH ta gabatar, kana tahau rokwan Allah kan idan san wannan bawa nashi alkairi ne a gareta yasa tasamesa cikin sauqi, ya shiga cikin lamarin ya daidaita al'amuran.
Idanko sanshi ba alkairi bane a gareta ya cire mata sanshi kadda ya barta dashi ko miskala zarratan..
Tana shafa addu'arta tafad'a tunaninsa.
Baqi ne shi irin kyakkyawan baqin nan wanda ake kira da black beauty, yana da hanci zir me kyan fasali, fuskarsa doguwa ce ga d'an sajensa mekyau, yana da ido Masu kyau na d'aukar hankali, jikinsa ko irin jikin nan ne irin na k'arfafan mazaje, ma'ana lafiyayyu Masu ji da kansu, shidai yana da jiki amma bacanja ba, dan jikin nasa bame muni bane, kallo d'aya zaka mai kasan yana da ilimin boko...
HAIRANAH na kawowa nan a tunanin nata ta lumshe idanta, wallahi ita dai tana sanshi, kuma koyana so ko baya so saiya Aure ta!!!.😨
Tana gama gayama zuciyar tata haka tatashi taje zata bud'e kofar falan nasu tajita a rufe, tasan NUWAIRA ce ta kulle dan karta fitta, hmm, yau bata jin futuna dan haka sai kawai ta koma bedroom d'insu ta haye gado, har a Lokacin hawaye bai dena zuba mata ba, cikin lokaci k'ank'ani ko bacci yayi awan gaba da ita...

NUWAIRA tadawo bedroom d'in nasu ta qarema HAIRANAN kallo taja tsaki, tace "wallahi indai ina tare dake bake ba zuwa wajen wani katan garde kice kina sanshi shashasha kawai..
Tana faɗin hakan ta juya dan bud'e ƙofar falan nasu dan jin kamar mamansu tadawo,

*Auntyn luv tace um um NUWAIRA ƙaddara tana kan kowa fah, kuma batu na luv ba'a cikamai baki inji XEE qawa ga SAILUBAH a samarin bana😍*
[






Aiko Maman nasu ce tadawo, macece kyakkyawa da ita, haka take y'ar duma duma fara tas da ita, kana dai ganinta kasan jinin fulanice...

"Sannu da dawowa mamah, NUWAIRA tace da Maman nasu hakan tana me karb'ar jakar hannunta cikin ladabi. Da murmushi akan fuskar Maman nasu ta amsa mata da.. "Sannu da gida NUWAIRA dafatan nadawo na sameku lafiya.
"Lafiya lau, "Toh madallah, gaskiya ban tab'a tafiya kamar yau ba, duk na gaji wallahi. "Sannu mamah, in kawo miki abinci ne ko ruwa, "aa, ruwan dai, dan naci abinci a gidan Ummi har tace ma in gaisheku, ina HAIRANAH ne banji mutsinta ba.
NUWAIRA tatab'e baki da miqama Maman nasu goran ruwan data d'auko a firija tace, "tana can tana bacci, da alama data dawo daga cefanan da gajiya ne, "OK, bari Nima nad'an kwanta kan la'asar tayi, maman tafad'i da kwantawa kan kujerar da take kai, Toh NUWAIRA tace mata da ficcewa zuwa kitchen nasu dan fara sharya musu abincin dare..

K'arfe huɗu HAIRANAH tatashi daga baccin nata, mafarkai tayi Masu kyau da masoyin nata, wai gata dashi har sunyi aure, wannan mafarki da tayi ya tsaya mata arai, hakan yasa taqara sakawa aranta lalle zai iya zama Mijin nata.
Bayan tayi sallah la'asar qara rokwan Allah tayi kana taje ta gaisar da mamansu, zata ficce daga gidan dan duba masoyin nata NUWAIRA tabi bayanta, bata kulata ba haka ta haura saman Layin nasu tadinga waige waigen san ganinsa amma Sam bata gansan ba..
NUWAIRA ta galla mata harara tace "anan dama kika had'u dashi, HAIRANAH tace "eh, wallahi Aunty baki gansa ba, kyakkyawa dashi, kuma daga ganin zaiyi hali mekyau.
NUWAIRA taja tsaki, "hmm, "tayaya kikasan hakan, qilama d'an shan jini ne ko me yanka mutune haka kawai dan d'ora kai damuwa dasan zuciya irin naki kika fad'a ƙaunarsa... "Aunty ya isheki haka, shekara biyu fa kika bani, bai kamata kidinga gayamin magana yanda kikaga dama ba, na gaya miki ban b'oye miki ba, ina sanshi da ƙaunarsa cikin raina, me yasa bazakiyi tunanin zuciyata zataji tsanar duk wanda zai aibantashi agareta ba, Aunty ke y'ar uwata ce, kuma Ciwan mace na y'a mace ne, nagaya miki idan har bazaki gaya min magana me dad'i ba Karki qara kulani akan hakan..
Ran NUWAIRA ya qara b'aci matuƙa, hakan yasa tace da ita, "insha Allah bazan qara miki magana akan hakan ba, kuma nafidda kaina daga cikin lamarinki gabaki d'aya tunda ban isa in baki shawara ki d'auka ba, tana faɗin hakan tajuyo abinta dan komawa gidan nasu..
Ai HAIRANAH najin hakan tayi saurin jawo hannunta cikin zubar hawaye tace, "haba Aunty, haba y'ar uwata, mezaisa bazaki fahimceni, mezaisa kiyi burus da jarabtar da Allah ya rubutomin, me zaisa bazaki bani kulawarki cikin da lallashi ba, nasan baki san so ba, dan baki tab'a yinsa ba bare ki fahimci zafin da nake ji araina, wallahi zuciyata zafi take min bani da buri ayanzu face ganin kyakkyawar fuskarsa, shine abin dazaisa nasamu nutsuwar da kika Sanni da ita, wallahi ban tab'a tsintar kaina cikin bala'i irin wannan ba, Aunty idan da ace kanki yazo bazan iya burus dake ba, dan Allah ki fahimceni, HAIRANAH takai ƙarshen zancen da rushewa da kuka gwanin ban tausayi...
Nan take ba tare da b'ata lokaci ba, NUWAIRA taji tausayin y'ar uwar tata ya kamata, nan tayi nadamar abin daya shiga tsakaninta da ita tun farkwan faruwar lamarin zuwa yanzu, nan ta rungume HAIRANAN cikin so da ƙauna tace, "Kiyi hakuri ƙanwata, yanzu na fahimceki, kuma Allah zai shiga cikin lamarin naki, nayi nadamar kasa fahimtarki da nayi tun da farko, ina sanki ƙanwata kuma insha Allah zan tayaki da addu'a kan Allah ya kawo miki sauƙin lamarin, yanzu share hawayenki Muje saimu tsara yanda zamu bulloma al'amarin..
Qara rungumarta HAIRANAH tayi cikin jin dad'in fahimtar tata da tayi tace, "wallahi aunty har naji dad'i araina, ko babu komai nasan al'amuran zasuzo min da sauƙi tunda Allah ya fahimtar dake..
Murmushi NUWAIRA tare da jan hannunta dan su koma gidan.

Bayan sunkai gidan ne Mama ta kalli HAIRANAH tace, "Yanaga idanki kamar Kinyi kuka.
Da murmushin yaqe NUWAIRA ta karb'e zancen da cewa "Yanzu kwaro ya shigan mata idan nata shine na wure mata shi.
Mama tace, "Ayya sannu aiko ga idan har ya d'anyi ja.

NUWAIRA DA HAIRANAH Kenan me karatu, su uku iyayen nasu suka haifa, Yayan su SABEER shine na farko ya gama karatunsa yana aiki a ma'aikatar Mahaifin nasu, baiyi aure ba har yanzu, yana dai laluban wacce zata dace dashi..
sai NUWAIRA me shekaru Ashirin da shidda yanzu, sai HAIRANAH me Ashirin da huɗu

Babansu d'an boko ne, hakan yasa yaketa Jan hankalin mahaifiyar tasu kan cewar bayasan yaran suyi Aure da wurri, yafi san suyi karatu me zurfi kana saiya aurar dasu..
Haka badan Maman nasu taso ba tayarda da tsarin nasa..
Ayanzu NUWAIRA ma tagama nata karatun, business itama ta karanta, tana aiki itama da mahaifin nasu, Saidai bata d'aukar aikin da mahimmanci, hakan yasa yace mata tafitto da mijin Aure, amma ta nutsu sosai ba sauri yake ba, tace mai toh.

Yayin da HAIRANAH tagama secondary skull ta tsaya kam dan kwata kwata HAIRANAH bata san karatu. Yarinyace me san wasa, wasa yayi mata yawa tun tana qarama, tana da

Please Login or Register in order to submit comment