Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

juya daukan wayarsa data fadi na mike idan guduwa zanyi kamani zaiyi,kawai ya sunkuya zai dauki waya na Arce ,nasan ina tsayawa zai ci Ubana, ina shiga su Meenat suka firgita suma sun dauka wani abu ne, jikin kofar yazo yace zaki fito ne,nace ni dai na fada ko gobe suka zo sai nayi musu,kwanan nan zan fara taka kowa, zaki fito ne sai na yankaki,nace ae idan anyi zuciya a biyani kudina,yace ko ina bayarwa ma Bazan taba baki ba,da na baki gwara na zubar kuma ko ina Tafiya ina taka kudi Bazan baki ba,shuru nayi masa Sabo da ina tsoro kar ko yar dubu daya ya hanani da me zanyi Cefane ko kudin Napep na schl din su Meenat.

Meenat ta kalli fuskata tare da cewa Sis dama ke ai akwai jure duka, shawara kawai mu daina fita ko palo sai in baya nan,Nace baki da hankali ai gwara ana damawa damu idan ya gano tsoronsa muke ji raina mana hankali zaiyi,ni yanzu da kike gani na Salo Salo zan dinga rikida ina canjawa tunda naga ba kudin nan za a samu ba bare idan na samu nace ya sakeni kinga gwara kawai mu samu na lallabashi mu samu kudin siyen kayan daukan wanka muci mu sha mu baza gayu,idan ya maidamu Family house a haka mun gama yawo kalli bamu da kayan sawa na kirki,

Meenat tace ni tsoro nake ji Sis bazan iya ko daga musu yatsa ba wannan uban kudi da suke dashi haka, tsoro ma nake ji kar a sakeki,nace ke ki daina min fatan saki yanzu gidan nan shine rufin asirinmu,ni ina son aurena wlh rike abina zanyi da daraja,gwara kawai nayi dan samun lada tunda kudin nan naga Alama ba sune komai ba, Meenat ta dinga dariya tace kowa ya tuba dan wuya ba lada Sis.

Ke na hakura da kudin na koma kama mutuncina ni kam harkar auren nan zan dawo na gaskiya,Idan ma ya sakeni Allah yagani,Meenat tace Good yanzu za a fara zaman aure kenan? Nace ae,tace to ai kin batawa mijinki rai sai ki fara zuwa ki bashi hakuri,haka ne miko min Katon hijab din can na Ammah nafi daraja a idonsa,hhhh Meenat tace yo wacce daraja zakiyi kinje wajen miji da Hijab ai kamata yayi ki dau wankan sugar,baki da hankali Meenat cewa zaiyi sonsa nake,ni kuwa ba sonsa nake ba bautar aure zanyi,so kike ya rainani ba class yana kallon tsaraici na,kin manta jiya da kika bude cinya kina lashe lashe a gabansa fa,to ai ni mantawa nayi dashi kuma in Allah ya yarda daga yau na koma yar gayu nima,ko kayan dadi ne sai nayi yanga zanci,kuma bazai kara ganin jiki na ba,Meenat ma ba hankali tace kin san kuwa Maza ba kunya garesu ba zaneki zaiyi kuma ta kalle miki jiki,nima nace ai yanzu zan fara bawa jikina tsaro.

Sadaf sadaf na fito da shirgegen Hijab dina,ba kowa a palo na tafi ina taku na nutsuwa irin nayi hankali fa,baya palo nayi ta Maza na haura samansa,har hadadden Bedroom dinsa na kwankwasa tare da Sallama na leka kaina ciki,na hango abinci lafiyayye da abubuwan dadi iri iri a gefensa yana ci yana aiki a system,Na murda handle na shiga,da mamaki ya kalleni yanda yasan tsorona na iya fitowa yanzu duk rashin kunyar da na masa,Har gabansa naje na durkusa tare da cewa sannu Aayan dan ni ba ruwana da wani yaya ko waye waye kawai Aayan tunda ba Masoya bane akan me zan boye suna.nace dan Allah kayi hakuri kaji wlh wasa nakeyi zanyi musu biyayya Bazan kara ba ni dai mu zauna lfy,da mamaki naji yace kin kyautawa kanki idan ma baki ba ke zaki sha wahala,ki nutsu ki san me kike abinda Family dinmu sukeyi bana wasa bane,har yau baki san dalilin auren Ki da na yi ba,kiyi abinda nace zan biyaki kudinki ko wani kike so ki fada min muna gamawa sai na warware aurenmu na aura miki wancan a ranar tare da kudade,nace to Alhmdllh ai ta kwana gidan sauki,amma da ni nufina zanyi bautar aurena tsakani da Allah,no..no..no Need kawai kowa yayi rayuwarsa cewar Aayan,nifa ba wai nufina aure kayi min wani abu na mata da miji ba ai na rigada nasan baza ka iya Yin komai ba,baka da lfy, a firgice naga ya dago tare da cewa a ina kika sani?nace ranar dana fara ganinka tare da Abbi time din da ka fadi nazo taimako ka min duka duk naji me kuke cewa,oh shine kika zo ki fada min kenan? karki jawo na goge miki hadda yanzu ki gani zan iya ko Bazan iya ba,nace ni ba haka nake nufi ba ina magana hankalina baya jikina sam yana ledar dana ga kayan tande tande a ciki har dogon wuya nakeyi haka nake ni Allah ya zuba min kwadayi a rayuwata tun ina karama Ammah bata yawo dani Sabo da babu dama naga me talla sai na mika hannu a bani,ko kuma nayi ta kuka sai an siya min,ko gidan biki idan akaje dani to fa kowa sai yasan kwadayi na,Ammah watarana sai dai ta goyani a baya tasa Zani ta daure ni har hannaye tam,sai dai nayi ta kuka a baya ina kallon masu tallan kayan ciye ciye.

Yana satar kallona yanda nake kallon abin ledar sai yace bari ya gwadani,Muryarsa naji yace ko zaki ci ne? Da Sauri nace a'a na gode ni bama na ci,murmushi yayi kana yace to shike nan dama na koshi zubarwa zanyi dasu,da Sauri nace kawo na zubar ma,a'a kyale idan zan fita zan zubar da kaina,Nace da dai ka kawo na hutar da kai kamarka dan gayu ka tsaya zubar da shara ai bai dace ba wannan sai irinmu,gaskiya ne dauki to kije dustbin kasa ki zubar,da Sauri na dauka tare da cewa sai da safe,yana ta jinjina kwadayi na don yasan ba zubarwa zanyi ba,kuma dama shi din yaga damar bani ne ganin yanda nake shi yasa yace na kallon abun shine tace a zubar,ni kuma tunanina wayo nayi masa na fita ina dariyar mugunta irin na cuceshi.

Ina shiga Bedroom na bawa su Meenat labari suka ce lallai Sister kin iya wayo,muka sha ice cream,Nama,lemo da wani chips yasha hadi.
Tun daga wannan Rana bamu kara ganin Aayan ba ko kamshinsa har muka kwashe sati biyu mu kadai muke rayuwa a gidan kuma sisi bai bar mana ba haka ya tafi,a bakin masu gadi naji wai yana Abuja,nima ban damu ba sam tunda Allah yasa ina dan boye kudi a hannuna kuma na saba da irin wannan ni dama tun ina yarinya a wahala na taso da tunanin ya zamu kare.

Sati daya shuru,biyu shuru,kudina duk sun kare gobe ma su Meenat basu da na zuwa schl nayi Cefane dana hannuna,muna zaune a palo na gama gyarawa Ma'eeshah kai na fara Yiwa Meenat kitso itama, door Bell muka ji, nace Ma'eesha je ki bude ta mike da gudu tare da bude kofar gani mukayi an mako kofar tare da ture Ma'eesha ta fadi gefe bakinta ya fashe,ba kowa bane face yan matan nan na gidan su Aayan su Uku har yau ban san sunansu ba, da sauri na mike tare da daukan Ma'eeshah ina mata sannu tare da goge mata baki da tissue,saman kujera na kwantar da ita ko kallonsu banyi ba naci gaba da Yiwa Meenat kitso,muna kallonsu suna ta jan tsaki ana yanga tare da taku dai dai muna kallo suka haura saman Aayan,da Sauri na mike tare da bin bayansu suna yanga na sha gabansu kafin su karasa bedroom din na riga su shiga ciki tare da zaro key din dake jikin kofar na rufe kofar da key na zare key din zan bar wajen suka tareni a palo dole sai na basu key dakin dan uwansu ne dole suyi abinda suka ga dama.

Kallonsu nayi sama da kasa sannan nace Bazan baku ba,a saman nan 2 palo ne ga Bedrooms har Uku kasa ma haka ku shiga duk inda kuka ga dama Amma banda dakin mijina.
Bazai yuwu ku dauki abu ya dawo yaga babu ba ni zai tambaya,hakki nane kula da kayan me gida tare da dukiyarsa,sannan dakin nan sirrinmu ne na ma'aurata bazai yuwu dan kuna danginsa ku shigar mana dakin bacci ba salon a ga gadon kwananmu, kaina sukayo gaba daya zasu dakeni na zame tare da guduwa muka shige Bedroom muka danna key suna nan tsaye cike da mamakin kalamai na tare da rashin kunya ta Amma ba komai zasu gyara ni Allah kawo ni Family house.

Nan take suka kira Aayan wai sunzo na zagi iyayensu,Yace su jirashi gashi nan ya dawo daga Abuja yanzu flight nasa ya sauka yama kusa da gida, 15 mnt muka ji motoci lokacin na fito daga wanka daure da towel na Sa Katon Hijab dina har kasa na fito don tunanina matan nan sun tafi sai na gansu a palo suna ta faman kallon kida a TV, dariya suka kwashe min da ita tare da cewa kaga yar kauye wai miji ya dawo Amma jibeta yanda ta Fito suna ta faman yi,ni dai ban kulasu ba na bude kofar da naji kara,wow yanda ya wani mugun kyau ba a cewa komai kamshinsa na tashi,Kallonsa na tsaya yi sai da yace Madam ya akayi ne yana murmushi ganin idon danginsa a wajen Amma nasan da basa nan ko kallona bazai yi ba,sai kallonmu sukeyi ganin idonsu yace ko Hug babu ya miko hannu zai rungumeni da Sauri Naja baya tare da cewa nayi fushi ai ka bata min,nan kuwa kawai ban so ya taba min jiki a wani auren business,Baki ya tabe sannan yace ni ko?yanda ya dage girar ya masa kyau,muryarsu muka ji sunce ur wlcm ya Aayan, tnx kawai yace musu yayi sama abinsa na dauki jakar nabi bayansa sama,su kuma suna ta tabe baki,ni na mika masa key ya bude dakin,Yana shiga Bedroom na ajiye masa jakar zan juyo naji yace me ya hada ku? Bakya jin magana wato ke ko? Duk abinda zakuyi karki sake kuyi min kokawa a gida tunda nasan kun saba,nace ni hauka nake na hada jiki dasu ai yanzu na girma Antynsu ce ni ai yanzu,zuwa sukayi tare da make min Ma'eesha harda fasa mata baki daga ta bude musu kofa,suka shigo har sama zasu shigar ma daki ni kuma naga bai dace ba ai nice matar gidan in banda an raina ni taya za a wuce dakin mijin mace kawai wai zasu dauki abu shine na kulle kofar na fada musu bai dace ba,ko ba komai idan wani abu ya bata ai ni za ace,Murmushi ya saki tare da cewa ashe kina da hankali,ina dashi mana ai kaine dan baka sanni ba kake tuna nin yarinya ce ni,ko magana bai kara yi ba ya wani shige toilet abinsa nima nayi waje,suna jiransa ya fito ya dauki mataki a kaina,amma shuru yama manta dasu gaba daya yana bacci abinsa.
Suna komawa gida suka fadi karya da gaskiya wurin kakarsu Hajja nan take tayi masa waya lallai ya dawo damu Family House a yau ba sai gobe ba.

Kawai ji mukayi yace mu hado kayanmu Driver zai maida mu can gidansu zamu koma da zama, haka muka shirya har kuka nayi a boye dan nasan shike nan mu kuma,Har part din Aayan na gidan Driver ya kaimu,dama na taba zuwa sau daya lokacin dana kai masa takarda ya nemo min Yarima abokinsa akan Aikin Ammah,part din ya tsaru harda na masifa,sama da kasa kasa 2bedroom da palo sama ma haka sai kitchen da store ya hadu iya karshe don yafi gidan da muka bari kyau da komai a kasa still muka zabi daki daya abinmu mu Uku,na duba kitchen da store wayam ba komai sai Indomie,kayan tea dana Coffee sai kayan sha dana gwangwani shirye cikin Fridge.

Yanzu za a fara rayuwar fa.









AsmaBaffa
[1/8, 1:24 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

KASUWANCI NA






36-40






Official






By AsmaBaffa






ZAINAB ATIKU SALAMA and MRS Hamza wannan page din sadaukarwa ce gareku.

Jinjina gareku
HEENDU
RAMCY MAKE UP
MOMMYN ZAHRA
HAJIYA ABOU
AUNTY SUMEE
HUMAIRA
ZULAIHAT
SAFEEYA AHMAD
Ina muku fatan Alkhairi tare da godiya da Sharhi.

Masu Sharhi na ko wanne Gp da wanda kuka min magana ta pc ina gani kuma zaku ganni Online wlh Simcard dina ne yake da matsala sai kun min Uzuri kafin na gyara,sako yana shigowa ina gani Amma ni Idan nayi reply baza su zo da wuri ba,kuyi min Sharhi ina gani kuma zan bawa ko wacce amsa Fatana kuyi min Afwa da Uzuri.








Kamar an sanar a gidan Radio haka muka dinga ganin yan gidan suna shigowa mata da Maza wasu na taba ganin su wasu kuma ban sansu ba,Kowa da kallon wulakancin da suke mana,ni kuwa ko magana banyi ba ko ina wuni bance da kowa ba nima kuma na cewa su Meenat karsu kula kowa,kaf yan gidan nan sai da suka sheda bani da mutunci bare kunya Sabo da zaman kawai da nayi a kujera ya isheka amsa, manyan ne kawai suke min kallon Banza ina kyalesu Amma indai mutum matashi ne ko budurwa yaro ko yarinya indai suka min sai na mayar musu da matartani ina daga zaune abina nima kuma basu Isa na gaishesu ba bare su Sa rai da mutunci na shigo.
Wasu manyan samari ne su Uku za suyi basu kai Aayan shekaru ba sunji labari ance musu Amaryar Aayan kyakyawace ta karshen gaske sai dai bata da kunya ko kadan,gata kuma kalar kauye ce duk iyayin Aayan ya kare a yarinya karama kamata kuma ba yar gayu ba,da sallama suka shigo bayan Sallar Isha Sabo da su Maza ne kuma suna da dan hankali,kallo daya na musu na dauke kai tare da amsawa a hankali,Ganin basuyi min kallon Banza ba yasa na saki fuska tare da cewa ina wuninku,suka ce lfy sannu Amarya ya gajiya nace Alhmdllh babu wanda ya kara magana,Sai kare min kallo sukeyi musamman wani a cikinsu kallo kamar maye hakan ma da Hijab dina,Sai ko naji yace Amarya ya kamata a mana girki muci mu ji,nace sai dai ku shiga kitchen da kanku ni yanzu sai na huta nasha gajiyar hanya daga wancan gidan zuwa wannan na jigata a Cikin mota Driver ya jijjigani da yawa a hanya na fada ina yatsina,mamaki ya kashe su abinda sun san gidan ba wani nisa da wannan unguwar Amma wannan yar rainin hankali ce wai mu shiga kitchen ma,

tasan ko mu su waye,kaji yar talakawa cewar daya a cikinsu ya fada a hankali bai san naji ba,daya kuma yace min kannen Aayan ne mu ni sunana Khaleel,ga Ameer sai wannan Mujaheed, nace good bari na shiga daga ciki,wanda ke yawan kallo na wato Ameer kenan yace a haba ko hira ba ayi ba,zama nayi kawai nayi shuru suma suna zaune sun dade sosai har wurin 8:30pm

Sai ga Aayan ya shigo rai a bace kamar zai daki mutane kadan yake jira,suna ganinsa suka min sallama suka fita,ni kuma na kalleshi yanda ya wuce da Sauri yana bin steps,Saman bed ya fada tare da kwantawa ruf da ciki ko me yake tunani oho ko wani abu akayi masa ban sani ba ni dai,nasan dai bazai wuce matsalar yan gidansu bace ni kuma ban san mene dalili ba bare nayi wani abu a kai,shi baya kulani bare nasan matsalarsu,ban ma san ko tarihin gidansu ba sai wanda na tsinta ranar ganina dasu na farko sai kuma abinda na fara gani yanzu a gidan kamar dai shi Aayan kadai shi suke warewa basa so Amma dai ban san komai ba,duk da haka sai naji tausayinsa,naji ba dadi me ciyar da kai ace yana cikin wani Hali dole ai kaji ba dadi sai kawai na wuce kitchen,Sharp sharp na dafa Indomie da kwai kar ma yazo yasa a kwashe su ya kawo mana su garin danwake shi yasa nace bari muci rabonmu,na bawa su Meenat na zuba wata a plate na nufi dakinsa can sama a nan na sha kallon haduwa.

Saman Bed na hangoshi a kwance ban san me yake yi ba bacci ko tunani,Aayan...Aayan na fada a hankali,a hankali ya bude idonsa tare da cewa Lfy? Abinci idan zakaci Indomie naga ka dawo daga Abuja baka ci komai ba,ko kaci? Kansa ya dago a hankali tare da kallo na ya dauke kai yace ni bana cin Indomie yanda ya fada kamar dan yaron goye a shagwabe,nace to me kake ci? Ai nasan baza ki dafa min ba bakya jin magana,fada zan dafa ma ai nayi hankali na daina, yaushe kikayi hankalin? Na daga kai ina tunani sannan nace an dade fa tun shekaran jiya, murmushin da bai shirya ba yayi kana yace Kosai nake so da kunun gyada sai danwake,nace to ai nan babu kayan yi a wancan gidan ne akwai,Waya naga ya dauka nan take naji yace a kwaso kayan dake kitchen da store na abinci a kawo masa part dinsa,wani bakin ciki ya dirar min shike nan mu baza muci abincin zamani ba,kamar yasan me nace sai naji yace shi kuka saba ci ai a gidanku idan na baku na yan gayu baza ku iya ci ba,nace mu dai zamu iya dan Allah,yace to ba yanzu ba sai watarana idan naga dama, cike da takaici nace shike nan ai,su Meenat basu da kudin Napep na zuwa schl,sannan nima dan Allah ka sani a schl,budar bakinsa sai yace ni bani da time idan kina da wani zan baki kudi ki zabi schl me araha private ya kaiki zan biya ni Bazan iya biya miki private me tsada ba,sabo da na raina basirarki, nace wai mene amfanin kudinka? Kallona yayi tare da Sa Headphone a kunnensa irin na takura masa haka na fita na kyaleshi cike da tunanin to wai me yasa ya aureni yana kallo ko kayan sawar kirki bamu da Amma ko Ya siya mana wasu to bai bamu abincin kirki ba ma sai wasu kayan sawa kawai dai raini ne ya jawo mana a danginsa.

Ina zaune a palo sai gashi an kawo komai na girkinmu irin na can gidan su dawa gero masara etc,Kitchen na shiga na fara shirin hada gyada da danyar shinkafa tare da lemon tsami na kunun gyada,ina cikin aikina sai ga samarin nan Ameer me kallon tsiya,khaleel da Mujaheed har kitchen suka ce Amarya girki ake shirya mana nasan ganin kwakwaf suka zo kuma sun gani su masara dasu geron,dan masifa suka ki fita daga kitchen din sai suka ce wai sai sun taya ni,nace a'a bana so kannena zasu tayani,sai ga Meenat ta shigo kitchen cikin English wears riga da skert tayi kyau Sabo da wanka tayi tare da fesa kwalliyarta da ta saba,aiko suka bi ta da kallo sunga me kyau da diri,ni kuwa a hijab nake baza su gane komai ba sai fuskata da take da tsananin kyau,Meenat tace Sis kawo na hada waken muna ta aikinmu tare suna kallo don zama sukayi a kitchen din wai sai an fara girkin sunci sunji,Ina tsoron tambayarsu gidan da ake markade na hakura mukayi a blender sai suka ga kosai mukeyi da kunun gyada,basa cin kosai su Amma suna shan kunun gyada,Aayan ne ya fito daga dakinsa Ya taho kitchen da niyyar daukan ruwa abin ya daure masa kai ganinmu gaba daya da rida ridan kannensa a kitchen muna yar hira jefi jefi sai tambaye tambaye suke mana akan girkin nan,ina tunanin zanga ya bata rai ko yaji haushinsu ko Ya musu magana su fita Maza bai dace su dinga shigewa mace me aure ba Amma sai naga ko a jikinsa ruwansa ya dauka tare da ficewa.

Muna gamawa naga sun zaro cups zasu fara eba,nace ku tsaya mijina fa? nasa ne dole sai na fara ebar masa,Ameer yayi murmushi tare da cewa Amarya ai ko nasan ne muna da yancin shigowa mu eba ko shi bai Isa yace kar mu eba ba,Kallonsa nayi nace to ni na Isa dan shi yasa ni nayi masa sai na ebar masa,Na gano ba so suke su sha ba takura min suka zo yi don kamar ma turo su akayi su Sa min ido.

Sai da na dauki wani jug me kamar flask na zuba ma Aayan, meenat bata ce mana komai Sabo da na hanasu magana akan dangin Aayan kosanta take soyawa,naje na ebarwa Aayan na ebar mana namu tare da kai mana Bedroom,na dawo lokacin Meenat ta gama soya kosai muka gyara kitchen sannan nace to zaku iya eba dan bakar jaraba suna palo sai da suka shigo kowa ya eba a cup suna sha duk wanda nayi suka shanye ba ruwansu da tambaya,Khaleel ma da yafi su rashin kunya Na Aayan yazo wai zai kara a ciki ya masa dadi, nan take na dauke komai tare da jerawa a wani tire me kyau sannan nace bazai yuwu ba kunsha rabonku nayi gaba na Barsu a palon,sama Na haura tare da knocking sannan na shiga yana zaune saman Sallaya yana addua na ajiye masa zan fita naji yace wait,ina tsaye ina jiransa ya gama tare da shafawa sannan naji muryarsa yace Zauna,can gefe na durkusa yace me suka ce miki su Ameer? Na bashi labari har abinda nace musu,yace to daga yau ko me suka ce ki musu kiyi musu ko nawa ne ki basu,nace ni Allah Bazan basu ba,nasha wahala kace na basu,to ba nawa bane nace ki basu,to me ya hanasu suyi auren su ko su tafi wajen iyayensu ni na haifesu da zan dinga wahala suna raina min Hankali,ina matarka tunda kannenka ne ai kamata yayi su dinga girmamani kuma sai suzo kitchen su tsaya min a kai ai duk kai kake basu kofa,kamar wanda ke jin tsoronsu ni ban gane maka ba,kace rannan na dinga ramawa yanzu kace na daina na bari kenan su takani ko? Shuru yayi bai ce komai ba,sai can yace nima kinga ban san me ke damuna ba ths month ina jin bani da lfy ni ban san ma meke damuna ba gaba daya,ina ke maka ciwo? Yace babu a jikina nake jin kawai da matsala bani da lfy ban san ya zan iya fada miki ba,tunanina mutuwa zaiyi sai na fara hawaye nace ni dai karka mutu dan Allah irin Ammah yanzu wa zai bamu abinci gashi muna ci muna koshi,kallona yayi da mamaki shi da yake bamu abincin talakawa Amma har dadi nake ji a haka ina fata kar ya mutu Sabo da wannan.

Miko min abincin,mika masa nayi sannan na zuba masa da Sauri wai dan kar ciwo ya kamashi ya mutu,ya karba a hankali yana cije lips ni tunanina ko jikin ne yake jin bazai iya karba ba,sai nace tsaya tsaya na karbi cup din nasa spoon a ciki ina juya sugar din sannan na rike masa a hannuna nace to bari na rike ma a haka kai kuma sai ka dinga sha ko na baka yanda nake wa su Meenat tunda baka da lfy? Banza ya min tare da bata rai yana ta fushi kuma yanzu kamar yaron da aka Zane,Sai ji nayi yace rike abinki ki sha,na fasa, yi hakuri gashi rike abinka Allah Sarki sha abinka kaji,ni kar na baka? Yace ae bana son naki, nace to gashi nan ni na tafi ma,na mike tare da bar masa dakinsa,na rigada na saba da Yiwa su Ma'eesha irin abun Yara idan zan basu abinci ko ina basu sai na dinga ta lallabasu shi yasa,ko ina basu ta dole.

10pm muna daki muna karatunmu ya shigo Bedroom dinmu tare da cewa zo,Maeesha tace Hi Uncle,murmushi ya mata tare da daga mata hannu,Meenat ma ta gaisheshi ya amsa da sakin fuska kadan,Hijab dina na Sa tare da binsa a

Please Login or Register in order to submit comment