Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ina kitchen sai girki nakeyi kamshi na tashi,Magrib nayi mukayi Sallah lokacin na gama miya tuwon danyar shinkafar nake karasawa,ina gamawa mukayi wanka da Sallar Isha tare da canja kaya marasa nauyi, Ma'eesha tasha 3qtr dinta dan me kyau da nake siya musu tare da yar vest na sa mata, Meenat kuma riga da skert tasa suma English wears na gwanjo amma masu kyau kalar yan gayu, ni kuwa doguwar rigar material nasa fitted nayi kyau amma ba kwalliya a fuskata.

A katon wani tire na roba na zubo mana miyar Kubewa danya da naman mu kowa yanka uku,Sai tuwon a leda har guda hudu manya,ga pure water shima na zubo a wata roba kalar ta Almajirai duk cikin kayan da Aayan yace a ciki zamu dinga cin abinci ne.
Na dakko mana komai muka zauna tsakiyar center Carpet na tattare rigata zuwa wajen hips gaba daya cinyata a waje take fara sal da Ita mul mul da su,Meenat ta fara dariya wai Sis ke baza ki taba cin abinci a hankali ba kuma sai rufe dankwali kin wani kwaye cinya jiba ana hango short wandonki,to mu da waye a cikin gidan daga ni sai ku,zamu fara ci kenan muka ji karar bude kofa kamshinsa ne yasa muka san shine ya shigo,Sallama yayi muka amsa na fara basu abinci a baki,tsabar sa ido shine yazo ya wani baje saman 3seater yana kallonmu a nutse,yanda yaga na kwaye cinya dankwali yayi kasa duk sabo da abinci,Maeesha tace Sis ki san masa abincin mana nayi banza da ita muna cin abinmu,ni na manta ma yana wajen Sam ina ci har cinyata nake dana da duka sabo da dadin girkin,idan na ci Loma daya sai na sosa kunne sai soshe soshe nakeyi kamar me kwarkwata ko cutar karzuwa sabo da ni idan da abinci a gabana mantawa nake da uban kowa,Meenat su Kansu dariya sukeyi tace sis ya dai wai abincin nan ko yafi Nama dadi ne,Ina lashe hannu tare da tsotse yatsu na ina tande baki nace ke Wannan gonar da aka shuka kubewar nan daban ce maybe kasar kalarta daban kinji har zaki zaki haka,wajen mutumin nan zan dinga siyowa,suka sheke da dariya shi dai Na'im yana kallo ina ta side plate din,Maeesha tace Sis ki kyale kwanon haka mana nace baki San ba kyau cin abinci ba tare da an side kwano ba ai sai Abar albarkar abincin a kwanon.

Aayan yana kwance yana ta faman kallon ikon Allah cike da alajabin abin nawa,muna gama nace muje a wanke hannu Muzo asha karatu,yana zaune yaga na Mike ina uban nishi tare da jansu muka je muka wanke hannu da baki sai ko muka kwaso jakan makarantarsu muka dawo palon kusa da shi yana kwance kai ka rantse nice shugaban masu ilmin boko na duniya yanda na faffake ina bude littatafai,Aayan yana jira yaji yanda zan fara koyawa kannena karatu.

Ga mamakinsa sai yaji Meenat ta bude wani English book tace fada min words din jiya naji,Bai san sanda ya bude baki ba wanda bamu San ma yana yi ba,Na fara cewa Singular and plural,Abu me guda daya da abu me biyu,Examples like Mango-Mangoes,Orange-Oranges,Bag-Bags,Lady-Ladies ina fada ina rubutawa a littafi har na gama,Maimakon nasa Ladies sai nasa Ladys nan take Ma'eesha yar karama taci gyarana tare da kwace biro tace sau nawa za ace miki haka ake rubutawa ladies wai yau kusan wata daya kenan kullum sai kin manta,Meenat tace to Saura mu fara present tense and past tense amma yanzu a koma baya muji,mene Noun? Nace Noun? Noun... to ....Noun.. dai shi sai na fada tunani tare da kallon sama kamar a nan zan samo amsa,nace to shi dai Noun... shine dai,nan take Aayan bai San sanda ya kwashe da dariya ba sai da muka kalle shi yanda dariya ke masa mugun kyau,Meenat tace Sis what is a Noun? Shine dai me? Na kara kallon sama tare da zura biro a bakina nace shi dai Noun is a name of....of.....yawwa shi dai Noun is a Name of Yawwa uhmmm....yes Animal dabbobi irin su Damusa, Kunkuru,zaki,kuma dai shi dai Noun is a Name of place like harda yanga irin na gano gaskiya harda daga yatsa kamar malama na kwalla da karfi nace like capital city of Nageria Abuja,na kara karfin muryata nace also kasar Masar,na daga kai sama nace yes Habasha,idan muka dawo gida Nigeria zan iya ce muku Rimin Gado,Kura,Kasuwar Rimi,yan Kura and also kofar wambai market,Aayan Dariya ta mugun kamashi duk uban labarin nan wai a Noun akeyinsa.

Meenat tace yes muna jinki sis,Nace kuma dai shi Noun is a Name of person na saki murmushi irin shegiyar nan nace like ni Mufeeda,Ammah Allah yaji kanta duk da ta riga mu gidan gaskiya amma zan sa da sunanta Fatima,Abba wanda ya arce,Maeesha kema kina cikin Noun,Meenat ma ta shiga ciki,Aayan ma gashi nan a kwance,Maeesha suka sheke da dariya, nace ah to dana fadi wasu banza na waje ai gwara na gida.

Na kara daga murya kamar me koyar wa a class nace Kai Noun shege ne wato shi ya hada komai harda Things kinga Bag,pencil,biro,spoon duk suna karkashin Noun.Meenat suka dinga dariya sosai suka ce kinyi dai dai amma labarin ai yayi yawa,nace wai me yasa Noun bai hado da abinci masu dadi a ciki ba aikin banza,ai kamata yayi ace akwai su Hen,su Ram,kabewar miya,Danwake,Taliya,Apple.
Aayan yana ta boye dariyarsa,Ma'eesha tace Saura Verb, nace Verb gaskiya ita bata dadi is an action word or a doing work, ni Verb bata birgeni sam,kamar yanzu munyi aiki yawwa Cooking,jumping,running,washing,kuji wani iskanci wai harda kallo watching ace yana cikin aiki,eating ma ai ba aiki bane amma a ce harda shi ciki,haka dai suka dinga tambayata ina bada amsa amma sai nayi dogon bayani da Hausa na cinye lokaci.
Ma'eesha tace daga yau an daina hausa sis duk bayanin da zakiyi sai dai kiyi mana da turanci kaf,na zaro Ido tare da cewa dan Allah kuyi hakuri ni dai me zance,Meenat tace wlh ba hausa gobe ki shirya naga Alama indai ba haka ba baza ki iya ba.

Sabon karatu sukayi min present tense an past tense,sannan sukayi nasu na manyan kwari tare da assignment ina kallonsu,sai kuma muka koma Islamiyya,anan kuwa nasan komai Qur'ani suke kara min da wasu littafan amma duk na iya tunda na iya karanta larabci da rubutu kuma ni nafi kokari a fannin Arabic sosai ko Aayan ya sheda daga jin yanda nake karatu ina cin gyaran su Meenat.har muka gama abinmu sannan Ma'eesha ta mayar da komai Bedroom ta dawo still Aayan yana kwance abinsa yana danna waya, nace su tashi muje su kwanta bai kula mu ba muma haka,amma yayi mamakin ganin yanda muka yi girki lafiyayye haka gamu yara kuma yasan fita nayi na siyo wasu abun amma abincin ya birgeshi sabo da shi yafi son abincin zallan hausawa fiye dana turawa.

Sai da ya dade sannan muka ji karar mota tare da bude gate wato mu kadai zamu dinga kwana a gidan,munyi addua na kara yi na tofa mana baki daya muka haye saman lafiyayyen bed din da bamu taba ganin irinsa ba muka fara bacci sosai,can cikin dare wurin 12:30 naji motoci sun shigowa gidan na farka tare da mikewa na daga labile na leka ta window Aayan na hango da ledojin take away dinsa a hannu ya dawo.A zuciyata nace dama yana kwana a nan? Na tabe baki tare da komawa na kwanta,shi kuwa yana shigowa sama ya haura yaci kayan dadinsa ya fesa wanka tare da shirin bacci yayi addua ya kwanta sai bacci.

Washe gari na tashe su mukayi sallar asubah tare da azkhar sannan nayi wanka suma suka yi tare da shirin makaranta ni kuma nasa kaya Atamfa riga da skert me kyau harda shafa powder tare da lipgloss,wake na gyara da sauri na fice tun gari baiyi wani haske ba na taka har inda ake markade sabo da Blender bata yin laushi yanda ake so,dan markade kadan nayi na dawo da sauri na daura ruwan dama Koko,sai na fara soya kosai yasha kayan miya kamshi ka rantse wani nama ake soyawa,Aayan yana jin motsinmu tare da kamshi yana tunanin wai ina muke samun abun girki me kamshin dadi haka, ruwa na tafasa na dama Koko me dadi da lfy,na ebi nawa a cup ina cin kosai ina kora Koko Malam,Meenat ma suka shigo sanye da uniform dinsu na zuba musu suka ebi kosai a plate da sugar suka fito Palo suna Shan abinsu,sai ga Aayan ya fito sanye da Jallabiya fara,suka ce ina kwana ya amsa ba yabo ba fallasa da lfy Alhmdllh,Ya kalli abinda suke ta ci bilhakki da gaskiya ganin yana kallonsu Ma'eesha tace Yaya gashi in zaka ci,baki ya tabe tare da cewa ban iya ci ba,d a dadi fa,yace am Ok,Meenat a tsorace tace ka dandana,a ransa yace wannan jagwalgwalon zanci ganin bana wajen ya mikawa Ma'eeshah hannu wai ta bashi ya gwada,da Sauri ta mika masa kosai daya yaci yaji shegen dadi,dama kosai yana dadi haka? Abinda ya ayyana a ransa kenan,Meenat tace a karo? Ba tare da yace komai ba ya mika hannu a karo masa,ta dauki plate din suka koma gabansa gaba daya Yana sama suna kasa zaune,Yana Sa hannu ya dauka yaci suma suna ci suna shan kokonsu,Maeesha tace Yaya a kawo ma kokon da dadi fa,karon farko kenan da ya kalli Ma'eeshah ya gansu kyawawa gwanin sha'awa ga tsafta,yace sai dai ki bani naki nasha,ta mika masa ba kunya ya karba yana sha da kosan,dan rashin Imani bai ce tazo a kara mata wani ba dan shi sam bai iya kula da mutum ba,ba ruwansa da wani caring ko kina cikin yanayi na Kaza yace je kiyi Kaza sam bai san wannan ba,yaci ya sha abinsa ya mike bai ce ko a dawo lfy ba yana uban takama da gadara ya koma sama abinsa,a haka na fito suka bani lbr nayi mamaki da ya iya ci,na Sa Hijab na rakasu a kafa har Babban titi tare da sasu cikin Napep suka tafi schl nace idan an tashi kar su taho su jirani zanzo na daukesu a schl tunda baza su gane gidan ba.komawa nayi gida lokacin yayi shiri zai fita an kawo motoci wasu kalar,ni na manta ma ina da aure Sabo da ba abinda na fasa yi ko ina fita nake yi,shima bai ce min ina naje ba ko mene ma nayi ina ruwansa ko kallo ban isheshi ba haka ya shiga mota aka jashi nima nayi ciki tare da fara gyara gidan ko ina.








AsmaBaffa
[1/6, 11:20 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

KASUWANCI NA






31-35






Official









By
AsmaBaffa






SAMEERAN GAYA yar ALBARKA ga page naki.

HAFSAT KHAIRAN Tare da MAMAN SAMHA ina gaisuwa.

JANNAT jinjina gareki me tarin yawa.






Dan Allah masu Sharhi kuci gaba da yi ina gani,kwana biyu Net yana bani prob zaku ga reply baya zuwa da wuri ina matukar damuwa wlh,fans kun san dai AsmaBaffa ba haka take ba,ina kokarin Yiwa kowa reply sai daí idan ban gani ba,dan Allah ayi min uzuri ko da wata tayi magana taji ban mata reply ba to wlh ban gani ba ko matsalar networkc.sai masu yi min magana ta pc kuma indai anga ba reply da wuri to net ne kwana nan matsala yake yi,kuma ko wacce nayi reply back sai yaki Tafiya sai da kyar,dan Allah ina kara baku hakuri za a gyara kuma ayi min sharhi na ina gani Sabo da nayi typing me kyau.

Sai kuma typing error ayi hakuri dashi,sai kuma kuskure na Dan Adam dole zaku ga abinda bai muku a ciki ba,har kullum ina so kusan cewa Sako ake isarwa,idan mutum shine star bazai yuwu ace baya kuskure a rayuwa ba,dole sai yayi abubuwa shima na kuskure tunda ana so a koyi darasi da shi ne,baza ace star shi ya Zama halaye 100% ba,so ayi hakuri aci gaba da karatu da Sharhi Insha'allah Novel zai tafi dai dai.
I really love my fans wlh sosai Sabo da so nake na dage ko wacce Insha'allah masu Sharhi sai na baku page Insha'allah sai daí mantuwa,wadda bajintarta tayi yawa har 2 ko 3 page ma zan bata suna nan kuma ina ta ganinsu AUTA, FlOWER ma suna ciki etc Bazan fadi sauran ba yan kuri ne zasu cika min Gp🤣.










Ko da na shiga gidan kawai aikina nayi ta faman yi sai da na gyara ko ina har Bedroom din Aayan ko ina sannan nayi mana miyar jajjage na siyo kifi na Sa mata,tayi dadi sosai,na dafa farar taliya na gama ,a gurguje nayi wanka na shirya tsaf sannan na maka Katon Hijab na tafi dakko su Ma'eeshah,ina zuwa suna fitowa da Sauri suka karaso inda nake tare da frnds dinsu wai zasu gaishe da Sis din frnd,harda gaisheni da turanci kawai na amsa tunda nima na dan iya a raina nace da kunyi hausarku Yara nafi karfi a nan wai su a dole yan private,shi kanshi me Napep yayi mamakin shegen gidan daya sauke mu,yace kamar wannan gidan ace za hau Napep ga yan mata zuka zuka haka,Me Napep tunaninsa ko yan aiki ne tunda yaga bamuyi kalar masu kudin ba,kawai sai ya fito daga Napep zai gwada sa'arsa a wajena ko zai dace da ya more ko yar masu kudi ce ai zaiyi auren jari.

Yashe baki yayi tare da cewa yan mata ku bar kudinku ai kyauta na kawoku ni,kamarki Hajiya ai kin wuce a karbi kudinki,na daure fuska tare da cewa kaga Malam karbi kudin ka ban son kinibibi ina da aure ni koma meke Ranka ka Adana kalamanka,yace yar yarinya dake yana dariya yace sake magana yan mata ido ba mudu ba ai yasan kima,tsaki Naja nace karbi da Allah kar mijina ya ganni a nan,yaki karba yana kallo na,muna haka sai ga motar su Abbi ta shugo tare da mata ciki manya biyu da yan matan nan dai abokan fada na su Uku, tare da dattijai su Abbi su biyu suma.

Cikina ne ya wani kulu kulu Sabo da tsoro nan take gumi ya keto min,na cillawa me Napep kudi Naja hannun su Meenat muka bi su ciki domin tuni sun shige da motocin su ciki,gashi basu san Code din kofar ba,nima ban sani ba Ma'eeshah ya rubutawa a paper jiya yace ta bani,dole suna jikin kofa suna jirana,a hankali na taho,suna bina da wani banzan kallo wanda saura kadan na fara Kuka,wata a Cikin manyan matan ta ja tsaki tare da cewa an kawo mana irin jaraba kuma dangin matsiyata sai abinda muka gani,Abbi yace taki yin Sauri ma kamar gidan ubanta,Yan mata a ciki daya tace zaku gaji da kallo indai wannan Villager din ce bata da kunya wlh zaku ce ni na fada muku,Dayan Babban yace wa zata Yiwa ai ko masa a saketa dan ubanta,cikin manyan matan wacce batayi magana ba tace dallah ki Sauri ki bude mana ko gidan uwarki ne wannan dole a maida ita Family house ko dan ta koyi Ladabi,nan take Abbi yace a'a ba yanzu ba tukun na gama planning idan lokaci yayi zakuji.

Ni kuma jin matar nan tace ba gidan Uwata bane jin za a zagi Ammah ta yasa zuciya tazo min wuya,haushi ya kamani gani dama da saurin fushi ni ban fiye jure a fada min magana a gabana kuma ace na danne ba zai wahala,ana fada min nake tunzura nima sai idona ya rufe ko za a kasheni sai na rama.
Ina zuwa gabansu na bata rai nasa hannu zan bude matar nan ta dungure min kai dan ubanki baza kiyi Sauri ba,a fusace na juyo tare da maka mata uwar harara ba ruwana ko uwar Aayance ni ban sani ba kawai kasa dannewa nayi,aiko yan matan nan da kadan suke jira suka fara salati suna zuga tare da cewa kun gani ko ai mun fada muku to wlh nan gaba ko marinta kukayi sai ta rama,Abbi yace Dan ban tan ubanki baza ki bude ba,aiko na kara harzuka kawai na fasa budewa Naja hannun su Meenat na juya inda na fito ina Tafiya a hankali cike da gadara ta nima,maganar duniya sukayi ko ehem basu ji muryata ba,ina ji suna lalalala lallai dole a dauki mataki ba karamar yar iska bace wannan magana ma tafi karfin tayi,shima dayan yace wannan tantagararriyar yar iskar tsagera ce,bata da kunya bata da mutunci kamar mu ta iya yi mana haka,ka duba Nafisa da Bilkisu babu abinda ba a musu ba Amma yaran nan basa iya daga mana ko yatsa,ka duba Shema'u zagi duka duk taci a gidan nan Amma ko daga ido bata taba yi mana ba sai wannan yar matsiyata,talakawa ma sauran kuwa daya aura daya ke yayan masu kudi ne dama su basu gaji tsiya ba,Abbi yace bar shegiya zata shigo gidan ne sai tafi kowa wahala da kanta zata bar gidan,nan take suka kira Aayan yayi Sauri yazo,minti 10 sai gashi a mota daya shike Driving,yana shigowa ya hango mu can gefe a zaune,gashi dama kuma Business din namu yace a gaban danginsa a nuna soyayya,ni kuwa na manta ma tunda ban gani a kasa ba,ba a biyani kudin ba,banci na ta da kai ba,nan take ya canja fuska ya koma nishadi da farin ciki ko kulasu baiyi ba sai wajena da ya taho yana wani murmushi muna hada ido sai ya maka min harara,yana zuwa kusa dani ji nayi kawai ya riko hannuna,na fisge hannuna yace film za ayi gasu nan zasu gane, nace can da matsalarku abinda ba sanin darajar business kayi ba ina ruwana ni, zan mareki kin san Halina wlh idan kika bari suka gane sai na yagalgalaki na koreki kuma,ni kuwa nasan zai iya mun samu rufin asiri ai ba shiri na mike,ina murmushin yake ya dauki Ma'eeshah a kafadarsa kamar yarsa yana mata wasa wai dan ace ana soyewa da mata kannenta ma ai kamar kannensa,Meenat tace a ranta kaga makirin Namiji a fili kuwa ya jawota kusa dashi itama ni kuma hannuna na cikin nasa,Maeesha an samu sake har wasa take da gashinsa a ransa yana ta jin haushinta tana lalata masa gashinsa me kyau yasha gyara.

Muna zuwa yace ur welcome, Abbi karami barka da yini,Aunty ya kuka tsaya a nan,My life bude musu mana,Abbi ya fara masifa wannan har kake kira da ur life yarinyar da ta zage mu taci mana mutunci yar Iska,Aayan ya bata rai a ransa fa Amma don yasan Halina ba tin yau ba bana iya hakura idan anmin abu,yasan tabbas zan rama indai sun min tunda yasan halin danginsa,a fili yace ko baki ganesu bane Dear,nayi shuru ya mintsini hannuna na saki murmushi tare da cewa ban ganesu ba naga suna fada ne tunanina kar suzo har gidan mijina suyi min sata,aiko nan take suka yo kaina ubanki zamu sata,yan matan nan sunfi kowa,Abbi yace Kafura da fuska kamar ta mage,na faki ido na Galla masa harara,yace wlh wlh sai nayi maganinki,na kara fakar ido na Galla masa harara tare da juya idona sannan na murguda baki,karaf a idon Aayan,a gabansu bai nuna ya gani ba,sai da muka shiga ciki na zame hannuna Meenat ta rada min ki kirashi da Babyna,nan nace Babyna kawo min Ma'eeshah taje ta huta nasan kasha nauyi,ya miko min ita tare da zama kusa da su Abbi,ni kuwa ko ta kansu banbi ba nayi Bedroom abina har suka gama fada da jaraba wa Aayan ina jinsu wai ya auro gadon rashin mutunci bani da tarbiya,shi kuma yana basu hakuri suka dai gama mitarsu suka bar gidan cikin bacin rai dama wai a haka ganin Amarya suka zo za ayi gulma.

Suna Tafiya ya haura Samansa yayi wanka da komai tare da cin take Away dinsa har Bedroom dinmu ya leko yace zo ke,lokacin wayata kawai nake dannawa ina game,su Meenat sun Tafi Islamiyya.
Na mike na bi bayansa har palo,yana zaune na durkusa a gabansa ya dauki dogon lokaci sannan yace ke baki da kunya ko? Ana tausayinki ba kya jin tausayin kanki,baki na turo gaba,yace ko nima zagina zakiyi,baki da hankali ai ko ba komai sun girmeki,kuma kina Matata ko darajata ai baza ki raina min dangi ba,nan gaba ke zaki sha wahala awajensu ni ba ruwana iya kaci idan sunce na rabu dake nayi musu abinda suka ce,kamar Abbi zaki kalla ki harara Kanin mahaifina ne fa kamar mahaifina ne.
Bazan hanaki yi ba tunda ke zasuyi ma ba ni ba,kinga ba ruwana,baki na kara turowa Hawaye yana zuraro min sannan nace haka kawai shike nan ni bani da yanci,ni mene baka Yiwa Kannena ba ashe da dadi kenan yanzu nayiwa naka kaji Haushi,sannan su zagar min iyaye sai nayi shuru Sabo da bani da zuciya ina...... wlh zuciyata bata mutu ba,babu wanda zai zagar min Uwa na kyaleshi ko shi waye,kai ko ni wlh Bazan dauki zagi da Duka ba sam bazai yuwu ba,bari kaji ko kai da bana so aka zaga Bazan kyale ba tunda yanzu kaine kake ciyar damu ko dan darajar wannan idan naga me cima mutunci sai inda karfina ya kare,sannan da kake cewa ana tausaya mana ai dai banzo gidanku nace ka taimakamin da sisinka ba bare kace taimako nazo nema,hasalima ni kake zalinta,tunda duk Aure ai aure ne ba banbanci,da kudinka Allah ya hore ma ka hana iyalinka sai daí ka bawa na waje ina zaka ci gaba ai baza suyi albarka ba kuma baza kaga dai dai a komai naka ba,tunda kana da Halin siya min Nama ka makale kudinka,ko kwai dan kwai ma babu,bare su madara me kwakwa ba daya bare kanwar biyu,sabo da son kudinka ko tsire baka siyo ba dan ka kyautatawa iyalinka,sai kudina na ma da suke hannunka tunda har yau Banga an fara bani kudin auren Business ba,ai in kana so nayiwa danginka biyayya to ka tabbatar sai ka karbi aurenka kace ba na kasuwanci bane tunda kai kace ba aure bane to mene hadina da wasu danginka da zan girmamasu,dadinka nake ji da zan mutunta su? kuma ko ba komai suma ai basu mutuntamu ba ko mu ba mutane bane bamu da daraja sai ku Sabo da kuna da kudi,Deal ne tsakaninmu zancen mutunci bai taso ba,a fara biyana kudi ayi a gama auren,idan kuma ka soke kasuwanci ka zabi daya ciki sai ka min komai da Allah yace miji ya sauke a kan matarsa nima zan sauke nawa,amma sai kazo kwata kwata ana abu ba akan dokar Allah ba mun tsara tamu dokar kace zaka zo da wani zance wlh kama zo da da bidi'a ....kau.....nake jin maruka ta ko ina a fuskata inba a lokacin sai da na dena gani kaf bana jin magana, yayi niyyar ya dinga ball dani kawai ya kyaleni da iya marukan da ban san adadinsu ba,na mike kuwa ko Hawaye babu na karkade jikina irin na gama kangarewa din nan nace Bazan fasa fada ba idan kana so na bisu wlh sai daí ka soke kasuwanci muddin kasuwanci za ayi wlh basu Isa ba ko su waye a danginka in dai sun min sai na take su nima,ni so nake ma ka kaini can Sabo da mufi goge raini,,na tattare skert zan Arce ya biyoni na kwalla kara nayi saman Bene da gudu,ya biyo ni a ransa yace yau sai ya hallaka yarin nan yana magana tana yi,ya auri mata manya manya ma magana basa iya yi masa sai wannan yarinyar, Ina gudu ina hakki nace dan Allah kayi hakuri karya nakeyi Bazan iya ba zan bisu sau da kafa,wayar chager naga ya fisgo ai na koma kasa da gudu garin gudu na fadi yazo kuwa cike da bala'i ya

Please Login or Register in order to submit comment