Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kwankwasa sai ko ga me gadi ya bude yana ganin budurwa yasan irin matan da Hon ke Tarawa kullum ne da fara'a ya tarbeni yace shiga yana ciki,nan ya min iso har cikin palon Hon,sai lokacin tsoro ya kamani,lokacin na hango Hon daga shi sai Singlet da gajeren wando yana latsa waya,da fara'a yana washe baki yace zauna mana kyakyawa me kyan sura,Nace ba sai na zauna ba idan zaka taimakeni to ka bani dan Allah,dariya yayi yace zo mana ke ya kike abu kamar bagidajiya ina ganinki wayayya zo muji dadi mana sannan na baki kudin a wuce wajen kawai,tsorata na karayi na fara ja da baya nace ni ance ba kyau namiji ya rike ma mace hannu nidai zan gudu,Hon yayi dariyar Kuruciyata yana lallabani yana hure min kunne amma naki matsawa ko kusa dashi,tasowa naga yayi ya taho jikina ya fara shafa min fuska yana kokarin cire min Hijab,yana sakin wani Gurnani ai da gudu na ja baya a rude na bude kofar na fice da gudin tsiya ko me gadi gani yayi kamar walkiya na bude kofa na fice wufff.

Ina Haki na fito da matsiyacin gudu na cukwikwiye Hijab dina na tattara skert dina ba takalmi a kafata tuni na watsar dasu,Na samu gefen titi kawai na Mike na dinga tsinka uban gudu ka rantse yan Mafiya ko Zaki ne suke Bina,ga unguwar shuru irin ta masu kudi ba kowa ba a ganin ko mota a titin,can naji karar mota ta bayana tunanina Hon ne haba ai sai na kara karfin gudu na yi nake kamar numfashina zai fita,a hankali motar take tafiya a saitina sai lokaci ina gudu na dan kalli glass din window din an sauke glass din ana ta min magana ta ciki gudu nake iya karfina da karfi nace wlh bazan tsaya ba Hon tsinanne dan Iska ina ta zagin me motar ji nake Hon ne ashe Aayan ne yake ta Bina da motar yana sheka dariya yanda yaga ina uban gudu kamar na tashin kiyama,tsabar mugunta sai yaki yin magana kawai yake ta Bina da mota duk inda nasha kwana sai yasha da motar yana ta dariya har sai da karfina ya kare tas na fara kokarin tsayawa Ashe ban sani ba idan gudu ya cika yawa yakai wani limit mutum kasa tsayawa yake da kansa sai an rikeshi kawai zai ta gudu ne,ina so na tsaya ina kokarin tirjewa amma ina gudu kawai nake falfalawa na fashe da kuka kuma ina ta gudu na kamar masifa har dai da kyar na samu na rike wata bishiya sannan na zube a kasa wajen ina maida numfashi,Dai dai lokacin Saurayi Aayan yana ta dariya harda kwalla sannan ya take birki a inda nake Kuuuuu yana ta dariya yana rike ciki,sai da na Huta sosai da sosai sannan na tashi tsaye ina karkade jikina,sai lokacin na hangoshi cikin motarsa Ashe shine ba Hon ba,kawai nima abin ya bani dariya kamar sabuwar Kamu na dinga sheka dariya harda kwalla,a ransa yace lallai yarinyar nan da alama mahaukaciya ce ko Aljanu gareta,na kalleshi saitin window na daure fuska sannan na maka masa harara,ai ko ya fito a fusace na firgita ba damar guduwa dan na gaji ina ji ina gani ya fito ya zabga min Mari sannan ya jefar dani a kasa keee ya daka min tsawa ba a min ko kallon Banza mind ur fucking Business,bana jin turanci tunanina yasan Business dina dana keyi a gida kawai sai nace dama ai ni Kasuwanci na nakeyi ina ruwanka dani haka kawai sai ka dinga cin zalina dan kaga bamu da kudi,ai kudin naku bana tsoron Allah bane tunda ba a taimako sai yawo a mota ana zalinci,tsaki yaja me karfi cikin takama ya koma labebiyar motarsa fuuuuuuu ya figi abarsa.

Ni kuwa na turo baki tare da cewa Allah ya isa wlh duk ranar daya mareni again Allah sai na rama za a gani ai,nan na gama Kuri na sannan na tafi gida abina.

Washe gari ban tsorata ba na kara shiri na tafi gidan Vice Chairman neman taimako amma haka na yini ban samu ganinsa ba sai yaronsa,Nace dan Allah wajen Vice nazo idan baza ka damu ba ka min hanya na ganshi,cikin daure fuska kamar zai bigeni ya hayayyako min da masifa ke malama an fada miki ya tafi Umrah bazai dawo yanzu ba,irinku dama yan mata makaryata da Iyayenku sabo da son abin duniya sai ku fara karya kuna zuwa Maula daga nan a lalata Ku yan iskan yara,har nawa kike amma har kinsan yawon Maula,nan dai yaron Vice ya min tatas na baro kofar gidan da takaici.
Ban dai kara hakura ba washe gari haka na kara shiryawa na nufi gidan wani Commissioner na Ilmi,a bakin gate kofar gidan na yini ina jira ko za bani dama na shiga ciki amma masu gadin ko kallona ba wanda yayi,har zan tafi sai ga wani ya taho da Jibgegiyar mota kida na tashi Malam nan take mukayi Ido hudu da wani Saurayi black Handsome dan gayu,sai kallona yake,ina tsaye aka bude masa gate,sai wani kallo yake Bina dashi kamar tsohon maye,nan take naga ya sauke glass yana murmushi tare da yafito ni da hannu wai naje,da sauri na karasa,sai kallo yake kare min tun daga sama har kasa yace yan mata wa kike nema?nace wajen Babanka nazo Commissioner na Ilmi da alama kai dansa ne ko?murmushi ya kara saki yana min kallon irin na yan duniya,yace ae dansa ne ni ya akayi?Nan na sanar masa taimakon da nake nema akan rashin lafiyar Ammah yace wannan ai karamar matsala ce Beauty,kawo na sa miki Number ta,nace ni bani da waya mu talakawa ne,baki ya tabe tare da dauke kai yana cewa ai kuna da amfani ta wani fannin,ban gane me yake nufi ba kawai naga ya miko min wata waya sabuwa dal a kwalinta amma karama ce Nokia me kyan gaske,yace kinci sa'a Baby na siyo wa yaron Mama waya karbi ki rike wannan ga sim card sabo bari na sa miki zamu dinga magana ta waya kafin Abba ya dawo sai a kaita asibiti.

Documents from AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels


Tunanina da gaske ne ba tunanin komai nace nidai ka bar wayarka amma ka bani Number dinka zan nemeka kaji,yace karbi karki damu kyauta na baki yan mata kamarki ba waya ai abin kunya ne,cike da tsoro dai na karba hannu na rawa garin zai miko min sai da ya shafi hannuna yana sani harda lumshe ido,da sauri na dauke hannuna ina godiya,da kansa ya hada min wayar da komai ya sa min Number dinsa ciki ya dauki number ta sannan ya miko min Dubu biyu wai na hau Napep,naki karba kawai sai ya zubar min da kudin a kasa yana shu'umin murmushi ya figi motarsa ya shimfida cikin wannan gida na alfarma,na dade a tsaye ina tunani kawai dai nace Allah gani gareka na kwashi kudin nayi gaba abina.

Danaje gida Ammah dan kar ta hanani amfani da wayar sai nayi karya nace Ammah yau dai na karbi kudin adashina na gidan Haule kinga na siyo waya sabo da baza a ace a gidan nan bamu da waya ko daya ba,nan suka dinga murna da tsalle,Ammah harda sa albarka tana murna dama yaran Zamani badai zuba karya a kifar da iyaye a corner can.

Next day ban hakura ba dai sabo da ina tsoro kar fa nazo ba a samu tallafi wajen Dan Commissioner ba kawai na shirya na Tafi gidan Dan Majalisa na tarayya da suke Zama Abuja,ni dai nasan ba lallai na sameshi da family dinsa ba domin wasu ma ba a Sanin inda gidansu yake buya suke su canja unguwa ko state dan kar a je musu Maula,ni kuwa tsabar jaraba sai da na kwakwulo gidan da tambaya tun daga unguwarmu nake bin gidajen manya ko wani ya sani,idan ance me zaki yi sai nace sako wasu zasu kai gidan da haka aka gwada min gidansa amma fa basu cika Zama a kano ba kawai dai zanje na gani ko me gadi na samu contact Dinsa ya min hanya, haka na fada Napep sai gidan Dan Majalisar tarayya Abuja,gidan kansa abin kallo ne sabo da ya hadu karshe.

Securities ko ina a gidan harda mutane a kofar gidan Yan maula,haka na kutsa kai cikinsu tare da tambaya ko me gidan yana nan suka ce ai rabon da yazo kano ma yau Shekara biyu kenan.
Baki na bude tare da mamaki wani ciki yace sai dansa Yarima Bobo da ake aikowa da sakon yan siyasa ana kawo musu,yanzu ma shi muke jira ya fito kin San shi a kwai gadara da wulakanci sai yaga dama yake fitowa ya bamu sakon Hon Rep,
Nan take nace aiko sai na jira dan nasa dan Ubansa ko shi waye,ina nan tsaye na gaji da jira har 2pm a wajen nayi Sallah saman dankwalina wata me tallan Fura tana zaune a kusa nace ta dama min ta Hamsim,haka ta dama furar tasha Nono me kyau da sugar, nace juye min ita a leda ki kulle,haka ta bani katon Dauri a farar leda na Fura da nono na bata ,sannan na siyi yogourt yar hamsim a leda tayi kankara,ina fara sha sai ga wani dan sanda yace Yarima yace Ku shigo ya ganku zai wuce Flight dinsa ya kusa tashi,da sauri mazan suka fada gidan yuuuuu,ni kadai ce mace haka na danna kai ciki ina Shan furata a leda yanda nake zuka kamar jariri ya kama Nonon uwarsa haka na lumshe ido ina tsotsa Malam ba ruwana.

Muna shiga ciki nan na hangame baki wajen kallon irin haduwa na gidan ba a magana,Saurayin muka hango chocolate dashi ya hadu sosai ga kyau ga iya wanka abin kallo yana kamshi yasha light blue shadda yana sheki ga motoci a gidan birjik,muka karasa gabansa yana zaune a wata farar kujera yana faman yanga da gadara,ido muka hada dashi yasha mamaki ganin harda yarinya haka,dan a wajensa bana Sahun yan mata
Ya fara sauraron wasu kawai muka ga Securities sun wani gigice sun nutsu waje daya tare da bude gate jikinsu na rawa,sai ga wasu motoci dalla dalla sun shugo gidan sun kai biyar kamar nasan motocin,ashe kuwa shine domin Saurayi Aayan ne me tashen kyau da Naira.

Gani mukayi Yarima ya fadada fara'arsa tare da mikewa ya tarbi Aayan da alama abokaine harda wani tafawa suna dariya,Yarima Bobo yace amma kai dan Iska ne Aayan tun safe kace zaka zo kasan yau zan koma Uk amma ka bata min time yanzu na daga flight dina sai 12am na dare,Murmushi Aayan ya saki cike da izza ya dage masa gira daya kana yace to ya akayi ne man sauri ka gama da mutanen nan naku kasan ban son jira,Yarima yace ai kai dan Iska ne ga sit can,kusa da mu ya zauna can nesa a wata kujera ta yan gayu,Juice aka kawo masa yana korawa,a raina nace Allah sarki talakawa mu ko ruwa babu me bamu.

Yarima yana ta ganin mutane yana sallamarsu da kudi,sai yace pls Ku mazane kuyi hakuri na sallami yarinyar can tunda macece,a raina nace Ashe yana da kirki,nan yace ke zo naji na sallameki sai lokacin Aayan ya kalli inda nake muka hada Ido,da mamaki ya kalleni lallai yarinyar nan wato har maula take zuwa gidan masu kudi sabo da son kudi,ko dai bata da iyaye ne oho,yana gani na karaso gaban Yarima ba tsoro na durkusa gaban Yarima tare da cewa ina yini?yace lfy tashi tsaye ki fadi abinda ya kawoki sauri nake ina da bako,ina durkushe a gabansa kaina a kasa kuma ina ta zukar Fura ta kamar yarinyar yaye,idan nayi magana daya biyu na zuki furata,babu wanda baiyi dariyar abinda nake ba kowa yana ganin ai yarinya ce,shi kuwa Gogan Aayan a zuciyarsa yake Dariyar kwadayi na,kuma sabo da kuruciya a gaban kowa ina mace ko dai bani da hankali ne. na karanta masa ciwon Mahaifiya ta,yaji tausayina kuma lallai yaga mu abin taimako ne,sai yace jirani a gefe bari na sallami sauran,

nan na Mike na koma gefe,Aayan ko kallona bai kara yi ba har Yarima ya gama da mutanen kaf suka tafi ya rage daga ni sai Aayan sai Yarima,yace zo ke,da sauri na karasa gabansu su biyu,yace ina babanki ko ya rasu? Bana so na fada a gaban Aayan wanda ke latsa waya,sai nace Sirri ne sai dai idan zamu koma gefe na fada ma,murmushi ya saki yace to ya Mike ya taso na kara kasa da murya da rada nace bacewa yayi ba a San inda yake ba,kawai ko guduwa yayi wa ya sani,dariya Yarima yayi yace to shike nan ki kawo takaddun asibitin naki mu gani,nace to ai naji ance zaka yi tafiya,no ki jira zamu fita da frnd dina sai mu saukeki ki dauko takardun,a tsorace nace tab wancan masifaffen ne zai yarda,kin sanshi ne?ya tambaya,nace ae na sanshi kullum sai ya mareni idan ya ganni,murmushi yayi yace to ki jira ai motata zaki shiga,murmushin da nayi shi ya tafi da Imaninsa ya tsaya yana kallona,sai can ya dawo hayyacinsa yace ina zuwa ya koma wajen Aayan dake ta faman cika yana batsewa,Yace kai Yarima kasan fa ban son jira wlh zan tafi ka tsaya kuyi hirar,ba class ba komai,Sorry let's go,Aayan da mamaki yaga na shiga Motar Yarima shima cike da takaici ya shiga nasa motar suka ja muka bar gidan cikin zugar motocinsu,sai da aka zo kusa da gidanmu suka tsaya,Yarima yace yarinya yisauri ki dakko mana na gani,ina fita na kwashe da gudu na karasa gida na fada daki na ebo kamar kiftawar Ido na fito da wani gudun kowa ya ganni sai ya tsorata ko wani abu ne ya biyoni,da gudu ina Haki na kawo masa takaddu ya sauke glass kasa ya karba ya gani tabbas da gaske nan ya miko min card dinsa yace ga Number ta na Nigeria dana waje ki kirani kiji,da sauri na daga kai sama,ya zaro Dubu goma ya bani yace gashi ki siyawa marar lfy ko ruwane,godiya nayi na karba, Yarima yace ki daina gudu kinji yarinya ba kyau mace tana gudu,da ladabi nace to na daina ai tsoro naji kar Ku tafi sannan na juya na dau hanyar shiga gidanmu,sai da naje bakin kofar gidanmu zan shiga na juyo baya sai naga Motar Yarima sunyi gaba sai Na Aayan yana kallon inda zan shiga kamar Munafuki muna hada Ido suka figi motarsu fiii suka kara gaba abinsu nima na shige gida.
Still ban gamsu da taimakon Yarima ba sabo da yan siyasa basu da tabbas ayi maka karya ka dauka gaske ne kayi ta jira ana ja ma rai,don haka kwana nayi ina tunanin cewar wanne gida kuma zanje nan take na tuno da wani dan kasuwa Hamshakin me kudi a GRA unguwar su Aayan,har matsuwa nayi gari ya waye na tafi,ga kuma gidan wata Mata nan ma Naji ance tana taimakon Talakawa.
Sannan Zan biya sakateriya ta unguwarmu wajen Kansila Adamu me tallafi ko Allah zai sa ya shigar da sunana cikin masu karbar tallafin Manoma na Gomnati.
Kuma duk a gobe zanje wani Training shima ko zan samu a dauki sunana cikin masu koyon sana'a idan ka gama a baka jari.gaskiya gobe ina da tsare tsare da yawa,don haka kosai ma kadan na soya na barwa su Meenat komai tare da shiryawa yau ba Hijab nasa ba mayafi na yafa nayi kyau yau doguwar rigar material nasa red and green mayafinta green da takalmin robata baki,Ammah nayiwa Sallama ta zuba min addua sannan na fita da addua a bakina.








AsmaBaffa
[1/3, 9:47 AM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

KASUWANCI NA






16-20





Official





By
AsmaBaffa







JIDDER ZARIA ina godiya kema ga page dinki.

Masu Sharhi kuna kasheni da dadi Allah dai ya saka.







Napep kawai na shiga 8am dai dai ina kofar gidan dan kasuwar nan me kudi dake Unguwar Su Aayan,abin takaici ba irin buga kofar da banyi ba amma ba wanda ya bude min hasalima me gadin ne yazo yace ai sun Dade da tafiya Kasar waje basa rayuwa a nan sai jefi jefi,haka na juya da Niyyar tafiya katsam sai ga yan matan gidan su Aayan su uku sun fito a cikin mota da Alama schl ko wani waje zasu je sunsha wanka da kyau,suna Shan kida,da sauri suka fito daga motar suka zo ba bata lokaci suka fara dukana,ina ihu nima ina ramawa Amma sunfi Karfina,nan take daya ta cire takalminta me tsini ta kwala min a kaina a akasi nan take na zube a Sume wajen na fitar da jini,ba Imani suka koma cikin mota suna murna sun rama abinda nayi musu suka shige mota,ina yashe a kasa ban san inda kaina yake ba,sai 10am Aayan ya fito yau a mota daya zai fita shi ke Driving ma,kawai ya hangoni a kofar gidansu cikin mawuyacin Hali,mamaki ya lullubeshi me ya kawo ni nan da sassafe ko dai Aljana ce ni,a tsorace ya tsaya tare da bude motar ya fito da ruwan roba ya watsa min,nan take na ja numfashi na Mike zaune a firgice ina Dafe goshina wajen da jini ya fita,mikewa tsaye nayi ina Jiri kamar zan fadi na dauki gyalena da kudin Napep dina,na fara tafiya ina Kuka gwanin tausayi,amma marar Imanin ko a jikinsa sai ma tsawa daya buga min yace me ya kawoki nan again da safe,ko kulashi banyi ba naci gaba da kuka na ina tafiya,shuru yayi tare da cewa Yau sai naga inda zata kara zuwa,ya shiga mota.

Yana gani na shiga Napep yana Bina a boye ban sani ba,tuna ninsa gida zanje amma ina sai yaga me Napep ya Parker a gate din wani makeken gida,na biya Napep ya tafi na shiga kwankwasa gida,Aayan dai yana mota yana Shan kallon ikon Allah mutum jini na zuba a jikinsa amma bata lafiyarsa yake ba ta neman Kudi yake.
Security ne yazo yana turanci where are u From? To ni dai Na gane me yake nufi amma bazan iya juya yaren ba sai nace na kakalo karya nace ni yar gudun Hijirace daga wajen Nijar nake,wajen Hajiya nazo a tallafa min Mahaifiyata bata da lfy,lokacin da nace haka Ashe Aayan yana bayana yaji komai harda yiwa Gate man signa yayi shuru,ni kuma ban san yana wajen ba sai nayi karya a akasi,abinda nacewa Frnd dinsa Yarima Bobo daban abinda na fada anan daban,sabo da bana so nayi ta tona sirrin gidanmu shi yasa ni a ganina idan nace yar gudun hijirace mahaifiyata ba lfy Zanfi samun tallafi kuma Ashe Munafuki yazo jin gulma.

Tuni gate man yaja tsaki tare da banke kofa ya rufe,ina juyowa muka hada Ido da Aayan yana mun mugun kallon tsana alamar yaji komai,karya ba kyau yan Uwa mu guji karya kanayi watarana sai asiri ya tonu duk da akwai dalilina na karyar amma ya dace kayi gaskiya a komai idan za a baka a baka don Allah. bai ce komai ba yana gani goshi na yana jini amma yayi tafiyarsa ya shiga mota,nima na siyi pure water na wanke Raunin tare da fuskata sannan na sa gefen gyalena na danne gaban goshin nawa Ina duba agogon robar dake hannuna,
lokacin Training yayi nan na nufi sakateriya inda za ayi,mun taru da uban yawa amma sai me hanya da gata shi ake dauka mu da bamu da hanya sai muka koma yan kallo muna zare Ido,

Ina duba lokaci na shiga wani part can cikin sakateriya nan na fara neman Kansila Adamu me tallafi aiko yana nan na sameshi a Office dinsu na kansiloli,masu son mata suna lashe baki ana kallona wanda kuma basu damu ba kallo ma ban ishesu ba haka na karasa wajen Adamu Kansila wanda yana daga cikin masu son mata,Adamu ko kudin Hotel zaka biya masa shi da mace to ba abinda bazai yi maka ba,kullum rayuwarsa a hotel take da mata,aikinsa kenan a kai mata hotel,ko so kake ka yaudari Adamu Kansila to ka biya masa Hotel ya kai mace ciki.

Ni dai ban sani ba muna ta hira da Adamu ana kallona a karuwarsa har muka jero tare da ketowa ta cikin mutanen dake sakateriyar har bakin titi ya rakoni yana cewa ki kwantar da hankalinki ai tallafi kamar kin samu ki kyale wannan na sana'ar aikin banza ne zan sa ki a me tsoka,ina murna still hannuna yana kan goshina na danne ciwon,Adamu yace me ya sameki nace bigewa nayi wajen shiga mota,yace sannu muje na kaiki Chemist ayi miki dressing,muka jera tare da Adamu Kansila muna hira yana ta murna ya samu Damar hure min kunne,yana wani taku da iyayi shi a dole Kansila me kudi,haka muke tafiya muna ta murmushi kamar saurayi da budurwa ga Adamu akwai wankan shadda gashi matashi dan kyakyawa dashi ba laifi dai,sai kallonmu akeyi,abinda ban sani ba Aayan yana can side din da mota yana tafiya a hankali yana kallon komai nawa da nakeyi don yace sai ya kure karyata bai yarda dani ba.

Yana kallo Adamu ya kaini chemist akayi min Dressing muka fito tare Adamu na kokarin rike min hannu na matsa gefe da sauri shi kuma yana borin kunya,amma duk da haka Adamu yace yaushe zamu hadu,nace ban gane ba,yace akwai maganganu da nake so muyi amma a Hotel zamu fi samun sirri ko? Nan take nace ban gane ba,yace au da nufin ki a banza zan saki a tallafin?ai ban gishiri na baka Manda,nan take bakin ciki ya mamayeni wato duniya baza a taimakeka don Allah ba,yan Iska sunyi yawa kowa sai ya nemi lalata ma rayuwa,ban san sanda naji haushin bata lokacina danayi a wajensa ba na fara masifa shi kanshi Adamu bai San bani da mutunci bani da kunya ba sai yau da nayi masa tatas daga karshe nace Algungumi a haka kamar mutum Ashe mata kake yiwa ciki to baka isa ba in dai hannu ne bazan bari ka taba ba bare kayi min ciki,ni tunanina ai kawai hannu ake rikewa ana yiwa mace ciki,nan na kara boye hannayena cikin mayafi tare da gallawa Adamu Kansila harara nayi gaba abina ina tafiyata a hankali,duk abinda nakeyi Aayan na kallona ban sani ba.Napep na shiga na koma gida nace na fawwalawa Allah na daina fita neman taimakon kowa Allah ya kawo min hhh naji wuya.

Kasuwancina na rike bilhakki da gaskiya domin yanzu har funkaso da miya nakeyi da yamma,shima na kan danyi masa Algus yanda za aci riba me yawa nifa komai nawa sai anyi cuwa cuwa.
Ammah kwana biyu da alama ciwonta kara karfi yakeyi sai addua muyi kuka mu gaji ina ta kiran wayar Yarima bata shiga idan kuma ta shiga ba a dagawa.
Haka na kira dan gidan Commissioner da gudu ya dauka sabo da yayi saving number,dama kwadayinsa ya tashi yana ta neman Number ta amma bata shiga har yana masifa cewar yayi asarar kudinsa ya bani waya Bai Mori kudinsa ba,shima muna fara waya naji yana kawo min maganar iskanci,Hello Baby ya kike?nace lfy idan na kawo maganar maganin Ammah sai naji yace za ayi yan mata karki damu sai ya dauko maganar iskanci me kikeyi yanzu?wanne kaya ne a jikinki? Ai da zan aureki kullum sai na miki sucking sau biyar,ni ba wani ganewa nakeyi ba da na gaji na gano lallai dan iska ne kawai sai na kashe wayar tare da cire layinsa na ballashi sannan na siyi sabo na sa a wayar da ya bani nace naci banza yaro nasa mata kudi naci gaba da neman Yarima

Please Login or Register in order to submit comment