Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

take ta mita tana yabon katifar da take duk ta jeme duk ta side tudun babu Sabo da taci duniya ta gaji gata siririya ta gaske,Ameer ya fito wajen Inna yace Inna ta dakina da nake bacci a birni sai tayi girman tsakar gidan nan gaba daya,kinga Bed dina kuwa like...Hannu Inna ta daga masa kaji shakiyin yaro yo ko Sarki ne ina zai samu katifa kamar girman tsakar gidan nan in ba karyarku ta yan boko ba,sai dai ka shiga gidan Radio a Sa zancenka a labarin nishadi na tatsuniya Amma ba a wajena ba baza ka samu karbuwa ba

Dariya Ameer yayi tare da cewa dan kawai baki sanni bane Inna kalli fatata fa kalli kyauna, me yasa kasan da haka baka Sako gadon naka a mota ka taho dashi ba karka dameni kaje kayi wanka ga abinci miyar harda Naman Zabo,Maeesha sai dariya suke har suka kai masa ruwan wanka bayi,yaga bayi ba rufi ba komai fayau ko murfin kofa babu gashi na kara da Ameer ya fito tare da cewa shi ya fasa wankan Tafiya gida zaiyi kar dare yayi masa bazai iya amfani da toilet dinsu ba,Toilet ce kadai zata koreshi daga kauyen,rokonsa sukayi yamma Liss yayi Manage zuwa gobe sai ya tafi,ya shiga haka ba yanda ya iya kayansa ma daya cire sai ta saman katangar ya mikawa Meenat ta rike masa su,

Ya mike yana wanka jikinsa duk kumfa wata yar fulani da kwaryar nono ta bayan gidan zata wuce sukayi ido hudu da ita ta kalleshi ya kalleta Amma iya kansa zuwa kirjinsa take iya hangowa ta wajen gidan,Ameer yaga taki dauke idonta ya ware mata hannu alamar zagi dakuwa yace karbi wannan kan Uwarki,bata gane ba ta tsaya tace me kace yace baki gane ba? Hakan nana yana ware mata yatsu wai yaren mutan kauyen ya mata na zagi Haka nanan,Tace ni yace a'a ubanki nake nufi baza ki bar nan ba sai na fito na fasa miki baki,Yar fulani tace yo ni ina ruwana da kai dan zanje tallana, ko tsirara na kalleka me zai firgitani,Kaga naga kalar ta Iro,Nasan ta Ja'e,har gaisawa na kanyi data Lawalli duk ranar kasuwa iya kaci kace ta wani fara ta wani ba to duk cikinsu ta Ja'e ce Baka wuluk me zaka bude min ido dashi ta ja tsaki tayi gaba,Ameer ya zaro ido waje tare da bude baki yana mamaki yace Ana iya shege a kauye ba kunya ba komai,ana cewa yan Fulani masu kunya etc ashe duk karyace, ya kwalawa Meenat kira ta bashi kayansa nan ma sai kanta ta sadda kasa sabo da kunya kar ta hango kirjinsa.
a gaggauce ya karasa wankansa ya karbi kayansa ya fito,Abincin ma ba dadi kasa ci yayi yace shi wlh gobe zai tafi da Safe,Gari na wayewa ko karya wa yace bazai yi ba,dama tun jiya ya karbi number din me motar da ya kawoshi jiya yace ya dawo gobe da sassafe ya daukeshi,Me mota yaji yanda ya samu kudi da Sauri ya Amsa, ai kuwa 8am sai gashi yazo daukan Ameer back to Cikin Gari,Ameer da murna ya dauki jakarsa tare da basu kudi da yawa har Inna sai godiya take tana Sa masa albarka, ya musu Sallama Meenat da Ma'eesha har mota suka rakashi ya shiga yana musu gwalo ta Glass suna dariya sai gida.

Yana dawowa Yace wai ya fasa Interview din ne shi yasa ya dawo ya bincika yaji bazai yuwu ba,Hajja sai murna take ya dawo lfy, toilet ya fada ya dinga dirzar jikinsa ya dade sannan ya fito ya shirya sosai ya nufo Part dinmu.

Ina kitchen ina Hada Chips na ganshi,Na dinga dariya naji abinda ya koroshi,nace ai kyaleka kawai nayi,Gaskiya Anty baku dace da Ruga ba ina sam kauyen baiyi ba,Abinci na zuba masa ya dinga ci Sabo da ya kwaso yunwa,yana ci yana bani labarin irin wahalar da yasha,Anty toilet ba rooping bare kofa ina Bazan iya ba, yasu Meenat fa? Ameer yace sunfi kyau acan,a kauyen zasu fi kyau Ameer? Ameer yace sosai Anty baki ga Meenat ba har wasu kumatu takeyi,Ina ta dariya nace to ko dai ita zan baka? Ameer yace wannan Masifaffiyar ai sai ta kashe ni ma gaba daya.

Yau kwana biyar da tafiyar Aayan kenan da kyar nake bacci tunaninsa ya Addabi zuciyata,na ma rasa inda zan Sa kaina gaba daya duniyar bata min dadi kullum ni kadai gashi yace Bazan fita ko ina ba, sai gyaran jiki da nake zuwa, tunda ya tafi bai kirani a waya ba nima ban nemeshi ba Amma ko bacci bana iya yinsa sosai Sabo da tunaninsa, Shima can Aayan hakan take baya iya komai sai tunanina,Yarima ya gama gane Aayan so ne kawai ya kamashi,ya kasa nutsuwa,baya iya bacci,abinda ya kaisu ma ya kasa komai,har Zazzabi yakeyi cikin dare na rashina kusa dashi.

Ameer ne kadai yake debe min kewa idan yazo muyi hirar ya tafi,idan ina bukatar abu shi zan bawa kudi nace ya siyo min Amma bazai taba karbar kudin ba da kudinsa zai siyo min komai me tsada da kyau, kullum idan ya dawo daga Office sai ya shigo kuma bai taba nuna min ko sona yake ba,ko wani abu na banza bai taba shiga tsakaninmu ba,mutuntani yakeyi yana bani girma na yanda ya kamata,
Shi Ameer ma tuni ya tuba da son Matar wani tunda yaji wani Wa'azi me Zafi,yaga ina bai kyauta ba,nan take ya fara Istigifari ga Allah ya cire komai a ransa,kawai ganin mutunci na yake dana Aayan sosai,sai kannena yanda suka daukeshi kamar dan Uwansu.

Idan ta kama watarana ko kitchen ya shiga idan yaga wanke wanke banyi ba sai ya tsaya ya wanke min ya gyara min kitchen sannan ya tafiyarsa,hakan yasa abinci sai kalar da yake so nake mishi ance ka kyautatawa me kyautata ma.yau da dare ina bacci wayata ta shiga Ruri ina ganin Number ce ta kasar waje naki dagawa nasan Aayan ne,kullum haka yake min har sai da muka kwashe kwana Uku kullum sai ya kirani yafi a irga Amma bana daga masa waya,har ya cika sati yana kirana kullum kuma bana dagawa.
Muna haka dashi katsam da yamma nasha wanka na cikin doguwar riga Ready made ina palo gidan yasha gyara littafin Hausa nake karantawa a wayata ina ta dariya ni kadai ashe Bell nata kara banji ba sai gani nayi an turo kofar a hankali har ya shigo ban sani ba,sai kamshinsa naji kawai ya cika wajen,da Sauri na daga kaina sama da Sauri ido hudu muka yi ba karamin Kyau yayi ba cikin kana nan kayan ya hadu karshe, Sallamar na Amsa kwarjini yasa na kasa yi masa abinda nayi Niyya,wani dadi,Sanyi,farin ciki,sonsa ya kara shiga jikina gaba daya na wani diririce,nace sannu da zuwa ka dawo lfy?kai da kace 2 to 3 wks zakayi Amma yau Sati daya ka dawo lfy? Harara ya watsa min tare da zama gefena muna gogar juna yace Baki da kirki Mufeeda,bani wayarki ya furta tare da fisgewa yaga Number ta kasar waje da ya kirani da ita har Saving nayi da sunansa Amma naki dagawa,kallona yayi yace kin ma san nine kika ki dagawa saima Saving da kikayi kin kyauta.

Kallonsa nayi nace kayi hakuri,kin hanani yin abinda ya kaini gashi dole na dawo me zaki fada min,Yaushe na hanaka? Yatsuna ya rike ya fara wasa dasu yana mirzasu ina ji har na fara jin wani canji a jikina,Gaba daya naji wani yarrr,shi kuwa har idonsa ya canja,ban san sanda na rungumeshi ba, mun dauki lokaci ya kankame ni a jikinsa sosai Nace ina zuwa na mike tare da nufar kitchen,

Da kallo ya bini kamar zai hadiyeni Sabo da canjin da ya gani a jikina komai nawa kara canjawa nake na kara cikowa,ga kyau dana kara ina sheki, lemukan dana hada na fruits na kawo masa tare da Dambum naman Kaza da nayi na ajiye a gabansa tare da zuba masa lemo a glass cup na bashi a nutse, yana kallona yana sha abinsa ni kuwa shuru na masa tare da dauke kaina har ya gama ya mike tare da da cewa bari nayi wanka naga bakiyi Missing dina ba,shuru nayi masa,yace sabo dake fa na dawo,a raina har ga Allah dadi nake ji marar adadi baya misaltuwa Amma a fili nayi masa banza sai ma turo Lips dana shiga yi.
Mikewa yayi yana murmushi yaja akwatinsa yayi samansa tare da shiga wanka yana tunanin canja masa da nakeyi kwana biyu bayan bai min komai ba.

Su Abbi da Hajja sun sawa Ameer ido a boye ba tare da kowa ya sani ba sun gano cewar karya kawai Ameer yakeyi ashe soyayya yakeyi da Kanwata Meenat,sun gama tabbatarwa ne lokacin da suka Sa CID daya ya dinga bin bayansa har lokacin da ya bisu Kauye ya dawo kuma,tare da Sauran bincikensu,nan take Hajja ta fusata me tsanani haka su Abbi ma,Abbi yace kyale shi zanyi maganinsu gaba daya Har Ameer din,Hajja tace Yaro ya maidani sakara lallai bai san wace ni ba idan na gano cewar mutum ya munafunce ni,wlh wlh nasan Malamaina basa karya Amma dan Iskan yaron nan nasan shine ya lalata komai,kuma ba shakka shi yasa yan fashi suka tare mu kwanaki tare da amshe maganin da muka karbo,Amma kyaleshi zai san ni yayiwa haka kuma sai ya auri Sajeeda.

Abbi yace abu na farko da zamu ladabtar dashi shine mu kwace aikinsa da na bashi a Company na,da mota sannan muce ya bar mana gidan gaba daya,kuma nasan basa shiri da Aayan bare yace zai taimakeshi,Abbi Sani yace ai ko suna shiri da Aayan kasan shi Aayan bai shiga sabgar mu bare zuriarmu,sabo da haka bazai taimakeshi ba.
Bayan sun gama shawara suka nemo Ameer ba mutunci suka masa tatas yana basu hakuri yana Abbi kai fa Mahaifina ne amma kamar baka so na? Abbi yace nafi son uwata da kai dan Iska ajiye min mukullin motar dana sai ma,amma ai da kudina na siya,Mari Hajja ta watsa masa a dalilin wa ka samu kudin aikin ai shi ya baka har ka siyi motar,Abbi yace na kwace aikin ma kuma ka bar gidan nan Banga Amfaninka ba baka bina baka bin uwata har ita zaka yaudara? Abbi bani da kamar ku fa bani da inda yafi nan ina kake so naje? Abbi yace part din nan kasan dai namu ne to kaje wajen ubanka Aayan ya baka inda yafi nan,Umman Ameer ma tana kuka tace kayiwa kanka wlh ba ruwana,kasan dai danginmu kaf talakawa ne baza su iya rike ka ba bare nace kaje can kai ka jawowa kanka kuma kasan Aayan bazai saurareka ba,Abbin America Baban Aayan kaine ka fara masa rashin kunya ko kulaka baya yi ka san da haka,kuma ka sani nan gaba zasu ce ka dawo gida kasan ba a ja dasu dole ka dawo kuma lokacin zasu daura ma aure da Sajeeda.

Ameer takaici ya kamashi yasan dama ko dansu ne na cikinsu basu da imani idan ya musu laifi horo me tsanani suke masa, ya shiga part dinsu ya kwaso kayansa da dan yawa ya fito yana jan trolley dinsa idonsa Jajir ya fito lokacin zan shiga mota zanje Gidan gyaran jiki,tunda na hangoshi nasan ba lfy.

Su Abbi duk sun leko ta saman Bene suna kallonsa yanda zai kare,Sai suka ga na fito da Sauri har wajen Ameer nace Kanina lfy?Ina zaka je haka? Murmushin karfin Hali ya kakalo tare da cewa Abuja Abbi ya aikeni,wlh ban yarda ba Ameer da gani ba lfy kuma nasan bazai wuce a kan kana shigowa part dinmu suka ce ka bar gidan ba nasan tsab zasu horeka ta haka baka ji maganarsu ba,shuru yayi min,nace haka ne ko? a hankali yace ae hakane Abbi ya kwace aikina da motata, to amma ai iya part dinsu zaka bari tunda gidan ba nasu bane su kadai ko?kai ya daga min gwanin tausayi,nace muje ga Bedrooms da yawa a part dinmu sai ka Zaba ma fa ka dawo namu,Anty kina ganin ya Aayan zai yarda? Kuri na nayi nace ai sai abinda nace a gidan nan ka kaddara nawa ne ma,Dariya yayi kawai ya biyo ni su Abbi suna kallo ta sama baki bude.

Muna shiga na bashi Bedroom daya me kyau a kasa Kusa da na su Meenat,yace ki fara fadawa Ya Aayan nace yana Office zan masa waya karka damu,Bari naje gidan gyaran jiki yanzu zan dawo akwai komai a kitchen idan kana so na fita abina na barshi ciki yana Hamdala ga Allah.

Waya nayiwa Aayan na sanar masa komai yace ba Matsala alfarmarki ce Baby baki da damuwa komai kikayi nasan ba matsala I trust u,kuma nasan Ameer baya shirme irin na sauran na yarda dashi bazai yi abinda zai sabawa Shari'a ba da matata ko wata. murmushi nayi nace na gode.






AsmaBaffa
[1/27, 11:26 AM] Asmabaffa: πŸŒ–πŸŒ–πŸŒ–πŸŒ–
πŸŒ–πŸŒ–πŸŒ–πŸŒ–

KASUWANCI NA






96-100






Official









AsmaBaffa









MEENAL AMFAL and MMN ADNAN ths page is for u tnx


MMN AMATULLAH Ina turo gaisuwa me tarin yawa.

REAL MAMAN WALEEDA jinjina da godiya Littafin yana Sweet yanda kika fara Lfy Allah ya baki ikon gamawa lfy tare da mu masu karatu,Allah ya kara Basira.



Kuyi Hakuri Fans yan ASMABAFFA FANS CLUB ne suka ce sun bani hutu na kwana biyu weekend na huta ba laifi na bane su suka jawo muku,kuma ko yau suka ce na huta zan hutaπŸ˜…





Na wuce gidan su Sayyah inda Mum dinta ke koya min yanda ake kula da miji etc sannan ta fara min Gyaran jiki ina shan na tsumi,sai wurin Magrib nayiwa Driver waya yazo daukana muka tafi gida Sayyah sai tsiya take min an kusa gamawa Aayan ya kwashi harka, ina dawowa na Iske Aayan da Ameer suna hira a palo kamar wa da kani na jini da Alama wata muhimmiyar magana sukeyi ta sirri, Ameer yace sannu da zuwa Anty nace yawwa ya hutu,Ya Aayan nace tare da daga masa hannu zan wuce Bedroom ya yafito ni da hannu ina karasawa ya miko ko min kumatu nasan me yake nufi cut nabashi kiss a kumatu na wuce, duk da cewa tunda yayi Tafiya ya dawo bama wani shiri dashi dan Romancing dinma da mukeyi ya daina taba jikina ko da wasa akan nace jikina yake so shine zai nuna min ba jiki na yake so ba,da dare da kyar muke iya bacci Sabo da mun saba idan mun kwanta muna yin abubuwa masu dadi tare da shiga rai,ina ta faman gyaran jiki Amma baya nuna min komai ko irin nayi kyau ko Ya rude a akaina abin yana kona min rai Amma ai ni na jawo.
Wanka nayi tare da shiryawa cikin wasu arnayen kana nan kayan da ya kawo min daga tafiyar da yayi,nayi kyau na fitar asiri sai Hijab na Sa har kasa Sabo da Ameer,Kitchen na shiga na fara shirya mana abincin Dare kamshin girkina ya cika gidan.

Ameer kuwa tuni Aayan ya bashi mota guda fyalleliya yana shiga su Abbi sai mamaki sukeyi,Daddy kusan kullum sai naje na gaisar da shi mun sha hira abinmu in ta bashi labarin mu,Sameera yar daba dukansu tare da yaranta an yanke musu hukuncin a gidan kaso na watanni 8 Sabo da Sameera me kudi ce ta basu cin hanci maimakon na shekaru sai na watanni kuma a hakan ma sunce baza suyi 8 mnths ba wata daya ma za a sakesu Sabo cin hancin da ta basu,kasar nan ba gaskiya a cikinta, Aayan kaji wai 8mnths kacal za suyi nace masa ina tura baki,yace Hmm bana son halaka ne da sai na Bada kudin wanda yafi nata a barta a ciki to Allah ya hana cin hanci da me karba da me bayarwa akwai ranar da Allah zaiyi maganinta gaba daya,Amma in kina so a bayar hakan to? Nace ae a bayar kawai dan ubanta ai akan gaskiya ne,a Bada kudin a tabbatar musu da hukunci me tsanani,Kanwata guda da aka bar min Amana nice kamar Uwarsu fa ai wlh Bazan yarda ba da Ammah na da rai kake jin zata yi alfahari dani Na karasa ina zare masa idanu kamar shine Sameeran,Dariya yayi yace to ke mene tunda Allah yasa ta fito lfy? Bazan yarda ba sam kamar kudin ubana haka nake fada Bazan yarda ba dole na tsaya a tabbatar da gaskiya a sharia ka bani kudin Kasuwanci na sai na biya dashi a tabbatar da anci uban Sameera a gidan kaso,yace za a baki tsigai,nace ae a bani kuma dole muje da kai ka wuce gaba ayi komai da kai,yace an gama Uwata, da kansa yaje ya kashe case din ya biya kudi masu mugun yawa aka canjawa su Sameera shekaru Har uku ba tare da nasan anyi ba,sai da ya dawo ya sanar min,nace kash Uku kacal? Laifin Kidnapping tare da niyyar kisan rai? Uku fa ai wlh ba a ci uban Sameera ba sam baza ta koyi darasi ba,sai kace kasar turai da suke da Imani,a Nigeria muke fa inda ba Imani ba a dauki dan Adam da daraja ba,Dariya ya dinga yi to so kike a kasheta wai ko ba a kashe ta ba nafi so ta tsufa a prison,sai gashinta yayi fari tass lokacin na kusa aurar da yan biyun da zan Haifa nan gaba yan mata,Aayan ya bude baki dama har yan biyu kike so ki Haifa?Nace ae Insha'allah su dinga min girki kullum,Aayan yace sai ki dage ki haifo su ai,Wai Ya Aayan ta ina ake Haihuwa kuwa? Yace ta cibi zaki ga ta bude kawai jariri ya fado,dariya nayi nace ba wahala ashe ma.yana ta min dariya yana tunani Allah yasa ya warke ya yi maganin gaba daya.

Bayan na gama girkin daren nawa Ameer yau bai dawo da wuri ba daga ni sai Aayan muka ci,. 8pm nayi shirin bacci da komai a dakinsa shi kuma naga yana ta cin kwalliya kamar ranar daurin aurensa sai fesa turaruka yake faman yi,nace ina zaka je? Yace wajen yarinyar nan ta Us ce tazo kuma a Hotel ta sauka ba dadi Budurwa kamarta ta zauna a Hotel ai ba mutunci ko kawai zanje dakko ta ne ta zauna damu kafin ta koma.

Kamar ana zuba min ruwan zafi haka naji a zuciyata,ji nayi kamar zanyi hauka gaba daya hankalina baya jikina Sabo da tsananin kishi,nace idan an Isa Allah ya dau raina yau ba sai gobe ba, nace Wayyo Jama'a ga Kwarto,Ameer ya dawo yana kasa yana juyowa ina ta ihun Kwarto a sama,shi dai yasan Aayan yana gida Amma yace bari ya gani kar ko wani ne daban da Sauri ya karaso Saman yace Anty Mufeeda lfy waye,Aayan ne ya fito cikin shirinsa yace kyaleta jeka kuruciyarta ce ta motsa,Ameer yana dariya yace Ya Aayan kaine kenan Kwarton Aayan yace ae fa gani,Ameer ya juya yayi tafiyarsa yana dariya a ransa yace Mufeeda itama irin yan fulanin garinsu ce kenan,Ni dai ko a jikina na fara kuka yana daukan Agogo zai fita na dakko Jambaki da Sauri na bude shi na dinga shafa masa a rigar ta ko ina na jefar da jambakin na kama rigar na dirje lips dina da ita kalar pink jambaki ga wancen Red,yace kinyi ta banzan dole zanje ya bude kofa kenan na jawo rigarsa ta baya,ina ta uban nishi ina Hawaye,hakan baza ta kaini ba na tsuguna na kwaso kafafunsa Amma ko motsi baiyi ba,sai ya biye min ya tsaya don yaga me zanyi masa tunda Hannunsa nake ta ja da karfi,sai ya biyoni tunanina ni nake jansa ta karfi ina nishi na jawoshi har Jikin Bed,ya tsaya kuwa,nace kwanta to dan Allah kaji ina ta kukana,yaki kwanciya na kara mikewa na danna shi kan Bed ta karfi,nan ma gani nake ai karfi nane ya kwanta sharab,yana kokarin mikewa na fada kansa na kwanta daf daf tare da rufa mana bargo tare nace ka dubi girman Allah ka kwanta,Sabo da me? Aljanune suka ce kar na barka ka fita kana fita zaka samu matsala,a lokacin kuma da Aayan yake son fita lokacin Abbi ya barbada masa Wani garin magani a kofar fita wajen part dinmu suna jira ya taka wajen,mu harga Allah bamu san da wannan ba kishi na ne yasa na hanashi fita.

Sai da Abbi Sani ya Kira Aayan a waya wai ya fita yanzu ga abokan Daddy nan sunzo duba Daddy daga Abuja kuma karya yake burinsu kawai suga Aayan ya taka maganin kafin gari ya waye,idan har gari ya waye to ya karye maganin ko an taka bazai yi ba,shine suka rasa yanda zasuyi ya fito suka hada abin da Wai Bakin Daddy sun san yanda yake kaunar Daddy dinsa.

Ta inda Allah ya tsare Aayan sai a ransa yace bari ya tsokaneni yaji shine yace ai wajen wata zaije,ni kuma uwar kishi shine sai da nasan yanda zanyi na hana fitar ta dole,a hankali na kai bakina zan masa kiss yace karki taba ni,why? Kince Sabo da jikinki nake taba ki so na daina taba ki,to Sabo da me kake tabani? Fadi gaskiya naji? Murmushi ya saki sannan yace Do not judge a person by their looks or the things they have. You do not love some one for their appearance or their nice cloths but because of their personality, their thoughts etc u have to Understand kinji?
Shuru nayi ina jin dadi yaci gaba Sometimes people don’t tell you how they truly feel about you but they will always show you so pay attention ki gane ba sai ance kullum ana sonki ba kamar yarinya ku yan mata haka kuke.

Baki na turo tare da cewa ni dai duk da yanzu ina jin turanci kayi min da Hausa yafi shigata sosai kai turancinka na turawa kakeyi duk a harde, murmushi yayi yace Ok ku mata sai kuyi shekara yafi goma tare da mutum yana ta nuna muku yana sonku Amma wai in dai bai ce i love u ba to kawai ba sonku yake ba,wani ma sai ayi ta cewa ai kawana ne,kuma in ka sake kana gani zata auri wani ta barka,sai kace daga baya ina sonki tace me yasa baka fada min da wuri ba bayan duk abubuwan da ka nuna mata na zallar so ne.

Murmushi nayi nace uhm munfi so muji gar da gar, kumatuna yaja da dan karfi sai da nayi kara sannan yace I LOVE YOU......I DO REALLY LOVE YOU,I NEED U,I LOVE EVERYTHING ABT U,U ARE MY SOULMATE BABYNA ya karasa furtawa tare da hade bakinmu waje daya yana sha,Dadin da nake ji ya wuce a fade shi,nan take na kara kankameshi,naji yana nema ya zarce nace bari nayi fitsari,a hankali ya sakeni na shiga toilet,na kulle tare da jingina da jikin kofar ina sauke numfashi da ajiyar zuciya bakina yaki rufuwa Sabo da murna,dama Sabo da kar ya gano ni yasa na gudo toilet Sabo da nayi murnata ni kadai,harda tsalle da murna ina yarfe hannun dadi,sai da na dade ina murna sannan na hade rai na fito daga toilet irin ko a jikina bana murna, gefensa na kwanta ya kalleni tare da saka hannunsa cikin nawa Baki ce komai ba Baby, akan me fa na furta ina yanga,do u love me too? Yatsina fuska nayi tare da cewa sai nayi tunani na duba naga ko ka dace,Murmushi kawai yayi tare lumshe ido ya jawo ni jikinsa Amma Sabo da iya shege sai na ja baya kadan tare da kwace jikina.

Shima bai takura min ba ya kyaleni kawai tare da daukan wayarsa dake uban ruri sunan Abbi

Please Login or Register in order to submit comment