Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kika sani ba,da sauri tace da gaske?yanzu ba gida daya kuke da yan iskan nan ba?nace ae ya canja min gida,to Alhmdllh gani nan zuwa anjima,misalin 5pm sai ga Nawwara ta rafka Sallama,muka amsa yau ma tayi kwalliyarta,muna ta hira ta gaji sai naji tace ina mijinki?nace yayi tafiya,nan take naga ta bata fuska,nace lfy? Dariyar yake tayi lfy alhmdllh kawai tambaya nayi,bari naga gidan naku gaskiya kinyi dace Hajjaju wannan uban gida haka haduwa,Su Ameer suna jinta tana ta zuba surutu,bari na shiga garden nasha kallo,nace bari na nuna miki,a'a jeki ki dafa min me dadi ni zanje da kaina kawai ba sai kin biyo ni ba,Mamaki ya kamani ni da gidana mace ta nuna ta fini saninsa zuwanta na farko kuma,Jeki to kawai na shiga kitchen na kyaleta,Maeesha suna kallonta suna jinta ta fice abinta ta gama Shan kallonta tana zagaye,Ameer daga baya yabi bayanta amma yana fita yaga kallo takeyi tana Selfie abinta tana tsinkar su Guava a lambu sai ya kyaleta ya dawo,ita kuma Meenat sai aka fara fushi dan me Ameer zai bi bayanta,bayan Nawwara ta gama kallonta sai ta dawo taci abincinta muna hira ta gama sa idonta ta Mike tace zata tafi,na rakata har gate na dawo.
Sameera yar daba da yaranta su har yau suna can a kulle basu samu damar fitowa ba,iya cin hancinta ta bayar ta hakura tana gidan kaso ana fafatawa da ita ko a prison Sameera tana cikin shegun matan da suka gagara.

Bayan sati Muna waya da Aayan yace kinji wai sai mun kara sati daya zamu dawo,ni kaina banji dadi ba na matsu Mijina ya dawo,nace amma na kira Daddy a waya fa yace min yana takawa,ae Malamin ne yace wai sai ya karasa mikewa da Saura,ajiyar zuciya na ja nace to ba damuwa Allah ya nuna mana,baki damu dani ba Babyna ko naga ko a jikinki ni ina nan cikin wahalar rashinki,nima na marairaicewa haba Mana karfin Hali da dauriya kawai nakeyi Allah amma bari na kira Ammah idan ta yarda gobe zanzo,da sauri yace yawwa yar albarka tambayeta muji,ina kashe wayar na Kira Ammah,ita kanta ganin Aayan har yar rama yayi yasa tace kizo goben to,Murna kamar me amma dan kar na fadawa Aayan ya sa rai yasa nayi masa shuru nace Ammah bata yarda ba,washe gari cike da zumudi nayi Shiri na barwa Su Meenat komai nasa Driver ya tafi dani Kauyen,Munje lfy kauyen Driver na ajiyeni nace ya juya ya koma,na dauki jakata sai kallona akeyi anga yar gayu ga kyau na shiga gidan Yar Uwar Ammah wato Inna tsohuwa,Ammah ta kalleni tana dama fura tace ai nasan sai kinzo dole,dariya nayi na rungumeta Ina gaisar da Inna tsohuwa,Mufeeda sai yau za azo mana ana can ana cin Amarci wlh kinyi dacen miji yaron kirki sai yabonsa akeyi a garin nan,Inna ai da gani kin San ya iya kiwo ma yanda na koma kalli fa,Dariya mukeyi da Inna tace ai naji kin cika mana gida da kamshi,yana ina ma Wai Inna?Ammah ce ta zuba min duka a baya baki da kunya Mufeeda yaushe kika dawo haka?dariya nayi tare da mikewa na kai jakata dakin Inna nayi Alwala tare da sallah,sai Ammah tace ga ruwa can kije kiyi wanka,Haka na fito nayi wanka da sauri na shafa lotion na sake kaya Atamfa me tsadar gaske Black and Green nayi kyau riga da skert kamar a sace ni,turare na fesa na fito sai mukayi ido biyu da Aayan wanda shugowarsu kenan tare da Yarima,Har zanje na fada jikinsa na tuna su Ammah na wajen,sai kawai na gaida Yarima tare da Aayan,Yarima yace au saida kika biyoshi kenan ko?daki na koma da Sauri sai ko Aayan ya biyo bayana, na juya baya ina murnar ganin mijina sai jinsa nayi ya rungumeni ta baya yana sakar min kiss a wuya ta ko ina,Ajiyar zuciya kawai muke saki,Kamar zai cinyeni haka yake tura kansa ko ina a jikina, yatsu na ya kamo yana kallon yanda nasha zanen lalle ba karamin kyau nayi ba,Dankwali na ya zame yana shafa gashina yana kissing dinsa,kallona yake kamar ya hadiyeni yace kinga kyan da kika kara kuwa?Ni ina nan tunaninki ya hanani sakewa,Bana iya bacci sosai fa,Murmushi nayi ai gani nazo to,amma baki fada min yau zaki zo ba Ashe Ammah ta yarda kizo,Ido na lumshe masa nace zo muje makwaftan Inna wata Tsohuwa ce tukuf sai tsaftar Masifa tana mugun so na ita kadai ce a gidan Masauki me kyau zata bamu a gidanta sai muna kwana a can tare,Ina Daddy fa? Daddy ya Zama dan gari har yana fita majalisa a kauyen nan,yanzu ma yana cikin dattijai can wata bishiya suna hira,Murna Nayi tare da Hamdala,Muryar Ammah naji tace ga abincinku Mufeeda,Yarima yana zaune kusa da Ammah suna ciye ciyensu,Abincin na fita na dakko a tire Fura lafiyayya da kuma Shinkafa da miya da salat,da yake Ammah na nan girki me dadi take shirya musu iri iri ba kamar farkon zuwansu ba da Aayan ke korafi ba dadi,shi yasa Ammah take musu komai da kanta.

A jakata na dauko Soyayyan Nama na zuba mana saman abinci,na kaiwa su Ammah nasu sai Dariyar Kwadayina Aayan ke yi,yace to ai ga nama nan a abincin amma sai kin kara wani,Nace ai wannan suyar tasha maggi,dariya ya shiga yi yace sarkin kwadayi yau zamuyi bacci tare gobe bazan tashi da wuri ba sai tsakar rana,Murmushi nayi masa me matukar kyau,Yau da kaina na bashi abinci har ya koshi ina lallabashi yana ta shagwabarsa,5pm yace bari nayi wanka muje gidan tsohuwar taki daga nan muje yawo,Ruwa na hada masa na kai masa har Toilet,Ammah tana ta jin dadi yanda taga ina kula da mijina gwanin sha'awa,ina kusa da Toilet din ya dinga min magana kasa kasa wai shugo ki min wankan,nace Ammah zasu kama mu yana gama wankan ya koma dakin da suke kwana ya shirya cikin 3qtr da yar riga fara yayi kyau,Na yafa mayafi na da Handbag na bishi muka fita,shi kuwa Yarima Bacci kawai bacci yace zaiyi ya gaji,Hannuna cikin nasa iska na kadawa muna tafiya cike da nishadi tare da jin dadi,sai da muka dan zaga a garin ko ina sai kallonmu akeyi Yace ana kallona shi mu tafi gida,Gidan tsohuwa Iya Makwafta da gidan Inna muka ya da zango,daki ma sai da na zabar mana,ya kasa hakuri dare yayi muje tun da yamma ya takura yana rokona Na bashi ko dan Kucili ne,Iya muka yiwa wayo wai bacci zamuyi Jiki na rawa ya fara sarrafa ni,Nima haka,yana kukan da karfi na toshe masa baki Iya zata gane mu fa,yace ke wannan Sirri ne Allah yana sawa abin Hijab,kin taba ji an kure mata da miji?sai dai a kure kwarto na bashi Amsa muna dariya,Iya muka ji tace ba kyau baccin bayan la'asar ki fito da dare sai kuyi,Nace Iya ba bacci mukeyi ba Wasu yakardu muke dubawa na sirri,Iya tace yawwa yan Albarka a barwa dare sai ayi baccin haka da kin fito ma kin tayani yanka Kubewa,Nace Da Karfi Iya bazan iya aiki ba yau na....Aayan yasa bakinsa cikin nawa Iya taji muryata ta wani shake tace yau ko yar Hirar ma baza kizo muyi ba kin kule daki da mijinki,Iya taji Shuru dadi ya tafi dani ko jinta bana yi tana ta Surutu ba wanda ya kula ta dama ga Iya da surutu bata iya shuru da bakinta,Yau kam Alhmdllh mun gwangwaje juna,munji dadinmu abin ba a cewa komai yau naji dadin da ban taba ji ba,Cike da nishadi yace to wankan ne matsalar,nace sai yanzu ka tuna Gashi har Magrib ta wuce,Fita nayi wajen Iya nace Iya za a samu Ruwan Zafi kafarsa na ciwo zai gasata,Iya ta gane amma sai tace gashi can na dora har ya tafasa cikin katuwar tukunya zai isheku gaba daya,shuru nayi Iya kuma ta wuce dakinta tare da cewa in kin gama abincinku yana kitchen,nace to Iya,Ruwa na hada mana tare muka yi wanka sannan muka tsarkake jikinmu, mun dan ci abincin Iya sannan nace zamuje mu dawo,Gidan Inna muka koma,Ammah tace ina kuka shiga haka?Nace muna gidan Iya,Yarima kuwa tun daga kallon da yakewa Aayan suna dariya yasan me muka je yi,Daddy yana dakinsa masauki tare da Aayan Mukaje na gaisheshi da murna ganin ya dawo lafiyayye,ina ta murna ina masa sannu,Daddy yanzu yawo ko ina,yace Alhmdllh Mufeeda Ashe kema kinzo cike da kunya nace ae Daddy.
Daddy yace Alhmdllh kafin Mu bar garin nan Iyayen Yarima zasu zo tare da dangin mahaifinku za ayi maganar auren Ma'eesha,tunda sun shirya Kansu sai kawai a tsayar da ranar biki,nace Alhmdllh tunda Ammah ta yarda ai ba damuwa,Aayan kuma yayi min zancen Meenat da Ameer ina so na wakilci abin ina tunanin Abbi Baban Ameer da kyar in zasu yarda musamman Hajja,amma idan mun koma gida zan tuntubesu da kaina naji.dadi naji nace to Daddy Allah taimaka,mun dan jima muna hira sannan muka fito.

Bayan kwana biyar Saura kwana biyu mu dawo gida dangin Abbanmu suka zo tare da iyayen Yarima nan aka bada kudin Aure aka sanya rana nan da 4Months,Daddy yace ya wakilci Ameer ai shima Ubansa ne idan mun dawo zai san yanda zaiyi dasu tare da Hajja har su yarda,Nan ba tare da Sanin Ameer da Meenat ba aka sa Rana suma Daddy ya bada kudin auren da komai,Sannan yace kar wanda ya fadawa Meenat da Ameer kawai ace na Ma'eesha da Yarima kawai za ayi.
Ana gama komai suka tafi cikin aminci,muma ranar tafiyarmu na zuwa Driver yazo da katuwar Mota muka musu sallama cike da kewar juna,Sunsha kyauta wurin Daddy musamman Malamin da yayiwa Daddy magani.

Mum dawo da kwana biyu Daddy yaje gida wajen Hajja kowa yasha Mamaki ganin Daddy ras dashi ya shigo da kafafunsa,Yaran gida Su Haneefa murna kawai sukeyi suna kwasar gaisuwa ana masa Congrat,Hajja ma taji dadi danta ya dawo fes,Su Abbi ne ko a jikinsu basu damu ba,an gaisa sunyi Hira,Daddy daga shi sai Su Abbi da Hajja yace Idan baza ku damu ba naga Ameer yana son kanwar matar Aayan suna son juna da sai ayi musu aure,kaga sai a hada ma dana su Khaleel su Ukun,Dafe Kirji Hajja tayi tace Ameer dinne yace yana sonta?Daddy yace ae har Kuka yake min kullum,Hajja dama tana son Ameer a rayuwarta nan tace bana son Matar da zai aura bana kaunar danginsu Amma da ace Ameer yana kuka a kanta gwara a aura masa ita,da Ameer dina ya zauna cikin damuwa gwara ko ma wace a bashi ita,ina Ameer din a nemo min shi karfa ace yana can cikin bakin ciki,Daddy yace ki kwantar da hankalinki Hajja,Abbi yayi tsalle ya dire ba wanda ya isa ya aurawa Dansa dangin Mufeeda dangin jaraba.

Hajja tace wlh baka isa ba ni kaina bana kaunarsu Amma akan Ameer ya shiga damuwa gwara a aura masa ita,tunda Ameer yana so na yarda ko wace ce a bashi farin cikinsa,Abbi zaiyi Magana Hajja tace kana kara magana ban yafe ma ba,kuma duk Wanda yaki yarda ayiwa Ameer dina Aure da wacce yake so ban yafe masa ba duniya da lahira.
Abbi yayi shuru yana Hararar Daddy yace ai sai kaje kuyi komai kuma kwandalata babu a ciki,Daddy yace ai gaba daya yaran nan kowa mata da Maza ko ba raina Aayan zai musu komai.kafin Daddy ya tafi sai da ya bawa Kowa na gidan kyautar makudan kudade musamman Hajja dasu Abbi,Su Mujaheed ranar sunsha Gori da zagi wajen Hajja tayi Kudi.










AsmaBaffa
[2/12, 6:12 PM] Asmabaffa: 🌖🌖🌖🌖
🌖🌖🌖🌖

KASUWANCI NA







117-118







Official







By
AsmaBaffa








Fans ina baku hakuri kwana biyu baku jini ba,Biki mukayi bana gida shi yasa kuka ji shuru.nasan kun jirani sosai ina neman Afwarku akan hakan.






REAL MAMAN WALEEDA wannan page naki ne,Allah kara basira da zakin hannu Novel yana Sweet.








Kwance nake a jikin Aayan ina zuba masa shagwabata a hankali yace ya akayi ne My life yana shafa mazaunai na da suke matukar birgeshi,uhm....ehm....ina shafa kirjinsa naci gaba da ina ina ta kaga ko...just...just...Show...me....love.. murmushi ya saki me kyau tare da cewa nifa kika cewa nine Maye kamar Engine ya akayi kuma, dariya na danyi kadan tare da cewa karya nayi to ai gwara ni da kai amma tunda ma yanga zaka yi min shike nan na fasa ma, dariya yake kasa kasa tare da cewa to shike nan muyi baccinmu naji dadi da kika fasa,Hararar wasa na watsa masa a hankali nace Zaka san ni kayiwa haka ai ba komai,kamar yayi bacci yayi lokacin kuma gaskiya da gaske ina sha'awarsa sosai don gaba daya Bazan iya Control ba,nace na Hakura Amma sai mutsu mutsu nake masa a jiki tare da goga jikina a nasa shi kanshi ya kasa jurewa karfin hali kawai yakeyi,gani nayi ina bata likacina ni da mijina kawai na fara lasar sassan jikinsa musamman wuyansa tare da lips dinsa,Kunne sai kirjinsa tare da cikinsa,yana jina yayi luf yana shan dadinsa bai san sanda yasa Hannayesa ya zare min rigata ba yar ficika da ita,Na gama Zama wet,abinda nake so yasan yana zautar dani ya shiga yi min su nima ina masa shima har muka samu abinda muke so,Jikinsa na shige sosai cike da nishadi,a hankali na dan rada masa Darling u r too sweet,ka iya komai,naji dadin da ban taba ji ba sai can cikin dare sai mu kara yi ko? Shima a hankali yace abinda kike so shi nake so soulmate ai ke kike juyani sai yanda kika ga dama,Murmushin dadi nayi tare da kara narke masa kamar wata jaririya shima biye min yakeyi.

Documents from AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels


Ameer yau yana part dinmu yana zaune saman Dining ya gama cin abinci yana aiki a System dinsa na Office da laptop dinsa Meenat ta shigo dawowarta kenan daga Schl sun fara lecture tuni a BUK agogon dake hannunta me kyau ta kalla taga 5pm Amma yau Ameer har ya dawo mutumin da watarana Sai 6pm yake Barin Office idan yaga dama,Ameer yana kallonta ta gefen ido ita bata wuce ba ta tsaya tana tunani,a hankali ya juyo ya zuba mata idonsa me matukar kyau,Ba karamin kyau ya mata ba,da Sauri ta dauke idonta tare da Sallama tayi a hankali ya amsa mata yana kallonta da Alama a gajiye take,wucewa bedroom tayi da Sauri wanka tayi sharp sharp ta sa kaya marasa nauyi riga da skert English wears ta fito saman Dining ta zauna,Bai kulata ba itama haka,aikinsa yakeyi kawai tana Satar kallonsa tana cin abincinta,shima satar kallonta yake ba tare da ta gane ba,idan ya kalli fuskar System din sai ya dago da idonsa kirr sannan yaci gaba da aikinsa,Itama a nutse take kalleshi ba sai dai ko idan sun hada ido su sakarwa Juna murmushi, Juice ta zuba glass cup ta dan kurba tare da ajiyewa a gefe,Ameer ya dauka ya kurba shima ya mayar mata inda ta ajiye kallonsa tayi shima haka ya kashe mata ido daya dama Ameer ya kware wajen magana da ido,yanzu sai ya zanceki da ido sai dai idan bakya gane yarensa,kallonsa tayi kunya ta rufe ta bata san sanda ta sa tafukan hannayenta ba ta rufe fuskarta tare da mikewa zata bar wajen,Hannunsa taji cikin nata ya dawo da ita shi kuma ya mike tunaninta Tafiya zaiyi ya barta ta sake sai taga kida ma ya kunna abinsa yana yar rawarsa su Zanku Dance tare dasu Shaku shaku dama gashi yaci uban kana nan kaya na yan duniya,Ma'eesha ce ta fito palo basu da labarin ansa bikin Ameer da Meenat tazo kusa da Ameer itama suna ta rawar tare bai san ta zama kanwa kuma suruka ba,itama haka dama sun saba kusan kullum idan suna nishadi sai sun cashe,Meenat dai dariya take sha kawai Sabo da Ameer baya girma maybe ko da dansa ma rawa zaiyi, Su Khaleel ne suka shigo da Sallama Amma kida yasa ko jin Sallamar ba wanda yayi,Sabeer tun daga kofar ma ya fara cashewa Shima,Maeesha kuma taji kunya ta koma ta zauna kamar saliha dama da Ameer suka saba,Mujaheed ne kadai Baya rawa Amma Khaleel ma yana bi da baki yana yi a zaune wakar Olamide latest,Aliyu kuwa harda Handkerchief a hannunsa yana faman sarrafashi yana yi,da Haneefa akazo tare da Meenal dama aikinsu kenan a gida tun farko su kunna kida suyi ta rawa yau tsohon Tsuminsu ya tashi basu ji kunyar uban kowa ba suka dinga yi iri iri,Ameer yana dariya yace Haneefa kin fadi wannan step din Kije Ma'eesha ta koya miki ta fiku iya wannan,Maeesha kamar munafuka tayi kamar bata san ma mene ake nufi ba wai ita saliha, Ameer duk sun zauna suna magana,Sabeer da Aliyu kadai aka bari suna ta rawarsu suna bin Kidan da baki Suna haka sai gamu mun fito tare da Aayan ba karamin kyau muka sha ba kamar kasace mu,Shadda muka Sa me tsadar gaske fara me aiki da bakin zare,nasa dinkin na Maza nawa na mata,kowa ya kallemu sai ya kara kamar wasu wankin engine haka muka fito muna kamshi,dama sun saba ba kunya ce dasu ba bare Aayan da basa jin kunyarsa tun farko basu kashe Kidan ba kuma masu rawar su basu fasa ba da wanda sukeyi a zaune magana baza suyi ba sai hannu suke dago mana wai gaisuwa ce,ina zuwa na kashe Kidan nace haba komai dadin kida shuru ya fishi,Meenat tace gaskiya mu ki kunna rawa muke kallo,Musabiha sukayi da Aayan sannan suka gaisheshi nima haka,Maeesha na Yiwa magana ki kula da kowa zamu fita sai dare zamu dawo,kunyi kyau cewar Meenal,nace tnx Aayan ya sa hannunsa a waist dina yana fada musu su jira baza mu dade ba zamu dawo,ai da Sauri suka ce a dawo lfy,muna fita suka warare uban kida a speaker din katuwar gaske.

Ko da su Khaleel suka zo suna ta fadawa Ameer Ango Amma bai kawo da gaske suke ba tunani yakeyi ko dama wasa kawai sukeyi,tunda shi baiji daga bakin manya ba ko Aayan taya zai yarda, Abinci Ma'eesha ta kawo musu da kayan sha suna ci suna Santi cikin Santi Meenal tace Allah mun gode ma ku duba hakoran engine na Markade har washi ake kaisu kuma baka isa sunyi shekara biyu ba,haka zaka gansu duk karfe ne amma ya Zama Siri Siri ya gama sidewa amma kalli Hakorin dan Adam yayi tauna yana Markade abinci luwai luwai ba tare da karar komai ba,shekara da shekaru bai lalace ko ya daina kaifi ba,amma hakorin Engine kuwa ana zuba Abin Markade zaku ji karar tasa ma ta canja,Ameer yace ai fa gaskiya girki yayi dadi,kuma su hakoran mutum idan kana tauna ko kara basa yi ba kamar engine markade ba kaji kafkafkafkagkaf dariya sukayi gaba daya.
Ni da Aayan kuwa tunda muka fita bamu tsaya ko ina ba sai gidan Ammah mun dade a gidan muna tsare tsare bikin su Meenat,daga nan yace Muje mu gaida su Hajja ban so zuwa ba amma ganin Manyansu ne yasa banyi musu ba muka je,Sajeeda dake gidan ita ta saukemu bamu samu tarba me kyau wurin Hajja dasu Abbi ba dama kuma bamu sa rai ba,bayan mun danyi Jimm kadan muka musu sallama muka fito.

Bayan zuwanmu gidan su Hajja da kwana biyar kawai na wayi gari bana son Aayan ya rabe ni kwata kwata,ni ba tsanarsa nayi ba Amma bana so naje kusa dashi ko yazo kusa dani,idan kuma baya nan zanji kamar na cinyeshi na damu dashi ina ta damunsa da waya Amma da zarar ya dawo gareni to kuma sai naji duniyar tayi min kunci Bazan samu jin dadi ba har sai idan na bar gidan Aayan sai na samu kwanciyar hankali,d a dare ko Bedroom idan na canja sai na koma jin Kukan Dabbobi iri iri,Aayan ya kasa gane kaina gaba daya mum shiga damuwa babu me kwanciyar hankali a cikinmu,Saida muka kwashe wurin sati biyu muna haka ko Bed bamu hadawa da Aayan,tunda ya gane sai ya dan ja baya da lallabani dole sai mun hada shimfida,abin mamaki kawai yake bashi,ina dakin dana warewa kaina ni kadai 9pm Aayan ya shigo yasha wanka,ina ganinsa raina ya baci kawai naji wani bakin ciki marar misali kuma ni ba shi nake jin Haushi ba bansan me ma nake jin haushin ba,Zama yayi kusa dani Na kara daure fuska,kallona kawai yakeyi da mamaki,Hannu na ya riko na fisge abina,ya kara rukowa da Sauri na boye hannuna Ina shirin yin Kuka,a hankali ya zuba min ido cike da so da kauna nima haka shi nake kallo yana bani tausayi Amma na kasa canjawa ban san dalili ba,Muryarsa naji yace Mufeeda a hankali,Ba tare dana kalleshi ba nace Naam muryata tana rawa zanyi kuka nace dan Allah kayi hakuri wlh ni ban san me yake damuna ba,Karki damu na gane na san lallai akwai Matsala tunda komai baki fasa yi min ba,amma me yasa yau baki yi min abinci ba tunda nine bakya so na rabeki,kin san kuma ke zaki bani abinci naci ko? a hankali na daga kaina kayi hakuri jiya ne banyi bacci ba sai da rana ina ta jin Kukan Zaki dasu Damusa a gidan nan sai da Asuba nayi bacci.

Ko gida zaki koma wurin Ammah mu gani bana son ganinki a wannan hali Sweetheart,da Sauri nace na gode Na gode dan Allah ka maidani wurin Ammah anan kamar zuciyata zata fashe haka nake ji,Nima Ina da Meeting a Abuja gobe zan wuce sai nan da 2wks zan dawo naso ace tare zamu tafi sai kiga komai nawa na Abuja Sabo da so nake mu koma can da zama na gaji da nan kullum matsala iri iri, bari na dafa ma ko Indomie ce,no ki barshi naci abinci a waje karki damu,gobe ki shirya na maida ke wurin Ammah yana gama fadar haka ya wuce.

Kuka na saki sosai ina son mijina Amma kuma na rasa me yake damu na,yau ma da kyar na samu bacci sai da Asuba na samu bacci ya kwasheni,da sassafe na tashi bacci a idona na fito zan daura Breakfast,Aayan na gani ya dawo daga Gym room yace kije kiyi baccinki zan siyo mana abinci,Ba tare dana kalleshi ba na juya nace to sai bacci,Shirinsa ya gama yi fes ya jawo Trolley dinsa ya ajiye min take away dina iri iri tare da Short note cewar ya wuce ga Ameer nan zai maidani wurin Ammah karshe yasa I love u My Wife.

Sai 2pm na tashi da sauri nayi wanka tare da Sallah sannan na jawo take away naci na koshi ina tunanin mijina,duk naji gaba daya kamar ma ba ni ba,kamar bani da wani amfani a duniya ba tare da Aayan ba,tunaninsa kawai nakeyi iri iri ina jin da a raina wanda da ace yana kusa dani bazan ji hakan ba,Sai dai ma bacin rai,Shiryawa nayi na kulle komai na kashe kayan Wuta na kira Ameer a waya da katuwar jaka ta na hado kayana,Babu wanda yasan me yake damuna,haka Aayan ma ko Daddy bai sanar masa komai ba duk da cewar Daddy ya tafi U.s zai huta kafin bikin su Meenat zai dawo,Ammah ganina da katuwar Trolley sai da gabanta ya fadi,Su Meenat ma haka,Ameer shi kansa tunani yakeyi ko dai ba lfy ba,Sai da muka gaisa dasu Ammah tace lfy dai ko?murmushin karfin Hali nayi nace lfy lau Ammah ya tafi Abuja ne shine nace ya barni na dawo nan kafin ya dawo shima kuma yace to ba matsala,Ammah ta bata rai shine zaki dawo wajena?ko wacce matar aure ba haka take hakura ta zauna ba,shike nan idan baya nan sai ki bar gidan kema,ke da hakkinki ne kula da gidanki,dukiyarsa da komai nasa sai ki

Please Login or Register in order to submit comment