Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

cikin halan don inji in yi masa fad'a ya daina kada ya sake??"

Dije ta b'ata fuska tare da ciro hannunta duka biyu ta nunawa Hajiya Mamar tace,. "Duba ki gani kowane hannu nawa da kike gani akwai cikinshi d'auke a ciki, gashi ina jin tsoron macizai da yawa idan na haifosu bansan ya zanyi da su ba"

Hajiya Mama ta yi murmushi irin nasu na manya tace "waton hannun naki ya rik'a ko ko ya abun yake ne?"

Dije ta goge hawayenta tace,. "Eh rik'e man ya yi har sau biyu shiyasa Nike jin tsoron ya sake yiman cikin, idan ba haka ba WALLAHI zan yi addu'a in mutu kafin lokacin sai ya san yanda zai yi da macizan idan sun fasa cikina sun fito"

Hajiya Mama ta rik'o hannunta tace,. "Wa ya sanar da ke hakan halan??"

Dije ta goge hawayenta tace,. "Innata"

Hajiya Mama ta yi Yar dariya sannan tace,. "Alhmdllh Innarki ta yi gaskiya sai dai ita baki gano abunda take nufi ba shiyasa, abunda take nufi shine idan har wani daban wanda ba Mjinki ba ya rik'a hannunki to anan ne za ki yi cikin macizan, amman kuma in dai har Mijinki ne ya tab'a hannun anan kam ba wani cikin macizai da zaki yi sai ma lada da zaki samu, ki yi tunani shin lokacin da ya rik'a hannun naki anyi maku aure ne ko kuma kafin ayi?"

Dije cikin sanyin jiki ta ce,. "Bayan anyi addu'ar d'aurin auren ne"

Hajiya Mama tace "Alhmdllh to kinga yanzu gaskiya ta fito saboda haka tashi mu je in rakaki da kaina ki yi kwanciyarki a cen da safe ki zo in baki wani labari"

Dije ta marairece Hajiya Mama ta rik'o hannunta suka nufi d'akin Safwan, Safwan kam yana kwance Kan gadonshi ya zurfafa dogon tunanin abunda yake so ya aiwatar saboda cikar muradin Abokinshi, yana cikin nazarin ne sai gashi ya ji k'wank'wasar d'akin cikin sanyin jiki yace

"Come in!"

Dije ta shigo kanta a duk'e tana zunb'urar baki, ba shiri ya yi zumbur ya mike tare da nunata da d'an yatsa yana fad'in

"Wa ya kawoki d'akin......."

Maganarshi ta mak'ale ne saboda ganin Hajiya Mama a bayanta, cikin sage hannu ya sosa kanshi ya sami gefen gadon ya zauna tare da duk'e kanshi yana feso iska a bakinshi, Hajiya Mama ta zaunar da ita a Kan gadon tace

"Ga Matarka nan sai da safe Ubangiji ALLAH ya baka ikon rik'e 'yar Mutane amana"

Tana k'are maganar ta d'ago fuskar Dije da hawaye suka wanke mata fuska shab'e shab'e tace

"Sai da safe 'yata ALLAH ya baku hak'urin zama da junanku"

Sannan ta fice daga Safwan har Dijen ba wanda ya yi dogon motsi har aka kwashi tsawon lokaci, sannan Dije ta mik'e tsaye zata fita ya yi saurin rik'o hannunta aiko ba shiri jikinta ya d'auki rawa tare da kallon hannun tana k'ok'arin k'wacewa, sai dai kasancewar ba rik'on wasa ya yi mata ba shiyasa bata sami damar k'wace hannun ba, cikin fushi tace

"Wai me yasa kai kake jin dad'in rik'e man hannu ne WALLAHI ka ci sa'a ance ba wani cikin su macizai da zanyi da WALLAHI duk na haifosu kaine na farkon wanda zan sa su ciccije yasin"

Safwan ya mike tsaye tare da sakin hannunta ya d'auko filo ya d'ora akan doguwar kujerar da ke d'akin, sannan ya je ya rufo d'akin ya dawo ya ce da ita

"Kinga wajen kwanciyarki a nan ki kwanta kuma kada ki kuskura inji minsharinki don ba abunda zai hana ni in fiddaki ki kwana waje matuk'ar kika dameni"

Dije ta kalli kujerar ta fisgo filon ta ajiye k'asan carpet d'in ta yi kwanciyarta tana murgud'a Baki, Safwan ya yi saurin kawar da kanshi gefe tare da dafe goshinshi ya yi jarumtar jan k'afafuwanshi ya hau gadonshi ya kwanta, ya d'auki lokaci yana nazari sannan ya yi saurin tashi zaune tare da kiran sunanta a hankali yace

"Khadija!!!"

Dije kam tuni Bacci ya yi awon gaba da ita, ya kirata ya fi sau uku amman bata san ma ya yi ba, jiki a mace ya sauko a hankali ya tallabota tamkar Yar yarinya ya d'orata akan gadon, yana gyara mata kwanciyar ne hular kanta ta sub'uce aiko sai ga himilin gashinta ya hango, don kuwa duk da zirin kitson duka suke a dunkule amman sunyi mata ganwo a baya, don a kallo d'aya za'a gano baiwar gashin da Ubangiji ya wadaceta da shi gashi baki k'irin.

Cike da mamakin ganin gashin nata ya sauko gadon ya kwanta kan kujerar tare da sauke wata ajiyar zuciya, haka ya kwana yanata juye juye saboda tunanin da ya dameshi wanda yasa shi kasa natsuwa.

Dije kam lami lafiya ta yi baccinta duk da zuciyarta cike take da tsoron had'a d'akin da ta yi da shi a matsayinshi na Namiji.

Shiyasa ko da Asuba ta yi ta rigashi tashi ta nufi k'ofar d'akin da nufin ta koma d'akin Hajiya Mama, sai dai ganin d'akin rufe duk da akwai key a jikin k'ofar amman ta kasa yanda zata yi ta bud'e d'akin, don kuwa jawoshi take yi iya k'arfinta amman ko gezau bai yi ba, ganin hakan yasa ta fara bubbuga k'ofar sai ga shi ya tashi firgigit tare da kai kallonshi gareta, cikin d'aga murya yace

"Wai ke me yasa kika cika rashin hankali ne? Me kike son yi ne?"

Ba tare da ta waigo ba tace, "fita zanyi"

Cikin sanyin jiki yace

"Kinyi SALLAH?"

tace "a'a itace zan je inyi"

Ya mike tsaye ya zo bayanta ya tsaya yace,

"Ki jira ki yi SALLAH kafin ki tafin"

Yana kare maganar ya nufi toilet d'inshi ya d'oro arwallah ya fito ya bata umurnin ta je ta yi arwallah a bayin ta yi SALLAH kafin ya dawo masallaci.

Dije kam yana fita itama ta fece zuwa d'akin Hajiya Mama, inda ta taradda ita tana sallahr itama, Kai tsaye ta wuce toilet d'inta ta yi arwallah ta fito ta saka hijabin da Hajiya Mama ta bata ta yi SALLAH da shi jiyan, sannan ta tayar da sallah'rta ba tare da ta tsaya shimfid'a komi ba, tana k'arewa ta fara jero adduointa a bayyane kamar yanda ta saba kullum kamar haka

"ALLAH ka sani Aljannah ka sa Innata da Baffahna da Gambo, Allah ka bani Miji nagari wanda zai dinga siyoman tsiren da Baffah yake siyoman, ALLAH ka sa in zama Likita in dinga yiwa Yaya Usmanu Allura, ALLAH ka sa nice Matar Malam Lawi a Aljannah"

Hajiya Mama da ke zaune tana lazimi ba shiri ta waigo tana kallonta zuciyarta cike da fad'uwar gaba saboda sunan Lawi da ta ji ta ambata.




Akafta😆





D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*


*NA HADIZA D/AUTA*



*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*


*Masha ALLAH Mutanen Dije sannunku da k'ok'arin comments all musamman wad'annan groups d'in:*

*Mata Rahama group*
*D/Auta Novel Fan's*
*Dijen K'arangiya fan's*
*TAURARI fan's 1&2*
*Fadar Ummun fareesa fan's*
*Fatima ce ko zarah fan's*
*Aseela fans group*
*Salmancy fan's group*
*Tamegari Novel fan's*
*K'aramar bazawara fan's*
*Daular Billyn Abdul*
*Kwai cikin k'aya fan's*
*Novels Arena group*
*Maman Maleek group*
*Zauren Uom Mumtaz & Zaratan Mata group*
*Dukanku all ina godiya sosai da dad'ad'an comments dinku kai har ma da wad'anda ban lissafo ba ku sani duk inda kuke HADIZA D/AUTA tana yinku all💋*

*Lamba ta 29*


Cike da mamakin abun Hajiya Mama ta dinga jan carbon tana kallonta har ta kammala jaye sauran 'ya'yan carbin da suka rage ta yi addu'a a gajarce ta shafa ta kalli Dije da har lokacin sai maimaita addu'ar take yi kanta a sama idonta suna kallon rufin d'akin, sai da ta bari ta kammala don kanta sannan tana k'ok'arin yi mata magana Dijen ta janyo jikinta ta k'araso gabanta ta duk'a tare da sunkuyar da kanta k'asa tace

"Ina kwana Hajiya ALLAH ya biya ya saka da gidan Aljannah ALLAH karo maku kud'i ku yi ta cin dad'inku"

Hajiya Mama da ke ta fad'in "Ameen Ameen" addu'ar Dije ta k'arshe tasa ta yi guntun murmushi sannan tace,. "Naji kin fad'i sunan Abokin Safwan Lawi shi miye dangantakarki da shi ne??"

Dije ta yi saurin gyara zamanta ta rufe ido tace,. "Shine ya so ya aureni Babana ya hana kuma bayan yace zai sakani Makaranta har in zama Likita"

Hajiya Mama ta yi shiru sannan tace,. "to ya aka yi shi Safwan aka amince ya aureki??"

Dije ta b'ata fuska tace

"Wai cewa ya yi nace Zan kashe Balan Duduwa bayan Ni WALLAHI ban tab'a cewa haka ba"

Ta k'are maganar cikin zubowar hawaye sannan caraf ta tuno da alk'awalin da Safwan ya yi mata akan cewa in tace itace ta fad'a zai sakata Makaranta, aiko ba shiri ta washe Baki tace

"Laah! Kinga na manta ashe aljanuna ne Suka fad'a ba Ni ba"

Mama ta sake zaro Ido tace,. "Aljanu gareki???"

Dije ta rufe Baki tace

"In fad'a maki gaskiya?"

Mama ta d'aga Kai ba tare da ta sami damar magana ba, Dije ta washe bakinta tace

"Tsakani da ALLAH Ni kam bani da komi amman fa ke kad'ai na fad'awa don ALLAH kar ki fad'awa kowa kinji?"

Hajiya Mama ta yi Yar dariya tace "idan har kina son kar in fad'a to sai kinyi man alk'awali ba zaki sake k'aryar aljanu ba kin amince?"

Ta yi saurin d'aga kai tare da cewa "ai dai ke Zaki sakani Makarantar Likitar ko?"
Hajiya Mama tace "in dai kina so Kuma Mijinki ya amince to Ni zan sakaki da kaina, amman sai in kin daina yawan surutu sannan duk abunda kika gani wanda Baki sani ba ki zo ki tambayeni"

Dije ta ce "WALLAHI Ni nama bari daga yau idan ma kina so ki lissafaman da me da me zan dinga fad'a kullum don bana son inyi abunda zai sa ki fasa sakani Makarantar, bayan kuma ga shi Ni nike son in dinga yiwa Usmanu allura saboda kullum sai ya dakeni ya yi ta man fad'a sai kace shi ya haifeni"

HAJIYA Mama tace "ya kike da shi?"

Tace "yayana ne fa Baki ganshi ba WALLAHI mugu ne Abu kad'an sai ya dakeni don ma Baffah baya bari ya dakeni wani lokaci, amman kinga Innata WALLAHI itama baki ga dukan da take yi man ba ko tausayina bata ji, amman ai ke nasan ba zaki dakeni ba ko???"

Hajiya Mama ta sauke tagumin da ta yi tare sauke wata nannuyar ajiyar zuciya tace

"Ba zan dakeki ba amman idan kin daina rashin jin da kike fa, don ko ita Innar taki don baki barin rashin jin ne yasa ta ke dukanki"

Dije zata yi magana sai ga wata Yar aiki ta k'wank'wasa d'akin da sallamarta, Hajiyar tace ta shigo ta shigo tana yi mata Ina kwana tare da sanar da ita an kammala komi na break fast d'in, ta bata umurnin da zata bata ta fice sai ga su Surry sun shigo kowacensu da Hijabinta har k'asa suna gaidata, fiddo ta zauna tana sunne dariyarta saboda ganin Dijen ya sa ta tuno shirmen da ta yi ta bugawa jiyan, Hajiya Mama tace da su su gayar da Matar yayansu

Fiddo ta zaro Ido tace

"Haba Hajiya ita wannan yarinyar na fa girmeta WALLAHI"

Surayya ta rik'o hannun Dijen tace,. "Matar yayanmu ina kwananki dafatar dai kin tashi lafiya?"

Dije ta washe Baki tace,. "ke kam kina da kirkinki don kinfi wannan mai ido mitsi mitsin"

Fiddo ta maka mata harara zata yi magana sai ga Safwan ya yi sallama, aiko ba shiri suka mik'e dukansu za su fita cikin rawar jiki Hajiya Mama tace

"A'ah fiddo ki k'arasa maganar ai ko don......."

Fiddo ta yi saurin d'ora hannunta a baki tana yiwa Hajiya nuni da hannunta alamun ta yi shiru, yana shigowa suka gayar da shi suka fice da saurinsu ya k'araso ya zauna tare da gayar da Hajiyar.

Dije ta kalleshi tace

"Ina kwana Malam?"

Safwan ya yi banza da ita Hajiya Mama ta yi kamar bata lura ba ta k'wallawa Surry kira sai gata ta shigo cikin fargaba, Hajiyar tace da ita taje da Dije d'akinsu ta yi wanka ta nuna mata duk abunda batasani ba, sannan ta ce ta je ta d'auko mata doguwar rigar da zata saka cikin kayan da tun kafin su zo aka siyo mata su na wuccin gadi, kafin ta zo aga girmanta da yanayinta a siyo mata wasu a d'inka mata dai dai ita.

Surayya ta d'auko rigar ta ja Dijen suka fice Hajiya Mama ta kalli Safwan d'in ta sauke ajiyar zuciya tace,.

"Ya tashin bak'in??"

"Lafiya k'alau yanzu na dubosu har ma naga an Kai masu abun breakfast ai"

Ta yi shiru sannan tace,. "to sai ka yi k'ok'ari cikin kwanan nan a k'arasa gyara abunda ke b'ukatar gyara a gidanka ka kai Matarka a cen ku zauna"

Safwan ya shafa kanshi yace,. "Ta yi zamanta a nan kawai Hajiya Mama in da hali ma ta shiga cikinsu delu mai'aiki kawai su ci gaba da aikin gidan"

Hajiyar ba shiri ta zaro Ido tace,. "Me kake nufi da hakan?"

Ya yi saurin dafe kanshi yace,. "ta zama 'yar aikinki kawai Hajiya don gaskiya Ni ba Zan iya zaman aure da wannan tatsitsiyar yarinyar ba, musamman ma dai a yanda take d'in nan Tiphical Yar k'auyen nan?, Kai ina bazan iya ba gaskiya ai sai ta janyo ayi man dariya, ALLAH na tuba Hajiya me zan tsinta a jikinta Ni Kam!? astagfirullah ALLAH ya rabani da kayan takaici WALLAHI"



Not edited😕

Ayi manage plss 😍😍




Akafta🤣






D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*





*Wannan page kyauta ce gareki sukutum Kanwata ta hannun damata, wadda nije jinki har cikin b'argona, ke ta daban ce a wajena HANNAH MAHMUD SUHANA ina yinki har abadan abade😍*


*Lamba ta 30*



Yana k'are fad'ar maganar ya mik'e tsaye zai fita har ya kai bakin k'ofa zai fita, Hajiya Mama ta kira sunanshi cikin wata muryar da shi kanshi sai da ya ji kiran ya fad'ar masa da gaba, cikin sanyin jiki ya dawo ya zauna tare da b'ata fuska tamkar wanda aka daka yace

"Nasan tambayar da kike son ki yi man Hajiya Mama plss ki yi hak'uri WALLAHI ni ma bansan me ya ja ni na kasa barinta ta auri D'ankauye irinta ba, ni dai abunda kawai na sani taimakonta na yi niyyar yi saboda naga tana son karatu sosai,kuma matuk'ar ta yi aure wannan bak'in k'auyen na su to gurinta ba zai tab'a cika ba, kinji abunda ya sa na aureta Hajiya Mama don nasan Mahaifinta ba zai bani ita haka kawai ba in zo da ita"

HAJIYA Mama tun daga kallon da ya ga tana yi masa ya gano cewa maganarshi bata yi tasiri a wajenta ba, shiyasa ya yi shiru dolenshi zuciyarshi cike da takaicin me ma yasa bai barta ta yi aurenta ba?.

Hajiya Mama ta sauke wata nannuyar ajiyar zuciya sannan tace,. "Baka sonta ka hana Abokinka Lawi ya aureta??? Bayan kasan cewa shi ma ai taimakonta yake son ya yi akan buk'atarta me ya hana ka taimakeshi ya sameta????"

Safwan ya sosa kanshi yace "ai baya garin ne shiyasa da ni ba abunda zai sakani wannan aikin, saboda haka ki barta a nan kawai ta shiga cikin ma'aikatan, su ci gaba da aikinsu kud'inta na wata idan an tara zan dinga aikawa iyayenta"

Hajiya Mama ranta a b'ace tace,. "Safwan ka fita idona in rufe yarinya dai ko kana so ko baka so yanzu ta zama matarka, kuma ko kai baka isa ka kunce shi ba matuk'ar ina raye, kai ko bayan raina ban amince da ka saki yarinyar cen ba matuk'ar ba wani k'wak'k'waran dalili ba"

Safwan ya yi saurin fad'in "haba Mama WALLAHI ni bana son zama da ita da sunan aure ki bari kawai a taimaketa ta yi karatun shikenan kin ga zamu sami ladar, amman a ajiye zancen auren kawai Hajiya Mama yafi gaskiya, don ni Makaranta ma zan koma in k'aro karatu har zuwa lokacin da zan sami wadda nike so in aura"

Ranta ya kai iya k'ololuwar b'aci tace,. "Tashi daga gabana Safwan bana son in sake jin wata magana daga bakinka, ka je kawai akwai ranar da gaskiya zata yi halinta, amman ina son ka fara cukucukun nema mata Makarantar saboda ka samu ka cika alk'awalin da ka d'auka tun wuri"

Safwan ya marairece yace,. "Don Allah Hajiya Mama kiyi hak'uri naga kamar ranki ya b'aci WALLAHI bana son ganin fushinki ke ma kin sani, kada ki bari wannan 'yark'auyen ta shiga tsakanina da ke don ALLAH"

Ta yunk'ura ta mik'e fuskarta a sake tace,. "Ka je ka ji da bak'in in sun kammala in zo mu gaisa amman ina son kafin su tafi ka kai Mahaifinta Gidanka ya ga muhallin 'yarshi"

Safwan ganin yanda yanayinta yake ya sa bai musa ba ya mike ya fice, zuciyarshi cike da tunanin yanda zai yi ya kunce auren cikin ruwan sanyi ba tare da ya b'ata ran Hajiya Mama ba.

Dije kam tana cen Surry tanata shiryata cikin tsanaki duk da taso ta zuba d'ige d'igen kwalliyarta da ta saba amman Surryn ta hanata, sai ko ga Dije ta fito Masha ALLAH da ita saboda daman cen ita mai kyau ce duk da ta kasance bak'ar Mace, amman bak'inta mai kyau ne don bai b'oyewa kyawunta fitowa ba, Dije sai wasar baki take yi tana kallon kanta cikin madubi ta makawa Fiddo harara tace da Surry

"Ashe haka nike da kyau ni ma ban sani ba? Ji rigar nan WALLAHI ta yi man kyau sosai amman ta Makkah ce ko?"

Surry tana 'yar dariya tace, "a'ah a nan garin aka siyeta ba ma ita kad'ai ba ce da wasu ma suna d'akin Hajiya Mama kuma donki kawai aka siyo su, ki yi ta sakawa ke ma ki zama 'yar gayu irin Fiddo"

Dije ta waiga ta kalli Fiddon da ke ta dariyarta tace,

"A'ah bana son in zama irinta irinki na ke son zama har da farinki ma don ALLAH ki sani a injinin da ake maku wanka da shi ni ma ya wankeni tas! in zama fara irinku in na koma garinmu su Ladiyo su kasa gane ni"

Fiddo me zata yi ba fashewa da wata arniyar dariya ba tace,

"to ai ke bak'in da shi aka haifeki mu ko farare ne na asali ta ya zaki had'a kanki da mu? Cab! Ki dai ciji bulo 'yanci tara sai kuma idan har farin shago kike so sai a siyo maki mayukan bleaching da allurori ki yi fess har ma ki fi mu farin tunda ke bak'ar gasar tsiya ce da ke, daga ganin Sarkin fawa sai miya ta yi zak'i to WALLAHI ki sake tunani don mu in banda k'addara ma mi yaya Safwan zai had'ashi da ke har ya kwasoki ya kawo muna cikin gida??"

Dije ta mik'e tsaye tace,. "Kan uban nan amman ina ganin baki san Dijen Baffah ba ne d'iyar Inna Hasiya kanwar Usmanu Mijin Hansai? Cabd'i jam ai billahillazi kada ki bari mu gauraya ni da ke, kin ganni yar tsiton nan ko ta tsaf zan had'a maki jini da majina in sauya maki kamannu cikin k'ank'anin lokaci, don ki gano cewa wacece asalin Dijen Baffah?ke garinmu kaf tsorona ake ji daga abokanaina har yaran garinmu duka, don haka ki daina shiga sabgata idan har kina son ki tsira a wajena"

Fiddo ta taso ta zo gabanta ta tsaya Surry ta yi saurin fad'in,. "WALLAHI kika tab'a 'yar Mutane ba ruwana sai na fad'awa Yaya Safwan"

Dije ta yi mata wani kallon tace,. "Ke wai a nufinki dukana zaki yi? Cabd'i jam to WALLAHI kar ma ki soma tun wuri na baki shawarar gari, idan kuma kinki ji ai ko ba zaki k'i gani ba don ko shi yayan naku yasan halina ku tambayeshi zai gaya maku don bai sha ta dad'i wajena ba shi ma."

Fiddo ta turata baya tace,. "Wai ke me kike tak'ama da shi ne bak'auyiyar banza d'iyar talakawa me kuke da shi a gidanku halan da Yaya Safwan zai k'yaleki ki rena masa wayo bai jibgeki ba??"

Dije ta kalli Surry tace

"Kin dai gani ko? kuma ke ce sheda ko? To duk abunda na yi mata WALLAHI kar ma ace za'a ga laifina, don ko yanzu sai da Baffahna ya yi man wa'azi yace kada in ce zan rama abu in yi hak'uri amman duk da hakan ta koma ba fa zan k'yaleta ba WALLAHI"

Fiddo ta fad'a gado tana cin uban dariya saboda ganin take yi Dijen ba wata ba ce a duka d'aya zata bugeta saboda ganin yanda take 'yar firit gata siririya ba wani kumarin kirki, Surry kam janyo hannunta ta yi suka fito zuwa diny suna karyawa abunsu tana cin dariyar Dije idan ta yi wani abun.

A gefen bak'i matan kuwa Hajiya Mama ta je sunyi Ina kwana sannan suka yi mata godiyar dawainiyar da aka yi da su, ta kawo alkhairi mai yawa ta Basu ta bangaren atamfofi da kud'i, sannan ta nufi inda su Baffah'n suma ta gaisa da su suma ta yi masu alkhairi sosai, Baffahn ya d'auko dunk'ulallin kud'i da zasu Kai dubu d'ari biyu ya mik'awa Hajiyar ya ce a yiwa Dije kayan d'aki da su, saboda ganinta da ya yi mace Mai nagarta da kamalar mutanen kirki a fuskarta.

Hajiya Mama tace ya barsu kawai ya je da su ya kara a kasuwarshi ita zata d'auki nauyin komi, Baffah ya dage shi kam ba zai koma da su ba a matsayinshi na Mahaifinta dole ne ya sauke nauyinta da ALLAH ya d'ora masa nata, sannan Hajiya Mama ta karb'i kud'in ta fito da nufin ta kira Dijen su yi sallama da Mahaifinta.

Aiko ba k'aramin dad'i Baffah ya ji ba da ya ganta ta sha wankanta masha ALLAH a lokaci d'aya ta fara canzawa, cikin jin dad'i ya dinga murmushi yana cewa

"Anya Dijengalata nan gaba ko zan ganeki kuwa? Wannan gayu haka ai sai in za ci canza man Dijen tawa aka yi"

Dije ta rufe fuskarta tana dariya tace,. "Ai Baffah ni ma naji dad'in zuwa gidan nan WALLAHI baka ga yanda Matar gidan take sona ba, sai dai kanwar Malaminmu fa WALLAHI Baffah ta cikani dukan tsiya zan mata sai dai a maidani garinmu"

Baffah ya zaro ido yace,. "Kar ki soma Dije Kar inji kar in gani ki barta ta ci albarkacin Hajiyar tunda kince tana sonki ko?"

Dijen ta d'aga kai tace, "Kuma ma ta ce zata sakani Makaranta fa"

Ya ce "to kin gani don ALLAH kar ki tab'a kowa gidan nan kinji ko Dijeta?, In har kina son in na tafi in siyo maki wata sabuwar akuya ki had'a biyu"

Dije ta washe baki ta ce "ina so Baffah ka siyo man ba zan biyeta ba ka ji?"

Haka suka dinga firarsu yanata d'orata akan hanya a fakaice har su Baba Ali su ka zo da tashar motar da aka d'auko masu har gida, sannan suka yi sallama cikin mutunta juna kowa yana ganin girman d'an uwanshi,

Dije kam da k'yar aka rabata da Baffah'nta saboda Uban kukan da take ci tana fad'in ta fasa karatun ita gida zata koma, don shi ma kanshi Baffahn sai da yayi guntayen hawayen rabuwa da Dijenshi.

Safwan ya yi masu jagora har katafaren gidanshi Baffah sai hamdala ya ke yi ga Ubangiji tare da jinjinawa hikimar Inna Gambo da ta fahimtar da hakan tun kafin ya zo ya ganewa idonshi.

Abokan tafiyarshi ma da matan sai jinjina kai suke yi suna fad'in

"ALLAH mai hikima yanzu wannan shi ne gidan Dije uwar tsiwa to ALLAh ya bada hak'urin zaman"

Safwan ya yi masu sha tara ta arzik'i sannan suka yi sallama da juna ya dawo gida su kuma Direba ya kwaahesu suka miki hanyar komawa gida.



Sauka lafiya😅






Akafta😊








D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*





*Masha ALLAH Mutanen Dije sannunku da k'ok'arin comments all musamman wad'annan groups d'in:*

*Ina farin cikin tayaki murnar cenye gasar da kika yi Ƙanwata waton Balkisu Muhammad Garkuwa (Ummi) ALLAH ya ƙara basira da ɗaukaka kuma ya ƙara dafa maki ga dukkan al'amurranki na yau da kullum tare da mu gaba ɗaya🤲🏻*




*Lamba ta 31*


Mai motar har ƙofar gidan Maigarin ya ajiyesu, kowane zuciyarshi cike da farin cikin nasarar dawowa gida lafiyar da suka yi, kafin kace me ƙofar gidan ta cika maƙil da yara da manya tare da wasu sauran matasan garin da suka rako motar tun daga farkon shigowa har zuwa ƙofar gidan Maigarin, sai kuwwa ake yi ana ta yi masu sannu da zuwa saboda uwar tafiyar da suka shawo.

Ba ƙaramin daɗi Maigarin ya ji ba saboda ganin karamcin da Safwan ya yi masu, don saƙonshi daban na musamman Safwan ya bada akawo mashi, don manyan riguna ne na alfarma waɗanda suka sha aiki tun daga sama har ƙasa kala biyu ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment