Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kallonta ne yasa ta ƙaraso wurinshi tare da hure masa ido da iskan bakinta ta ce

"It's time for lunch my dear"

Ya rungumota jikinshi yana lakuce mata dogon hancinta ya ce

"Ki godewa ALLAH idan har kinsa Malaminki ya zauce a kanki"

Ta yi wani yarr da ido ta ce "rufani ka saya ai sai ka janyo ace wannan ɗaliba ta wuce gona da iri idan har ta zarta sanin malaminta"

Ya sauke mata wani kiss a goshi sannan ya shirya cikin wasu kayanshi da aka ajiye a ɗakin, sannan ya riƙo hannunta suka fito suka nufi sashenshi da yake tsakiyar na su ita da Zee, inda acen ne ma suka kai komi da suka dafa saboda kawai a nunawa Zee cewa su sun san me suke yi, kuma wannan duk yana cikin shawarar Aunty Ummin da take ta baiwa Dijen akan neman zaman lafiyarta ita da abokiyar zamsnta, har zasu zauna kan diny ɗin Dije ta yi saurin ce wa

"Malam plss ka fito da Amarya ta zo mu haɗu ayi lunch don cikina har ya fara kiran ciroma"

Safwan yana ƴar dariya ya ce "sannu acici to jirani in zo minti ɗaya"

Sannan ya bi wata ƙofa ya yi sashen Zee inda ya taradda ita tare da ƴan uwanta biyun da ƙawarta Ruma da suka zo tarbarta, bayan sun sake gaisa ne ya ke cewa da ita ta zo su je aci abincin, ta nuna cewa ita sam bazata je ba ta riga da ta ci wanda su Ruma suka dafa mata, Ruma ta yi mata signal da ido sannan ta miƙe ta biyoshi ranta a haɗe saboda takaicinshi da take ji a zuciyarta tare da munafukar Matarshi a cewarta, wadda ta sha alwashin ko da bala'i sai ta fiddata gidan ta ƙarfin tsiya, tunda har ita zata nunawa kissa da kitifiri don salon kawo mata reni har da kiranta ƙanwarta wai, haka ta yi ta saƙe saƙen zucinta har suka shiga falon nashi, sai dai hango Dijen da ta yi tana ta Saving abinci a plates kala kala yasa ta ji wani bala'a'en kishi ya taso mata, musamman yanda ta ga har da wani sabon wankan ta sake yi don ta nuna mata cewa sunyi wani abu da Safwan ɗin, tunanin hakan yasa ta ja ta tsaya ta ƙi ƙarasawa wajen diny ɗin, ta rungume hannu tana yi mata wani kallo sai wani girgizar jiki take yi saboda a wuya take ƙiris take jira ayi wadda za'a yi.

Safwan ya ja kujera ya zauna Dijen ta janyo masa abinci a gabanshi tana dariya ta kalli Zee ta ce

"Ƙamshin girkina zai yi maki illa Amarya matuƙar baki yi gaggawar ƙarasowa ki ka fara cinshi ba"

Zee ta yi mata wani kallo sama da ƙasa mai cike da reni sannan ta buga wani uban tsaki tace

"Wahainiyarki ta kiyayi ramata tun wuri WALLAhi, ke ce matsiyaciya wadda abinci ya dama saboda haka ki je ki tambayo wacece Zee kafun ki fara yiwa mutane iyayin tsiya, baƙar munafukar banza annamimiya mai shiga tsakanin mata da mijinta, WALLAhi tun kafin in nuna maki wacece Ni ki kama kanki da ni"

Tana ƙare faɗar maganar ta yi masu wani mugun kallo sannan ta buga wani uban tsaki ta juya cikin fushi ta koma inda ta fito, Safwan kam sai cin abincinshi yake yi ba tare da ma ya nuna damuwarshi akan duk abunda ta faɗa ba, ya ɗago fuskarshi ya kalli Dijen ya wayance tare da faɗar

"Sakin bakin na minene? Ko zaki bita ki bata haƙuri ne? Saki jiki ki ci abincinki in har kina son farin cikina, to ki tattara komi ki ajiye a gefe ki fuskanci gabanki tare da Mijinki da ke kusa da ke, saboda haka dawo nan kusa da ni sai mun fi jin daɗin cin abincinmu"

Dije ta yi shiru sannan ta goge guntuwar ƙwallah da ta cika mata ido
ta dawo kujerar da ya ce, yana dariyar da iyakacinta fuska ya ciko spoon da abincin ya nufo bakinta, ta yi masa wani kallo zuciyarta cike da takaici ya girgiza mata kai ta yi saurin haɗiye kukanta.

Haka suka ci abincin kowane zuciya ba daɗi sai dai ba laifi sun ciyar da junansu sosai, sannan ya ja abarshi suka yi ɗakinshi inda ba ɓata lokaci ya fara saitata a hanya, kafin ka ce me shima ya fara rikicewa tare da zaucewa akan Dijenshi, don kuwa tun haɗuwar fatar jikinsu ya gano akwai banbanci tsakaninta da Zee sosai haka ma akwai tazara mai yawa a tsakaninsu, to balle da ya sami sa'ar shigewa fadar gwamnatinta sai ga shi da fasa wani ihun daɗi yana kuwwa, saboda gaba ɗaya ya zauce mata ni'imarta tasa ya kiɗime babu abunda ke fita bakinshi sai ihu da sambatun daɗi.

Zee kam tana cen su Ruma suna lallashinta ne ta jiyo ihunshi, cike da mamaki ta yi saurin dawowa falon sai dai fahimtar abinda yakewa ihun ne yasa ta dafe ƙirji ba shiri, tare da zuwa ƙofar ɗakin tana dukan ƙofar a haukace tana tsine masu dukansu.

Ganin kamar ba su ma san tana yi ba yasa ta bazama aguje ta yi ɗakin ajiyar fetur ta kinkimo jarkar ta fito da gudu kamar wata mahaukaciya, ma'aikatan gidan suka bita da kallo cike da mamaki duk da duhun magriba ya kawo jiki a lokacin.

Tana zuwa ta fara watsa fetur ɗin ta ko'ina cikin falon da ƙofar ɗakin tana surutan faɗin

"Sai na kasheku dukanku yau yan bura'uba azzulumai macuta, ALLAH ya tsine maku gaba ɗayanku WALLAHI yau sai na kasheku"

Ta yi sashenta aguje gudu ta ɗauko ashana su Ruma suka biyota da gudunsu don su ga abunda yake faruwa, tana zuwa ta kunna ashanar cikin bushewar zuciya ta cillata ƙofar ɗakin.







Wayyo ALLAHna😳🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️wuta 🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️wuta ku yo agaji🏃🏻‍♀️.





Akafta😝








D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Rigiji Gabji wani kaya sai Amalii ina gwanayen wasu ga nawa 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻har ga ALLAH ruwan sharhinku akan book ɗin Ƙarangiya yana faranta man rai ba kaɗan ba, haƙiƙa dole inyi alfakhari da ku saboda ku ɗin nawa ne ba ƙarya,ina miƙa ɗinbin godiyata gareki ƴargata Maman Sultan, irin godiyar da baki ba zai taɓa iya zayyanowa ba, alkhairin ALLAH ya kai maki har ƙasar Niger cikin gidan Baban Sultan akan gadonki wanda kike bacci a kuma gefen da kike kwanciya😝😜*


*Lamba ta 64*


A zafafe Ruma ta yi wani tsalle ta cafke ashanar cikin wani firgici da tashin hankalin da ya ziyarceta, don garin cafke ashanar fetur ɗin da ke malale ƙasa tyles ɗin ya jata ta faɗi tim! A ƙasa, amman duk da hakan sai dai ta yiwa ashanar murzar bala'i duk da zafin ƙunar da ya ratsa hannun nata, cikin fushi ta miƙe ta yo kan Zee zata ƙwace ashanar, Zee ta ƙara yin baya cikin bushewar zuciya da ta yi dacen aka janye mata imani a zuciyar don babu abunda take so irin ta ƙonesu da kowa ma da ke gidan har itama kanta, saboda a ganinta hakan ne kawai zata yi ta cire zafin abunda take ji a zuciyarta, Ruma tana girgiza kai cikin ruɗewa tace

"Kar ki aikata abunda zaki zo ki yi danasani daga baya"

Hawaye suna zuba akan fuskar Zee da idonta suka rikiɗe zuwa jajaye saboda tsallar tsagwaron bushewar da zuciyarta ta yi, ta sake kunna wata ashanar hawaye suna zuba akan fuskarta tace

"Matuƙar na barsu da rai bazan taɓa yafewa kaina ba, ya zama dole su ɗanɗani azabar mutuwa dai dai da cin amanar da suka aikata ma....."

Wani mari ne da ya sauka akan fuskarta ne yasa ta yi saurin sakin guntuwar ashanar da ta kusa cenyewa a hannunta, Ruma ta yi saurin taketa da ƙafa ta murje, a zafafe Zee ta waiga domin taga wace mai ƙarfin halin ce ta mareta, yanda ta ga fuskar Surayya da ke tsaye gefenta tana huci yasa ta yi wata gajerar dariya ta ce

"Wow sannu fa ki ce masu mutuwar yau yawa ne da su? To ki jira ke ma saura kaɗan naki ajalin ya iso ku sa da ke"

Tana ƙare maganar ta fiddo wata ƙwarar ashana kafin ta kyasta ta sake jin wani uban naushi da Surayya ta sauke mata a gefen fuskarta, ba shiri ta saki ashanar ƙasa Ruma ta ɗauke ta fice da ashanar cikin sauri, Zee ko ta yi cikin Surayya suka fara kaiwa juna duka, kafin ka ce damben bala'i ya kacame a tsakaninsu ƴan'uwan Zee ɗin su biyu da ke tsaye suna kallon abunda ke faruwa suna rabon faɗan, sai ga Husnah aguje itama kamar wata zakanya ta rufarwa Zee suka yi ta mazgarta ita da Surayya, sai dukanta suke yi kamar ALLAH ya aikosu tun tana ƙoƙarin kare kanta har ta koma laƙwas Husnah ta kwashe mata ƙafafuwa ta faɗi ƙasa ba shiri, Surayya ta yi saurin haye ruwan cikinta suna ta duka duk da ƙoƙarin hanasu da ƴan'uwan Zee suke yi, amman hakan bai hanasu yi mata dukan kawo wuƙa ba.

Safwan da Dijenshi kam basu ma san me ke faruwa ba har sai da Surayya ta kirasu a waya ne take sanarwa da Safwan ɗin abunda Zee take yi don a lokacin itama suna sashen Dijen ne wani ma'aikaci ya zo aguje yake sanar da su abunda ke faruwa, shiyasa hankalin Surayya a tashe ta kira Safwan ɗin saboda zuciyarta ta bata cewa Zee ba alkhairi zata shuka ba, tun yanayin da ta ganta lokacin da suka dawo ta yi sashenta cikin fushi, bayan ta gama kiran Safwan ɗin ta sanar da shi abunda aka faɗa masu ne ta ce da su Husnah su kira Aunty Ummi su sanar da ita kafin ta je ta ga abunda ke faruwa, aiko sai gashi tana zuwa ta ji kalaman da Zee take faɗa Shiyasa bata yi ƙasa a gwiwa ba wajen kai mata hannu.

Ko da Safwan ɗin da Dije suka fito cike da firgici akan fuskarsu, sai ga wani sabon firgicin da ya sake sakasu ruɗewa saboda ganin gaba ɗaya falon warin fetur ne da wani wanda bai ƙasara bin iska ba malale a ƙasa, Safwan ya kai kallonshi inda su Surayya da ke ta jibgar Zee har lokacin, ya yi saurin katsa masu wata uwar tsawa suka zabura cikin firgici daga su har ita Zee ɗin da ke kwance ligya ligya don ta daku ba ƙarya.

Ya ƙasaro wajensu ya kallesu ɗaya bayan ɗaya ya ɗaga murya a fusace ya ce

"Wai me ke faruwa ne wai??"

Zee ta miƙe da ƙyar ta kalleshi cikin wani kallon reni da kumburarren bakinta da suka fashe ta ce

"Ni zaka tambaya don ni ce zan yi ajalinku dukanku ka sani ka ƙara sani dukanku sai na kasheku"

Tana ƙare maganar ta yi sashenta aguje ko wa ya bita da kallo, cikin fushi Safwan ya bita ƴan'uwan Zee ɗin da Ruma suka biyoshi a baya suna bashi haƙuri, Dije ko ta yi wurinsu Surayya tana tambayarsu mafarin abun.

Safwan yana kaiwa sashen nata sai ga ta sun ci karo da ita da sharɓeɓiyar wuƙarta ta nufoshi gadan gadan da nufin ta soka masa ita, ya yi jarumtar riƙe tsinin wuƙar ya fisgeta da ƙarfi wuƙar ta yankeshi sosai amman duk da hakan bai yi ƙasa a gwiwa ba wajen kai mata wani wahalallen mari har sai da taga taurari, sannan ya dinga kai mata duka ta ko'ina kamar wani zaki, itama har da su ƙarfin halin kuwar faɗin sai ta kasheshi duk da uban kashin da take sha, don kuwa da ya yi wani ball da ita har sai da ta kai bango, sannan ya damƙo gashinta ya janyota ƙiii ya fito da ita har gindin Motarshi, sannan ya jefata motar ya saka lock sannan ya faɗa cikin zafin nama ya tada motar ya yi wani uban ribas sannan ya fisgeta da ƙarfin tsiya ya fice, bai zame ko'ina da ita ba sai headquarter'r ƴansanda, kai tsaye ya nemi ganin D.p.o ya damƙa masu ita da hannunshi tare da sanar da su cewa Matarshi ce take son kasheshi, su riƙe ta a hannunsu su yanke mata hukunci dai dai da laifinta, suka karɓeta suka jefata ɗakin ajiya suka kulle sannan suka sanar da shi zasu yi ƙwaƙƙwaran bincike akan case ɗin idan har komi ya kammala ta aikata abunda ake tuhumarta da shi to zasu yanke mata hukunci dai dai da laifinta.

Sannan ya baro wurinsu tare da wasu ƴansanda da za su zo yin bincike akan abunda ya faru, shima ya nufo gida saboda damunshi da kiran da ake ta yi, don yaso zuwa ayi masa kanikancin hannun da ya yanke da shi, amman yanda yake jin zuciyarshi ne yasa ko kiran da ake ta yi masa ɗaya bai ɗaga ba, sai na Hajiyarshi ko shi don baya iya ganin kiran yaƙi ɗauka, sai dai bai iya furta ko kalma ɗaya ba sai "to" kawai da ya faɗa, saboda tsananin ɓaci ran da ya cunkushe masa zuciya.

Ko da suka shiga gidan suka taradda kowa a harabar gidan ana jiran zuwanshi, cike da ruɗewa Aunty Ummi ta nufoshi tana faɗin

"Ba abunda ya sameka ko to Alhmdllh mun godewa ALLAH Hajiyarmu ba abunda ya sameshi"

Ya baiwa ƴansandan dama suka shiga ciki suna ta bincikensu, har wuƙar da galam ɗin fetur duk sai da suka fito da su duka, sannan suka fara yiwa mutane tambaya ɗaya bayan ɗaya, don har su kansu ma'aikatan gidan ba'a barsu ba sai da aka tambayesu suka faɗi abunda suka sani, sannan ƴansandan suka bar gidan tare da rahotannin da suka naɗa a wayoyinsu.

Safwan da ke jikin Motarshi tsaye ya ƙaraso wajen Hajiya Mama yana dafe kai ya zauna kan wani ɗan dakalin da aka zagaye wasu flowers, hannunshi da suka hango da ya yi bala'in walshewa da wuƙa kowa hankalinshi ya tashi, Hajiyarmu ta ƙaraso wajenshi ta ce

"Garin ya ya haka ta faru??"

Ya yi shiru sannan ya yarfa hannu saboda jinin da ke ɗiga har lokacin ya ce

"Ni ma bansan abunda yake faruwa ba har sai da Surayya ta sanar da ni"

Hajiya Mama cikin damuwa ta ce

"Ina ita Zainab ɗin?"

Ya yi shiru sannan ya ce, "tana hannun ƴansandan"

Ko wa ya yi shiru yana nazarin abun a ranshi sannan Hajiyar ta ce

"To ka je a yi maka dressing ɗin hannun sannan ka dawo muna jiranka"

Safwan ya miƙe zuciyarshi kamar zata fashe ya kalli su Ruma da ke tsaye dukansu sun sha jinin jikinsu ya ce

"Kada in dawo in taradda ku cikin gidana"

Sannan ya ja Motarshi ya fice aguje, su Hajiya Mama suka yi sashen Dijen suka zauna, inda su ke ta lallahin Dijen da ke ta kuka saboda tunda ta ji abunda Zee ta ce a bakin Surayya hankalinta ya tashi ta fara kuka, sai ga shi kuma ta hango Safwan ɗin yana jan Zee a ƙasa hannunshi sai zubar jini yake yi, akan hakan ta sake ruɗewa tana ta kuka don jin take yi kamar ma ta bar masu gidansu ta koma garinsu tun kafin a kasheta ga banza, don ganin ƴansandan ma yasa ta ji wani tsoro ya sake kamata.

Ko da Safwan ya dawo an ɗaure masa hannu da bandeji bayan an ɗinke masa ƙatuwar yankuwar da ya yi, ya shigo ya zauna idonshi akan Dijenshi da ke sharar ƙwallah idonta sun yi ja saboda kukan da ta sha, cikin sanyin jiki ya ce

"To ke me kike wa kuka kuma yanzu?"

Aunty Ummi ta ce "dole ta yi kuka tunda bata taɓa ganin irin wannan bala'i ba a rayuwarta, wannan matar ƙaddara ai babu mai fatar ALLAH ya haɗashi da ita bale ta zowa mutum a matsayin kishiya"

Ta ƙare maganar cikin yin wani kalar mere kamar wata yarinya, Hajiya Mama ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce

"Yanzu dai abunda ya faru ya riga da ya faru fatanmu kawai ALLAH ya taƙaita wahala kuma ya tsare gaba"

Safwan ya dafe kanshi da ke ta sara masa ya ce, "ai kuma yanzu sai dai ta bi wasu shanun don nikam WALLAhi saki uku ringis zan dannawa shegiya, don bana fatar ko a hanya in sake haɗuwa da ita bale ta sake zama gidana"

Surayya ta yi saurin faɗin, "hukuncin da ya dace ita kenan baƙar arniya mai zuciyar kafuran farko"

Hajiya Mama ta maka mata wata harara Surayya ta ce,. "Haba Hajiyarmu yanzu da ace ta kashe muna su ai da mu ta bari da shiga uku, don duk hukuncin da za'a yi mata ba lalle ne ya zama dai dai da abunda ta aikata ba"

A harzuƙe Husnah tace "Ni WALLAHI na ma so mun illata shegiya kafin Auncle ya zo"

Aunty Ummi ta ce "ai WALLAHI da ace ina kusa sai na ja shegiya na damalmala kanta cikin fetur ɗin sannan in fito da ita tsakar gidan nan in ƙyasta mata ashanar sai ta ci wutar ƴar shegiya"

Hajiyarmu ta yi saurin faɗin "to kenan da ke da ita duk hukuncinku ɗaya in har kika aika wannan shirmen, yanzu dai abu ɗaya ya rage ka kira Mahaifinta ka sanar da shi abunda ke faruwa"

Safwan ya ɓata fuska ya ce "Ƴan'uwanta da aka yi a gabansu miye amfaninsu da ba zasu sanar da su abunda yake faruwa ba?"

Hajiyarmu ta ɓata fuska ta ce, "kaine ke da haƙƙin sanar da su ba wasu ba, saboda haka ka kirasu yanzu ka sanar da su abunda ke faruwa"

Safwan cike da jin haushi ya ɗaga waya ya kira Daddyn Zee ba tare da jiran komi ba ya ce

"Na saki Zee saki biyu a bisa sunnah da in ana yin ɗari duk sai nayi mata, don haka ayi gaggawar zuwa a kwashe mani tarkacen kayanta cikin gidana"







To fa 😳😳😳kai ko Malam Safwanu saki haka da sauri 😔









Akafta🙌🏻







D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Am sorry fo you my FANS😊 jiya kun ji Ni shiru ko? To ku yi haƙuri yanzu gani tare da ku😸fatana kawai ku biyoni mu je🏃🏻‍♀️*


*Lamba ta 65*



Yana ƙare maganar ya kashe wayar cikin fushi ya miƙe zai bar falon Hajiya Mama ta kira sunanshi a hankali cikin wata murya mai cike da alhini, ba shiri ya waigo ta ce da shi ya dawo ya zauna, sannan ya dawo ya zauna sai wani cika yake yi alamun a wuya ya ke sosai, Hajiya Mama ta sake kiran sunanshi ta ce

"Abunda na ce ka aikata kenan? Me yasa kai a koda yaushe baka iya dafa mutum cikin ruwan sanyi ba?, Nasan Zainab bata kyauta ba amman shi mahaifinta laifin me ya yi da har zaka yi masa wannan cin fuskar?, Yanzu idan kai ne a matsayinshi wani ya kiraka ya saki ƴarka irin haka wane irin hali kake tsammanin zaka shiga?, To bari ka ji banji daɗin abunda ka aikata ba, don Mahaifinta komi lalacewarshi ya gama maka komi tunda har ya ɗauki ɗiyarshi ya baka, don haka ka sani laifin wani baya shafuwar wani, saboda shi mutum daraja gareshi mussaman wanda ya ke sama da kai irin haka, saboda haka ka dinga kwatanta adalci akan duk wanda mu'amala ta haɗaka da shi, don da ace ka yi cuta gara ace kai ne aka cuta, don yanzu wannan abun da ka yi masa har abada ba zai taɓa mantawa ba, tabbas kam ƴarshi bata yi abunda ya dace ba amman ka sani kai ka yi abunda ya fi wanda ta aikata muni"

Safwan da su Aunty Ummi Suka kallota cikin mamaki ta ce

"Eh tabbas haka ne don ita da makami ta yi niyya kasheka cikin fushi, kai kuka ka yi amfani da dafin harshe ka caki ubanta da mummunar maganar da dole ne ta daki zuciyarshi, ko baki ji ance dafin harshe ya fi na takobi zafi ba?, to bari ka ji yanzu wannan raunin da ta ji maka a hannu zai iya warkewa har wurin ya koma tamkar ma ba'a yi, amman dafin abunda ka yi wa mahaifinta ka sani har abada ba zai taɓa goguwa a cikin zuciyarshi ba, saboda haka ka daina yanke hukunci cikin fushi a koda yaushe idan har kasan abunda zaka faɗa ba mai kyau bane, to ka yi ƙoƙarin danne zuciyarka ka yi shiru saboda faɗar Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama da ya ce(falyaƙul khairan auliyasmut, ka faɗi alkhairi ko ka yi shiru) saboda shi baki dafi ne da shi wanda idan aka yi maka wata mummunar magana har abada ba zaka taɓa mantawa da ita ba"

Safwan ya shafo kanshi da hannunshi mai lafiya ya ce "na yi kuskure Hajiyarmu kuma Insha ALLAH bazan sake maimaita kwatankwacin hakan ba...."

Kiran wayar Safwan ce ta katse maganar da yake yi, cikin sauri ya duba mai kiran sai ga shi da kallo Hajiyar cikin sauri ya ce

"Mahaifinta ne"

Hajiyarmu ta ce

"Ka ɗauka ka ji to"

Ya ɗaga ba tare da ya ce ƙanzil ba ya saka hands free, sai ga muryar Mahaifiyar Zee cikin wayar tar! tar! tana kuka tana faɗin

"Me ke faruwa ne? Me ya sami Zainab ɗin ne? ga Daddynta nan ya faɗi rai a hannun ALLAH sai sunanta ya ke kira, me ke faruwa ne na ce?"

Ta ƙare maganar cikin kuka tare da ɗaga murya Hajiya Mama ta yi masa nuni da hannu alamun ya sanar da ita, cikin sanyin jiki ya fayyace mata abunda ya faru a dunƙule, mahaifiyarta ta fasa wata uwar ƙara tare da cewa

"Innalilahi wa'Inna ilairraji'un, Allahumma ajirni fi musibati wa alkhalifni khairun minha"

Sannan ta kashe wayar gaba ɗaya jikin kowa ya yi sanyi, ran Hajiyar a matuƙar ɓace cikin tagumi ta ce "ka ga abunda nike sanar da kai ko? To idan har ka yi sanadin mutuwarshi sai kasan abunda zaka faɗawa ALLAH idan kun je lahira"

Hajiyar Mama ta miƙe cikin fushi zata fita ya yi saurin shan gabanta yana bata haƙuri tare da su Aunty Ummi, Dije ta duƙa ƙasa ta riƙo leɓen zanenta cikin kuka ta ce

"Ki yi haƙuri Hajiyarmu kada ki fushi da Malam don ALLAH ki yafe masa"

Hajiyar ta duƙa ta ɗagota tare da share mata hawayen da suke ta zuba a idonta ta ce, "komi ya wuce na haƙura insha ALLAHu amman matuƙar yana son in yafe masa to sai ya furta ya mayar da Zainab a matsayin matarshi"

Dije da su Aunty Ummi da shi kanshi suka zaro ido waje saboda bugawar da zuciyoyinsu suka yi, cikin tabbatarwa ta sake ce wa "haka na ce kuma haka ni ke son ayi don hakan kawai zai rage raɗadin baƙin cikin abunda zai faru ga mahaifinta, wanda ko kaɗan bani fatar ace kai ne ka yi silar mutuwarshi da hannunka, duk da bana fatar hakan amman ka sani duk ya mutu a sanadin wautarka to baka yi wa kanka adalci ba"

Safwan da su Aunty Suka yi shiru kowa da nazarin da yake yi a zuciyarshi, Dije ta je gabanshi tare da haɗa hannuwa biyu alamun roƙo ta ce

"Don Allah Malam ka dawo da ita a matsayin matarka plss"

Cikin tsananin ɓacin rai ya ce "na dawo da ita da sauran igiya ɗayar da ta rage a tsakaninmu, amman WALLAhi bazan taɓa yafe mata abunda ta aikata man ba"

Yana ƙare faɗar hakan ya bar wajen cikin ƙunar zuciya, Hajiyar ma ta ce da su Aunty Ummi su zo su tafi gida, kasancewar isha ma ta wuce kuma ga shi wasu cikinsu ko SALLAHr magrib ma ba su yi ba, har bakin motar da ta kawosu Surayya da Dije suka rakasu, bayan sun tafi ne itama Surayya ta kira Mijinta ya zo ya ɗauketa, Dije ta nufi ɗakinta ta yi sallolinta sannan ta nufo ɗakinshi da ke sashenta, inda ta taraddashi zaune akan carpet fuskar haɗe ya yi shiru alamun ya faɗa cikin dogon nazari, ta sami gefenshi ta zauna tare da riƙo hannunshi mai yankuwa ta ɗora saman jikinta, cikin sanyin murya ta ce

"Don Allah ka daina wannan damuwar komi da ka ganshi daman cen rubuce yake mune ba mu sani ba, sai abun ya faru ne mu ke ganinshi tamkar sabon abu, don ALLAH Malam ka daina wannan damuwar WALLAhi bana son ganinta a fuskarka ni dai"

Safwan ya kallota da jajayen idonshi da suka rine saboda tsabar ɓacin rai ya ce "Ta ya bazan yi damuwa ba? Bayan Hajiyarmu ta sani mayar da wannan matar bala'i cikin rayuwarmu,yanzu ta sami damar yin haka ina ga abunda zata aikata a gaba? Hajiyarmu me yasa ta kasa gano Zainab ba alkhairi ce ga rayuwarmu ba? To Wallahi ko da ace zata dawo ɗin to
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment