Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ɗaya suka fice falon, aiko na biyo bayansu sai naga sun nufi sashen Zee, na bisu cike da mamaki a raina nace

"Lalle so duk so ne amman son kai ya fi yau ko ga shi na gani da idona"

Ina biye da su har falon Zee inda na hangota cikin shiga ta alfarma tana ta hidima da ƴan'uwanta da suka zo daga Gombe, abun mamaki Asiya naga ta manna da gudu ta rungumeta tana ihun faɗin

"wayyo Aunty Zee Ina yinki WALLAhi"

ZEE tana dariya ta bi Asiya da kallo ta ce "Ni ma haka ƙanwata saukar yaushe?'"

Asiya ta washe baki ta ce "mun jima munata neman inda zamu ganki tare Ni ke da ƴan'uwana suma masoyanki ne na haƙika kamar Ni, don lokacin da wannan ƙaddarar ta sameki mune muka yi ruwa kuka yi tsaki akan kare maki martabarki agun abokan adawa"

Zee ta sake rungume Asiya cike da jin daɗin maganar tata ta janyo hannunta ta ce

"Oya ku zo mu je masaukinku na daban ne ai"

Ɗiyar ɗakina da Daughter Rufaida Suka biyo bayansu suna dariya, aiko sunga tarba kuma sun ga gata don kuwa Zee komi nata na tarbon baƙint ta yi abunta daban bayan na gidan.

Shiyasa suka baje suka kwashi Gara abunsu ina yi ina haɗiyar yawu saboda ina jin tsoron in fito su gano leƙen asirinsu na zo yi.

Haka aka yi taro cikin farin ciki da annushuwa kowa ya tafi yana murna saboda anyi masu komi a wadace babu ƙwange hannu a cikin lamarin ko kaɗan.

Taro ya watse lafiya kowa ya nufi gidajenshi anata yabawa sannan da yi wa jariri da Mahaifiyarshi addu'a, da yi masu fatar ƙarin buɗi mai alkhairi ko don wasu su amfana.

Don yan garinsu Dije daren da zasu koma gida ne Safwan ya cikasu da abun alkhairinshi, suka ruɗe sai zuba godiya suke yi, haka ma ZEE ta yi masu alkhairi dai dai iyawarta suna ta godiya da yi masu addu'ar zaman lafiya ga junansu.

Dije da su Ladiyo suna ɗakinta ana firar bankwana Ladiyo ta kalli Dije cike da urgewa ta ce

"Ai ke Dije yanzu ba abunda ya rage maki a duniyar nan illah ki cika da imani ki je lahira ki sami aljannah, don WALLAhi duk abunda ake yi ALLAH ya yi maki saboda haka ki godewa ALLAH"

Dije ta yi dariya ta riƙo hannunta ta ce "Alhmdllh K'awata wannan kalmar itace kalmar da kullum nake yawan faɗa a bakina, saboda Ni kaina sanan ya yi man baiwar da ba kowa ya yi wa irinta ba"

Jummala ta ce ", TABBAS ke ƴar baiwa ce a cikin mata don ga shi ko mu yanzu ta sanadinki mun fara zama ƴaƴan baiwar, don kuɗin da kika aiko muna kwanaki wallahi Ni dai sun yi man tsanin alkhairi Ni da Garbatina, don kuwa yanzu haka birni yake zuwa yana siyar da fitullu kala kala na zamani masu batur da masu aiki da zuƙar nefa, kamar da wasa ya fara kasuwancin sai ga shi yanzu kullum abu sai haɓaka ya ke yi, WALLAhi mun gode sosai mukam"

Lanti da ta yi tagumi ta ce "ai Ni bance komi ba Dije don WALLAhi har zaucewa na so yi lokacin da Usmanu ya kawo man su har gida ya ce in jiki wai mu ja jari, haka naga abun kamar almara WALLAHI"

Dije cike da mamaki ta kalli Hansai saboda neman ƙarin bayani don ita bata ma san kan zancen ba, kuma bata da masaniyar komi akai, Hansai ta yi dariya ta ce

"Habibynki ne ya turowa wani saƙon ya baiwa Baban yaron nan ya kawo muna ya ce in ji ki abamu mu abokanki"

Dije ta ji wata ƙwallah ta sauko mata cike da jin ƙara ƙaunar mijin nata, saboda ita ko kaɗan bai sanar da ita anyi hakan ba sai yanzu da ta ji a bakunansu, Mune ta sauke ajiyar zuciya ta ce

"Dole ki yi kuka don farin ciki ya yi a rayuwa, ALLAH ya ƙara buɗe maku hanyoyin samu ta ko'ina ko don mu na kusa da ku mu amfana"

Gaba ɗaya aka ce "Ameen"

Dije ta share hawayenta tana dariya ta ce "Mune naga yanzu kin rage surutu mi ye sirrin halan?"

Mune ta yi dariya ta ce

"Hmmmmmmmm ai ke dai in ana SALLAH ba'a magana, don kuwa akan halin har sakina ma Ummaru ya yi na dawo gida, saboda wani faɗa da na haɗa tsakanin matan yayan Ummaru, duk da a zahiri Ni iya gaskiyata ce na faɗi, amman duk wanda ya ji zai ɗauka cewa munafucci ne"

Lanti tana dariya ta ce

"To da gaskiya ta bayyana ai ALLAH ya wankeki ko? Kuma ki godewa ALLAH tunda har hakan ya zamo sanadin shiriyarki kika daina yawan faɗi ba'a tambayeki ba"

Dije ta kalli Jummala ta ce "me ya faru halan"

Ladiyo ta fashe da dariya ta ce "ki tambayi ƴar gidan taki mana sai ta fi iya bada labarin yanda ake so"


Mune ta cire taguminta ta ce "Matan yayan Ummaru ne suke ta faɗan kishi kullum a tsakaninsu, shine ranar na ji ɗaya tana faɗawa wata abokiyarta cewa zata sakawa abokiyar zaman shinkafar ɓera a abinci ta mutu, to shine Ni kuma na ji tsoro na je na sanarwa wadda ake so akashen, aiko ta sanarwa da mijinsu sai ko ga shi wadda ta ci alwashin ta kawo mata abinci ta ce bazata ci ita sai ta ci ta ƙi ci, daman an shirya hakan mijin ma ya kafe akan dole sai taci abincin ta ƙi ci, rigima ta rikice gida ya cika da mutane ƙarshe dai abu har gaban Maigari, aka baiwa kyanwa ta ci bata yi komi ba itama aka tilastata dole sai da ta ci, abun mamaki ba abunda ta yi shine aka fara kuka ta ce daman na ce sai na ƙalla mata sharri, nan mutane suka yi ta tsine mani ana cewa da ni daman cen Ni Munafuka ce, gashi yanzu zan haɗa rigima don kawai na tsani ɗayar, ke a taƙaice dai akan hakan Ummaru ya sakeni na koma gida sai daga baya da gaskiya ta fito aka gano makirci ne ta ƙulla ashe ta ji lokacin da nike faɗawa waccen ɗin, shine ta liƙaman sharri sai cikin ikon ALLAH bayan bana gidan faɗa ya haɗasu ta ɗauko taɓarya ta ce sai ta kashe kishiyar, da komi ya lafa aka gano gaskiya don ta yi iƙirari da bakinta akan cewa itace ta faɗa na ji a lokacin, shine fa ya dawo da ni gidanshi bayan an ja kunnena da faɗi ba'a tambayeka ba, to tun daga haka na kame bakina ba ruwana da faɗin abunda bai shafeni ba, kinji mafarin shiriyata, yanzu ko a gabana aka yi abu WALLAhi ba abunda ya dameni bale in fad'a"


Dije tana dariya ta ce "Alhmdllh ƙawata baki dadi wallahi yanzu ki ce ko a gabanki mu yi kashinmu ba zaki faɗa ba? "

Mune tana dariya ta ce "tabbas Ni ce ma zan sakayaku in yi maku labule don kar a ganku"

Gaba ɗaya aka saka dariya, haka suka yi ta tuno baya suna mayar da zance suna dariya, sun ɗauki lokaci sunata firarsu har dare ya raba sannan suka je suka kwanta.

Tunda sassafe suka yi sallama da kowa suka kama hanyar zuwa inda suka fito, da nufin sati yana zagayowa itama zata bi su ta je wankan gida a garinsu .


Haka ko aka yi Satin yana zuwa Fiddo da Zee da wata dattijuwaar da zata dinga taimakonta suka rakata zuwa garinsu ta jirgin sama da zai rage masu hanya zuwa sannan su ci gaba da motar, saboda kawai Yaron Safwan da ko ƙuda baya son su hau kanshi bale wahalar doguwar tafiya irin wannan.

Ko da Jirgin ya saukesu motar tana jiransu saboda tuni ta taso sannan su daga baya suka biyo hanya, kasancewar an samu ci gaba sosai a babban birninsu Dijen har cikin ƙauyensu, shi yasa basu sha wata wahala ba suka isa ƙauyen ƙiriu garinsu Dijen Baffah.

Mamaki bai kashe Dijen ba har sai da suka isa ƙofar gidan nasu taga kamar ma ba nan ne ba, don kuwa gida ne na alfarma Safwan ya ƙyanƙyara masu saboda kawai ya basu tukuicin faranta masan da ƴarsu take yi a kullum, ga kuma hasken solar ta ko'ina tun daga ƙofar gidan har cikin gidan fes yake masha ALLAH tare da sabon fentiin da ya ƙara fito da kyawon gidan.

Baki sake Dije take kallon gidan don ko kula da masu yi mata sannu da zuwa bata yi ba har suka isa cikin gidan ita da su Zee, Baki bud'e ta ƙura wa inna ido cikin shiga mai kyau ta buɗe wata doguwar freezer tana fito da wasu gorunan ruwa tana saka wasu, bakinta washe ta ke faɗin

"Sannunku da zuwa mutanen Yola sannu da zuwa"

Fiddo kanta mamaki abun ya bata saboda tasan yanda gidan ya ke acen baya, Zee kam wasar bakinta kawai ta ke yi har suka shiga falon Inna da ya ƙawatu da kujeru irin na ƴan gayu, Suka zazzauna Dije kam ƙurya ta shige saboda kukan da ya zo mata kuma ba zata iya danneshi ba, haka ma bata son ta yi shi a gaban Zee ta fahimci wani abu.

Inna ta fara jera masu abinci kala kala da ruwa da lemuka tana faɗin "ku sha ruwa kun kwaso hanya kam"

Fiddo ta karɓi Sayyid hannun Zee ta ce

"Inna ba zan baki yarona ba tunda har baki yi murna da zuwanshi ba"

Inna ta rufe Baki tana dariya ta ce "ku yi ta kaya Ni mai Malam me zan yi da wannan mijin cikin zane komai sai anyi masa?"

ZEE ta ɗauki ruwa tana tsiyayawa a kofi tace "ai dai inna shi sabon miji daban yake tsoho, idan kuma kika bari ya yi fushi ya ce ya fasa kuma shikenan sai mu nemo masa wasu matan"

Shigowar Hansai cikin tsantsar farin ciki yasa Inna Bata Sami damar mayar masu da amsa ba, Hansai ta karɓe yaron tana ihun faɗin

"Wayyo daɗi ɗanmu ya zama ɗan turawa Inna duba ki gani"

Inna ta ƙarɓeshi da bisimillah tana faɗin

"Waɗannan uwayen dai akwai kuri, to ALLAH yasa kafin ku haifu wasu sun rigaku haifuwar"

Ta ƙare maganar tare da zaunawa tana gyara masa hannun rigarshi ta kayan sanyin da ke jikinshi ya sauko ƙasa ya rufe tafinshi, Zee tana dariya ta ce

"Mu dai na mu muka sani Inna don zamu iya bugun ƙirji mu ce namu ya fi na kowa"

Inna tana dariya ta ɗagashi sama tana yin miƙa yana wani botsarewa alamun ya ji daɗin hakan, Inna ta kalli Fiddo ta ce

"Ku ne da yaron amman baku iya renon ba, to ku biya kawai a tayaku renonshi kawai"

Dattijuwaar da suka zo da ita tana dariya ta ce "Mutum da Matarshi har sai an biya? To a biyosu bashi idan ya girma sai ya biya da kanshi"

Sai ga sallamar Baffah ya shigo Dije da ke ƙuryar ɗaki tana kuka Hansai na lallashinta Muryar Baffah ta sa ta fito da saurinta ta taryeshi cike da jin daɗin ganinshi ta durƙusa tana gayar da shi, cike tsantsan farin ciki ya ke amsawa sannan ya tsaya bakin ƙofar falon ya gaisa da su Zee, sannan ya yi masu sannu da zuwa tare da tambayar mutanen gida, bayan sun ƙare gaisawar ne ya yi ɗakinshi Dije ta biyoshi zuciyarta cike tsantsan farin cikin ganin yanda yayi ƙiba hankalinshi a kwance, ta zauna tana wasa da yan yatsunta suka sake gaisawa a tsanake sannan ya kalleta yana ƴar dariya ya ce

"Wa ya taɓa man Dijeta daga zuwanta?"

Dije ta share hawayenta tana dariya ta ce "naga gida ya yi kyau Baffah ashe haka ka gyara gidan?"

Yana dariyarsu ta manya ya ce "na gyara ko aka gyara man? ki yi haƙuri shi ya ce kada a sanar da ke sai in kin zo kin gani da idonki, don yanzu haka bamu fi wata uku da tarewa ba, saboda cikin ƴan watanni aka yi komi aka gama, mutane da yawa sunyi mamakin yanda aka kammala ginin cikin lokaci kaɗan, Alhmdllh kam mun godewa ALLAH da ya had'amu da mutanen kirki masu mutunci da sanin Yakamata, da ace duk sauran mutane haka su ke da ina tabbatar maki mabuƙata ba zasu taɓa yin kuka ba, to matsalar da aka samu irinsu ƙaɗan ne a cikin al'umma"

Dije ta share hawayenta ta ce "Ni ban ma san mi zan ce ba Baffah saboda tun da naga wannan gyaran nasab aikinshi ne, haka fa ya aikowa da su Ladiyo kuɗi Ni banma sani ba ya ce in jini su ja jari"

Baffah ya yi murmushi mai cike da jin daɗi ya ce "daman ita addu'ar a kullum mutum ya yi bata faɗuwa ƙasa banza, don haka muka roƙa kuma ga shi ALLAH ya cika muna gurunmu fiye da yanda muka yi tsammani, da ina da iko da na tara mutane na sanar da su cewa kada su gaji da yiwa ƴaƴansu addu'a, duk halin da suke a kullum su ci gaba da yi masu addu'ar shiriya saɓanin faɗin aibinsu a bakinsu, saboda addu'ar iyaye bata da shamaki wajen Ubangiji, da sunyi take tafiya sai dai ayi jinkiri wajen ganin sakamakon addu'ar, yanzu ga ki kamar ba ke ba kin natsu kin ajiye shirme da tsokana, kin ajiye jan faɗa da abun maganar da kike ta janyo muna a cen baya, ga shi Sakamakon haƙurin da muka yi ALLAH ya mayar muna da alkhairin da bamu zato ba bale tsammani"

Dije ta ce "hakane Baffah ALLAH ya ƙara shirya maka Ni"




Ameenn 🙏🏻





Akafta🤪








D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*ALHAMDULILLAH!!!! ALHMDLLH!!! ALHMDLLH!! GIDAN AURE shine sunan book ɗina da zanyi a gaba, wadda take buƙata zata biya kuɗinta 300 kacal ta hanyar transfer ta wannan account ɗin HADIZA D AUTA 1230094555 access Bank, idan kuma kati ne zaki turo aritel ko mtn na ɗari uku to za'a turo ta wannan numbar 09032685442*

*Ƴargata Maman Sultan Ubangiji ya baki lafiya yasa kaffara, Mrs Naseer ina miƙo gaisuwata zuwa gareki akan namijin ƙoƙarinki ga book ɗina, my Ambash ALLAH ya saukeki lafiya mu zo mu ci rangyem, Asma'u Umar ki yi haƙuri na goge laifina🤗*



*Lamba 72 last page*


🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚


Baffah yana murmushin jin daɗi ya ce "Ameen Dijengalata amman fa ko haka aka tsaya Alhamdulillahi, don ba abunda za mu ce wa ALLAH sai godiya ALLAH ya sawa aurenmki albarka ya baku zaman lafiya ke da Mijinki da abokiyar zamanki duka, kuma ya baki ƴaƴa nagari masu albarka waɗanda zasu yi maki fiye da abunda kinka yi muna na alkhairi"

Dije sai "Ameen Ameen" take faɗi zuciyarta cike da jin daɗin samun iyaye nagari, sai da suka ɗan taɓa fira sannan ta dawo falon Inna suna cin abincin ana ci gaba da fira cikin raha da barkwanci.

Kwanansu Zee ɗaya direba ya kwashesu suka suka koma suka bar su Inna da kewarsu tare da jinjina lamarin Ubangiji, ganin yanda dukansu daga Zee har ita Fiddon sun saki jiki da su kamar cewa daman cen ƴan'uwan juna ne.

Bayan su Inna sun dawo daga rakiyarsu ne Hansai ta goye Sayyid ta yi ɓangarenta, Dije ta faɗa kujera tace

"Wash ALLAHna WALLAHI Inna gaba ɗaya jikina ciyo yake yi"

Inna ta zauna tana ƴar dariya ta ce "sai kin yi haƙuri kam don yanzu jikinki yake haɗewa daga ɗaukar ciki da haifuwar da kika yi, wani zubin ma har zazzaɓi wasu su ke yi a wannan lokacin"

Dije ta dafe goshinta ta ce "ai kam dai nima ina jin abinda nike ji a jikina"

Inna ta kalleta da kyau sannan ta ce

"Naji daɗin yanda yarinyar nan ta sauko kuka fahimci juna ga shi yanzu zamanku gwanin burgewa"

Dije ta yunƙura ta ta shi zaune sannan ta kalli Inna ta ce "kin dai gani Inna ga shi yanzu kamar ba'a yi ba ashe da kirkinta sharrin sheɗan ne da kuma mugun kishin Abban Sayyid da take yi"

Inna ta sauke ajiyar zuciya ta ce "duk macen duniya dole zata yi kishin mijinta, ke ba mijinta kawai ba duk abunda kake so a rayuwa dole ka yi kishin ganin wani ya raɓeshi, sai dai na wani ya fi wani don kowa da kalar dauriyarshi, shiyasa kika ji na ce da ke duk runtsi ki sa ya dawo da ita a matsayin matarshi, saboda ko da ta fita dole ne ya auri wata, kuma ita zata iya shigowa gidan da shirinta ƙarshe ma ta janye maki Mijin ya koma gareta a barki da cizon yatsa, amman in ita ce sanadiyyar wannan abun da ta aikata zai dakushe mata karsashi akan ko ma aikata wani mummunan abu saboda ganin igiya ɗaya ce ta rage a tsakaninsu, saɓanin wacce zai auro ba ita, don ba lalle bane ba ace ku fahimci juna, bale kuma ta barki ki ji daɗin zama gidan aurenki ko zama da Mijinki lafiya, don wata mace sharrinta ko sheɗan ya sarawa bala'in da ke tattare da ita, amman yanzu kin ga komi ya zama tarihi kuna zaman lafiyarku Masha Allah, wanda hakan da kuke shi zai ƙara farantawa mijinku rai ya ji daɗin kyautata maku"

Dije ta cire tagumin da ta yi ta ce "Lalle Inna na yarda da aka ce abunda babba ya hango yaro ko da ya hau sama bazai iya hangowa, kuma naji daɗin biyayyar da na yi wajen sakashi dawo da ita, yanzu ga shi abun Ni ma ya zamo mani alkhairi don baki ga yanda ta ke son Sayyid ba, bata bari ya zauna hannuna matukar ba abincinshi zai sha ba, kuma ina bashi take sake karɓeshi su tafi, shi kanshi Abbanshi sanadin wannan halin kirkin da take yi ne yasa ya sake mata sosai suna ɗasawa, sai dai wani lokacin ina jin ba daɗi idan naga yana kulata Inna, Amman idan na tuno da cewa itama fa Matarshi ce kamar Ni sai in baiwa zuciyata haƙuri don bana son ta fahimci ina jin zafinta"

Inna ta yi shiru sannan ta ce "hakan da kike yi ya yi kuma shine abunda ya dace ki yi, don yanda kike ji haka itama take ji amman ta ke haƙura saboda neman zaman lafiyarku, ALLAH ya baku haƙurin zama da junanku itama kuma ya bata nata rabo"

Dije ƙirjinta ya buga amman ta daure ta ce "Ameen inna Bari in je in kwanta Wallahi wani bacci nike ji a idona"

Inna ta bita da kallo cike da jin daɗin ganin yanda hankali ya shige Dijenta, sannan ta ce

"Duk baccin da ki ke son yi ai wannan baturen baya barinki sai dai in bai rikice ba"

Daga cen cikin ɗakin Dije ta ce "WALLAhi sai in tafiyata gidan Gambo in sha baccina in barku da shi ku yi ta fama"

Inna tana dariya ta ce

"Ai duk inda zaki je ki ɓoye sai an kai maki shi acen tunda mu bamu da abunda zamu ba shi"

Dije ta yi saurin faɗin

"Gaskiya Inna uwaye suna shan wahalar renon ƴaƴa a rayuwa"

Inna ta fashe da dariya ta ce

"Kamar yanda aka sha taki ba ai duk uwar da kika gani da ɗanta to ita kaɗai tasan wahalar da ta sha da abunta lokacin da yana ƙarami har girmanshi, ALLAH dai ya jiƙan iyayenmu da rahamomi Wallahi"

Dije ta ce "Ameen" sannan ta yi kwanciyarta aranta tana jinjina irin yanda iyaye mata suke shan wahalar reno musamman farkon haifuwa, wanda ita sai yanzu ta gano cewa ashe ba ƙaramin haƙuri Inna ta yi da ita ba, cikin zuciyarta sai addu'a take zubawa Innar saboda tuno irin abun maganar da ta yi ta janyo masu a baya, tana cikin tunanin ne wani ta yi dariya wani ta ɓata fuska har bacci ya yi awon gaba da ita.

****

Rayuwa mai daɗi Dije ta yi a gidansu saboda komi yi mata ake yi aikinta bacci da cin abinci sai kuma baiwa Sayyid nono, sannan da baiwa Malaminta dama wajen ƙara macewa kanta, don kuwa suna maƙale a waya ko wane lokaci yana nuna mata irin kewarta da ya yi, tare da sanar da ita da ta cika wata ɗaya a garin zai zo ya kwashesu su koma, cikin dubara take ta hilatarshi har ya bar zancen don bata son ya gano bata son komawar a lokacin, kada ya ga kamar ita bata yi kewarshi ba kamar yanda kullum yake sanar da ita irin damuwar da yake ciki, don Zee ta so binshi acen Abujar ya ce ta jira anan Yolar zai dinga zuwa akai akai wurinta, dole ta haƙura amman ba don ranta ya so ba sai don samun zaman lafiyar da ko kaɗan bata son abunda zai janyo wata fitina a tsakaninsu.

Satin Dije Uku a garin ta yi ɓul ɓul daga ita har yaronta gwani sha'awa saboda kulawar da suke samu wurin Inna da dattijuwar matar, a gefe ɗaya kuma Gambo da bata gajiya da dafa mata abubuwa tana shanyewa, don wani zubin acen ma take kwanciyarta daga ita yaronta da dattijuwar, ga Yan garin na su kowa sai nan nan ake yi da ita da kuma yaronta, don ma Gambo bata son ana yawan fita da shi don ƙa'ida ne kullum sai ta tofeshi da addu'o'in tsari, sannan ta ce dole itama Dijen sai ta tosheshi da addu'o'in saboda kariya daga sharrin mutum ko aljan da wasu masu kambun baki, saboda farin yaron da yanda yake kyakkyawa ga shi ɓul ɓul dole ne mutane su yi shaawarshi, sannan uwa uba ga shi fes fes kullum cikin shiga ta alfarma kuma irinta wayayyun ƴan birni.

****

Wasa wasa Dijen Baffah sai da ta yi wata biyu a garinsu sannan Angonta ya garzayo ya kwashi Matarshi da yaronshi suka koma Yola, suka bar su Inna da Baffah da mutanen garin da kewar Dijen da ɗan baturen yaronta mai kama da indiyawa samfurin larabawa kalar yan Ethiopia.

Hajiya Mama ba ƙaramin daɗi ta ji ba da ta ga yanda yaron da mamarshi suka yi sharr abunsu, cike da tsananin farin ciki ta karɓe shi tana ta yi masa wasa yana wasar baki, Fiddo ta karɓeshi tana faɗin

"Coming to your mama my beautiful boy"

Hajiya Mama ta kalleta tana dariya ta ce "in dai ɗanku ne ga shi nan don ma na yi maku kara na ɗauka?"

Fiddo tana dariya ta ce "WALLAhi Hajiyarmu son yaron nan Nike yi, don ALLAH ki ce da Yayanmu su tafi da Ni Abuja don bana son a rabani da shi ALLAH"

Hajiyar tana dariya ta ce "ki jira idan kunyi jarabawar ƙarshe sai ki tattara inaki inaki ki koma cen duka tunda ke baki fatar ki je naki gidan mijin sai taya wasu zaman aure"

Dije dai dariya kawai ta ke yi cikin dariyar ta ce "ai Insha ALLAHu acen ma zamu yi mata aure don bama fatar a raba uwa da ɗanta"

Safwan da ke shigowa ɗakin ya ce "ba inda zata je don tana kammala karatunta zamu auradda ita"

Fiddo ta zumɓuro baki ta ce "to ai Ni bani da miji"

Dije ta dafe baki ta ce "Mukhtar ɗin fa? Ko an ɓata?"

Ta miƙe tana dariya ta ce "yarona zo mu je tunda yau haɗe man kai ake yi a gidan"

Ta fice suka bita da kallo Safwan ya ƙaraso ya zauna suna ci gaba da firarsu kafin lokacin tafiyarsu ya yi suka tafi duka har Fiddon cen gidan nashi, inda Surayya da wasu yan'uwa suke acen suna tsumayin zuwansu.

Aiko shigarsu gidan mutane suka zo tarbarsu cikin farin ciki ana yi mata Barka da dawowa, Zee ta karɓe yaron tana ta juyi da shi Safwan ya riƙo hannunta ya yi mata raɗa ta yi saurin rufe ido, Dije ta bisu da kallo cikin gefen ido sannan ta shige sashenta tare da mutane tana dariyar yaƙe, Zee tayi sashenta da Sayyid tana ta murnar dawowarshi.

Dije kam tana shiga ta faɗa toilet tana share ƙwallar kishin da ya turnuƙota, sannan ta watsa ruwa ta ɗauro arwallah, bayan ta fito ne Surry ta ce "haba Hajiya daga zuwa ba wani jira sai shige abunki ki barmu a falo muna jiranki?"

Dije ta washe baki cikin ƙarfin hali ta ce "Tom bari in shirya in zo inji me da me aka tanadarwa baƙuwar?"

Surry ta riƙo hannunta ta ce "ki daina ɓoyo nasan me ke damunki to Aunty zee dai ciki. E da ita shiyasa kika ga yayanmu ya hanata
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment