Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ne ya faru cen Gida? "

Lawi ya kara sunne kai yace,. "A'a Baba akan dai matsalar nan ne"

Maigarin ya ce,. "Wace matsala Kuma? Ko ta Yar Gidan Malam Sanda?"

Lawi ya d'aga kanshi yace,. "Eh ita to yanzu abun ya Kara rikicewa saboda ko magana ma an hanata tsayawa ta yi dani"

Maigarin ya yi shiru sannan yace,. "Ka yi hak'uri yarona Ni zan ga Malam Sanda duk yanda muka yi zan neme ka"

Lawi ya mike tare da yi masa godiya ya yi d'akinsu, zuciyarshi cike da takaicin bala'in da ya janyowa kanshi yana zaman zamanshi.

Maigarin kam bai yi k'asa a gwiwa ba dakanshi bayan magrib ya yi tattaki tare da mukarrabanshi suka nufi gidansu Dije, cike da mamaki Baffah'n ya shimfida masu tabarma suka zauna tare da yi masu sannu da zuwa.

Bayan an k'are gaggaisawa ne Maigarin ya yi gyaran murya yace,. "Malam Sanda nasan zaka yi mamakin abunda yasa na yo tattaki zuwa wajenka?, To ba komi ba ne akan matsalar Bakon yaron cen ne da Yar wajenka Dije, a zahirin gaskiya yaron nan dai na gano ba k'aramin so yake yi mata ba, shiyasa nace bari in zo in jaddada maka zancenshi da muka yi a kwanakin baya, shin har yanzu kana kan bakanka akan bazaka baiwa mutumen nesa yarka ba Koko ya abun yake?"

Baffah kam Nan take wani sabon b'acin Rai ya ziyartoshi amman cikin dariyar yake yace,. "Ranka shi dad'e ina mai jin kunyar sanar da Kai cewa na yiwa Dije Miji, kuma insha ALLAHu wata mai kamawa Zan auradda Dije ga Bala dan Gidan Mariganyi Mamman jikan Inna Duduwa"





To fa rigiji Gabji😳 lalle akwai kwacagiya😝




Akafta🤣







D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*





*MUTANEN DIJE K'ARANGIYA INA GAIDA KOWA ALL ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU👍🏻*


*Lamba ta 21*


Gaba d'aya jikin kowa na wurin ya yi sanyi sai cen Maigarin ya yi jarumtar fad'in,. "A komi ALLAH Ubangiji yasa hakan shine alkhairin"

Ya yunkura ya mike tsaye yana saka talkaminshi yace da abokan tafiyarshi,. "Ki tashi muje sai mu yi masa bayani idan har ALLAH zai sa ya fahimcemu"

Haka suka bar k'ofar gidan kowa jiki ba kuzari saboda ganin duk girman Maigarin ya zo neman abu wajen Baffah amman ya rufe idonshi ya kasa yi masa wannan alfarma, shi Kam Baffah ko a jikinshi hasali ma hankalinshi kwance ya nad'e tabamar ya shige cikin gida, inda kai tsaye ya kira Usman ya ce ya je ya kira masa Balan Duduwar, sannan ya shige d'aki abunshi Inna ta bishi da kallon mamaki jin aiken da ya yi na neman Bala, cikin sanyin jiki ta bishi d'akin tace

"Malam ALLAH dai yasa lafiya?? Naga Maigari ya zo wajenka kuma ga shi na ji yanzu ka ce a kira Bala"

Baffah ya yi saurin fadada fuskarshi da murmushin yace,. "Abunda kike so ne za'a yi maki tunda na hango hakan shine mafita akan matsalolin da suke son kunno man kai cikin gida"

Inna ta bishi da kallo Baki sake tace,. "Ka yi man bayani yanda Zan gane Malam"

Baffah ya fito d'akin tare da d'auko buta ya fara sabuwar arwallah har ya k'are ba tare da yace kanzil ba, sannan ya mike ya kalleta yace

"Wata mai kamawa Zan yiwa Dije aure da Balan Duduwa tunda har yana sonta"

Inna ta zaro ido waje tace,. "A'a Malam gaggawa fa aikin shedan ce, ka bari abi komi a hankali kar a zo ayi abu don neman mafita wata sabuwar matsalar ta bullo"

Baffah ya kalli Inna shekeke sannan ya nufi hanyar fita yace,. "Alkhairi muke fata kuma shi zamu gani"

Ya fice ranshi a b'ace Dije da ke k'ofar Inna ta k'araso wajen da Innar take tsaye cikin kokwanto tace,. "INNA naji Baffah yana zancen aurena da Balan Duduwa da gaske yake yi ko wasa???"

Inna ta maka mata wata Uwar harara ta nufi madafi tace,. "Ki jira idan har ya dawo sai ya amsa maki tambayar da bakinshi tunda ai ba Ni kika ji na fad'a ba"

Dije ta ja buta ta yi bayi tana gungunin cewa,. "Ai na rantse da ALLAH ni Malam Danbirni zan aura cabd'i! Haka kawai in aureshi ya hanani zuwa Makarantar koyon Likitanci hum! lalle ma ko"

**

Baffah Kam tare da Bala da Usman suka yi sallahr Isha sannan suka garzayo gida, Baffah yasa Usman ya shimfida masu tabarma a zauren gidan, sannan yasa aka kawo masa tuwonshi ya yi wa Bala tayi Bala cike da jin nauyin surukuta yace,. "Alhmdllh"

Baffah ya kalli Balan yace,. "Naji labarin cewa kana son Dije ko?"

Bala ya sunne kai cike da jin kunyarshi, Baffah ya ce

"Magana zamu yi mai Muhimmanci saboda auradda ita nike son yi idan har kashirya aurenta to ka fito da karfinka Ni zan aura maka Dije duk lokacin da ka shirya"

Cike da tsananin farin ciki yace

"Na gode Baffah" Balan kam bakinshi ya kasa rufuwa saboda tsabar murnar ganin nesa ta zo masa kusa, cikin jin nauyi ya nunawa Baffah amincewarshi tare da godiya akan wannan karamci da ya yi masa, sannan ya yi masa alk'awalin zai turo iyayenshi kurkusa ayi komi a gama cikin kankanin lokaci.

Haka suka rabu zuciyarshi cike da farin ciki uwa uba ma da Baffah'n ya bashi damar ya fara zuwa zance wajen Dijen don su fahimci juna kafin lokacin auren ya zo.

Baffah kam bai shigo Gida ba har sai da ya tabbatar Dije ta yi bacci don ba ya son ta janyo abunda zai sa ya jibgeta a banza, don tunda ya dawo masallacin ya ga yanda ta makure jikin gini tana sharar hawaye yasan akwai magana, don baya raba d'aya biyu yasan taji zancen aurenta Balan shiyasa, sai dai a mamakinshi ko da ya shiga cikin Gidan ya taradda ita idonta biyu jikin ginin har lokacin tana gyangyadi, jin shigowarshi yasa ta yi saurin mik'ewa ta nufoshi tana fad'in

"WALLAHI Ni Baffah ban son Bala ba zan aureshi ba"

Baffahn ya yi mata wani kallo yace,. "Baki sonshi wa kike so??"

Dije ta yi saurin kamo gefen dankwalinta tana wasa dashi tace,. "Ni Baffah ba wanda nike so WALLAHI Ni gurina kawai inje Makarantar gaba in zama likita"

Baffah ya zaro Ido waje yace,. "Au shirmen ya kitsa maki kenan ko? To ai kwanan nan zanyi maganin abun, ai WALLAHI ko bani so dole ne in auradda ke cikin gaggawa tun kafin su kaini ga maganar banza"

Yana kare maganar ya shige d'akinshi zuciyarshi cike da jin tsoron sharrin wad'annan bak'in Yan bokon ga Yar guda gudar yarshi Dije, wadda ko kuda baya so ya tab'a masa ita matuk'ar yana da ikon hakan.

Dije kam ranar kwana ta yi tana sharbar hawayenta saboda sam sam ita bata son auren kacakam ballantana auren Balan, idan son damunta ne ace ta yi karatu mai zurfi ta zamo abar alfakhari cikin kauyensu, amman ina kash tasan gurint sam bazai tab'a cika ba muddin ta auri Bala, don dama ace Lawi ne da zata sakawa ranta cewa gurinta zai cika komi daren dad'ewa.

Ko da Safiya ta waye da d'ar d'ar ta shirya don ta zaci Baffah'n ya hanata zuwa Makaranta, amman sai gashi bai hanata ba har da yi mata ALLAH ya kiyaye, saboda yasan Shirin da yake yi akan auradda ita d'in cikin kankanin lokaci.

Dije sukuku ta zo Makarantar Lawi ya so ya yi mata magana amman tuno irin gargadin da Maigarin ya yi masa akanta yasa ya yi k'ok'arin kawar da kanshi gareta, don ko da aka tashi ma sai da kowa ya watse Makarantar sannan shi ya nufo masaukinsu, don gaba d'aya ma shi zaman garin ya gundureshi jin yake yi kamar a saman kaya yake, Alla Alla yake yi su kammala service dinsu su bar Garin, don akan hakan ma har abokin nashi ma sun fara zaman doya da manja dashi, gashi shi ma Maigarin yace ya zame hannunshi idan shi zai iya ga fili ga mai doki.

**

Cikin wata d'aya aka kammala neman auren Bala da Dije inda aka kawo komi na auren Rana kawai ake jira ta zo a sha shagali, izuwa lokacin Dije ta saduda dolenta saboda ba tirjiyar da bata yi ba akan auren amman Baffah'n kam ya kafe ba gudu ba ja da baya, don ita kanta Innar ganin akan auren Dije zasu samu matsala da Baffah'n shiyasa ta zubar da makamanta ta fara shirye shiryen auren Dijenta.

Ana saura sati d'aya bikin Dije suka zana jarabawar kammala primary, kowa sai murna yake yi inda shi Kuma Lawi yake cike da bak'in cikin rasa Dijen da yayi, Safwan kam ko kad'an bazaka gano yanayin da yake ciki ba, asali ma shi hankalinshi kwance yake ta d'aukar photuna da su Dije da sauran yaran Makarantar, Dijen ma ba wata walwala akan fuskarta don kuwa a kallo d'aya zaka gano sauyawar da ta yi, don kuwa gaba d'aya ra zabge sai Ido da karan hanci don izuwa lokacin har wata natsuwar dole ta ziyartota, duk nacin da Lawi ya yi akan yana so ya yi sallama da Dije bai sami wannan damar ba, saboda ganin yanda Safwan ya keta hidimar d'aukar pic's d'inshi da su Dijen.

Sai da aka gama ne ya samu ya yi wa Dije sallama tare da mika mata wata envelope idonshi jawur tamkar ya yi kuka, don shi ya kuduri aniyar ba zai jira ayi auren Dijen da shi ba, da nufin tun da sassafe ya had'a inashi inashi ya bar garin, don shi Safwan ya ce ba ranar zai tafi ba ya yi gaba shi zai biyoshi ta baya.

Dije tana kuka suka yi sallama da Lawi ta tura envelope d'in da ya bata a jaka ta nufi gida,. Kai tsaye ta shige toilet ta bud'a envelope d'in saboda ta matsu taga me ke ciki gashi bata son Inna ta gani.

Aiko sai gashi tana budawa taga wasu Yan hannu da zobe masu bala'in kyau sannan da bandur d'in kud'i sababbi kal yan d'ari bibbiyu, Dije ta zaro ido tare da goge hawayenta cikin sauri ta rungume kud'in da sauran kayan ta fashe da kuka gwanin ban tausayi, sai dai ita bata san duk abunda take yi Inna tana hankalce da ita, shiyasa lokacin da taga ta dad'e bayin ta biyo sawunta sai ko gashi ta ganta durk'ushe kasan bayin tana ta kuka, cikin tausayawa ta isa wurinta ta tadata Dije ta yi saurin yunkurin b'oye kud'in sai ga takardar kud'in ta yage kud'in sun zubo shaaaa! A k'asa.



Ku yi hakuri da kuskuren da kuka gani yau ban yi editing ba🤦🏻‍♀️



Akafta😉







D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*





*MUTANEN DIJE K'ARANGIYA INA GAIDA KOWA ALL ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU👍🏻*


*Lamba ta 22*


Daga Inna har Dijen gaba d'aya zaro Ido suka yi suna kallon kud'in, cikin firgici inna ta yi saurin fad'in

"Dije me nake Shirin gani yau Ni Hasiya?"

Dije ta yi saurin duk'atawa tana ta tattara kud'in har ta kammala sannan ta mik'awa Inna tace,. "Karb'i kyauta ce aka bani"

Inna ta tak'i karb'ar kud'in ta tsuke fuska tace,. "Gaya man duk fad'in garin nan waye mai arzik'in da har zai iya baki wad'annan mak'udan kud'in sababbi k'al da su haka?"

Dije ta saka hannu ta share hawayen da har lokacin basu daina zubo mata ba tace,. "Malaminmu D'anbirni ne ya bani wai tashi gudunmuwa ce yace ko Daddawa a siya man"

Inna ta maka mata wata jar harara tace,. "To WALLAHI Ni ba ruwana in har Baffah'nki ya ji wannan magana,sawunki a likkafa ki tattara kayanshi da kud'inshi ki je ki Kai masa salun alun ba wanda ya ji ba wanda ya gani"

Dije ta sake fashewa da wani sabon kuka tace,. "Ni dai Inna ina son awarwaron da zoben, don ALLAH ki bari in mayar masa da kud'in kawai don ALLAH Inna"

Ta k'are maganar cikin marairecewa gwanin ban tausayi, Inna ta karbe kud'in da awarwaron da zoben ta janyo hannunta suka fito tana janye da hannun Dijen har d'akinta, sannan ta samo wata leda baka ta zuba kud'in da kayan ta k'ulle jabau! Ta mika mata tare da had'e fuska alamun ba wasa tace,. "Karb'i kije ki mayar masa da kayanshi yanzun ba sai anjima ba"

Dije ta karb'a har ta fito ta dawo tace,. "To Inna ki bari in cire kayan Makarantar in saka na Gida"

Inna ta taso mata kamar zata daketa tace,. "Bazan bari ba nace ba za'a bari ba zaki je ko sai na sab'a maki ne yanzu Nan??"

Dije ta fice tana tafe tana gunguni har ta kai wani lungu ta bud'e ledar ta cire awarwaron da zoben ta k'ulle ledar ta nufi gidan Inna Gambo, sai da ta samu wani waje cikin dabara ta b'oyesu d'akin Gambon sannan ta fito ta nufi gidan Maigarin, sai dai rashin sa'ar da ta taka tun kafin ta isa daga nesa Maigarin da ya hangota ya bada umurnin a hanata zuwa wurinshi, saboda yaci alwashin daga Dijen har Baffah'n ba zai sake shiga cikin shirginsu ba, sai dai ita kam ta nace akan ita bazata koma ba don wurin Malaminsu ta zo ba wurinshi ba, Maigari kam ganin rigima zata b'alle ne a tsakanin Dijen da wani yaronshi yasa yace a kyaleta, kai tsaye ta nufi k'ofar d'akinsu Safwan ta fara rafka sallama sai dai ta yi har ta gaji ko sau d'aya bata ji an amsa mata ba, cike da k'unar rai ta fad'a d'akin da k'arfinta sai dai wayam ba kowa d'akin, tana k'ok'arin fitowa ne ta ji ta yi karo da mutum da sauri ta ja baya tana sosa goshinta da kan Safwan ya buge, Cikin tsoro ta rab'a ta gefenshi ta fito jikinta yana rawa ta fara fad'in

"Don ALLAH ka yi hak'uri wajen Malam na zo na yita sallama banji an amsa ba shiyasa na shigo in ga ko lafiya"

Safwan ya maka mata wata Uwar harara sannan ya rungume hannu a K'irji ya ce,. "Lafiya kike nemansa? ba naga kunyi sallama ba ko Mahaifin naki ne ya amince zai bashi aurenki ne shiyasa kika zo yi masa albishir? "

Dije yanayin fuskarshi da tambayoyinshi sun sakata daburcewa, cikin rawar murya tace

"Kyautar da ya bani ce na zo kawo masa kayanshi sabida gidanmu ance bazan karb'a ba"

SAFWAN ya yi wani mere yace,. "Sai Kuma aka yi rashin sa'a shi ya bar garin gaba d'aya ya koma gida, cen zaki bishi garinsu ki kai masa ko yaya?"

Dije ta zaro ido tace,. "WALLAHI na koma da su sai sun janyo man gagarumar matsala, don ALLAH ka karb'a ka ajiye masa idan ka koma sai ka bashi abunshi kace na gode sosai ALLAH ya had'a fuskokinmu a aljannah, kuma ka yi masa albishir insha ALLAHu nice Matarshi a Lahira idan munje cen"

SAFWAN ya galla mata wata jar harara da jajayen idonshi da suka rine lokaci d'aya yace,. "Zaki bar wajen nan ko sai kin janyo na karairayaki a kaiwa kwad'ayayyen angonki sauran k'asusuwan???"

Dije ta yi saurin ja da baya tace,. "Don girman ALLAH ka karb'a WALLAHI dukana za'a yi gidanmu idan na koma da su"

Safwan ya buga mata wani uban tsaki ya shige d'akinsu tare da fad'in,.

"Idiot!!!"

Dije kam sanin idan ta koma da su gida akwai matsala ta lallaba ta jefa ledar kud'in cikin d'akin ta zank'ara da gudun tsiya, Maigarin da mutanenshi suna ganin fitowarta da gudu suka bita da kallo, Maigari ya mike tsaye jikinshi yana rawa yace

"Bari in je in dubo yaron Mutane kada ta kasheshi mu shiga uku, tunda shi har yanzu bai tashi barin garin ba duk da kyamar garin da yake yi"

Sauran mutanen su ka biyoshi baya har zuwa d'akin sai dai ganinshi da suka yi kwance yana latsar waya ne yasa hankalinsu ya kwanta, sannan suka koma suna ci gaba da yi da Dije da Baffah'nta, inda wasu suke ganin laifinshi akan abunda ya yi wa Maigarin yayin da wasu suke ganin hakan da ya yi shine dai dai.

Bikin yana saura kwana Uku aka gyarewa Dije d'akinta ram! gidan Inna Duduwa,Wanda Balan ya ci gado ga Mahaifinshi da ya mutu, don asalima d'akin Mahaifiyarshi ne da ta yi zama ciki lokacin da Mahaifinshi yana raye, don yanzu haka tana wani k'auye tana aurenta da yaranta biyar bayan Balan.

Biki sai kankama yake yi Bala da abokanshi da kawayen Dije Su Jummala sai shagalin bikinsu suke ta yi, don ana saura kwana biyu ne aka shirya wani bikin tauri a k'ofar gidansu Balan, inda yan tauri suka baje sai nuna k'warewarsu suke yi, sun burge iya burgewa in da bikin wasar taurin ya d'auki lokaci har cikin dare anata fafatawa da zaratan jaruman Yan taurin.

Ko da safiyar JUMU'A ta waye aka shiga hada hadar hidimar d'aurin auren a k'ofar gidansu Dijen, don tun kafin aje masallacin JUMU'A aka fara shimfida sabbin tabarmomi da ledar buhu manya manya aka malale k'ofar gidan ko'ina, ko da aka ta so mutane ta ko'ina sai b'arkowa suke yi zuwa k'ofar gidan Baffah'n Dije Malam Sanda, Baki na nesa da na kusa Kai har na manyan biranen da Baffah yake abun arzik'i da su sai da ya gayyatosu zuwa daurin auren shalelenshi Dijengala.

Cikin bak'in da ake zuwa daurin auren har da wasu fararen dattijai na hango tare da motocinsu na alfarma, inda kai tsaye hankulan mutanen k'auyen ya karkata kansu saboda alamun hutun da ya bayyana a jikinsu, nan take za'a banbancesu da mutanen garin saboda kamarsu daban da take ko da ko a cikin duhu.

Wani Dan'uwan Baffah'n shine zai yi waliccin Dije, yayin da wani kanen Baban Bala zai karb'arwa Bala auren Dije, soron Gidansu Dije nan ne aka yiwa wad'annan bak'in alfarmar masauki akan saman sababbin tabarmin da Baffah'n ya tanada don kawai wannan Rana.

Kai tsaye Liman ya nemi ganin waliyyin Ango da waliyyin Amarya duk suka hallara, Baffah kam bakinshi kamar gonar auduga saboda tsabar farin cikin ganin wannan Rana mai d'inbin tarihi a wajenshi da Dijenshi, saboda auren Dijen yana daga cikin abubuwa masu muhimmanci a rayuwarshi, don yasa a ranshi ko yau ya kwanta dama shi gurinshi ya cika tunda har ya auradda 'yarshi guda mace da ALLAH ya albarkaceshi da ita a doron duniya.

Kafin kace me sai ga Liman ya fara hud'ubar aure cikin ikon ALLAH sai jin aka yi mai sanarwa fad'in auren ya fara shelar shewa an d'aura auren NANA HADIZA wadda aka fi sani da suna DIJE tare da Angonta MUHAMMADU SAFWANU JABB'I YOLA.




Durum! dum! dam! dum! dum! Haka naji gaban Baffah yana ta luguden fad'uwa tare da sauran mutanen da ke wajen da ma ita kanta Dijen da ke bayi tana ta gurzar kuka na tashin hankali.



Oh! oh! rigiji Gabji 😳 Ni kam taya aka haifu a ragaya😱🤔 HAJIYA DUDUWA kar ki zargeni don ni ma bansan komi ba🙌🏻🏃🏻‍♀️




Akafta👻




D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*





*LUV U SO MUCH ALL MY FAN'S💋Ina jin dad'in yanda ku ke kaunar book din Dije K'arangiya yawanku ya kai bazan iya lissafoku ba amman ku sani ina yinku sosai all my guys👍🏻*


*Lamba ta 23*



A zabure Baffah'n ya mik'e cikin sabon tashin hankali marar misaltuwa ya nufi wurin k'anen Mahaifin Bala yana fad'in,. "Daman shi haka sunan Balan na gaskiya yake?"

K'anen Mahaifin Bala yayi d'an murmushin yak'e yace,. "An samu akasi ne Malam Sanda don ba da Bala aka d'aura auren ba"

Baffah'n yana jin haka ya rud'e tashin hankalinshi ya k'ara k'aruwa cikin zaro Ido waje ya nufi wurin Liman ya shak'o wuyanshi yace,. "Da wa ka d'aurawa 'yata aure ne?? mugu azzalumi ai WALLAHI sai na yi shari'a da kai matuk'ar baka yi gaggawar kwance wannan mugun auren ba"

Cikin masifa Baffah'n Dije ya shak'e Liman tare da kai masa wani azababben naushi mutane suka rirrik'eshi, kafin ka ce me wuri ya hautsine hargitsi tare da gutsuri tsoman jama'a, saboda ruwan bala'in da Baffah yake ta zubawa cikin d'aga murya yana hargowar cewa,. "Ai WALLAHI in duk garin nan za su taru a kaina bazan lamunta ba sai an kwance wannan bak'in auren da aka k'ullawa 'yata, Ni na haifeta kuma nace ba zan bada ba shin auren dole ne ko ita kad'ai ce 'ya mace a garin nan"

Kai rigima fa tun ana ganinta a wasa sai ga abu tana shirin zama Babba, don kuwa Baffah sai zillo yake yi akan sai an barshi ya daki Liman, ana cikin rigimar ne sai ga sak'o daga Maigarin ya aiko duk kowa ya hallara a k'ofar gidanshi, Baffah'n kam har kowa ya tsiyaye aka barshi shi kad'ai k'ofar gidan yanata sauke ruwan sababi, Inna da sauran matan da ke cikin Gidan suka fito sunata bashi baki.

Maigarin ya yi ta aikowa da sak'on neman Baffah'n ya kai sau uku sannan ya nufi gidan Maigarin har lokacin bai daina sambatun fad'anshi ba tamkar wani tabab'b'e sabon kamu.

Abun mamaki k'ofar gidan Maigarin cike dank'am da d'an'adam maza da mata yara da mayan, sai dai kuma idan aka yi la'akari da yanda kowa yake son ya ji k'waf to hakan ba abun mamaki ba ne ba saboda ba Baffah'n kad'ai ba wasu da yawa suna son su san shin ta yaya aka haifu a ragaya?, Baffah'n da idanuwanshi da ba abunda ke cikinsu a lokacin face tsagwaron tashin hankalin da yake ciki jin yake yi gaba d'aya kowa haushi yake ba shi, yana muzurai zuciyarshi awa garwashin wuta saboda tsabar k'unar da take yi masa, ba tare da ya zauna ba ya tsaya k'ik'am yana huci tamkar wanda ke shirin kai naushi.

Maigarin ya kalleshi da kyau yace,. "Malam Sanda ka zauna wannan taron ba don kowa aka yi shi ba face donka da kuma 'yarka Dije"

Baffahn ya makawa Maigarin wata jar harara yace,. "Me kuma zan zauna a fad'a man yanzu? wanda ya wuce muguwar kullalliyar da kuka k'ulla kuka rufeni kuka baiwa 'yata Mijin da ba Ni na zab'a mata ba???, Sai na gani da Ni da ku wa ye yake da ikon auradda ita??don ku ma sani wannan auren k'addara mai cike da bak'ar manufar tamkar an kwanceshi an gama"

Ya k'are maganar cikin huci tare da zabgawa Liman wata muguwar harara sannan ya yi kyafci, Maigarin ya k'ara cewa da shi

"Da kasan irin ta'adin da 'yarka ta shirya idan anyi auren da wanda kake son ta aura d'in,to da baka tsaya gaban Mutane kana wannn shirmen ba, Kai godiya ya dace ace ka yi wa Mutane ba wai ka tsaya kana yi wa mutane karatun hauka ba"

Aiko cikin nasara maganganun Maigarin sun saka Baffah cikin shakku da tsoron abunda zai fito akan wani aikin ashsha da Dije ta aikata ko take Shirin aikatawa, saboda yasani sarai ba son auren take yi ba haka ma yasan wacece ita da ayukanta, shiyasa cikin sanyin jiki ya ja k'afafuwanshi zuwa kusa da wad'annan manyan alhazawan bak'in fuskar ya zauna.

Maigarin ya kalli Safwan da ke cikin manyan kayanshi da suka fito da zallar kyawunshi na Bafillacen usali, ya yi shiru na d'an lokaci sannan Maigarin yace da shi

"Yi masa bayani da bakinka don ya san cewa muma ba ma cikin mutanen da zasu cutar da wasu ma bale shi"

Safwan ya gyara zama tare da yin gyaran murya yace,. "To a zahirin gaskiya yau kwana shida da 'yarka ta iskeni har d'akina tana sanar da ni cewa muddin ba'a aura mata Abokina ba to ko ita duk ranar da aka kaita gidan Mijin da ka zab'a mata zata kashe kanta shi ma ta kasheshi, ta hanyar saka masa shinkafar b'era su ci dukansu su mutu murus daga shi har ita"

Aiko ba Baffah'n ba har ta mutanen da ke wajen sai da suka fara salatin fad'in "Innalilahi wa'Inna ilairraji'un"

Cike da fad'uwar gaba Baffah'n yace,. "Wannan k'azafi ne aka yiwa Dijeta don kuwa sam k'wak'walwarta bazata yi wannan tunanin marar amfani ba, dududu duka Dijen guda nawa ta ke? da har za'a ce tasan da wannan mugun tunani kai ina da sake WALLAHI"

Ya mike tsam! da nufin barin wajen Safwan ya yiwa Bala wani kallo k'asa k'asa aiko sai ga Bala da mik'ewa tsaye yana fad'in,. "Baffah ka tsaya ka ji gaskiya ce ake fad'a don Nima bakina da nata tace dani duk ban janye aurenta da Ni ba sai ta kasheni ta kashe kanta, shine na zo wajen wannan Abokin wanda take so d'in na nemi alfarmarshi akan ya aureta Ni na hak'ura ko don mu shawo Kan matsalar, to Abokin ya tafi kuma an yi ta nemanshi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment