Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Aunty Ummi don ALLAH ki tayani roƙon Hajiyarmu ta dawo man da matata WALLAhi a takure nake sosai da rashin sanin inda take, don ALLAH Aunty ki ce ta bani matata WALLAhi buƙace nike da ita kamar in kuwata"

Dije ta yi saurin cire wayar a kunnenta ta goge kwallar da ta sauko mata ta miƙawa Husnah wayar cikin sanyin jiki ta fice ɗakin ta nufi ɗakinta da aka ware mata ita kaɗai, Husnah ta bita da kallon tausayi ta kara wayar a kunnenta saboda maganar da yake ta yi yana kiran sunan Aunty Ummin cikin magiya, cikin wata muryar tausayawa dukansu ta ce

"Auncle Mummy bata nan ta fita idan ta dawo za'a sanar da ita ka kira"

Cike da jin haushinta ya ce, "uban wa ya ce ki ɗauki wayar kin san bata nan?"

Ta yi saurin faɗin

"Sorry Auncle....."

Kittt ya kashe wayar cike da jin haushinta, Husnah ta sauke wayar ta yi shiru tana nazari sannan ta miƙe ta nufi ɗakin Dijen, sai dai kukan da ta ji tana yi ne yasa ta yi saurin isa wurinta tana faɗin

"Plss Aunty Khady ki yi haƙuri ki yi shiru ki sanar da ni abunda kike wa kuka, Ni kuma insha ALLAHu zan taimakeki ko don ki sami farin ciki"

Da ƙyar ta shawo kanta ta yi shiru sannan Dijen ta miƙe zaune tare da share hawayenta ta ce, "kin yi alƙawalin ba zaki faɗawa kowa ba?"

Husnah ta yi mata kallon tausayi ta ce, "ki faɗa kawai Auntynmu ni nace da ke zan taimakeki in dai hakan zai sakaki farin ciki"

Dije ta ce

"Ya zanyi in dinga communicate da Auncle ɗinku ba tare da ya gano ni ce ba?"

Husnah ta yi shiru sannan tace, "ki bani yau zuwa gobe zan samo maki number'rshi da yake using da ita yanzu, ke kuma sai a buɗa maki whassapp ki dinga yi masa magana a ɓoye amman fa plss kada ki bayyana masa inda kike, har sai lokacin da Hajiya Mama ta sanar da shi da kanta, don WALLAhi Mummy tasan da Ni a wannan lamarin kinsan zan ci Ubana ne a hannunta"

Dije cike da jin daɗi tace "na amince My Husny don ALLAH ki taimakeni WALLAHI da kinyi man haka kin gama man komi don sai naji daɗi sosai, kuma kin ga ke ma ai zaki sami lada"

Husnah tana dariya ta ce "ai naji haushin da wayar Mummy take da security na fingerprint WALLAhi da yanzun nan zamu samota"

Dije ta dafe goshi tace

"Ai shiyasa ma kika ga bana taɓa wayar Aunty saboda ba abunda zaka iya yi da ita idan ma ka ɗauka"

Haka suka yi ta shawarwarinsu har dare lokacin da Aunty Ummi ta yi bacci, sannan Husnah ta je ta lallaɓa ta saka yatsanta da ta yi lock ɗin da shi ta cire securityn, sannan ta yi saurin shiga wayar ta ɗauki number'r Safwan a wayarta ta ajiye wayar ta fito cikin sanɗa, sannan ta dawo wurin Dijen da ke ta tsumayin jiran fitowarta, kai tsaye ta bata numbar ta yi saving a wayarta, sannan ta nuna mata duk yanda zata yi da yanda zata shiga da fice cikin whassapp ɗin, sannan ta yi mata sai da safe ta shige ɗakinsu.

Dije kam cike da tsananin farin ciki ta shige nata ɗakin ta dantse, sannan ta haye gado cike da murna ta fara shiga contacts list ɗinta sai ga number'r Safwan ta fito raɗam tare da hotonshi da ke dp, inda ya sha ƙananun kaya sun fito da kyaunshi sosai sai dai ƴar ramar da ya yi, amman duk da hakan sajenshi da ɗan ƙaramin gemunshi sun ƙawata fuskarshi gwanin burgewa, ya fito bafulataninshi na usuli mai cikar zati tare da tarin kamala da ke tattare da fuskarshi.

Dije ta yi zooming hoton sosai tana shafo fuskar sannan ta kai bakinta ga hoton ta yi mai kiss ba shiri ta rufe fuskarta tana dariya alamun jin kunya, sannan ta shiga ta fara yi masa sallama, aka yi dace yana online amman bai kula da ita ba ma balai ya duba yaga ko wace ce, saboda ganin baƙuwar number Kuma daga Nigeria, don in da sabo ya Saba da gayyar mata da maza masu son cuso kansu gareshi ta ƙarfin tsiya, shiyasa bai cika damuwa ma da ire irensu idan ya gani ba, Dije kam ganin bai amsa ba yasa ta sake turo masa emoji na kuka mai ɗauke da ƙwalla kamar haka😢ta sake ce wa

_Salam!_

Amman nan ma shiru cike da jin haushi ta shiga gallery ta Ciro wani pic ɗinta Wanda daga ita sai guntuwar t.shirt baƙa ba ɗankwali sai dai ta yi cropping ɗinshi ta cire fuskarta ta bar ƙirjinta kawai tare da jelar gashinta da ta sauko a kafaɗunta har gaban ƙirjinta, sai da ta tabbatar da hoton ya shiga sannan ta yi offline zuciyarta cike da jin daɗin ganin photonshi.




Dijen Baffah banda jan rai hwa🙄






Akafta😝







D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Na gode sosai da addu'o'inku gareni i luv u all my guys💋*



*Lamba ta 60*



Sai dai ƴan mintuna a tsakani ta kasa haƙuri ta dawo abun haushi har lokacin bai duba ba, cike da takaici ta kashe datar ta kwanta abunta tare da ƙarewa pic ɗinshi da ta ɗauka kallo, haka ta kwana cikin begen Mijinta tare da mafalkinshi kala kala.

*****

Malam Safwan kam sai da ya kammala uzurin da ke gabanshi zuciyarshi ta ƙawata masa duba sauran text's ɗin da ake turo masa da numbers mabanbanta, cikin nasara ya kawo kan na Dijen Baffah cike da mamaki ya bi massages ɗin da kallo

_Salam_

_😢_

_Salam_

Sai hoton da ta turo wanda idonshi a kan dukiyar fulaninta da suka cika ƙirjim fam kamar za su fasa rigar su fito, ba shiri ya haɗiyi wasu yawu da suka tsinke masa, sannan ya sake yin zooming ɗin pic ɗin haka kawai ya tsinci kanshi da faɗin

"I like it"

Amman a zuciyarshi ya ce _ita kuma wannan wacece take son janyo hankalina da abunda na fi so a jikin mace??._

Haka kawai ya ji ya kasa ɗauke kanshi daga pic ɗin sai ga shi da tsintar kanshi cikin wani yanayi marar misaltuwa, cikin wata kasala da ta sauko masa ya mayar mata da reply kamar haka

_wslm plss wace ce?_

Sannan ya kashe wayar yana ta ƙarewa pic ɗin kallo duk da wani sashe na zuciyarshi yana yi masa kashedi da kallon pic ɗin, kuma ta shawarceshi akan ya goge hoton sai dai kuma ya kasa baiwa zuciyarshi haɗin kai, saboda ba ƙaramin kyau suka yi masa a ido ba.

Dije kam ko da safiya ta waye tana gama SALLAHr asuba ta janyo waya ta duba cike da zumuɗi tare da fatar ya ga massages ɗinta, ai kuwa sai ga shi ta ga ya duba har da su reply, cikin rawar jiki ta mayar masa da amsa kamar haka

_"Am the one how was the day??"_


Sannan ta sake ɗauko wani pic ɗin wanda daga ita sai rigar bacci mai siririn hannun vest, ga shi ko bra babu a jikinta sun fito sosai masha ALLAH ta yi crop ɗinshi ta cire fuskarta, sannan a ƙasan photon ta rubuta

_Good morning my life partner._

Sannan ta sauka ta nufi kitchen ita da su Husnah da wasu ma'aikatan gidan biyu suna shirya abun break fast, Bayan sun ƙare ne ta dawo ɗakinta da nufin yin wanka, amman zuciyarta ta ƙawata mata ta duba ta ga in ya ga saƙonta, sai dai ganin bai hau online ɗin ba yasa ta yi saurin shigewa toilet domin ta yi shirin zuwa school.

Dije har ta je makarantar ta dawo tunaninta yana kan wayarta, saboda son ganin wane saƙo ne ya turo mata, aikuwa cike da ɗoki ta duba wayar sai ga reply ta gani kamar haka

_"Idan ba zaki buɗe fuskarki ba kada ki sake yi man magana"_

Cikin daburcewa Dijen ta yi shiru tana nazari sannan ta yanke wata shawara ta sake ciro wani photon wanda ta yi daga ita sai wata doguwar riga half gown ta kanti da wani wando skin tight baƙi, inda ta juya gefen fuskarta kawai ya fito don gaba ɗaya ma bayanta kawai aka ɗauka sai gefen fuskarta ga gashinta ya zubo har gadon bayanta, sannan a ƙasanshi ta rubuta

"Good bye"

Aka yi da ce shima yana online saboda ya kasa natsuwa zuciyarshi sai hasko masa fuskar Dije take yi a matsayin mamallakiyar photon, shiyasa ya ce idan ba za'a turo fuska ba kada a sake yi masa magana saboda kawai ko wacece ta bayyana kanta, sai ko ga shi wannan photon da ta sake turo masa na ƙarshe ya tabbatar masa da lalle Khadijarshi ce, saboda ko a mafalki ya ga gefen fuskarta sai gano ita ce bale a ido biyu, sai dai kuma kokwanton da ya ke yi akan anya zata iya aikata hakan gareshi,sai ga shi da tsintar kanshi cikin wani tsantsar farin ciki marar misaltuwa, cike da zumuɗi ya yi saurin mayar da reply da cewa

_"wow! wonderful babe! plss Ina buƙatar wasu pic's ɗin amman masu ɗauke da kyakkyawar fuskar da ke jikin wannan tsadadden body"_

Cike da jin daɗin yabon da ta ji ya yi mata ta yi saurin rufe furkarta Kamar a gabanshi, kasancewar itama a matse take da son Mijinta na ta cikin sauri ta mayar masa da reply ɗin cewa

_"Thanks my angel"_

Safwan ya bi text ɗin da kallo zuciyarshi cike da tsanani ƙaunar Dijenshi, duk da bai tabbatar da ita ɗin ce ba amma jikinshi ya ba shi ita ɗin ce shiyasa ya sake cewa da ita

_"More pictures plss"_

Ta mayar masa da reply ɗin

_" No bye"_

Ya yi saurin rubuta _" wait! wait! plss my precious what's your name?"_

Dije zata mayar masa da amsa kenan ta ji muryar Aunty Ummin zata shigo ɗakin, cikin sauri ta ajiye wayar ta faɗa toilet, ko da ta zo taga bata ɗakin ta ce

"Ki fito ki ci abinci Ni bana son yi wa kai horon yunwa"

Daga cen toilet ta yi gyaran murya alamun ta ji ta sannan Aunty Ummin ta fice ɗakin, cikin sauri Dijen ta tuɓe Uniform ɗinta daga cen toilet ɗin ta yi wanka a gurguje ta fito, sai ga kira ya shigo wayarta tana duba sunan mai kiran ta ji ƙirjinta ya buga dam! Amman ta yi jarumtar ɗauka sannan ta ajiye wayar akan gadon ba tare da sanin cewa Video call ne Safwan ya kirata ba, ta ƙurawa wayar kallo ta kasa ɗauka bale ta saka a kunnenta sai ganin fuskarshi ta yi cikin screen ɗin wayar ta yi saurin zaro ido waje tare da dafe ƙirji, inda shi ma ɗin ita yake kallo cikin mamakin yanda ta koma saboda daga ita sai guntun towel iya cinya, ga abubuwan da yake so cike fal a ƙirjinta ba shiri ya tsinci kanshi cikin wata kasala tare da faɗin

"Khadijah me yasa kika tafi kika barni? Me na yi maki da ......."


Fisge wayar da aka yi a hannunshi ne yasa maganar da yake yi ta katse, saboda ZEE cike tsantsar kishin kiran sunan Dijen da ta ji ya ambata yasa ta ƙaraso wurinshi ba tare da ya kula da ita ba, hango yanayin da Dijen ta ke ne duk da bata ga fuskarta da kyau ba yasa ta ji wani bala'in kishi ya rufeta, wanda ya janyo ta fisge wayar da ƙarfi tare da dokata ga ƙasa ta tarwatse, ya bita da kallon takaici ranshi a matuƙar ɓace ya ɗaga hannu ya watsa mata wani wahalallen mari har sau biyu, sannan ya zare belt ɗin jikinshi ya yi ta mazgarta tana ihun neman taimako babu mai cetonta, sai da ta lallasu da kyau sannan ya saurara mata cikin fushi ya ce

"Akan wannan rashin hankalin naki WALLAhi zaki janyowa kanki wahala a hannuna, ko an ce maki ina cikin mazajen da mata suke juyawa ne?, Ke har kin isa ina tare da matata ki hanani yin abunda nake so?, To bari ki ji akan wannan haukar ta ki zaki janyo wa kanki komawa Nigeria WALLAhi, saboda ina da ikon da zan datse karatun naki gaba ɗaya idan kuma akwai wanda ya isa ya ce sai kin ƙarasa to sai ya dawo da ke in gani"


Yana ƙare maganar ya wuce fuuu ya fice ya barta tana ta kuka tare da mamakin wai ita ce yau Man ɗinta ya daka akan matsiyaciyar Matarshi.




To fa su Zee an Fara sanin wanene Safwanu😊







Akafta😝







D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Ina alfakhari da ku my fans saboda ku ne ƙashin goyon bayan duk wata ɗaukaka da zan samu, ina yinku all a ko'ina kuke kuma a duk inda kuka kasance, tsakanina da ku sai son so fisabilillah😅*


*Lamba ta 61*



Sai da ta ci kukanta ta ƙoshi sannan ta baiwa kanta haƙuri dolenta, don bai dawo gidan ba har sai da ya tabbatar da ta yi bacci sannan ya shigo, saboda baya son haɗa ido da ita akan nauyin dukan da ta janyo ya yi mata, duk da wani sashe na zuciyarshi yana ba shi cewa ko kaɗan bai yi laifi, don yanda ya ƙagu da yasan inda Khadijarshi take komi zai iya aikatawa akan wanda ya ke so ya toshe masa ƙofofin da da zasu sadashi da farin cikinshi.

Sannu a hankali ya ƙaraso wajen wayarshi da ke tarwatse har lokacin, ya duƙa ya ɗauki kangalwar wayar ya zare sim cards ɗinshi sannan ya saka cikin wata sabuwar wayar da ya siyo, sai dai baƙin cikin rashin saving ɗin numbar Dijen da bai yi ba tun farko yasa ya dannawa Hajiyarshi kira, bayan sun gaisa ya marairece murya ya ce

"Haba Hajiyarmu plss don ALLAH ki sanar da ni inda aka kai Khadija, saboda jikina yana bani cewa ba aikatau Khadija ta je ba, don ALLAH ki tausaya man Hajiyarmu ki bani matata WALLAhi ina sonta sosai"

Hajiya Mama ta yi shiru sannan ta ce

"Ka kwantar da hankalinka duk lokacin da ka dawo ƙasar nan insha ALLAHu zaka taradda kHadija a gidanka zaune tana jiran dawowarka"

Cike da tsananin jin daɗi ya ce "in dai haka ne to ni ai sai in tattaro kayana kawai in dawo gida Hajiyarmu"

Ta ɓata fuska kamar tana ganinshi ta ce "shi karatun na ka idan ka dawo wa zai ƙarasa maka shi ne?bayan saura lokaci kaɗan ka kammala"

Safwan ya sosa kanshi yana murmushin jin daɗi ya ce "to Hajiyarmu me zai hana ayi mata viza kawai ta samemu anan ɗin ta tayamu zaman, kin ga in mun kammala sai mu dawo gida tare gaba ɗayanmu?"

Hajiyar ta yi ƴar dariya sannan ta ce "ita kuma karatun nata fa? Sai ta ajiye ta zo ta tayaku naku karatun kenan? to bari ka ji idan ka kawo wasa ko ka dawo bazan bari ka ganta ba, matuƙar baka natsu ka ƙare karatunka da ya rage saura ɗan lokaci ba"

Safwan ya durƙusa ƙasa kamar a gabanta ya ce "plss Hajiyarmu don ALLAH ko numbar da zan sameta ne a bani plss sai mu dinga gaisawa, don wallahi rashin jinta zai iya janyo inyi asarar duka shekarun da na ɓata a baya wajen karatun"

Hajiya ta yi shiru sannan ta ce "zan baka numbar khadija amman da sharaɗin bazaka tambayeta inda take ba har sai ka jira na sanar da kai da kaina, kuma ko da ka gano daga baya ba zaka ga laifin wadda take wurinta ba don Ni na bata khadija da hannuna"

Cikin zumuɗi ya ce "bani numbar kawai Hajiyarmu wannan duk mai sauƙi ne in dai har na sami number'rta"

Ba ɓata lokaci Hajiyar ta saka Fiddo ta yi masa sending number'r ta whassapp cike da zumuɗi ya yi Saving ɗinta a cikin wayarshi sannan ya danna mata kira.

Dije kam kasancewar bata nan tana school saboda lokaci ba ɗaya ba, kuma ga wayar ma a kashe take shiyasa ya yi kira ya kai hamsin amman bai sameta ba, cike da jin zafin hakan da takaici ya yi kwanciyarshi akan kujera ya ƙi zuwa wurin Zee da tunda suka yi aure basu taɓa raba wurin kwanciya ba sai ranar, haka wanibacci mara daɗi ya fisgeshi mai ɗauke da mafalkin khadijar saboda tunaninta ne a zuciyarshi har baccin ya yi awon gaba da shi.

Zee cikin bacci ta shafo gadon ta ji wayam ba kamar kullum yanda ta saba shigewa jikinshi tana shagwaɓa ba, ta yi saurin buɗe idonta tare da kaiwa kan gadon kallo sai gata da miƙewa zaune ba shiri, cikin mamakin sababbin halayen da ya tsiro mata ta sauko gadon ta fito falon, in da ta hangoshi kwance da alamu ma baccin yake yi, nan take wani kuka ya zo mata ta janyo ƙafafuwanta ta ƙaraso bakin kujerar ta yi duƙuso, sannan ta ɗora kanta saman ƙirjinshi ta fara kuka ƙasa ƙasa, cikin bacci ya jiyo sautin kukanta ba shiri ya buɗe ido tare da shafo kanta da ke saman jikinshi, ya yi shiru yana sauraren kukan nata ba tare da ya ce da ita ƙanzil ba, ganin ta ƙi daina kukan ne ya yi dubarar cire kanta ya miƙe zai bar wajen ta yi saurin riƙo ƙafarshi ta ce

"Ka kasheni kawai tunda har ba zaka iya cewa da ni in yi haƙuri in daina kukan ba"

Safwan ya fisge ƙafarshi ya koma ɗakinsu ya yi kwanciyarshi, Zee ta biyoshi cikin fushi ta hau gadon tare da ciyo kwalarshi daga kwancen ta ce

"WALLAHI tun da ba wukaƙantatta ka ganni ba ka yi kaɗan ka wulaƙantani akan wata matsiyaciya"

Kalmarta ta ƙarshe ba ƙaramin baƙanta masa rai ta yi ba, amman ya yi mata shiru tana ta surutanta na cin zarafi gareshi ga kuma Dijenshi, sai da ya ga renin hankalin nata zai yi yawa ne ya yi saurin miƙewa zaune da nufin kai mata wani wawan mari, cikin tsoro ta kwarma ihu tare da sakinshi ta maƙe jikin gadon tana kyarmar tsoro, cike da takaici ya kalleta ya tabbatarwa kanshi idan ya biyewa zuciyarshi ba ƙaramin duka zai yi mata ba, kuma a yanayin jikinta ba ƙaramar illah zai yi mata ba idan har ya ce kullum ya saki ƙwanji ya yi ta jibgarta, shiyasa ya nunata da hannu ya ce

"Ki kiyayi kawo man ƙananan rashin kunya matuƙar kina son jikinki ya tsira da dukana, idan kuma kin fi son in yi ta jibgarki a banza to ki ci gaba da nuna man kalar taki rashin kunya"

Yana ƙare faɗar maganar ya gyara kwanciyarshi ya kwanta abunshi zuciyarshi cike da ƙuncin rashin samun Dijen da kuma takaicin rashin kunyar da Zee take son yi masa,wadda ko kaɗan ba ya jin zai iya ɗaukar mata wannan halin renin da take son kawo masa.

Ganin ya yi fushi da yawa ne ta janyo jiki ta faɗa jikinshi tana share hawayenta ta ce

"To ni dai ka yi haƙuri ai kai ne ka janyo komi muna zamanmu lafiya"

Ya saka hannu ya tureta ta sake maƙaleshi tana yi masa wani salon da ta san zata samo kanshi, amman duk da ya ji abun har cikin jikinshi a hakan ya mazge ya nuna bai ma san me take yi ba, ganin haka yasa ta marairece tana ba shi haƙuri cikin muryar kuka tare da yi masa kalamai masu nuna karayarta a zahiri, sannan ta samo kanshi amman tare da alƙawalin ba zata sake yi masa irin hakan ba, itama ta roƙeshi duk abunda zai yi da Dijen ya yi a waje amman da ya dawo gida lokacinta ne, akan hakan suka shirya yarjejeniya har ta ciyo kanshi suka lula duniyar ma'aurata, duk da cikinsu kowane zuciyarshi ba daɗi amman hakan bai hanasu gamsar da juna ba.

****

Dije kam itama a ƙagauce ta dawo saboda tunanin sahibul ƙalbinta don ba kiran da bata yi masa ba amman wayarshi ta ƙi shiga, ta hau online ta yi ta bulayin jiranshi nan ma bai hau ba, ta yi ta ajiye masa saƙo ya fi goma na damuwa da rashin jinshi amman bata ga ya duba ba, dole ta haƙura ta kwanta, da safe ma cikin sanyin jiki ta yi komi ta nufi makaranta ba kuzari saboda rashin jinshi da bata yi ba, shiyasa yanzun tana dawowa ko Uniform bata cire ba ta ɗauko wayar ta kunna, abun haushi har lokacin bata ga ya duba massages ɗin da ta tura masa ba, dole ta ajiye wayar ta cire kayanta ta shiga wanka.

Da marece sakaliya suna harabar gidan ita da su Husnah da sauran yaran gidan suna shan iska ne kiranshi ya shigo wayar, ta yi saurin komawa ɗakinta ta rufe sannan ta ɗauki kiran da ya zama na uku zuwa huɗu bata ɗauka ba, cike da jin daɗin ɗaukar da ya ji ta yi yace

"Plss! Khadijah me na yi ake son horani da wannan babban horon?"

Cikin ƙasa da murya ta ce "wane horo?"

Ya ce "ga shi nan mana ana ta yi man kala kala, plss ki daina kashe waya bana son in kiraki in ji ta a kashe kin ji??"

Ta ce "tom".

Ya sauke ajiyar zuciya ya ce "kina a ina yanzu haka kuma ke kaɗai ce ko kuwa??"

Cikin daburcewa ta ce

"A'inah nake?" Ya ce "Eh ina nufin a ɗaki ko falo ko kuma kitchen Ko karatu ki ke yi ne?"

Ta ce "a'a ina ɗaki kwance kawai na ke kuma ni kaɗai ba kowa"

Ya yi saurin faɗin

"We'll idan na ce ki yi man wani abu zaki iya yi?"

Ta yi shiru sannan ta ce "eh"

Ya ce "ok tom Ina son ki tuɓe all ki ɗaukar mani pic's ɗinki Kamar guda goma ko fi haka, amman da sharaɗin duk kika zo cire wani abun sai kiñyi man pic a hakan kafin ki cire wani, tukunna ma menene a jikinki?"

Dije da jikinta ya ɗauki rawa ta yi shiru sai da ya yi tambayar sau uku sannan ta ce "riga da siket ne na atamfa"

Ya ce "ok tom oya fara ɗaukar pic ɗin a haka sannan ki cire ɗankwali shima ki ɗauki pic haka zaki yi ta yi har sai kin gama cirewa all sannan ki yi man na ƙarshen wanda shi ne nafi buƙata akan kowane, na baki minti goma kacal idan kin kammala zan kiraki"

Dije ta yi shiru tare da sauke wayar a kunnenta, jikinta sai rawa yake yi saboda tsoro da kunyar wannan abun da yake son ta aikata, har minti goman ta cika ya sake kira bata ko motsa daga inda take ba, shiyasa ya yi ta kira bata ɗauka ba wani bayan wani haka ya yi ta kira tana kallon wayar amman ta kasa taɓa ta, ƙarshe ma kashe wayar ta yi all zuciyarta cike da jin haushin me ma yasa ta bashi fuskar da har zai zo mata da irin wannan fetsara, ta yi kwance tana ta nazarin huɗubar da Inna ta yi mata akan duk abunda ya nema wajenta ta yi masa matuƙar ba saɓon Allah a ciki, cikin sanyin jiki ta buɗa wayar ta kira Sis Aysha da ta ke hardace da numbarta da ta ba su tun makaranta, lokacin da ta taɓa zuwar masu Visiting ita da Hannatu bayan ta ƙare makarantar.

Kasancewar suna communication da juna ne yasa ta kirata tana shiga kira ɗaya biyu ta ɗauka, bayan sun gaisa cike da jin nauyi ta ce da ita zata turo mata text sai ta duba don ALLAH ta bata amsar da ya dace, minti biyu a tsakani ta gama rubuta text ɗin ta tura mata, sai ga reply ya shigo mata akan ta yi masa duk abunda yake buƙata tunda mijinta ne ba wani cen daban ba.

Cike da jin nauyi ta yi duk abunda ya umurceta sannan ta gama ta tura masa su ta whassapp duks sannan tura masa text kamar haka

"Ga saƙon cen na tura idan ka hau online zaka gani"

Tana ƙare tura masa ta kashe wayar all sannan ta sake kimtsa jikinta ta fito suka ci gaba da sha'aninsu ita da yaran gidan, har dare bata kunna wayar ba sai da ta zo kwanciya ne ta buɗa saboda ta ga Ni Ko ya duba, aikuwa buɗe wayar ke da wuya sai ga kiranshi yana shigowa a wayar, ba shiri ta dafe goshi sannan ta ɗaga wayar zuciyarta cike da jin nauyinshi, amman sai ga shi dole yasa ta ware saboda kalaman ƙaunar da yake ta zazzage mata a cikin kunne suna sauka cikin gangar jikinta, inda cikin lokaci ƙanƙani suka tsintsi kansu cikin wani sabon yanayin buƙatuwa da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment