Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

junansu, akan hakan ya kirata video call suka ci gaba da shan soyayyarsu hankali kwance duk da Dijen ba wani sakin jiki take yi da shi ba.

Wasa wasa sai ga Dije zaman ɗaki ya fara aurarta don kuwa yawan kiranta da yake yi yasa bata zama cikinsu Husnah, don yanzu ita kanta Aunty Ummin har ta fara yi mata tsarguwa akan soyayyar da suke kwasa, saboda yanda suke baje kolinsu ita da Malaminta abun ba kama hannun yaro, saboda da an taso school baya dawowa wurin Zee sai dare ya tsala sannan ya dawo ya lallaɓa ya kwanta, tun bata kulawa har ta zo ta fara damuwa tana yi masa ƙorafin rashin zama gidan da baya son yi, ba wani rufe rufe ya sanar da ita saboda baya son ranta ya ɓaci shiyasa ya ke zamanshi a cen wajen don kada ya shigo ya yi wani abun da zata ga kamar ya ci mata fuska, Zee ta fashe da kuka ta ce da shi ita sam bata yarda ba dole ne itama ya bata haƙƙinta itama tana buƙatar kulawarshi kuma ya bata lokacinshi su yi fira tunda ba ta da wani wanda zai ɗebe mata kewa a gidan bale su yi firar.

Ganin ta ɗaga hankalinta ne akan dole sai ya zauna gidan ya fara rage lokacin da yake yi a wajen, cikin haka ne watarana yana chatt da Dijen wani uzuri yasa ya ajiye wayar ya fita, jikin Zee yana rawa ta ɗauki wayar ta fara yi masa bincike saboda ko kaɗan baya bari ta taɓa masa waya, sunan da ta ga Ni saman contact chat ɗinshi ne ya ja ra'ayinta da shiga kundin ma'adanar, sai gata da zaro ido waje saboda mugun ganin da idanuwanta suka yi mata don kuwa photon Dijen ne daga ita sai wata vest shara shara ko hannu bata da kuma gaba ɗaya shafin dukiyar fulaninta duk a waje don har kan nipple ɗinta ana hangowa cikin yar rigar, ba shiri ta kai zaune dafe da zuciya hawaye suna zuba akan fuskarta tamkar famfo, fige wayarshi da ya yi ne a hannunta yasa ta yi saurin kallo inda yake idonta a kanshi ta ce

"Eh kam naga abunda kake ta aikatawa kullum shiyasa baka bari in tab'a wayar, wanda akanshi ne ma ka ke ɗaukar lokaci a waje baka dawowa gida sai dare ya tsala, to ita kuma wannan yar aikin taku da ka ce wa aikatau aka kawota gidanku yanzu kuma akanta ka lalace??, To billahillazi wannan karon sai dai ayi abunda za'a yi ko ni ko ita WALLAhi, don kuwa akanka wallahil'azim ko kasheta zan iya yi matuƙar ta sake shiga sabgarka, na fi son idan har na kasheta ni ma a zo a kasheni"







To fa wata sabuwa na yi nan WALLAh🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️ tun kafin Zee ta gano ina masu leƙe ta shaƙo wuyana😅




Ina baran adduarku akan ALLAH ya baiwa Mahaifiyata lafiya mai ɗorewa😢saboda kwana biyun nan jikin sai a hankali😭





Akafta😝





D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Alhmdllh jikin Mummy ya yi sauƙi masha ALLAH, naji daɗin addu'o'inku sosai da sosai, hakan ya tabbatar man da cewa ni ma ɗin ashe kuna yi na😉, don da har na fara kishi da Dijen Baffah saboda yanda naga kuke sonta da yawa, shine na yi zaton kamar ta fini matsayi😅 ashe dai Ni ma ɗin ta ku ce ba algus tom Alhmdllh na gode sosai🙏🏻*


*Lamba ta 62*



Safwan ya bi ta da kallo baki a sake ya ce "wai ke me yasa ko kaɗan ba ki da hankali ne?, Yanzu ke ashe zaki iya kashe mutum da hannunki saboda kishi?"

Ta murguɗa masa baki tare da riƙe ƙugu tace, "kai da bakinka ka sanar da ni cewa ƴar aikinku ce, kuma daga kai har munafukar ƙanwar ta ka kun nuna man cewa ita ce ke sonka kai baka sonta, to yanzu kuma akan mi take bibiyarka? kuma sannan har ka bata damar da Ni ma da kake aure baka bani irinta ba? Ga shi ka janyo ta yi nasarar shiga tsakanina da kai, don na tabbata akanta ne kake raba daren da kake yi a waje, to WALLAHI ka ji da kyau ka ƙara ji matuƙar baka sanar da ita ta fita sha'aninka ba WALLAhi ka ji na rantse sai na watsa mata fetur na ƙoneta ƙurmus kowa ma ya huta da mugun halinta na bin Mazajen mutane, yar iskar banza baƙar karuwa ALLAH ya tsinewa iyayen da suka kawota duniya ma balle it.......... "

Saukar marin da ta ji ne a kumatunta yasa ta yi saurin haɗiye sauran maganar, cike da mamaki ta ke kallonshii hawaye suna sauka akan idonta ta ce

"My man ni ce na zama jaka a hannunka saboda matarka?, Yanzun ma kuma saboda da tsananin lalacewar akan wata ƙaramar karuwa ka ɗaga hannu ka mareni?"

Safwan ya yi saurin ɗaga hannun da nufin ya ƙara kai mata wani marin, me ya tuna kuma ya dunƙule hannun ya naushi iska sannan ya nunata da yatsa kamar zai tsole mata ido, jikinshi sai tsuma ya ke yi saboda tsabar ɓacin ran da ta cusa masa, ya ce

"Duk ranar da kika sake kiran Matata da sunan karuwa to WALLAHIL'AZIM kin ji na rantse a ranar zaki gano ainahin wanene Safwan, don kuwa sai na yi maki dukan da a RAYUWARKI kaf ba'a taɓa yi maki irinshi ba"

Sannan ya cisgo gashinta da ƙarfin gaske ta yi ƙara fuskarshi daf da tata suna kallon juna ido cikin ido ya ce

"Wannan da kike gani ita ce Matata Khadija kuma Uwargidana wadda kike da labarin na aureta tun kafin ke, zancen Ƴar aiki ya riga da ya wuce tuni don daman cen kawaici ne na yi maki na ƙi sanar da ke gaskiyar wacece, saboda kawai bana son ranki ya ɓaci idan kin ji ina da aure, to amman yanzu tunda har kin gano komi to kenan ɓoyon da nake maki ma ba shi amfani, saboda haka ki kwantar da hankalinki zan baki wata dama"

Ya fidda wayar da key ɗin da take ya damƙa mata wayat a hannu cikin fusata ya ce "karɓi ki shiga chat ɗina da ita da kike son ganin abunda ake yi maki ɓoyo kullum, to yanzu ki shiga duk inda kike so na baki wannan damar ki karanta komi kuma ki ga komi da idonki, kin ga kin hutar da ni akan duk wani labari da zan sake ba ki a yanzu kuma da gaba ma idan ta kama, na ba ki awa biyu ki yi duk abunda kike so saboda kawai idan kin ta shi kashetan sai ki haɗa da Ni, ke in ma da hali ki fara ta kaina kafin zuwan lokacin da za ki haɗu da ita itama ki kashetan"

Yana ƙare maganar ya fice ya barta da waya a hannu baki a sake kamar wata sakarya, idonta akanshi suna zubar da hawaye wasu bayan wasu, saboda tsabar baƙin ciki da takaicin da ya cika mata ciki, cikin sauri ta jefar da wayar kan kujera itama ta durƙushe ƙasa tana wani irin kuka gwanin ban tausayi.

Saboda izuwa lokacin ta fara yin nadamar biyewa son zuciyarta da ta yi ta aureshi, yanzu ga shi ba'a je ko'ina ba ta fara cin karo da takaicin auren mijin wata da ta yi, don ta tabbata inda Aminu ta aura to da babu yanda za'a ya yi mata irin wannan wulaƙancin akan wata mace, tuno irin renin hankalin da ta yi wa Aminun yasa ta ƙara sautin kukanta, don har awa biyun suka cika ya dawo bata daina kukan ba.

Ganin hakan ya ji jikinshi ya yi sanyi ya zo inda take ya ɗagota daga durƙushen ya zauna kan kujerar da ita a jikinshi yana bubbuga bayanta alamun ta yi shiru, saboda shi kanshi zuciyarshi cike take da ƙuncin da ya fi nata, saboda har ga ALLAH ba da son ranshi ya ke yi mata abunda ya ke yi ba, kawai dai don ya kasa controlling ɗin kanshi ne akan Dijen Baffah, shiyasa ya ke jin komi ma zai iya aikatawa in dai hakan zai farantawa Dijenshi, don izuwa lokacin ya fara fahimtar irin yanda take sonshi itama, kawai dai tana ɓoyewa ne don bata son ya fahimci itama ta yi kewarshi don wata manufa ta ta da shi bai gano nufinta ba, haka ya danne ta shi damuwar ya koma lallashinta har ya samu ta yi shiru sai dai ta ƙi cewa da shi ƙanzil har suka shiga bacci.

****

Haka rayuwar auren nasu ya ci gaba da zama yau fari gobe baƙi, duk da ya rage wasu abubuwa da yawa don kawai su sami zaman lafiya, amman kishinshi da Zee ta ke yi abu kaɗan ne zai janyo masu matsala sai an hau sama a dawo a shirya, don izuwa lokacin ita kanta ta matsu da su gama karatun su dawo gida, saboda tunanin da take yi yawan yi akan ita fa muddin bai canza hali ba idan suka dawo gidansu zata koma, ta sa Mahaifinta ya karɓar mata takardarta, don ba zata zauna ciyon zuciya ya kasheta da ƙurciyarta ba akan wata ɗiya macen da bata fita da komi ba.

Haka rayuwa ta yi ta shurawa sati ya zo ya wuce wata ya zo ya wuce shekara ta gangaro itama har ma ta nemi wucewa, sannu a hankali sai ga su Safwan sun kammala karatunsu, sun ƙara wasu watanni ne saboda su harhaɗa komi sannan su dawo, duk da turawa sun so su riƙesu su yi aiki da su ko na shekara ne, amman fafur Safwan ya buga kanshi akan cewa ƙasarsu za su koma itama ta moresu.

***

Dije kam a lokacin tana Ss 3 har ana cukucukun fara jarabawar candy, ga shi Hajiya Mama ta yi wa Safwan alƙawarin duk lokacin da zai dawo zai taradda ita cikin gidanshi, sai dai karatun da take yi yana so ya wargaza alƙawarin, don bata son ta dawo ba tare da ta kammala karatunta ba, amman duk da hakan da lokacin dawowarshi ya ƙaraso dole ba don dukansu sun so ba Aunty Ummin ta tattaro khadija ta dawo da ita Yola.


Hajiya ta zaunar da ita ta fayyace mata komi dalla dalla akan auren da Safwan ya yi ba tare da saninta ba, sannan ta sanar da ita alfanun kaita Abujar da ta sa aka yi don kawai itama ta san minene rayuwa, Dije tasha kuka saboda kishin auren da ta ji ya yi, amman sannu a hankali Hajiya tana ta tausarta tare da nuna mata cewa ita ɗin tana da damar dawo da Mijinta hannunta don ba'a fita da komi ba, sannan ne hankalinta ya ɗan kwanta ta ji sanyi a ranta ta saki jikinta, sai dai duk lokacin da ta tuna da wata mace a tare da shi sai ta yi kuka a ɓoye.

Hajiya Mama ta saki jiki ta gyarewa Dijen Baffah ɗakinta tamkar kowace yarinya mai gata a wurin iyayenta, itama kanta ta fara gyarata ciki da bayanta lungu da saƙonta, don takanas ta nemo wata Mata ta dinka tsima Dijen tun tana jin daɗin karamcin har ta kai ta fara nuna gajiyawarta, dole Hajiya ta ce a dakatar da komi sannan aka koma gyara mata jiki Dilka halawa duka ba wanda ba'a yi mata ba, jikinta ya dawo smuth har wani sheƙi yake yi, ga fatarta hutu yasa ta murje ta cire baƙin ta zama chocolate color, ga gashinta Kuma da kullum yake ƙara cika masha ALLAH, shi ma ba ƙaramin gyara ya ke sha ba a hannun Matar, Fiddo kanta ba Dijen ta burgeta saboda ganin yanda gaba ɗaya ta sauya tamkar ba ƴar ƙauyen da ta sani ba, saboda ta zanzare ta zama wayayyi ƴar boko musamman yanzu da Safwan ya ƙara buɗe mata idanuwa da salon Soyayyarshi, amman duk da hakan ba wata magana mai tsawo da ke haɗasu, saboda ita kanta a yanzu jinta take yi dai dai da kowa, musamman idan ta tuno da ita ɓangaren Amarya take shiyasa ma ko kaɗan bata shiga shirgin Fiddon matuƙar ba dolen dole ce ta janyo ba.

Ana gobe su Safwan za su da wo ne Hajiya ta saka Aunty Ummi da su Surayya da sauran wasu ƴan uwa suka yi wa Dijen rakiya gidan angonta Safwan, zuciyarta cike da farin cikin ganin wannan rana mai cike da ɗinbin tarihi a rayuwarta, saboda tsabar murnar ganin muhallinta har da kukan farin ciki Dijen ta yi, musamman da ta kalli ko'ina sama da ƙasa gabas da yamma Kudu da Arewa taga uwar dukiyar da aka narka mata, ta yi sha'awar ina ma ace Inna da Baffah'nta da ƙawayenta su ma su zo su ga muhallinta, ta ruƙunkume Aunty Ummi sai kuka take cisga, Fiddo kam sai wani yatsine yatsine take yi zuciyarta cike da jin haushin kwashe masu dukiya da Hajiyar ta yi ta zube a ɗakin Dijen, a ranta ta ƙara tabbatar da cewa lalle ba ƙaramin asiri su Baffah su ka yi masu ba musamman ita da SAFWAN ɗin.

Surayya tana dariya zuciyarta cike da jin daɗi ta yi mata raɗa a kunne sai ga Dije ta sunne kai cike da kunya tana dariya, saboda cewar da ta yi

"Ba wani kuka yarinya gobe iwar haka har kin mance da mu kina ta Mijinki"

Haka suka tasata da wasa har ta ware tana mayarwa Surayya suna gidan har dare sannan aka barta da Husnah da wata dattijuwar da zata riƙa yi mata hidima, haka ta kwana cikin farin cikin dawowar Angonta masoyinta kuma Malaminta Muhammad Safwanu JABB'I YOLA.






Ayyururui Amarya ta ango🥳






Akafta😝







D/AUTA Ce✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Ruwan sharhin da kuke ta bugawa akan book ɗin nan ba ƙaramin daɗi yake sakani ba, saboda haka ku ci gaba da fafatawa ni ma in ci gaba da sambaɗo maku labarai😉😂*



*Lamba ta 63*



Tunda sassafe Surayya ta zo suka shiga kitchen sunata hidimar ɗora abincin tarbon baƙi kala kala, ko da sha biyu na rana ta yi duk sun kammala abunda ake buƙata, Dije ta je ta sullo wankan da sai da ta ɓata lokaci sosai wajen wanke ko'ina lungu da saƙo na jikinta, tare da ɗimama kanta da turarukan wanka masu daɗin ƙamshi, waɗanda a hankali har sun fara bin jikinta saboda yanda take yawan amfani da su akai akai tun dawowarta Abuja.

Bayan ta yi SALLAHr azahar ne Surayya ta zauna ta tsara mata kwalliya cikin tsari irin na wayayyun yan birni, kafin ka ce me sai ga Dijen Baffah ta fito sharr! Abunta cikin wata rantsattsiyar shadda golden color har sheƙin maiƙo take yi, ga ɗinkin da aka watsawa shaddar na stone work shuwari stone sai walwalniya suke yi ta ko'ina idan ta motsa, sannan ga danƙareriyar sarƙarta ta gold da ta ƙara ƙawata kwalliyar, wadda Hajiya ta bata a matsayin kyautar suruka lokacin da za ta zuwa gidan mijinta, ta sha manyan awarwaro da agogo tare da Zoben azurfan da ke maƙale a yatsanta na biyu, wanda ya ƙara fito mata da zarazaran dogayen yatsunta da suka sha ƙunshin jan lalle masha ALLAH.

Dijen Baffah ta yi kyau iya kyau kamar ka saceta ka tsere saboda wankan ya hau jikinta sosai ya zauna, suka fito harabar gidan sai ɗaukar photuna suke yi ita da su Surayya da Husnah, Fiddo kam latsar wayarta kawai take yi saboda fushin da take yi na tilastata da Hajiya Mama ta yi akan sai ta zo gidan, don ta so ta yi zamanta acen gida tunda dole a cen ne zasu fara zuwa su ga Hajiyar sannan su yo nan gidan.

Shiyasa tunda ta zo ba wanda ta shiga sha'aninshi sai sabgoginta ta ke ita kaɗai, yanda ta share kowa haka duk cikinsu kowa ya shareta suna ta harkokinsu.

****

Malam Safwanu kam suna fitowa jirgi ya ja numfashi ya shaƙi iskan ƙasarshi ta Nageria da ƙarfi tare da lumshe ido ya kallo Amaryarshi da ke gefenshi cike da wani salon da shi kaɗai yasan ma'anar kallon, ganin haka ta ƙara maƙale hannunshi da take riƙe da shi tare da ɗora kanta a kafaɗarshi tana murmushin itama, don on ready ko da suka sauko direba yana airport ɗin yana jiran saukarsu, shiyasa ba tare da ɓata lokaci ba ya kwasosu suka nufo unguwarsu Hajiya Mama domin su fara gaisawa kafin su je cen gidan nasu, Zee haka kawai ta tsinci kanta da faɗuwar gaba tare da jin kwatakwata bata son zuwa gidansu Hajiya Mamar, saboda tunaninta ya tafi ne akan cewa Dijen tana gidan, sai dai har aka gama gaisawa da juna cikin farin ciki da ɗoki tare da murnar ganin juna bata hango ko mai kama da Dijen Baffahn ba, taji daɗi sosai a ranta saboda tunaninta har lokacin tana cen Makarantar da aka ce tana yi, shiyasa ta saki jiki sai wasar baki take yi anata gaggaisawa kafin su yi sallama da juna su fito gidan, tare da rakiyarsu Hajiyar da Aunty Ummi da yaranta da wasu ma'aikata mata da suka biyosu suna yi masu addu'ar sauka lafiya, Safwan ya kalli Hajiyar bakinshi yana rawa saboda son tambayarta da ya ke yi akan alƙawarin da ta yi masa, cikin dariya Aunty Ummi da ta fahimceshi ta yi saurin faɗin

"Mun kai maka tana cen kai take jira"

Zee da ke mota tana wasar baki ba shiri ta ji ƙirjinta ya buga, duk da ce wa bata gano ma'anar inda maganar ta dosa ba amman ta yi wasiwasin cewa

_"Anya ba wannan mayyar yarinyar ba ce ake magana a kanta ba kuwa?"_

Sai gata da haɗe fuska tana dariyar yaƙe har suka bar gidan, cike da tsananin farin da jin daɗi Safwan ya riƙo hannunta ya ce

"Hajjaju ayi murna mun dawo ƙasarmu ta gado, sai hankali ya kwanta ga ki kusa da Daddynki da kullum kike ta faɗin kin matsu ki ganshi, tsorona ɗaya shine kada ace gulmata ce ake zumuɗin kai wa?"

ZEE ta yi dariyar yaƙe ba tare da ta ce komi ba, saboda faɗuwar gabanta da ya tsananta bugawa cikin sauri da sauri, har suka je bakin kantamin Gate ɗin gidan nasu bata ji natsuwa ta zo mata ba, hankalinta ya fara ta shi ne lokacin da Direban da ya ɗaukosu ya ke ta buga horn wani bayan wani alamun sanarwar zuwansu.

Ai kuwa kafin ma su je parking space ya ajiye motar sai ga su Surayya da su Husnah tare da Ruma ƙawar zee da wasu ƴan'uwanta biyu aguje sun fito, su Surayya daga sashen Khadijar suna ihun murnar dawowarsu, yayin da su Ruma suka fito daga nata sashen cike farin ciki, gaban Zee ya ƙire ya faɗi ba shiri ta yi saurin fitowa tana ƙarewa gidan kallon yanda aka ƙawatashi da sabon fenti, sannan ta dawo da kallonta ga su Surayya da suka maƙalkale Safwan suna murnar ganinshi, su Ruma suka ƙaraso wurinta cike da murna suna yi masu sannu da zuwa, Fiddo ta saki Safwan ta nufo Zee inda ta wani haɗe rai tana yi mata wani mugun kallo, ba shiri Fiddo ta sha jinin jikinta tare da wayancewa da dannar wayar da ke hannunta.

Cen sai ga wani taku da ya ja hankalinsu duka tare da shaƙo wani daddaɗan ƙamshin da iska ya kwaso ya shaƙawa Zee cikin hanci tamkar da gayya cikin lamarin, ta yi saurin kallon inda take jin sautin takun takalmin sai gata da dafe ƙirji ba shiri, cikin matsanancin faɗuwar gaba tare da dakan luguden da zuciyarta ta ke yi ne ta yi mutuwar tsaye, Dukansu suka ƙurawa Dijen kallo musamman ita da ta kafeta da ido ƙur har ta ƙaraso wurinta, cikin sigar duniyanci Dijen ta rungume Zee fuskarta ɗauke da fara'a ta ce

"Oyoyo Ƙanwata sannunku da zuwa da fatar kun iso lafiya"
Ta ƙare maganar tare da fesheta da wani sabon murmushin da Zee ta kasa gano ko na minene, sannan Dijen ta saketa ta nufi Safwan ɗin da tunda ya ƙyalla idonshi akanta gaba ɗaya ya susuce, yanda ya ke kallonta cikin shauƙin sonta da ke fisgarshi haka ita ma Zee ta bi ta da kallon mamaki, tare da su Ruma da suma ta zamo masu tv saboda kallo.

Dije kam tana zuwa ta yi saurin maƙaloshi tare da yin tsalle ta kai masa kiss a kumatu sannan ta faɗa jikinshi ta ruƙunƙumeshi sosai cikin wani tsantsar farin cikin ganinshi tana faɗin

"Am happy to see you my Husby, your welcome key to my life"

Daga Safwan ɗin har su Zee kasa ɗauke idonsu suka yi gareta saboda tsabar mamakin da ta ba su, duk da wani sashe na zuciyarshi yasan fiye da hakan ma zata iya aikatawa tunda har yasan kalar koyarwar da ya yi mata, sai dai ita Zee mamakinta ya Sha bambam da na shi don kuwa ita ƙarfin halin yarinyar take mamaki musamman da ta kirata ƙanwarta, amman kasancewar itama ɗin ba baya ba wajen kishi shiyasa ta yi saurin ɓoye kukan da ya zo mata ta nufi sashenta su Ruma suka dafe mata baya suka barsu anan ko waiwayensu bata sake yi ba.

Ganin hakan ya sa Safwan ɗin sakin jikin ya mayar mata da martanin sumbar da ta yi masa a leɓenta, sannan ya ɗora kanshi saman wuyanta ya kai mata wani zazzafan kiss ta yi saurin zullewa tare da riƙo hannunshi tana dariya ta ce

"Oya mu je daga ciki kada ka janyo muna abun magana gaban mutane"

Saboda yanda ma'aikatan suke ta satar kallonsu a fakaice ga kuma fiddo da ke tsaye itama, lura da hakan yasa ta hilatoshi suka shige sashenta, wanda shi biye da ita kawai yake amman sam gaba ɗaya ya manta kowa da komi sai ita, yana jin wani daɗi yana huda ko'ina na jikinshi saboda farin cikin ganinta, yau ga shi ga ma'ul hayatynshi Dijengalar Baffah kuma Black cat ɗin shi ada, wadda yanzu ta zamo masa fitilar da yake amfani da haskenta matuƙar yana son ya gane gabanshi.

Surayya da su Husnah da sauran wasu ma'aikatan gidan tuni suka kwashi kayan da Direba yake fitowa suka fara shigarwa sashen Zee, sannan suka koma sashen Dijen inda ita kam tuni ta shige da Mijinta ɗakin da yake mallakinshi a cikin sashen nata ta fara ɗorashi a saiti, don tun shigarsu ya janyota jikinshi ya fara yamutsata tare da aika mata da saƙunan kisses tamkar wani zautaccen mayen ƙarfe, ganin in ta biyeshi za su ɓata lokuta masu yawa yasa ta yi dubarar riƙe hannunshi cikin wani kallo ta ce

"Plss mu je ka yi wanka ku ci abinci kai da Amaryarka kada ta ɗaukeni mai rowa, don na tabbata dukanku kuna buƙatar abincin"

Ta mairaire fuska har da riƙe kunne alamun ban haƙuri sannan ya miƙe tare da dafe goshi yana yi mata kallon mamakin irin wayewar da ta yi masa ta bazata, sannan ya riƙo hannunta ya ce

"Wayo ko? To ai mu je ɗin sai ki tayani wankan don na fahimci so kike ma ki nuna kin fini girma"

Dije ta yi yar dariya sannan ta rufe fuska da hannu ɗaya ta ce

"Ni dai mu je ɗin kada ta ga an ƙyaleta"

Sannan suka je toilet ta haɗa masa komai zata fito ya ce ta jirashi amman daga nesa don baya son ta ɓata masa kwalliyar, ita ko ganin hakan yasa ta yi nazarin kawai ta taimaka masa tunda Surayya ta sanar da ita hakan ma yana ƙara shaƙuwa tsakanin ma'aurata, aiko ta saki jiki ta ajiye kunyar ta taimaka masa sai gata itama ya janyota suka faɗa ruwan ya yi nasarar cire mata kayan ya dinga mammatsewa tare da tanɗewa da lashe abubuwan da ya fi so a rayuwarshi, duk da take jin zafin zafin abunda ya ke yi amman ta nuna masa lalle itama ɗin yanzu ba da bace, da ƙyar ta lallaboshi suka fito toilet ɗin bayan dukansu sun tsalkake jikinsu.

Yana rama sallolin da suka kubce masa ne ta sulale ta wata ƙofar da ke sadata da ɗakinta ta sake yin wani sabon shiri cikin wani danƙareren less bulue black, Wanda aka yi wa ɗinkin riga da siket ya hau jikinta sosai, saboda ɗinkunan takanas Aunty Ummi ta ɗinka mata su Abuja don kawai ta ji daɗin tarbon Angonta, bayan ta kimtsa fess abunta sannan ta sake feshe jiki da turarukanta masu daɗin ƙamshin sannan ta koma wurinshi, yanda ya lalace da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment