Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yi mata ba, asali ma shine ya ƙara banbantata da sauran mata, don fatarta ta murje luwai luwai ta washe gwanin burgewa, ga ƙirjinta cike fam da dukiyar Fulani kuma a tsaye suke ƙyam! ba alamun zasu ranƙwafa a gaba, saboda girkin kwarya ne da su sun cika fam kuma sun baje a ƙirjinta, duk da ba wai sun gama girman bane amman a hakan ma sai sambarka.

Ana saura kwana takwas bikin Surayya ne su Dije suka kammala zana jarabawar j.l.cn tasu, cike da farin ciki da jin daɗi suka baro makarantar tana ɗokin zuwanta gidan saboda shagalin bikin Surayyar da zasu yi.

Aiko tana dawowa suka ci gaba da shirye shiryensu tare da abokan Surryn yan jami'a, don Surry ta kammala degree ɗinta na farko cikin nasara ba tare da samun matsala ba, Fiddo ce ta yi candy a lokacin.

Ana cikin hidimar ne gaba ɗaya suna babban falo sunata tsare tsarensu ne Safwan ya kira Fiddo, cike da tsananin jin daɗi ta cire wayar daga caji ta ɗauka tana faɗin

"Oyoyo big bros don ALLAH ka zo cikin lokaci plss kasan fa kai ne idonmu"

A cen gefenshi ya ce

"Kada ki ji komi zan zo har ma da Auntynki itama zata zo bikin kuma wajenki zata sauka"

Fiddo ta yi wani tsallen jin daɗi sai dai suna haɗa ido da Dije ta maka mata harara tace,. "Kada ka ji komi big bros bani ita mu gaisa idan kuna kusa"

Zee ta karɓa cike da jin daɗin ganin yanda ƙanwarshi ke sonta tace, "Sannu Sis ki tanadi masaukina insha ALLAHu da ni za'a sha shagalin bikin Surry ki zuba idon ganina kinji"

Fiddo ta yi saurin faɗin "kina da babban masauki big Aunty fatana kawai ALLAH ya kawoku lafiya"

Safwan ya karɓa yace

"Ina Surryn?"

Fiddo ta yi wajen Surry ta miƙa mata wayar cike da jin daɗi ta ce

"Amaryar Yaya Safwan ma zata zo bikin wayyo daɗi"

Diirim! dum! Ba shiri kirjin Dije ya buga, cikin son jin gaskiyar abunda kunnuwanta suka jiye mata aranta tace

_"Amarya? Wace Amarya kuma?..."_

Tunaninta ya katse ne lokacin da Surry ta kara mata wayar a kunne cikin sassauta murya tace, "Yaya Safwan ne"

Gaban Dije ya ƙire ya faɗi ba shiri cikin ɗimaucewa ta ji wani kuka ya zo mata ba tare da ta tantance ba, saboda maimakon ta ji muryar Safwan ɗin sai jin ta yi Zee tana cewa

"Ina fatar zaku tarybeni a matsayin Matar yayanku, kuma ku ɗauki cewa tamkar ma an ɗaura na shigo familynku"

Cikin sauri Dije ta saki wayar ta miƙe da gudu ta nufi ɗakinsu, saboda zuwan wani dunƙulallen abu a ƙirjinta, wanda ya janyo ta kasa juriya bale ta haƙura da kukan bazatan da ya zo mata.





Gareku reader's shin minene wannan abun da ya ziyarci zuciyar Dijen Baffah????????😢









Akafta🤞🏻







D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Domin farin cikinku kawai mutanena😅*



*Lamba ta 43*



Dije dunƙule kan gado tana kuka ta ji an dafa kanta cikin sauri ta goge hawayenta ta ɗago fuskata, aiko caraf ta yi ido huɗu da Hajiya Mama fuskarta ƙumshe da damuwa, ta yi jarumtar washe bakinta guntayen hawayenta da suka maƙale suka faɗo, cikin basarwa tace

"Me aka yi maki Hajiyata?"

Hajiya ta sake dafa kanta ta shafo dogon gashinta tace,. "Naji komi Surayya ta faɗa man ki yi haƙuri ki barni da shi ai zai zo garin ya sameni ina jiranshi"

Dije ta yi saurin faɗin

"Ki ƙyaleshi kawai Hajiya Ni na haƙura da duk abunda ALLAH ya ƙaddaro man, haka kuma ma zan yi biyayya ga duk abunda kika umurceni"

Hajiya Mama cike da jin daɗin canjin da Dijen ta samu a wurinsu tace,. "Ki yi ƙoƙari ki nuna masa cewa fa ke ma mace ce duk runtsi kada ki bada wata ƙofa da shi ko yarinyar zasu renaki"

Dije ta ɗaga kanta alamun gamsuwa Hajiyar ta riƙo hannunta tace, " saki jikinki ki koma ku je kuci gaba da shirye shiryenku, ki yi kamar daman cen komai bai faru ba"

Sai da tasata ta je toilet ta wanko fuskarta sannan suka fito tare.

Haka aka ci gaba da hada hadar tare da Dijen duk da zuciyarta ba daɗi amman hakan bai hanata nuna annushuwa kan fuskarta ba, sai dai kuma Fiddo tasha jinin jikinta saboda faɗan da Hajiya Mama ta yi mata akan abinda ta yi a gaban Dijen, duk da ta ci alwashin bazata fasa nuna ƙaunar budurwar Safwan ba ko don Dijen ta ji haushi.

Ana saura kwana huɗu bikin ne Safwan ya diro Nageria tare da budurwarshi, sai dai ita ta yi garinsu sai taga gida sannan ta zo bikin daga baya, a ranar da ya diro gidan da marece za'a je yin wani event mai suna tea party, duka Amarya da ƙawayenta da ma ita kanta Dijen da Fiddo duka sunyi shigar wani yadi milk da kalar cofee, kowacensu ta sha makeup irin na classic ladys masha ALLAH gwanin burgewa, har sun shishiga motoci ne aka manta da agogon Amarya akan stool ɗakinsu, shine Dijen ta fito ta koma cikin sauri da nufin ta ɗauko ta dawo ana jiranta su tafi.

Ta ɗauko agogon ta fito kenan a tsakiyar babban falon suka yi karo har tana ƙoƙarin faɗuwa, cikin sauri ya riƙota ta faɗo jikinshi tare da riƙeta ƙam ƙam don kar ta faɗin, jikinta yana ɓari ta yi saurin kai kallonta gareshi saboda turaren da ta ji ya tabbatar mata da cewa shi ne, ido cikin ido suka kalli juna dukansu a lokaci ɗaya gabansu ya faɗi ras! ras!, Cikin sauri ya saketa duk da bai tabbatar da cewa ita ɗin ce ko ba ita ba, itama kanta ta aro wata jarumta ta yi kamar ma bata taɓa ganinshi ba ta duƙa ta ɗauki agogon da faɗi ta fara taku a hankali cikin wani salon da ita kanta batasan ta iya irinshi ba ta fice, Safwan ya bi bayanta da kallo har ta ɓacewa ganinshi amman bai daina kallon ƙofar ba, cikin wani hargitsatstsen yanayi ya ja jakarshi ya nufi ɗakin Hajiya Mama, don gidan shiru saboda mutane da yawa sun tafi partyn.

Dije kam har ta shiga motar suka tafi ƙirjinta bai daina bugawa ba, saboda ganin bazatan da ta yi masa duk da daman cen tasan da zuwan nashi a ranar.

Sun gudanar da bikinsu masha ALLAH ansha rawa Amarya da Angonta sun gwangwaje tare da abokan ta da yan uwa da abokan arziƙi, Dije ma ba'a barta a baya baya bayan photunan da aka sha kala kala kowace da kalar nata salo ba ƙarya.

Bayan an watse taron ne wani ya biyo Dije har gida saboda tun a cen wajen ta ɗauki hankalinshi sosai, yana biye da komi nata har suka dawo gidan, suna ƙoƙarin kwasar wasu kaya ne a bayan boot ya yi mata sallama.

Ba shiri ta ɗago tana ƙare masa kallo sama da ƙasa sannan ta amsa masa sallamar a yangance, cike da jin daɗi ya yi wani tsadadden murmushi yace

"Khadijah ko?" tayi saurin zaro ido waje tace

"Ni? ko dai wata Khadijar?"

Matashin saurayin yace, "ke dai tawa khadijar"

Dije ta zaro Ido waje ta kinkimi kayan da zata ɗauka ta yi cikin gida don ita sam ma bata kula da Safwan da ke zaune harabar gidan yana chat da Zee ba, Amman shi tun daga nesa ya ƙura mata kallo har ta shige, sai dai kuma ganin wannan matashin saurayin ya bita da kallo ne yasa ya yi saurin miƙewa ya soka wayar aljihu ya nufo wurinshi, wanda kafin ma ya isa sai ga Dije da Fiddo sun zo kwasar wasu kayan, Saurayin ya sake nufar Dijen yana faɗin

"Haba Khadijah ki tsaya ki saurareni mana, WALLAHi takanas wannan zuwan da na yi a nan donki kawai na zo"

Ganin Safwan a wurin yasa ta yi saurin washe baki tace, "ALLAH sarki ka yi haƙuri daman na je ne in ajiye kayan in dawo, to ya kake dafatar ka zo lafiya?"

Cike da mamaki Safwan da Fiddo suka bita da kallo, Fiddo ta yi saurin faɗin

"Malam ina zaka kai zunubin fira da matar aure?"

Saurayin ya zaro ido waje zai yi magana Dije ta yi saurin faɗin,

"No! no! Share da ita wasa ce take yi maka dubanni da kyau, kai kanka ai kasan banyi kama da matan aure ba ko?"

Fiddo zata sake yin magana Safwan ya yi mata alamu da ta yi shiru, dole tayi gum ba shiri saboda bala'in tsoronshi da take yi , Dan Saurayin kam ya bi Dije da wani shu'umin kallo sama da ƙasa ita ko sai wani girgizar jiki take yi tana fesa masa wani murmushin da ita kaɗai tasan ma'anarshi, sai dai ɗagowar da zai yi a ƙoƙarinshi na son mayar mata da martanin kallonta Karaf yaji saukar naushi a fuskarshi, kafin ka ce me ya fara lallasuwa a hannun Malam Safwan, don kuwa sai da ya ci nasarar haɗa masa jini da majina, da ƙyar aka ƙwaceshi a hannunshi don saboda baƙar zuciya irin tashi duk tambayar da ake yi akan me ya yi masa ƙanzil bai iya furtawa ba, hasali ma shigewa ya yi ɗakinshi ya dantse yana kuncinshi shi kaɗai.

Dije kam zuciyarta fes ta kwashi sauran kayan ta yi cikin gida,inda ta taradda Fiddo tana gayawa Hajiya abinda Dijen ta yi wanda har ta janyo aka yi faɗan.

Hajiya ta yi murmushinta mai cike da ma'anoni tace da Dijen kawai ta daina yin irin wannan wautar saboda shi aure ba'a wasa da shi, amman bayan haka ba wani faɗa ko jan kunne da ta sake yi mata, Fiddo kam ganin ba wani mummunan matakin da Hajiyar ta ɗauka akanta yasa ta ci alwashi a ranta na cewa

_"sai na zuga Yaya Safwan ya jibgi shegiya kafin ya koma tunda ita Hajiyar mutanen ƙauyen sun shanyeta bata ganin laifin wannan munafukar ƴar tasu"_

Haka Safwan ya kwana cikin kuncin Dije kam ko a jikinta asali ma yi ta yi kamar ma batasan ta yi wani laifi ba, ko da safiya ta waye aka fara hidimar yin kamun Amarya wanda mutane da yawa sun ci buri a kanshi ciki kuwa har da Dijen Baffah, don kuwa tun da sassafe suka je gidan lalle tare da Amarya, bayan an ƙare ne suka halarci wajen gyaran gashi sai ga Dijen Baffah ta fito shar tamkar wata sabuwar Amaryar, masha ALLAH da ita gwanin burgewa bayan sun dawo gida ne saboda ɗakinsu mutane sun yi yawa ta yi ɗakin Hajiya domin ta shirya, saboda lokaci yana so ya ƙure masu saboda daɗewar da suka yi a wajen saloon ɗin.

Cikin sauri ta tuɓe ta shige wanka a gaggauce ta fito da guntun towel ɗinta iya cinya amman a hakan da shi take yin tsalle tana goge dumbujen gashinta da ya sami ruwa ta gefe ɗaya, ba tare da ta damu da gudun shigowar wani ba saboda baƙar wautarta, sai ko gashi ta yi wani tsalle ta saka gefen towel ɗin tana goge bayan kunnuwanta, wanda hakan ya yi dai dai da shigowar Safwan, cikin rawar jikin ta gyara sai ga guntun towel ɗin ya suɓuce ya faɗi ƙasa.

Ba shiri ya dafe kai tare da zaro ido waje saboda abunda ya gani ya janyo masa wani abu a zuciya tamkar bugun guduma, cikin sauri ta yi wata kuwwa tare da kwasar towel ɗin ta koma toilet aguje ta dantse tana rufe fuska alamun jin nauyin abunda ya faru, makyarkyatar tsoron hukuncin da zai yanke mata, tare da tsananin jin haushin kanta akan abinda ya faru don kada ya ce zai faɗawa wani ko ya rena mata hankali, daman cen ba da wata ƙima yake kallonta ba bale yanzu da ya ganta irin ganin da kowa na duniya bai taɓa yi mata irinshi ba sai shi.

SAFWAN kam wani sabon tashin hankali ne ya ziyarceshi, dafe da goshi ya fice ya nufi ɗakinshi inda yake jin wani masifar ciyon kai tamkar ya rabe masa biyu saboda tsabar saran da yake yi masa.

Cikin zafin nama ya jawo jakarshi ta tafiya da ya zo da ita ya fiddo wasu tablets ya afa a baki ya kora da ruwa sannan ya kwanta shiru yana nazari, tare da ƙoƙarin kawar da gizon da halittar Dijen take yi masa a ido, sai duk wani motsi nashi abun ya ke kallo a ido ya kasa goguwa akan hasken gilashin idonshi, cike da jin haushi ya ɗauko wayarshi ya fito harabar gidan ya zauna yana waya da Zee, inda take sanar da shi cewa gobe Alhamis zata zo insha ALLAHu.

Suna cikin wayar ne ya fara hango mata suna fitowa kowace da shirinta har ma an fara kwasar wasu ana kaisu inda za'a yi taron kamun.

Ya ci gaba da wayarshi yana yi yana kallon ta ina zai hango Dijen, sai dai duk iya nacinshi bai hango ko mai kama da ita ba, ya kasa haƙuri ya mike ya nufi cikin gidan sai dai tun kafin ya isa cikin babban falon ya hango bayanta wata ƙawar Surry tana ɗaura mata ɗankwali, wanda ba tantama zuciyarshi ta bashi cewa itace don izuwa yanzu ya fara hardace tsarin surar jikinta.

Fiddo fito da shirinta tana hangoshi ta nufo wurinshi tana gayar da shi cikin ladabi tace

"Big bros yaushe Auntyn zata zo ne?"

Idonshi akan Dijen yana kallon bayanta yace,. "sai gobe zata zo amman ki ce da waccen yarinyar kada ta kuskura ta fita gidan nan bada izinana ba"

Yana gama faɗar maganar ya fice ya faɗa Motarshi ya fisgeta cikin zafin nama ya bar gidan aguje, cike da jin daɗi Fiddo ta nufi wurin Dijen tana wata yatsina tace

"To ke kinji ya ce kada ki kuskura ki fita gidan nan ba tare da izininshi ba"

Cikin tsananin faɗuwar gaba Dije ta zaro ido waje tace

"Inji waye?"

Fiddo ta yi mata wani kallon uku saura kwabo tace

"Wanda yake da ikon hanaki fitar idan kuma bai isa da ke ba ki je ƙofa a buɗe take"

Tana ƙare maganar ta fice abunta fuuu tare da wasu ƙawayenta tana yatsine yaysinen ƙara turawa Dije haushi, Dije kam cike da tashin hankali ta fisge kanta daga ɗaurin ɗankwalin da ake yi mata ta nufi wurin Hajiya Mama, inda ta taradda ɗakin a cike fam da wasu yan uwansu, cikin sauri ta dawo ta makure tana sharar ƙwallah a gabanta mutane suke ta ficewa zuwa Kamun, har abokan ango suka zo ɗaukar Surayya ganin tana kuka ne yasa tace da ita ta daina kuka bari ta je ta faɗowa Hajiyarsu, sai dai Surayya abokanta suka matsa mata ba shiri ta bisu saboda jiranta da ake yi.

Duk mai niyyar zuwa wurin kamun ya tafi amman Dije tana makure tana kuka ba tare da Hajiya ma ta sani ba, har sai da wata ta ganta ta je ta sanar da Hajiyar sannan ta zo tana tambayar abunda ya gabata zuwa kamun.

Ba ɓata lokaci Dije ta sanar da ita saƙon da da barwa Fiddo ta faɗa mata, aiko take ran Hajiyar ya ɓace ta fara faɗa tare da danna masa kira, tace da shi duk inda yake ya yi gaggawar dawowa gida ya ɗauki Dije ya kaita wajen kamun da kanshi, sannan ta jaddada masa cewa minti biyar ta bashi ya zo ya tafi da ita, tace da ita ta je ta sake gyara fuskarta kafin ya zo.






Jinjina ga Hajiyarmu ta mutunci👍🏻




Akafta😍





D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*SPECIAL THANKS FOR YOU MY OMEESHER, ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKI HAR GADON BACCINKI, HAƘIƘA MARYAM OMEE KE ƊIN TA DABAN CE A WURINA,KI SANI INA YINKI HAR ABADAN ABADE, ALLAH YA BAR ZUMUNCINMU HAR ALJANNAH, ALLAH YA KAREKI DA SHARRIN MUTUM DA NA ALJAN DA DUK WANI ABU MAI CUTARWA A DORON DUNIYA, UBANGIJI YA ƘARA DAFA LAMURRANKI YA ƘARA KAWO MAKI HASKE CIKIN RAYUWARKI, TABBAS NI DA KE AKWAI ƘAUNA IRINTA FISABILILLAH.*





*Lamba ta 44*


Cike da jin daɗi Dije ta koma ɗakinsu ta wanke fuskarta sama sama a gurguje, saboda kwalliyar da aka yi mata tana nan raɗam, ƙara gyarata kawai ta yi tare da sassaita ɗaurin ɗankwalin sai gata ta fito shar! da ita masha ALLAH, idonta kawai zaka kalla ka gano kukan da ta sha saboda jan da suka yi, amman a hakan ma ta fito ɗagwas ɗagwas abunta, ta ƙara feshe jikinta da turaruka ta ɗauki jakarta ta fito falo, zamanta bai kai na minti huɗu ba sai ga sallamarshi ya shigo yana wani ɓata fuska yana cin magani, ba tare da ya ma kalli inda take ba ya nufi ɗakin Hajiya Mama, daga nan inda take tana jiyo shi yana faɗin

"Don Allah Hajiyarmu ki bar yarinyar nan renani take so ta yi fa, kuma ke kin zo kina goya mata baya ta je ta yi abunda bai dace acen, ki barni da ita don ALLAH ɗazu fa a gaban kowa ta nuna cewa ita bata da aure to a hakan za'a dinga barinta tana shiga ko'ina duk inda taso?"

Hajiya Mama ta maka masa wata jar harara tace, "to Ina ruwanka don tace bata da aure? Auren ne da ita to? ka ga Safwan kar fa ka nemi takura man yarinya, ka barta ta yi abunda take so don kai ma an barka ka je ka yi abunda kake so ko?, To itama tana da ƴanci abarta ta sakata ta wala tunda kai baka so ALLAH zai bata rabonta a gaba, kuma umurni na baka ka ɗauketa yanzu ka je ka kaita cikin ƴan uwanta"

Tana ƙare faɗar haka ta koma ɗaki abunta ta barshi a tsaye zuciyarshi kamar ta tarwatse saboda baƙin cikin da kalaman Hajiya suka sakashi, ya fito fuu yayi waje Dije ta bishi da kallo ganin bai ce da ita ta taso ba yasa ta ƙi binshi, amman sai ga ƙarar tada Motarshi tare da uban horn da ta ji ya fara bugawa iya karfinshi wani bayan wani, cikin sauri ta miƙe ta fito ba tare da ma ta damu da yawan horn ɗin ba ta fara tafiyarta a yangace tana wani basarwa itama fuskarta a haɗe, cike da masifar jin haushinta ya yo kanta da motar kamar zai kaɗeta, amman kasancewar itama zuciyarta a wuya take ko ɗar bata ji ba, asalima tsaye ta yi tana kallon gefe tare da riƙe ƙugu tana girgizar ƙafa, a zuciye ya fito cikin masifa ya ɗaga hannu da nufin sharara mata mari, kallon da ta yi masa yasa ya yi saurin dunƙule hannunshi, sai dai ya yi jarumtar nunata da yatsa yace

"Don kin ga Hajiya tana ɗauke maki shine zaki kawo man ƙananan iskanci ko?, To WALLAHi da kin cikani ɗaukarki zan yi in mayar da ke garinku, don ni aure zanyi bazan juri zama gwauro ba akanki baƙar baƙauyiyar banza, wawuya kawai wadda bata san darajar aure ba in banda ƙaddara ma ni me zai sa in rasa matar da zan aura sai ke?"

Ya nunata a wulaƙance sama da ƙasa sannan ya buga wani uban tsaki ya juya ya shige motarshi tare da rufo ƙofar da ƙarfin bala'i, ganin ko motsi ta kasa yi illa kallonshi da take yi fuskarta a haɗe tana wassafa irin abunda zata yi masa ta huce, yasa ya leƙo da kanshi yace

"WALLAHI idan baki zo ba tafiyata zan yi sai dai aga laifina"

Dije ta yi masa wani mugun kallo sannan ta tako ta buɗe bayan motar ta zauna itama ta jawo Kofar da ƙarfi har sai da tayi ƙara tace garam!, Ba shiri ya waigo baya yace

"Uban wa kika ajiye ya zamo direbanki?"

Ta yi banza da shi ya sake maimaita maganar nan ma ta sake yin banza da shi illa gefe da take kallo tana wani cin magani, aiko a zafafe ya fito ya buɗe murfin ya fisgota iya karfinshi sai gata da faɗowa jikinshi, ba kunya ya saka hannu ya rungumota gaba ɗaya tsantsan don ya kasa controlling ɗin kanshi, cikin zafin nama ta tureshi tare da nunashi da hannu tace

"Babban gangancin da zaka yi kenan a rayuwa ka ce zaka taɓa jikina, don WALLAHi sai na nuna maka cewa Dijen ce dai wadda ka sani ba wata ba, haka ma zan banbance maka tsakanin Khadijah da Dije, idan kuma kana musu ka sake taɓa wani sashe na jikina ka gani, ko an gaya maka cewa ni ƴar iska ce kamar matsiyaciyar budurwar da zaka aura?"

Ta buga masa wani uban tsaki ta buɗe gaban seat ta zauna ta wani hakimce tana wani faɗi tana bajewa,, madadin ya ji ta ɓata masa rai sai kawai ya tuntsure da wata dariyar mugunta, ba tare da ya ce da ita ƙanzil ba ya faɗa motar ya ja da ƙarfi yana tafiya yana shafa gemunshi yana murmushi, kasancewar Dije ba wani sanin garin ta yi ba shiyasa bata gane inda yake bi da ita ba, har sai da suka kai wani katafaren gida wanda tun daga bakin Gate ɗin gidan zaka gano ba ƙaramar nera aka kasa wajen haɗashi ba, maigadi ya yi saurin wangale masa Gate ɗin yana faɗin

"Sannu da zuwa ranka ya daɗe"

Safwan yana amsawa cikin isa kamar ba shi bane ya ke ta faman murmushi ba, cikin faɗuwar gaba Dije ta yi saurin kai kallonta gareshi ta kalli gidan tace

"Ba fa nan ake kamun ba, me ya kawomu nan kuma??"

Ya yi banza da ita ya fice ya karɓi key hannun Maigadin ya leƙo da kanshi saitinta yace,

"Zaki fito ko sai na fito da ke?"

Dije ta ɓoye firgicinta da take ciki tace

"Idan ka ga na fito to ka kaini inda Hajiyarmu ta ce ka kaini ne"

Ya ce "ok to jirani Bari in zo minti biyu"

Ta murguɗa masa baki tare da bin bayanshi da kallo har ya buɗe wata ƙofa da ta kasance gefe ɗaya na farkon shigowa gidan, ya shiga minti biyu zuwa uku sai gashi ya fito tana ganinshi ta wani juya kanta gefe tana cin magani, yana zuwa ya buɗe motar ya riƙo hannunta ta fisge ya sake janyo hannunta da ƙarfi ta riƙe kujera tana faɗin

"Ba nace kada ka koma taɓani ba? Zaka sakeni ko sai na janyo abunda gaba ɗaya unguwar nan zata taru akanka?"

Ba tare da ya damu da zancenta ba ya janyota gaba ɗaya jikinshi tana tureshi yana ƙara maƙaleta ya janyota iya ƙarfinshi tana tirjiya amman sai da ya shiga da ita cikin gidan, cikin tsoro Dije tace

"Ni dai tsaya mu fahimci juna WALLAHi ba a nan ake bukin ba don ALLAH ka kaini inda ake yi"

Ta ƙare maganar cikin kuka saboda ganinta da ta yi har ƙuryar wani ɗaki ya yada ita akan ƙatuwar katifar da ke shimfiɗe cikin ɗakin, tsoronta ya ƙaru ne lokacin da taga yana rufe ɗakin da key, cikin firgici tace

"Don girman ALLAH ka yi haƙuri WALLAHi ni ba ƴar iska ba ce"

Safwan ya waigo yana wata dariya yace

"To Ni da ke waye ɗan'isakan a cikinmu?"

Ta yi saurin faɗin

"Ni ce, Ni ce WALLAHi"

Ya ƙumshe dariyarshi yace,. "To ai ko yanzu zamu gwada ƙwanji irin na ƴan'iskan ai kin iya ko?"

Ta yi saurin girgiza kai tana matsar ƙwallah ganin ya fara cire riga ne ya sa Dije shiga cikin wani mugun tsoro ta zaro ido waje cikin kuka tace

"Ni Dije yau me nake shirin gani ne?"

Safwan ya mazge ya fisgota ta faɗo jikinshi ya fara yunƙurin zuge mata zif ta yi saurin riƙe hannunshi tana kuka tace

"Ka ji tsoron Allah kada ka ci amanar iyayena don kaga basu garin nan"

Safwan ya fisge hannunshi cikin jajayen idanuwanshi ya kalleta ido cikin ido yace,. "Kika kuskura na sake jin wata magana ta fito bakinki sai kinyi danasanin furta ta"

Dije ta yi saurin rufe bakinta tana toshe kukan da zai fito saboda tsabar tsoron da ya bata amman bata daina zubar hawayen kukanta ba, saboda tana ji tana gani ya zuge zif ɗin rigarta tare da zura hannunshi ta ciki, tashin hankalinta bai ƙaru ba har sai da ta ji inda hannunshi ya sauka, ta yi wata zabura tana ƙanƙame jiki tana faɗin

"Ka tausaya man don ALLAH wallahi Ni ba ƴar iska bace kai ma sheda ne don ALLAH kada lalaceni"

Safwan kam laushin dukiyar fulaninta da yaji a hannunshi yasa shi ɗimaucewa, cikin wata siriryar murya yace

"Ba wani abu zanyi maki ba amman WALLAHi idan kika sake yiman gardama sai kin nemi mai ƙwatarki hannuna"

Dije tana kuka tace

"Ka ceci rayuwata WALLAHi Baffahna ya ji wannan labari kasheni kawai zai yi ba zai barni da raina ba,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment