Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

mi ye sunanta??"

Lawi yace,. "Secondary". Dije ta yi saurin maimatawa tace,. "Sakandari?"

Ya ce,. "Eh".

Tace "shekara nawa ake yi a gama to?"

Yace "shekara shida ce itama kamar primary"

Dije ta zaro Ido cikin sanyin jiki tace,. "Anya ko Baffahnah zai barni in yi karatun kuwa??"

Lawi cikin farin ciki yace,. "Me zai hana ke dai kawai kice masa kina son akai ki idan har ya amince ko kina cikin karatun sai a yi muna aurenmu ki je kici gaba a gidana"

Dije ta rufe fuskarta cike da jin kunya ta tashi ta zank'ara da gudu aguje ta nufi gida cikin tsananin farin ciki, Lawi ya bita da kallo yana dariyar shirmenta musamman da ya tuno da zancen zai lalatata ya yi mata ciki don ba ya da imani.



Dijelawis asha luv lfy🤣


Akafta😛






D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*





*MUTANEN K'ARANGIYA GA JINJINAR BAN GIRMA👍🏻😝*


*Lamba ta 18*



Da tsallen jin dad'i ta shiga gidansu sai wasar Baki take yi, Inna ta bita da kallon mamaki wadda ta fita tana kuka yanzu kuma itace ta dawo tana wasar Baki, aiko sai da ta zauna daf da Inna sannan ta kwanta saman cinyarta tana rufe ido da tafukan hannayenta, Inna ta shafo dunbujen tulin gashinta da kullum ba'a wuce yi mata tsoro hudu a saman Kan nata, saboda bala'in jin zafin kitso ne da ita gashi gashin a cikenshi yake da kuma tsawonshi tubarakallah, don ko shartar gashin za'a yi mata idan an kwance sai duk makota sun sheda, saboda kururuwar da zata dinga yi tana kukan wayyo ita zafi, shiyasa kullum kitsonta tsoro hudu ne don ko shi d'in sai Inna ta ajiye bulala a gefe sannan ake yinshi tana kuka har da su majina shabe shabe, saboda in ta kawo mata reni kai tsaye ta ke mazgarta da bulalar, shiyasa in dai har ranar kitson ta zagayo to ko Baffah dole ne sai ya siyo mata wani Abu a matsayin cin hanci don kawai a samu ta natsu a yi kitson lami lafiya, amman da ta canye abun sai a koma tarxomar da aka saba kullum.

Tana shafar gashin kan nata tace,. "Yau kuma me ya saka 'yar Baffah farin ciki irin haka??, Ke da kika fita da kuka to me ya sakaki wannan murmushi da kike ta yi?"

Dije ta tashi daga kwancen ta rufe fuskarta tace,. "Inna mun shirya da D'anbirni har ma ya yi man alk'awali zai sakani Makarantar Likitoci in dinga yiwa mutane allura"

Inna ta zaro ido waje tace,. "Au kin amince zaki aureshin yanzu??"

Dije ta rufe fuskarta alamun jin kunya tare da d'aga kanta, Inna ta bita da wani kallon yaron man kaza tace

"Kina sonshi kenan?"

Dije ta mik'e da sauri zata shige d'aki tace,. "Ni WALLAHI fa bana sonshi amman zan aureshi saboda ya kaini Makarantar koyon Likitanci"

Har zata shige ta dawo baya tace,. "Kin ga shikenan Ni sai in dinga yiwa mutane allura ba har sai an tafi zuwa birni ba"

Inna ta maka mata harara tace,. "To sai aka ce da ke in har kin aureshi a nan garin zai zauna da ke ko?, to bari kiji garinsu nisa ne dashi ke asali ma sai anyi kwana biyu ana tafiya kafin aje cen d'in, kin ko ga Baffahnki ba zai tab'a bari ki yi auren ba saboda nisan da ke tsakaninmu da su"

Dije ta dawo tare da kumbure fuska tana dire diren kafa tana fad'in,. "Ni WALLAHI Inna ina son in zama Likita don ALLAH ki ce da Baffah ya barni in aureshi don ALLAH"

Aikuwa caraf sai ga kunnen Baffah da ke shigowa tare da Usman, cike da mamakin abunda ya jiyowa kunnenshi ya k'araso idonshi akanta yace,.

"Me naji kina fad'a ne???"

Dije ta isa wurinshi da sauri ta rik'o hannunshi tana share yan guntayen kwallar da suka zubo mata tace,. "Baffah D'anbirni yace dani idan na aureshi zai sakani Makarantar likitoci in zama babbar Likitar Mata don ALLAH ka barni in aureshi WALLAHI ina son zama liktanya Baffah don ALLAH kaji?"

Ta k'are maganar tare da d'aga kanta ta kalleshi cikin marairecewa, Baffah ya k'wace hannunshi da ta rik'e ya tureta gefe ya wuce yana fad'in

"Ke wace irin yarinya ce da kullum shirmenki k'aruwa yake yi? Sai ana murna anga sauyi sai kuma ki k'ara tsunduma ruwa? To bari kiji ni zan ganshi da kaina in sanar dashi cewa ba Zan bashi ke ba, tunda har baiji kunyar zaunar dake ya sharara maki wannan k'arya ba, ke kuma da yake ba wayau ne da ke ba kika amince da zancenshi na yaudara, to WALLAHI na sake jin ma kin tsaya da shi kunyi magana sai kinsan d'anjaki dukiya ne, tunda ke kwakwalwarrki bata hasko komi sai shirme mara tushe bale makama, ke Makarantar ma kin daina zuwa daga yau sai nagani in akwai wanda ya isa yasa ki koma"

Haka ya yi ta sababin fad'a Dije kam ta rabe jikin gini sai kukanta take sharba, Usman ya maka mata wata jar harara yace

"Wawuya kawai mara hankali ke in banda wauta irin taki ma me 'yanbirni irinsu zasu yi dake ne? Da har zaki yarda da karyar da ya shinfida maki??ke da ko wanka har yanzu baki iya ba sai bak'ar jik'a jik'ar daud'ar da kike yi kullum, har sai Inna ta gaji da kazantarki ta yi maki a hakan za ki je birnin?? ALLAH yasa ma Baffah ya hanaki sake zuwa Makarantar da gaske muga ta iyayin bacci da Littafin Boko a karkashin filo"

Ya buga mata wani uban tsaki ya shige d'akinshi, Dije ta bishi da harara tare da murgud'a Baki tace,. "Ai billahillazi in na zama likita ko zaka mutu bazan yi maka allura ba"

Usman har zai shige d'akinshi ya waigo yace,. "ALLAH ma ya tsareni da allurarki WALLAHI, kuma yarinya ta jira idan har taga ta zama Likitar sannan"

Dije ta bi k'ofar da kallo tana harare harare sannan ta yi tsugunne tana wasa da kare tana zane k'asa tana rubuta,

_WALLAHI Ni sai na zama likitar nan_

Ta goge ta sake rubuta

_Idan ba haka ba daji Zan koma da zamana acen kuraye da sauran namun daji su cenyeni tunda har ba'a sona._

Haka ta lalace a wurin ta yi ta shirmenta har sai da Inna ta fito ta korata ta shiga d'aki.

*****

A bangaren Lawi kuwa tana tafiya ya nufi wurinsu Maigarin Baki har kunne yake sanar da su cewa Dijen ta amince, Maigarin ya yi masa wani kallo yace

"Yaro man kaza to bari kaji gaskiyar lamarin Mahaifinta ya tabbatar man da cewa ba zai baka aurenta ba, don haka kaje ka nemo wata in har sha'awar aure a cikin garin namu kake yi, ka duba da kyau Akwai sa'o'inta da yawa a garin har ma da wad'anda suka fita, duk Yar da kake so ka nemota Ni zan shige maka gaba har sai ka sameta, matuk'ar ba wannan masifaffiyar yarinyar bace"

Lawi murnarshi ta koma ciki, cikin sanyin jiki yace

"Idan har ba zan sameta ba a bar zancen wata kawai Baba"

Yana kare fad'ar maganar ya mike ya nufi d'akinsu zuciyarshi sai hasko masa fuskar Dije take yi lokacin da take rufe fuskarshi alamun jin kunyarshi, don kuwa saura k'iris ya rage ya ci k'asa saboda wani uban tuntuben da yayi, cikin yamutse fuska ya shiga d'akin ya fad'a kan katifarshi ya baje tare da d'ora hannu a saman goshinshi yace

"Hasbunallahu wa ni'imal wakil!"

Safwan da ke ta game a wayarshi da ko caji har sai sun kaita babban garin sun samo sannan su yi ta maneji har lokacin da ya sake cenyewa, shiyasa suka fara shawarar saka Generator su huta da zirga zirgar kai cajin da suke yi.

Ya yi saurin kai kallonshi gareshi ganin yanayin da ya ganshi yasa ya ajiye wayar ya tashi zaune yana kumshe dariyarshi yace

"Yanzu Kai don baka da imani shine kake so ta yi ciki?? To WALLAHI Ni babu ruwana idan ka janyo ta haifi macizai"

Ya k'are maganar cikin shekewa da wata arniyar dariya tamkar ba Safwan ba, saboda ba k'aramin dad'i ya ji ba akan wannan wasar kwaikwayon da Lawi ya yi da Dijen, Lawi ya mike zaune cikin damuwa yace

" Seriously WALLAHI ina son yarinyar sosai, bansan ta ya zanyi in shawo kan Mahaifinta ba, har in samu ya amince ya bani aurenta"

Safwan kam sai kallonshi yake yi da gabanshi da ke ta fad'uwa da sauri da sauri, cikin dakiya yace dashi

"To ita yarinyar ta amince da kai ne halan?"

Lawi ya dafe kanshi yace, "bana jin yarinyar yanzu saboda na fahimci ta inda zan shawo kanta cikin sauk'i in janyo ra'ayinta a kaina, don ko yanzu na gano tana sona k'urciya ce kawai tak'i bari ta gano hakan, amman Mahaifinta ne matsalata don yanzu Maigari yake sanar dani wai yace shi ba zai auradda d'iyatai gareni ba saboda munyi nisa, to Ni WALLAHI idan zai amince sai in dawo nan garin da suke karkashinshi in nemi aikina a nan, idan na samu sai in zauna nan din mu shimfida rayuwar aurenmu Ni da Matata"

Safwan ya yi masa wani kallo yace,. "Su Kuma iyayenka da sauran danginka sai ka yi ya ya dasu??"

Lawi ya yi saurin fad'in, "Zan dinga zuwa Ina dubosu ai WALLAHI ya fi man da dai ace in rasata gaba d'aya"

Safwan ya buga wani uban tsaki yace

"Lalle akwai alamun tabin hankali a Kwakwalwarka tunda har zuciyarka take hasko maka hakan shine dai dai, yanzu akan mace macen ma wannan kucakar yarinyar ace zaka rabu da kowa naka akanta?? WALLAHI ka yi kuskure don tun wuri ka ajiye wannan shirmen banzar, ko ka manta cewa Kaine fitilar da Mahaifinka da mahaifiyarka da kannenka suke haskawa su ji sanyi?? Ka yi nesa da su ta ya ya kake ganin zasu dauki hakan a matsayinka na mai taimakonsu???"

Lawi ya furzar da iska a bakinshi yace, "ba zaka gane ba ne Abokina WALLAHI ina mugun son yarinyar, nima bansan ya aka yi har ta sami irin wannan mazauni a zuciyata ba kada ka ga laifina plss!"

SAFWAN zuciyarshi sai dakan lugude take yi muryarshi a sarke yace,. "Yanzu kai duk matayen da ke duniyar nan ka rasa wadda zaka so sai wannan bagidajiyar??"

Lawi ya maka masa harara yace,. "Plss abar zancen na godewa ALLAH da har ya b'oye maka abunda ni na hango, wanda a birnin ma ire irenta ne suke d'aga kai suna hurar hanci suna tak'ama, don WALLAHI wannan yarinyar da ka ke renawa ta shiga birni ruwan birnin suka wanketa tas tasha jar miya to WALLAHI ba k'aramar mace za'a yi ba"

SAFWAN cikin fushi yace,. "Da bak'in??"

Lawi yace,. "Ni bakinta bai dameni ba don asali ma bak'inta mai kyau ne idan fatarta ta sami man shafa pure wanda zai gyarata sosai WALLAHI sai ka sha mamaki idan ka ganta wata rana"

Safwan cikin sanyin jiki yace ,. "Shi kuma kauyancin fa ka yi ya ya da shi haka kawai ka sakata Mutane ta dinga kwafsawa???"

Lawi ya sauke nannauyar ajiyar zuciya yace,. "A tsarina tun fil'azal kai ka sani bana son wayayyiyar mace, nafi son macen da komi sai na d'orata akan hanya, wadda duk tarbiyyar da na bata akanta zata hau ta yi tafiya har a cimma nasara a gaba"

SAFWAN ya maka masa wata jar harara kamar ya dakeshi yace,. "To dai ita wannan yarinyar bazata tab'a yi maka abunda kake so kuma kake ta hasashe ba"

Lawi ya yi saurin fad'in "Saboda mi?"

Kai tsaye SAFWAN yace,. "Saboda ba zaka aureta ba"

Lawi ya zaro Ido waje yace,. "Au! don kai kake so ka aureta kenan ko ya ya??"

SAFWAN ya yunkura kamar zai dakeshi yace,. "ALLAH ya rabani da wahala WALLAHI, Kai din ma bazan barka ka aureta ba"





Tofa🤔 Kai ko MALAM SAFWAN banda hana ruwa gudu fa😕





Akafta😊







D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*





*Masu comments da masu share bani da bakin godiya gareku sai dai ince ALLAH ya biyaku ya saka maku da alkhairi, naga comments dinku all kuma na gode sosai dukanku I love you gabza gabza😉*


*Special gift for you my..... HAJIYA DUDUWA Ina yinki sosai wlh💋*


*Lamba ta 19*


Lawi ya bishi da kallo har ya fice sannan yace,. "WALLAHI ka yi kad'an ka hanani abunda nike so, don son Dije cikin jinina yake kuma aurenta kamar nayi na gama don haka ka zura ido ka yi kallo"

SAFWAN ya dawo da kanshi yace,. "Ka rok'i ALLAH ma akan ka bar garin nan lami lafiya ba tare da ka janyo anyi cikin macizai ba"

Lawi ya mike ya fito shima tare da dafa kafadarshi yace,. "Stof jocking my man WALLAHI da gaske nike son yarinyar, don ALLAH ta wace hanya ka ga zanbi in shawo kan matsalar??"

Safwan da kanshi yake duk'e ya d'ago da jajayen idanuwanshi ya d'orasu kan Lawi yace,. "To be sincere Abokina wannan yarinyar ba ajinka bace, kuma kasancewar iyayenta gidadawa ne zaka sha matuk'ar wuya idan kace ala dole itace zaka aura, shawara d'aya zan baka akan ka bi komi a hankali in matarka ce zaka aureta komi tsanani kuwa, amman idan ka tsaurara to garin neman gira zaka fa rasa Ido, baka ga auren baka ga Mutuncinka da mutane suke gani a garin nan, don yanzu kafin aje ko'ina ma shi kanshi Maigarin zai ga kamar baka ji maganarshi ba, tunda har ya fad'a maka gaskiyar abunda Mahaifin yarinyar yace, tare da guje maka aibin da ke tattare da auren yarinyar"

Lawi ya yi shiru sannan yace,. "Wai Abokina ko dai sace yarinyar nan zan yi ne?, Idan muka yi aure na dirko mata ciki acen sannan in dawo masu da ita, nasan izuwa lokacin dole ne ma su hak'ura su janye tsattsauran ra'ayinsu akan kin aurena"

SAFWAN ya bishi da wani kallo baki sake yace,. "Lalle baka cikin hayyacinka to bari kaji kasan ALLAH WALLAHI duk inda ka kaita ka b'oye Ni sai na zakulota na dawowa da iyayenta 'yarsu, don tun wuri ma ka ajiye wannan bak'in kudurin naka tun kafin zuciya ta debeka ka aikata abunda daga baya zaka zo kana danasani, Ni in bancin k'ulafuci irin naka ma me aka yi aka yi wannan bak'ar magen?? Wadda ita kanta har yanzu bata san me ye duniyar ba, to kaje ka aikata duk abunda kake so tunda har ni baka d'aukeni Abokin kwarai Mai baka shawarar gari ba"

Yana kare fad'ar maganar ya tafi abunshi ya bar Lawi da tunanin zuci mai cike da neman mafita akan matsalar auren Dijen Baffah da Inna Hasiya kanwar Usmanu Mijin Hansai.

***

A bangaren Dije kuwa tsawon kwana biyu ta daina kula kowa a gidan, don Baffah yace da ita bazata sake zuwa Makarantar bokon ba, shiyasa ta k'ara shiga kunci kullum ta shige d'aki tanata kukanta har sai INNA ta fara balbalin fad'a sannan ta yi shiru, don tun tana yin banza da ita har ta fara shiga damuwa akan kuncin na Dije, don Baffah in ya fita gonarshi sai gaf da magriba yake dawowa, kuma da ya dawo yake yin arwallah ya nufi masallaci sai isha yake dawowa, sannan shigowarshi gidan ke da wuya zai fad'a wanka don ko da zai kammala sauran abubuwan tuni Dije ta yi bacci, shiyasa baya sanin halin damuwar da take yini da shi ganin hakan yasa Inna ta fara yi masa korafi akan sabon sauyin da Dijen ta shiga, cikin tashin hankali ya nufi d'akin Innar inda take ta baccinta tana sauke ajiyar zuciya, cikin tausayi Baffah ya kalli Inna yace

"Gobe idan ALLAH ya kaimu na amince ta koma Makarantarta amman da sharadin bata ba wannan yaron, idan ta amince shikenan don shima zan je in fad'awa Maigari ya ja masa kunne sosai akan 'yata, don kada in zo in saki baki ya yi mani sakiyar da babu ruwa don Yan birnin nan ba kunya ce da su ba"

Yana kare maganar ya juya zai fita cikin damuwa yace,. "Ni dai WALLAHI ALLAH banji dad'in zuwan bak'in nan garinmu ba, haka kawai muna zamanmu lafiya su zo muna da wani tsirfin tsiya"

Inna ta bishi baya cikin sanyin jiki tana k'ara zayyana masa irin kuncin da Dijen ta saka kanta akan rashin zuwanta Makarantar.

Aiko tun Asuba Inna ta yiwa Dije albishir da zuwanta Makaranta, cike da d'oki Dije ta je ta d'ora ruwan zafin wanka ta sullo wankanta tas, ta shirya cikin uniform d'inta da suke cikin rigar filonta da kullum take matashin kai da su, sunsha karin guga fess da su sai wasar Baki take yi ta nufi d'akin Baffah da ke zaune yanata laziminshi da ya zame masa jiki kullum, ta durk'usa har k'asa cikin wani sabon ladabi tace

"Ina kwana baffah"

Ya kalleta cikin jin dad'in ganin yanayinta yace,. "Lafiya Lau Makarantar za'a je ne?"

Dije ta washe baki tace,. "Eh nagode Baffah da ka yafe man WALLAHI baka ji yanda naji ba kwana biyu da bana zuwa, har mafalkin Makarantar nake ta yi"

Baffah ya tashi daga kishingidar da yake ya zauna da kyau yace,. "Idan har kina son in barki kici gaba da zuwa to ki yi man alk'awali ba ki ba sake kula Yaron nan, idan kuma kika kuskura na ji ance an ganki da shi to ko ki sani ba ki ba sake zuwa ko k'ofar Makarantar nan, in kin amince shikenan ki tashi kije idan kuma kinga ba zaki yarda da hakan ba to ki je ki cire tufafin ki yi zamanki gida tunda ba da karatun za'a tambayemu cikin kabari ba"

Dije ta yi saurin fad'in

"Na yi maka alk'awali Baffah in kuma na sab'a ka ce man shegiya"

Baffah ya yi saurin runtse idonshi yace,. "Kinga haukarki ko to kar in sake jin kin Kira kanki da suna shegiya kinji ko??"

Ta d'aga kanta alamun gamsuwa .





Akafta😝




D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*





*COMMENTERS GA JINJINAR BAN GIRMA👍🏻*


*Lamba ta 20*


Sai da ta yi masa alk'awali sannan Suka yi sallama ta fito ta nufi Makaranta, tana tafe tana wasar baki musamman idan ta tuno watarana ita Likita ce, sai wassafa yanda zata dinga soke Mutane take yi suna ihu, ita kad'ai sai faman murmushi take yi bisa hanya har ta isa makatantar, inda ta taradda Malam Safwan zaune bakin barandar ya duk'e kanshi ya lula zuzzurfan tunani mai zurfi,don har ta kawo wurinshi ta gayar dashi bai ma san ta yi ba, ganin ya kyaleta yasa ta murgud'a masa Baki ta wuce abunta, tana gaf da shigewa class ne ya ankara da ita aiko cikin sauri ya d'aga murya yace

"Hey!"

Taso ta share amman dai ta waigo don tana da tabbacin da ita yake, amman duk da haka sai da ta nuna kanta tace

"Ni?"

Ya d'aga mata kai sannan ta dawo zuciyarta cike da tsoron laifin me ta yi masa kuma?, Aiko tana zuwa gabanshi zata yi kneel down ya yi saurin girgiza kai yace,. "No! no!"

Dije ta mik'e cike da mamakin sauyawarshi ta kura masa kallo sai da ya yi shiru sannan cikin yaren hausa yace,. "Me ya hanaki zuwa Makaranta kwana biyu"

Dije ta zaro ido waje saboda tsananin mamakin da ya bata bakinta yana rawa tace,. "Malam ashe daman cen ka iya hausa?"

Hararar da ya maka mata ce yasa ta yi saurin rufe Bakinta tace,. "Sorry ser"

Ya sake maimaita tambayarshi Dije kam nan take ta bata fuska tace, "Baffahna ne ya hanani zuwa"

Cike da mamaki Safwan ya yi saurin cewa,. "Saboda mi?"

Dije wasu hawaye suka gangaro mata tace,. "Saboda Abokinka yace yana so ya aureni shine ya hanani zuwa Makarantar, yanzu haka ma sai da na yi masa alk'awalin bazan sake kulashi ba sannan ya barni na tafo, don ALLAH Malam ka ce dashi ya yi hak'uri ya daina yiman magana har sai na kare Makaranta, don WALLAHI ina son karatun bana son a hanani zuwa kuma gashi ma ina son ya kaini Makarantar Likitancin da yace zai kaini"

Ta k'are maganar cikin zubowar wasu ruwan hawayen, Safwan ya yi shiru yana nazarin maganganunta sannan cen ya d'ago da kanshi ya kalleta cikin sanyin jiki ya ce "kina so ki yi karatu mai zurfi bayan kuma kinsan hakan ba al'adar garinku bace, ko akwai wadda ta tab'a zuwa Makarantar gaba da primary a garin nan?"

Dije ta girgiza masa kai tace,. "Ko d'aya duka aure ake masu, yanzu haka ma cikin kawayena Hansai da Ladiyo da Jummala duk suna da Miji da an tashi aure kawai za'a yi masu"

Safwan ya yi saurin zaro ido yace,. "Cabd'i jam! To ke ba'a yi maki Mijin bane?"

Ta rufe fuskarta tace,. "Ai Ni ba wanda ma ya tab'a cewa yana sona sai mutum biyu"

Cikin kureta da kallo tare da had'e fuska yace,. "Su waye Mutum biyu din?"

Dije ta rufe fuskarta tace,. "Kunyar fad'a nake ji WALLAHI"

Shi kanshi gano wannan firar bata dace da Malami da dalibi ba yasa yace,. "Ok to je ki shiga class amman Kika kuskura naji kince da wata na iya Hausa I will purnish you"

Dije ta dafe bakinta tana k'umshe dariyar da ta zo mata tace,. "Ba zan fad'a ba ai"

Safwan yana shirin sake yi mata magana ne ya hango Lawi zai shigo Makarantar ya yi saurin fad'in,. "Oya go to your class"

Dije ta tafi tana ta k'umshe dariyarta saboda gargadin da yayi mata ya bata dariya, don ganin renin wayon nashi ma ya yi yawa ashe ma ya iya hausa amman kullum yake ta zuba masu zallar turanci, sannan zagin da tasha yi mashi da Hausa ita da su Lanti ashe duk yana ji amman yake yi kamar bai san me suke fad'a ba, sai dai laifi kad'an zai sa ya yi ta harararsu yana muzurai, k'arshe ma haka zai k'are karatun ba tare da sun fahimci komi ba.

Lawi kam tun daga nesa da ya hango Dije yake ta sauri sai gashi kafin ya k'araso har ta wuce, cikin damuwa ya isa wurin Safwan ya zauna ya na bin class d'in su Dijen da kallo, Safwan ya yi masa wani kallo ya yi wani mere yace

"To yarinyar nan dai ka d'aga mata k'afa don yanzu ta ke sanar dani Mahaifinta ya hanata zuwa Makaranta ne saboda kai, idan har da gaske kana sonta to ka barta ta yi karatunta, don an gargad'eta a gida duk ranar da aka sake ganinta da kai za'a cireta daga school d'in gaba d'aya"

Lawi ya yi saurin fad'in

"Innalilahi wa'Inna ilairraji'un kai wannan bala'i da me yayi Kama?? WALLAHI kwana biyun nan da ban ganta ba jinsu nayi tamkar shekara biyu, Abokina ka taimaki rayuwata WALLAHI mutuwa zanyi idan har ban auri yarinyar nan ba"

Safwan ya yi saurin mik'ewa tare da buga wani uban tsaki ya barshi a nan ya shige Ofishin Malammai, Lawi ya bishi da kallon mamaki sannan ya yu shiru yana nazarin mood d'in abokin nashi akan matsalar, da kullum baya bashi goyon baya akan soyayyarshi da Dijen, asali ma sai Kara dakushe masa karsashi yake yi kullum safiya, a ranshi yace

_"shin wai shi baya da imani ne da har ba zai taimakeni na samu abunda yafi soyuwa agareni ba?, Ko don shi har yanzu bai San zafin son bane?"_.

Ya furzar da iska mai zafi a bakinshi ya mike ya nufi office d'in ranshi a b'ace, saboda damuwowin da suka yi masa yawa ga rashin goyon bayan Safwan akan masoyiyarshi Dije, ga kuma wata bakuwar matsalar da aka kunno masa da ita, don rashin magana da Dije a wurin ba k'aramin purnishmen ne aka bashi ba, yarinyar da har gizo take masa a ido baya da wani mafalki a Yan kwanakin nan sai nata, lokaci d'aya a rabashi da ita irin haka ai an ci da zalinshi.

Ranar har aka tashi ba wata walwala ko wata huld'a mai k'arfi da ta shiga tsakanin Abokan biyu, abun takaicinma lokacin da aka tashin k'iri K'iri Dije ta ki tsayawa ta ji uzurin Lawi da ke son yin magana da ita, saboda tsoron a ganta aje a fad'awa Baffanta Safwan kam ba k'aramin dad'i hakan ya yi masa ba, ya sake girmama lamarinta saboda ganin ashe rashin kunyarta da sauk'i tunda har tana jin maganar iyayenta.

Lawi kam ko dakinsu bai nufa ba ya isa wurin Maigarin cikin damuwar da ta kasa boyuwa akan fuskarshi, Maigarin ya kalleshi cikin tausayawa don yasan labarin gizo baya wuce na koki, amman duk da hakan sai da ya wayance yace dashi

"Yarona lafiya Na ganka haka? ko wani abun
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment