Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

je mu ɗin ai sai mu yi sauri mu kammala"

Fiddo cike da jin daɗi ta kai su ɗakinsu da ta riga da ta shirya shi tsaf saboda tarbonsu, ta nuna masu toilet sannan ta fito zuwa kwaso masu kayan abincin, Safwan da ke tsaye jiki ba kuzari damuwa fal ranshi yace

"Zo nan ki ji"

Fiddo ta ƙaraso wajenshi cikin sassauta murya yace,. "Don Allah ki yi duk yanda zaki yi ki nuna mata cewa ba wani abu tsakaninmu da yarinyar cen, don WALLAHi idan bata amince ba yau sai na ci uban yarinyar nan a gidan nan"

Hajiya da ke bayansu cikin shirinta na fita zuwa bikin ta ce,

"Wa za'a ci wa Uba kuma a gidan nan yau?"

Safwan ya gyara tsayuwarshi tare da sosai kai yace,
"Wata ce Hajiyarmu"

Hajiya ta ce "ALLAH ya taimakeka to tunda ba Khadijah kake nufi ba don WALLAHi idan har da ita kake ka kuskura naji ka daketa akan wata sai na baka mamaki"

Tana ƙare faɗar haka ta sa kai ta tafiyarta, Safwan da Fiddo suka bita da kallo har ta wuce, sannan ya nufi ɗakinsu Fiddon ranshi a matuƙar ɓace saboda jin haushin taka masa burkin da Hajiya Mama take yi akan Dije.

Yana shiga ya taradda Zee dunƙule tana kuka ƙawarta tana lallashinta tana bata baki, tana ganinshi ta yi saurin zuwa ta cakumo rigarshi cikin kuka tace

"Daman abunda ka shirya man kenan Shiyasa ka matsa akan in zo bikin ƙanwarka??, To na zo na gani tabbas kana da matar da zaka aura ƴar Uwarka ALLAH ya baku zaman lafiya Ni na haƙura na bar mata ALLAH ya bani dangana, amman ka sani sonka shine ajalina idan ka ji saƙon mutuwa to shine sila"


Safwan ya dafe goshinshi cike da wani takaici da ruɗewa yace, "ki yi haƙuri my fiance na gaya maki yar aikin gidan nan ce, tukunna ma ina wadda na taɓa sanar da ke an so a haɗamu aure da ita to ai itace wannan"

Ta yi masa wani kallo mai cike da tuhuma tace, "eh kam lalle yar uwar taku ce yanzu ta zama yar aikin naku ko? Hmm! To bari ka ji bazan ja abun da tsauri ba na haƙura na bar mata kai kawai"

Tana ƙare faɗar maganar ta fisgo gyalenta da ƙarfi zata fita ya yi saurin riƙo hannunta cikin damuwa yace "plsss Zee ki fahimceni mana, wallahil'azim a shirye nike da in aureki a kowane lokaci, ki bani dama domin in tabbatar maki da hakan idan kin aminta yanzu ma kafin mu koma ayi auren kawai mu tafi abun mu cen mu zauna idan kinsan hakan zai kwantar maki da hankali"

Zee ta kalleshi zuciyarta cike da jin daɗi tace, "promise?"..

Yace "promise"

Sannan ta rufe fuskarta tana dariyar jin daɗi, Safwan ma ba shiri ya mayar mata da martanin dariyarta zuciyarshi fess saboda ganin ya tufke abunda Dije ta warware masa.

Fiddo ta shigo ta ajiye kayan abincin tana wasar bakin jin daɗin ganin Zee ta washe tace, "masha ALLAH Auntynmu har naji daɗi da kika saki fuskarki, yayanmu ba shi da wata matar da zai aura a yanzu face ke, don wannan munafukar yarinyar da kika gani itace take sonshi sai dai shi ko kaɗan ba ya sonta, ta yi masa haka ne a gabanki don kawai ta haɗaku faɗa, daman gurinta bai wuce ki yi zuciya ki bar mata big bros, to don ALLAh Auntynmu ki bata kunya kada ki bari ta rabaki da yayanmu kinji"

Zee ta washe baki tace, "na gode ƙanwata ina jin daɗin yanda kike sona ke da yayanki, kuma insha ALLAHu bazan taɓa nuna damuwata akan wani abu da zata sake yi ba, matuƙar ba my soul ne ya nuna kulawarshi akanta ba, to agaskiya anan kam bazan taɓa jura ba don Ina kishin inga wata mace ta raɓeshi bayan ni WALLAHi"

Fiddo ta fara zuba masu abincin tace, ",kwantar da hankalinki don ba ma zai kulatan ba saboda daman cen itace kawai da baƙin nacinta"

Haka dai Fiddo ta yi ta basu kulawa tana wanke zuciyar Zee daga tsatsar da Dije ta sakawa ruhinta, har suka ƙare komi cikin kulawar Fiddo sannan suka ajiye motarta da suka zo da ita Safwan ya ɗaukesu suka tafi bikin.

Shigarsu hall ɗin ke da wuya Safwan ya hango Dije tsakiyar fili tana ta cashewa abunta, zuciyarshi a take ta zo wuya saboda ganin yanda ƙaton hall ɗin ya cika ya batse tsakanin maza da mata.

Fiddo ta wuce da su Zee tana ta gabatar da ita ga ƴan'uwa da abokan arziƙi, sai dai abinda bata sani ba mutanen da yawa wadañda basu san da zancen auren ba sunyi mamakin auren da Safwan ɗin zai sake yi, bayan ga Dije dake hannun Hajiya kuma itama tana amsa sunan Matarshi.

Safwan kam cikin dubara ya fice ya sa wata ƙawar Surayya ta kira masa Dijen, sai dai cikin rashin Sa'a Dijen ta ƙi biyo ƙawar Surryn saboda gargaɗin da Hajiya ta yi mata akan kada ta biyewa Safwan ɗin ya daketa a banza, ƙiri ƙiri tace da ƙawar Surryn Hajiya tace kada ta fita ko'ina, dole haka ƙawar taje ta sanar da shi, aiko ya ƙara hawa akan fushin da Dijen ta saka shi, ya yi ƙwafa ya koma hall ɗin

Sai dai rawar da ya ga tana ta cisga ne yasa shi dafe goshinshi ba shiri, ranshi a ɓace ya kasa haƙuri ya nufi wurinta gadan gadan da nufin kai mata wani bahagon mari, tana hangoshi ta yi saurin ficewa filin ta nufi wurin Hajiyar tana haki, ya wayance ya fara zubawa Surry likin kuɗi daga nan ƴan'uwa suka cika filin suna yi masa liƙi yana yi masu shi ma, ta ko'ina sai zubo kuɗi ake yi har sai da mc ya bada umurnin kowa ya koma ya zauna abar Amarya kawai a tsakar fili.

Ganin hakan ya baiwa Zee damar fitowa ita da ƙawarta suka fara watsawa Surry farfaru bugun Abuja, Hajiya Mama ta ciro kuɗi a jakarta ta miƙa wa Dije tace itama ta je ta watsa, cikin jin daɗi ta karɓa ta isa wurin ta fara mannawa Surryn kuɗin sannan ta dawo tana mannawa Zee cikin murya ƙasa ƙasa tace

"Da kin daina wannan zaƙewa tunda dai har yanzu baki riga da kin shigo familyn ba, amman kuma ba komi a hakan ma muna godiya, sai dai kuma ga shawara ki adana sauran kuɗinki don rabawa malamai su ji daɗin yi maki addu'ar ƙwato zuciyar wanda ake yi dominshi"

Saboda salon yaudara irin na Dije tana liƙa mata kuɗin fuskarta a sake take maganar, wanda bai ji ba ba zai taɓa fahimtar cewa wai wata baƙar magana ce take faɗa mata ba, don shi kanshi Safwan ɗin ya yi mamakin ganin Dijen tana wasar baki ga Zee, uwa uba ma har da su watsa kuɗi don a ɗauka cewa bata san zafin kishi ba.

Har aka watse taron Zee maganganun Dije suna yawo cikin kwanyar kanta, sai dai idan ta tuno da zancen aurensu da Safwan ɗin da ya zo mata da shi sai ta ji wani sassafci a ranta, duk da tasan cewa itama za'a sha fama da ita kafin a janye zancen auren wani da ke kanta.

Dije kam har aka shiga bacci bata bari sun haɗu da Safwan ba, saboda ma tunda ya fita raka Zee gidan ƴan'uwasu da suka sauka a cen, bai dawo gidan ba har sai da dare ya tsala sannan ya dawo ya shige zuciyarshi cike da jin daɗin shima ya kusa angwancewa, sai dai wani sashe na zuciyarshi yana ingizashi akan ya koyawa Dije hankali kafin ya bar garin, amman yana jin tsoron abunda zai janyowa kanshi wajen Hajiya Mama.

Ranar juma'a ranar ce ta kama ta ɗaurin aure kuma ayi walima, haka ranar ce kuma Malam Lawi ya diro garin tare da wani abokinsu da ke cen Gomben, saboda gayyatar da Safwan ɗin ya yi masu, cike da jin daɗin gani junansu kowa yake ta ɗokin ɗan'uwanshi, sai firar yaushe gamo ta ɓarke a tsakaninsu ihunsu kawai ke tashi a ƙofar gidan bayan sun dawo ɗaurin auren.

Kasancewar a harabar filin gidan ne za'a yi walima shiyasa aka kafa rumfuna manya manya aka ƙawataa wurin sosai.

Dije ta fito zata je cen wajen ne idonta ya kai kan malam Lawi, cikin sauri ta zaro ido cike da jin daɗin ganinshi ta nufi wajensu fuskarta a washe take faɗin

"Rai kan ga rai Malam? ashe ina da rabon sake ganinka a duniya?"

Lawi cike da mamaki ya bi ta da kallo tun daga sama har ƙasa saboda ganin yanda gaba ɗaya ta sauya kamannu kamar ba Dijen da ya sani ba, wadda ko a mafalki da siffarta ta ƙauye yake hangota, sai dai kasancewar yasan cewa da da yanzu ba ɗaya ba ne, saboda yanzu igiyoyin aure sun yi masa shamaki da ita, auren ma na Abokinshi Safwan, shiyasa ya wani basar ba tare da wani sakin jiki ba ya ce

"Amarya kinsha ƙamshi ya garin? da fatar kina lafiya?"

Dije ta washe baki cike da jin nauyinshi tace, "Malam saukar yaushe haka babu sanarwa?"

Lawi ya kalli Safwan ya ga yanda gaba ɗaya yanayinshi ya canza ya yi gajeren murmushi yace, "wannan kuma laifin angonki ne tunda shine bai sanar da ke ba"

Dije ta kai kallonta gareshi ta yi ɗan murmushin yaƙe sannan ta ce

"Bari in je in dawo Malam ai da nasan kana nan da tun ɗazu ka sha tarbata"

Lawi ya bita da kallo yana wani murmushi cen kuma me ya tuna ya yi saurin kawar da kanshi a gefe yana wassafa siffarta cikin bular doguwar rigar da ke jikinta, ta yi mata kyau ɗagwasgwas ta zauna a jikinta, ga ɗankwalin rigar da ta yafo gaban kanta gaba ɗaya a buɗe yake har ana hango kwantaccen gashin kanta da yasha gyara ya kwana, ga sajen gashin ma ya kwanta luf luf a gefe da gefen fuskarta, girarta ma cike tafi da gashi gazar gazar da ta ƙara Ƙawata mata fuskar, duk da bata yi wata doguwar kwalliya ba amman yanayin tsarin shigarta ta burgeta sosai.

Daga shi har Safwan sun faɗa tunanin da su kaɗai suka san me suke tunawa, tunaninsu ya katse ne lokacin da Dijen ta dawo tana murmushi tace

"Malam zo mu je falon baƙi ka ci abinci ko?"

Abokinsu da suka zo tare da Lawin ya kalli Dije cikin murmushi yace, "Au Wai abun ƴar wariya ce daman?"

Dije ta waigo tana dariya tace, "yi haƙuri idona ne suka rufe ruf WALLAHi a duk wurin bana hangen kowa sai malamina kawai"

Ba Safwan da maganar ta daka a ƙirji ba har shi kanshi Lawin ba shiri ya waigo, saboda maganarta ba ƙaramin dukan zuciyarshi ta yi ba.




To fa wata sabuwa 😝






Akafta😅





D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*My fans bakina ba zai iya misalta farin cikin da kuka sakani ba, naso in zayyano sunayenku to amman yawanku ya kai ba zan iya lissafoku duka ba, amman na gode 🙏🏻na gode🙏🏻 sosai Alkhairin ALLAH ya kai maku duk inda kuke💃🏻ku daɗe ku yi ƙarko mutanena👍🏻*



*Lamba ta 47*



A harzuƙe ya taso da nufin kai mata duka sai ga motarsu Zee ta kunno kai harabar gidan, cikin sauri ya nufi motar yana washe baki saboda jin daɗin ganinta, Dije ta kai kallonta gareta take wani ɓacin rai ya ziyartota, amman a hakan ta kalli Lawi ta yi wani murumushi tace

"Zo mu je Malam"

Lawi ya yi shiru sannan yace da abokin nasu mai suna Kamal yace, "zo mu je Abokina don wannan tafiyar dole ne a buƙaci rakiyarka"

Kamal kam sai kallon motarsu Zee yake yi mamaki fal ranshi yace da Lawi, "Abokina baka gane wannan yarinyar ba ne?"

Lawi ya kai kallonshi ga motar inda Safwan da Zee suke tsaye jikin motar suna fira kowanensu cikin farin cikin ganin ɗan'uwanshi, Lawi yace

"Kai ne idon gari Abokina ban gane su ba gaskiya"

Kamal ya ce, "budurwar Aminu ce fa wadda ya susuce kanta kullum yana dakon ta kammala karatun da take yi ayi auren amman Mahaifinta sai ja masa rai yake yi, ko kallon zumuncin da ke tsakaninsu ba ya yi, ya fifita son zuciyar ƴarshi akan na kowa"

Lawi yace, "Eh kam sai yanzu na tuna amman kasan ni daman bansan yarinyar ba ai labarinta kawai nake ji"

Dije tana tsaye tana saurarensu ba tare da ta ma nuna tasan wani abu da ke faruwa ba, cikin dariyar yaƙe tace

"Ai kam dai yanzu sai dai Aminu ya yi haƙuri saboda ita ce matar da Malam Safwan zai aura tare suke karatu a cen ƙasar wajen"

Daga Lawi har Kamal suka zaro ido cike da mamakin jin wannan zance a bakin Dije, haka kawai Lawi ya tsinci kanshi da cewa

"To ke har kin amince kenan?"

Dije ta yi shiru tana yar dariya mai cike da takaicin da ke cin zuciyarta tace, "ku zo mu je mu barshi ya ji daɗin firar don kada mu takurashi"

Suka wuce Safwan da hankalinshi gaba ɗaya yana kansu saboda tsabar kishin da ke cin zuciyarshi, ya bisu da kallo ranshi a matuƙar ɓace yace da Zee

"Zo mu shiga ciki ku gaisa da Hajiya"

Zee ta bishi da kallon mamakin me ke damunshi tace, "my man what's wrong with you?? Ko na yi maka wani abu ne?"

Safwan cike da ƙunar rai ya shafo kanshi ya ce

"No! no! kada kiji komi mu je kawai"

Yayi gaba Zee ta bishi da kallo ƙawarta ta riƙo hannunta suka shiga cikin gidan, suna shiga suka yi kiciɓis da Fiddo ya ce da ita ta kaisu wajen Hajiyar idan sun gaisa abasu muhalli a wajen walimar, sannan ya barosu ya nufi ɗakin baƙin da zuciyarshi take ta azalzalarsa akan ya je ya ga wace irin wainar ce ake toyawa, ai kuwa sai ko ya taradda Dijen ta gama zuzzuba masu abincin tana miƙawa Lawi lemun da ta zuba masa a cup, daga ita har shi murmushi ne kwance a kan fuskarsu, idonshi a rufe yana zuwa bai wata wata ba ya fella mata wani wahalallen mari har sai da ta saki cup ɗin saboda tsabar tsoronshi da kuma azabar da ta ziyarceta, cikin wani masifar ƙarfi ya fisgo hannunta suka fice Kamal da Lawi suka bisu da kallo, cikin tsananin ɓacin rai Lawi ya dafe kanshi zuciyarshi sai tafasa take yi saboda zafin marin da Safwan ya yiwa Dije ya ji shi har cikin ranshi.

Kamal ya kalli Lawi yace, "wai wannan guy ɗin mi ke damun ƙwaƙwalwarshi ne?, Ko da yake banga laifinshi ba fa don ko ni nan ina da irin wannan mata WALLAHi dole ne na yi kishinta, amman kuma yasan yana sonta zai tsirowa kanshi auren Zee da rana tsaka?"

Lawi ya yi shiru saboda ɓacin ran da yake ji yasa ya ma kasa furta wata kalma a bakinshi, sai shafa ɗan ƙaramin gemunshi da yake yi yana nazari.

Safwan kam bai zame ko'ina ba sai ɗakinshi da Dijen, yana shiga ya saka key tare da wurgar da ita a tsakiyar falon yana ƙare mata kallo yana nazarin ma wane hukunci zai yanke mata don ya ji sauƙin abunda ke azalzalar zuciyarshi, cikin takaici ya cakumo gashinta da ƙarfi ya miƙar da ita tsaye, cikin jin zafin da ke ratsa kanta tace

"Don Allah ka yi haƙuri WALLAHi bazan sake ba"

Safwan ya turata baya da ƙarfi ta yi taga taga zata faɗi kuma ya yi saurin riƙota cikin fushi yace

"Kasheni kike so ki yi ne ko kuwa?, Me na yi maki Kika zaɓi ki tozartani cikin mutane?, To WALLAHi tunda har ke baki san darajar aure ba zaki janyo in fiddaki Makarantar da kike kwaɗayi gaba ɗaya, don na fahimci duk wannan rawar kan naki don kin ga an baki damar yin karatun ne, to daga yanzu ba zaki sake zuwa wata makaranta ba da sunan karatu idan ba islamiya, ita ɗin ma anan gidan za'a zo a dinga koyar dake saboda kawai ki san muhimmancin auren da ke kanki"

Dije ta kalleshi ido cikin ido tace,. "Wane aure naji kana faɗa ne? Auren da kai da bakinka ka ce da ni kada in yarda cewa wani yasan kai ne mijina? To Ni yanzu WALLAHi na gaji da wannan wahalallen auren, tunda mai sona tsakani da ALLAH ya bayyana ka barni kawai in auri wanda ya soni tun kafin ka aureni, don ni shi Nike so........."

Wani marin da ya kaiwa bakinta ne yasa ta yi saurin dafe bakinta tana zubar ƙwallah tace, "ko zaka kasheni ba zan fasa faɗar cewa ina son Malam Lawi ba tunda har kai bakasan darajata ba, shi nake so kuma shi nake da gurin zaman aure da shi idan ba haka ba kuma WALLAHi zan koma garinmu gaba ɗaya na haƙura da makarantar bana so"

Ta ƙare faɗar maganar cikin kuka ta durƙushe tana gunjin i kukanta gwanin ban tausayi, cikin wani sabon tashin hankali ya yi durƙuso gabanta har ya so ya shafo kanta, me ya tuna kuma ya yi saurin miƙewa tsaye yace

"Da ace zai amince ya karɓekin da nafi kowa farin ciki, to amman yanzu haka ko da kuɗi aka bashi ke bazai taɓa karɓar ki ba, ko ni nan don Allah ya ƙaddaro da zaki zama matata da ke kinsan baki kai matsayin wadda zan iya rayuwar aure da ita ba, nasan ba abinda ke damun zuciyarki a yanzu face kishi ko? to ki kwantar da hankalinki da anyi aurenmu da Matata Zee zamu bar maki ƙasar gaba ɗaya sai ki ji daɗin karatun naki"

Dije ta miƙe tsaye hawaye shaɓe shaɓe akan fuskarta tace

"Ai Ni ma kasan ba roƙarka na yi nace sai ka aureni dole ba, saboda haka ka barni da shi ka ga idan har bai aurenin ba.."
.
Ya kaiwa bakinta duka yace, "WALLAHi na ji kin sake zancen wani da aurena akanki sai kin gano baki da wayo, wai me kike taƙama da shi ne ba budurci ba? to zan karɓe shi yanzun nan inga ta yiwa mutane wata firiritar tsiya"

Ya fisgota da ƙarfi ta faɗa jikinshi ta fara tirjiya amman hakan bai hanashi cire doguwar rigar da ke jikinta ba, surar jikinta tasa ya ƙara ɗimaucewa a HAUKACE ya fara yamutsata son ranshi, Dije ta na ƙoƙarin kare kanta wajen kai masa duka shi ko yana cen duniyar tsimuwa da muguwar guguwar sha'awarta,don kuwa gaba ɗaya ya susuce sai wasa yake yi da jikinta ta ko'ina yana sauke wani nishin mai bayyana tsantsar kiɗimewarshi akanta, ganin da gaske yake yi zai ci amanarta ta dinga rarumo abubuwa tana kai masa duka da shi, ya yi nasarar rabata da komi na jikinta sannan ya wurgata kan gadonshi, Dije ta firgice iya firgici ta fara ihun neman taimako amman bai ji kunyar rufe bakinshi da nata ba cikin mayen bala'in wutar sha'awarta da ke fisgarshi, cikin dubara ya fara aika mata saƙon da ya fara cin galabarta, ganin haka yasa ya dinga yamutsata iya son ranshi yana wani gurnani tamkar wani ƙaton rago.

Dije ta kasa jurewa ta firgice masa da kalar tata haukar, cikin nasara ta kai hannunta ga laptop ɗinshi dake gefen gadon ta ɗaga ta kwaɗa masa ita a kai, ba shiri ya saketa dafe da kanshi yana faɗin

"La la la ni zaki yi wa rotse?"

Dije ta sauko jikinta yana rawa ta mayar da doguwar rigarta ta buɗe ɗakin ta fice aguje, Safwan ya bita da kallon mugunta yana dariya a ranshi yace

"Komi wayon Amarya....."

Da ƙyar ya samu ya yi control ɗin kanshi ta hanyar kora kwayuj magungunanshi da ruwa sannan ya dinga sakarwa kanshi ruwa har da ya ji zuciyarshi ta yi sassauci sosai akan damuwar da take ciki, sannan ya yi wanka a gurguje ya fito ya nufi inda su Lawi, don lokacin ma har an fara walimar sautin wa'azin malamar da ke yi wa Amarya huɗuba duk ya karaɗe gidan.

Yanayin da ya taradda Lawin ne yasashi saurin washe baki yace, "Abokina ya dai ko har ka fara kewar gida ne?"

Lawi ya yi masa wani kallo sannan ya gyara zamanshi yace, "banji daɗin dukan khadija da ka yi ba gaskiya, yakamata ka fahimci cewa mata suna da wata darajar da duk namijin kirki ba zai taɓa iya ɗaya hannu ya dakesu ba, ka tuna kar garin nan bata da kowa sai kai shin kasan ba zaka riƙe ƴar mutane amana ba me yasa ka aurota??"

Baki sake Safwan yake kallon Lawin cikin mamakin titsiyen da yake son yi masa yace "ka ga malam wannan kuma ba abinda ya shafe ka bane, Khadija Matata ce ina da ikon da zan yi mata koma mine don haka don ALLAH ka daina saka man ido akan duk wani abu da aka ga nayi"

Lawi ya sauke ajiyar zuciya yace, "idan kasan ba zaka riƙe masu ƴa tsakani da ALLAH to ka mayar da ita gaban iyayenta yafi da ka kawota nan ka ajiye kana dukanta, don WALLAHi matuƙar baka daina ba da kaina zan je garinsu in sanarwa iyayenta irin abinda kake yi mata, sannan wannan auren da naji wai zaka sake yi to idan baka ajiye wannan shirme ba tabbas Ni kuma a shirye nike karɓar Khadija a hannunka ko ta halin ƙaƙa"





To fa tsugunne bata ƙare ba kenan🙀😢shin Lawi ko Safwan ina team Dije ku fito ku afafata🤪





Akafta😍






D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Ina yabawa ƙoƙarinku COMMENTERS😉*



*Lamba ta 48*



Safwan ya bishi da wani malalacin kallo yace, "idan har ka ga ka sami damar auren khadija a dai nan wannan duniyar da muke ciki to ka ɗauka cewa bana numfashi ne a doron duniyar, sai ka jira idan har na mutun sai ka yi murna ka garzayo ka auretan, amman yanzu kam WALLAHi bazan taɓa baka damar mallakar macen da na fi so fiye da kowace mace da zan aura ba duniya, kar ka ɗauka cewa wai ka fini sonta to WALLAHi kashi ɗaya cikin goman da nake mata to ko rabi ba zaka kwasa ba, amman bazan taɓa ɗaga mata ƙafa ba matuƙar ta yi man abunda bai gamsheni ba, saboda haka ka kawar da kanka akan matata ka yi gaggawar fito da taka matar don wannan kam ta yi maka nisa, saboda na fahimci cewa idan ban fito na yi maka gwari gwari ba to zaka janyo man abunda zai saka jinina ya hawa, yanzu ga shi daga zuwanka ka firgice mani mata na kasa gano kanta"

Ya kalli Kamal yace, "Aboki ka yi masa wa'azi don ya gano kallon matar aure ma haramun ne balle ya tsaya mayar da yawu da ita yana jin daɗin zancenta, to ka zama sheda WALLAHi ya sake tsaf zan yi masa ALLAH ya isa akan matata"

Kamal yana dariya yace, "banga laifinka ba abokina saboda haka kai Malam ka tsaya iya matsayinka na malam kawai, don kaji a gabanka mijin ɗalibar taka ya kawo ƙararka"

Lawi da ke saurarensu zuciyarshi fess da jin kalaman Safwan, ba shiri wata dariya ta suɓuce masa ya kalli Safwan ɗin yace

"To kai mijin ɗalibata ka ji tsoron Allah ka riƙe man ita amana kada ka bari ɗalibata ta yi kuka matuƙar kana son inci gaba da koya mata dabarun biyayya gareka"

Safwan ya maka masa wata jar harara yace, "kar ma kasa ranka zan bari ka sake ganinta, don ba zaka sake janyo man kwaɓata yin ruwa ba"

Lawi yana dariya yace

"Kwantar da hankalinka nima na kusa angwancewa yanzu haka saura wata biyu masu zuwa insha ALLAHu"

Safwan ya yi saurin washe baki yace "ko kai fa? Ai da ka taimaki kanka gaskiya, zaman tuzururantaka ai ba daɗi ne da shi ba, ka ga ni naji daɗin daushen farko har wani sabon lambun nike son in ƙara ninƙaya a ciki"

Kamal ya yi saurin faɗin, "wai da gaske ne kai zaka auri Zee" Safwan ya washe baki yace

"Insha ALLAHu kwanan nan ma kuwa don bazan koma school ba har sai an shafa fatiha in kwashi matata mu bar maku ƙasarku"

Lawi ya yi shiru na ɗan lokaci sannan ya ce, "Abokina gaskiya zan sanar da kai wannan yarinyar da kake gani yanzu haka da mijinta da za'a haɗasu aure a gida, me zai hana ka riƙe matarka ka barta ta je ta auri zaɓin gidansu? WALLAHi ina jin tsoron haƙƙinshi ya kamaku kai da ita, don abinda ka yi mani ba kowa ne yake da sauƙin zuciyar yafiya ba, ka janye jikinka ka barta ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment