Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

uwa uba kuma ita Dijen da ta kasance matar aure inda gaba ɗaya dukansu sunyi mamakin jin cewa wai ita Dijen matar aure.

Hakan da aka yi shi ya janyowa Dije suna a cikin makarantar, sai dai kuma waɗanda abun ya shafa tuni sun k'ulla gaba da sabuwar ƙiyayya a tsakaninsu da ita, inda wasu da yawa sun ci alwashin cewa sai sun ja mata abun da za'a koreta makarantar.



Not editing😻

😝😝😝😝



Akafta😝





D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*BAƘON YANAYI ne sunan Book ɗin don haka idan kin san baki karantashi ba to ki garzayo da gudunki don kar ayi babu ke, da 300 kacal zaki sameshi a complete ɗinshi ki yi yanda kike so, don ke da kanki zaki banbance tsakanin tea da shayi kada ki bari a yi babu ke salonshi daban ya ke da saura don tun daga sunan zaku gane cewa fa shi ɗin na daban ne, ga mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09032685442 sai na ji ku👍🏻😅*



*Lamba ta 34*



Dije kam bayan kwana biyu ta ji sauƙi sai dai shatin bulolin da suka rage su ƙarasa warkewa kawai, inda ƙawarta Hannatu da sauran wasu da principal ɗin tasa su kula da ita sosai, sun bata kulawa tamkar ƴar uwarsu ta jini don ba ƙaramar gata tasha a hanunnsu ba, don wata prefet ma mai suna Zee Baby takanas ta maidata wurinta tana tarairayarta tamkar ƙanwarta ciki ɗaya, saboda shagwaɓar Dijen da yanayin barkwancinta yasa ta shaƙu da ita aɗan zaman jinyar da tayi clinic na kwana biyu.

Dije kam tana jin ta samu kanta ta fara komawa kan harkokinta kamar kullum, saboda yanzu ɗaurin gindin da ta samu wajen principal ɗin da sauran wasu prefet ɗin yasa take jinta ita wata ce.

A ɓangaren Malamai ma Dijen Baffah ba ɓoyayya bace, don duk malamin da ya shiga ajinsu tabbas sai yasan da zamanta, don kuwa ba laifi tana catching ɗin karatun yanda ake ɓukata.

Akwai wata rana ma wata malamar Hausa ta rubuta masu test cikin ɗoki Dijen Baffah itace ta farkon wadda ta fara gamawa ta miƙa, Malamar sai jinjina mata take yi saboda daman cen akwai jituwa tsakaninsu sosai, don saboda saurin gane karatunta da take yi kafin kowa ya gane.

Bayan an kammala ne aka haɗawa Malamar takardun ta fice wani malami ya shigo, bayan kwana biyu da rubuta test ɗin sai gashi hissar Malamar ta zagayo ta dawo, cike da ɗoki kowa yake murna saboda test ɗinsu da ta fara raba masu, wadda kusan kowa ma na ajin ya canye amman Dije cike da mamaki ta ƙurawa takardar kallo, cen dai ta kasa haƙuri saboda jin Malamar tace duk wanda yake da wani ƙorafi ya faɗa, aiko cikin sauri tace

"Malama naga nan ƙasan tambaya ta biyu kin zagaye mani baki bani marking ko ɗaya ba, gashi kuma na bada amsar karin maganar da kika ce a kawo guda biyar"

Malamar ta zo gaban desk ɗin Dijen ta tsaya ido cikin ido tace da Dijen,

"Karanto karin maganar muji me kika rubuta?"

Dije ta fara kwantawa kamar haka

"ALLAH ya kashe Uwar Ubana lafiya"

Malamar ta ce da ita

"Ƙara dubawa dai ki ga"

Dije ta sake karantawa kamar farko, Malamar tace ta dai sake dubawa da kyau aiko Dije ta ƙara ƙurawa takardar kallo tana karantawa fillah fillah tace

"ALLAH ya kashe Uwar.... Uban......ki lafiya"

Aiko ba sauran Yan ajin ba har ta ita kanta Dujen sai da ta zaro ido saboda ita har ga ALLAH ba haka taso ta rubuta ba, Malamar ranta a ɓace tace

Da sauran abokan zaman Dije wa zai riƙe mata ita?,kusan mutum huɗu ya fito yace "shi, shi," aiko cikin tsananin ɓacin rai Malamar ta kalli Dijen tace

"Daman jira nike yi ki kawo kanki Khadijah yau sai na wulaƙantaki"

Aiko jikin yan ajin yayi sanyi ƙalau saboda ganin yanda take ɗasawa da Dijen amman yau take faɗar haka, aiko Malamar ta sa aka kira sergent ya zo ta karɓi bulalarshi tace da Dije ta kwanta, cikin tsananin tsoro Dijen ta fara roƙonta akan ta yi haƙuri WALLAHI ita ba abunda ta je rubutawa ba kenan kuskure ne, aiko Malamar ta kasa sauraren magiyar da Dijen take ta kwantar da ita ƙasa flat ta dinga zuba mata buloli tun yaran class ɗin suna lissafi har suka gaji suka daina, don kuwa dukan Dijen take yi ba na wasa ba duka irin na fitar hankali har sai da Dijen Baffah ta yi suman ƙarya sannan ne ta ƙyaleta ta daina dukanta ta kwashi tarkacen kayanta ta tsallaketa ta fice.

Hannatu da sauran abokan Dijen suka taso suka talalllabeta suka yi store ɗinsu da ita, aka fara yayyafa mata ruwa ana yi mata fifita, Dijen ta fashe da wani azababben kuka gwanin ban tausayi abokan sai lallashinta suke yi, Hannatu kam itama kukan take yi saboda tsananin tausayin Dijen don ba ƙaramin duka ta ci ba a hannun Malama Ubaidah ba, amman duk da hakan baisa ta kasa turo wata prefet waton sabuwar Captain ɗin House ɗinsu Dijen, akan ta baiwa Dije aiki mai tsanani kullum safiya tare da rakiyar wasu buloli goma kullum ba fashi har na tsawon sati biyu.

Aiko Dije cikin jinyar raunukan ta fara yin aikin kamar gaske sai ko gashi rana ta uku tun Asuba ta saka Uniform ɗinta daga Masallaci bata dawo House ɗin ba ta bi wata ƙofa tayi area classes abunta, akaci nemanta har aka gaji amman ba'a ganta ba dole akasa wasu suka yi aikin tunda ba'a ganta ba.

Sai bayan an dawo school ne prefet ɗin ta ganta ta yi mata faɗa sosai tare da jan kunnenta akan gobe ta sake tserewa linka mata aikin za'ayi, amman duk da hakan bai hanawa Dijen sake fecewa ba wata safiyar haka suka ci gaba da yi har prefet ɗin ta haƙura don kanta, amman kam Dije taci alwashin sai ta rama abunda Malamar ta yi mata komi daren daɗewa.

Aiko sai gashi wata rana Malamar tana yi masu karatu ta ce da Dijen taje Office ɗinsu ta ɗauko mata jakarta da zata ɗauki wani abu, aiko Dije tun daga cen ta yi sa'ar cafke wani ƙadangare ta jefa mata a jakar ta kawo mata, cikin Sa'a aka kirata ga waya da saurinta ta zura hannu da nufin ɗauko wayar aiko ta cafko ƙadangaren, ba shiri ta fasa wata uwar kuwwa ta saki jakar ƙasa, cikin sa'a ƙadangaren ya yo tsul ya fito ya haye ƙafafunta ya yo saman jikinta aguje, ba shiri Malamar ta fara ihu tana cilli da kayan jikinta tsakanin gyalen da dankwalinta har ma da yunƙurin cire doguwar rigar da ke jikinta, sai gashi anyi Sa'a ya fito jikinta da sauri ya fice don shima neman hanyar tserewa yake yi.

Aiko cikin tsananin firgici ta kwashi kayanta jikinta sai rawa yake yi ta zo zata fice taci tuntuɓe ta faɗi sai ga Malama ƙasa ta baje dafe da ƙugu tana yamutsar fuska, cikin jin kunya ta yunƙura da ƙyar riƙe da ƙugunta da ya bugu ta fisgi gyalenta a hannu tamkar wata zararra ta yi waje, inda fitarta ya baiwa ƴan ajin damar fito da dariyarsu da suke ta ɓoyewa, Dije Kam har ƙasa ta kai dafe da cikinta tana wata irin arniyar dariyar muguntar da ta yi, cikin ranta tace..

_"Gobe ma ki sake dukana da wani ƙaramin kai naki sai kace Ladingo ta baki aro😝"_

Yaran ajin ma kowa sai uban dariya yake ci musamman idan sun tuno ihu da kururuwar da Malamar ta yi, musamman dai faɗuwar da ta yi ta baje ƙasa tare da yin zaman yan bori.

Sai bayan sun koma Hostel ne take sanarwa da Hannatu cewa itace ta saka mata ƙadangaren, Hannatu ta rufe baki tace

"Don Allah Ni dai to kar ki bari wani ya ji aje a sanar da ita ki sake shiga uku"

Dije ta yi saurin faɗin

"Tab! Ai WALLAHI duk ta kuskura ta sake dukana sai na yi mata abunda sai ta yi kuka"

Hannatu ta zaro ido waje tace,. "Ni dai Ƙawata ki rage tsokano abunda zai saka ayi ta dukanki a banza don ALLAH"

Dijen ta yi shiru tace

"Ke Ni fa in banda nike son Karatun nan ko to yasin da na jangwalo abunda makarantar nan zata hautsine gaba ɗaya"

Hannatu ta yi shiru sannan tace,. "Wai ni kam Khadijah ke bakya gajiya da janyo abin magana ne??"

Dije ta ƙyalƙyale da dariya tace,. "Cabd'i ai ni idan banyi ba bana jin kaina dai dai yanzu dai mu je ki rakani inyi fitsari"

Suka rankaya gefen wani Pampo Dije ta tsugguna tana fitsarin tace da Hannatu ta je wajen wasu yara da ke cikon ruwa a bokitansu tace da su ita senior ce su bata ruwan tayi tsalki ko taci Ubansu.

Aiko Hannatu ta nufi wurinsu ta sanar da su saƙon Dijen suka bada ruwan jikinsu yana rawa ta kai mata, Dije kam bayan tayi tsalkin ne ta yunƙura kenan zata tashi ta hango wata prefet cikin waɗanda ta janyo aka karɓewa ɗankwali, ta zo da wasu yara da bokitai cike zata ɗibi ruwa aiko ba shiri Dijen ta koma tsugunnen tamkar fitsarin take yi da gaske don bata son ta ganta, aiko Dije tana zuƙunne wajen har ƙafafuwanta suka yi sanyi, kasancewar prefet ɗin cin layi ta yiwa yaran bayan ta cika bokitanta ne idonta ya kai kan Dije da ke tsugunne tace

"Ke don Ubanki zo ki ɗauki ruwan nan mu je"

Dije ta yi kamar bata ji ba ta ƙara shan jinin jikinta, prefet ɗin ta ƙara ɗaga murya tace

"Ke wai don Ubanki ba da ke nake magana ba wai? Zaki taso ki zo ki sai na ci Ubanki"

Yaran suka zaro ido suka ce "laaaah! Ashe ba senior bace ita shine tace in bamu bata ruwa ba zata ci Ubanmu???"

Prefet ɗin ta zaro ido tace "haka tace da ku??"

Suka tabbatar mata aiko cikin sauri ta je ta cafko ƙugun Dije ta janyota har gindin pampon tace

"Yau sai na koya maki hankali don Ubanki ɗauki ruwan mu je"

Dije ta ɓata fuska tace

"Bana ɗibar ruwa ko a gidanmu saboda aljanuna basa bari in ɗora Abu saman kaina".

Prefet ɗin ta yi wata shewa tace,. "Ashe ko yau zanyi bikin cin Ubanki don ko ɗiyar wa ce ke a garin nan sai na cakwaɗaki sai dai a koreni gaba ɗaya in bar makarantar"

Cikin tsoro Dijen ta ɗauki bokitin ta ɗora a kanta sauran yaran suka ɗauko wasu su ma, prefet ɗin tana gaba suna biyarta sai kawai Dije taci tuntuɓe sai ga bokitin ya yi sama ya faɗo ƙasa gaba ɗaya ruwan suka zube ƙasa itama suka jiƙata.

Ba shiri prefet ɗin ta waigo tana ƙarewa Dijen kallo sama da ƙasa tana wassafa irin abunda zata yiwa Dijen ta soshe haushinta da take ji.



Ni dai kam ba da ni ba yasin nayi nan🏃🏻‍♀️don kar ace nasan mafarin faɗan😛




Akafta😅







D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Duniya Rawar ƴanmata na gaba sai ya yo baya zamani adon tafiya ne baya ɓoye baiwata aha💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻*

*Sonki a jinin jikina yake my Hannah ina yinki sosai har cikin ɓargona alkhairin ALLAH ya kai maki har gadon baccinki my besty💋*



*Lamba ta 35*



Cikin zafin nama ta kaiwa Dije wani bahagon mari, Dije ta dafe gefen fuskar tare buɗe baki tana faɗin

"Laaa! Laaa! Laaa! Mu kika mara? Ashe ko yau zamu yi luguden dafuwar kanki a kogin burunduƙusuru zunbukur, ayyihuhu kibiyarmu zama daram iso ta hannun damana"

Ta ɗaga hannunta sama kanta ƙasa tana wani surutai kafin kace me sai ga Dije ta yi tsalle ta ɗale prefect d'in tare da cafko gashin kanta da ƙarfi cikin ikon Allah sai ga tsoron prefect ɗaya a hannun Dijen ta raboshi daga cikin ƴan'uwanshi ta jefar, ta sake komawa ta cafko fuskarta iya ƙarfinta ta fara yakuceta ta ko'ina cikin wasu irin surutai da ita kaɗai tasan ma'anarsu, cikin ƙanƙanin lokaci sai ga jini ya fara saukowa tun daga cikin kan prefect d'in yana gangarowa zuwa jikinta, saboda tsoro ɗaya da Dije ta cire mata aiko jini ta ko'ina sai zubowa yakeyi, azabar hakan tasa prefect ɗin ƙwacewa ta arce da gudun bala'i tana faɗin a taimaketa saboda ganin ya firgitata gashi bai daina saukowa ba, Dijen ma haka bata daina biyarta ba aguje itama tana faɗin

"Ai billahillazi yau sai mun kasheki dole ne ma sai mun sha romon kanki a cikin daren yau"

Prefect kam tana gudun ceton rai tana faɗin,. "Ku rabani da ita tun kafin takasheni jini jini ku taimakeni zata kasheni"

Mutane kam kowa ya hango Dije sai ya dare shi ma ya nemi maɓoya saboda ganin abunda ta yiwa Prefect ɗin wanda a duba ɗaya za'a ce aikin baƙaƙen aljanu ne, duba da yanda Dijen take ƴar firit da ita amman ta ci galabar Prefect ɗin da take ƙatotuwa.

Aiko saboda ganin kowa yaƙi yarda ya tunkari Dijen a riƙeta yasa Prefect ta ƙara ƙarfin gudunta ta nufi bakin Gate wurin Baba maigadin Hostel ɗinsu, tana kaiwa ta yi Bayan maigadin tana kururuwar ya taimaketa, Dijen ma itama tana isa ta yi wata irin arniyar ƙara cikin ƙaraji tace

"Murkutus riƙe muna ita a cire shegen kan nan!!!!"

Tayi cikin Baba maigadin da nufin ta cafkota aiko ba shiri Prefect ta some saboda tsananin tsabar tsoron da taji, Maigadin cike da jin haushi ya cira wata ƙatuwar bulalarshi ta doki ya sakarwa Dije har sau biyu, Dije jin azabar saukar bulalar yasa itama ta yi wani tsalle ta faɗi ƙasa tana surutan faɗin

"Ku tafi da ruhinta ga mu nan zuwa ku je ku je fa yanzu a fara dafuwar tarugu da tattasai duka a saka kar a saka gishiri a saka sugar ihu wayyo ALLAHna WALLAHI sai mun kashe duk wanda ya sake taɓa muna goɗiya"

Tana ƙare faɗar haka ta yi ɗif sai yawu take fitowa a bakinta tana furzarwa suna sauka kan fuskarta tana gurnani, ganin haka yasa wasu Prefect suka nufi ƴar'uwarsu suna zuba mata ruwa ta farfaɗo amman duk da hakan jinin da ke fita cikin kanta yasa ya sake bugeta ta tafi luuuu suka rirriƙeta suna kiran sunanta, inda wasu kuma suka nufi Dijen anata ƙoƙarin talallabarta tana ihu tana botsarewa.

Kai tsaye wasu da yawa suma aljanunsu suka fara tashi kafin ka ce me Makarantar ta hautsine da tashe tashen aljanu, sai yarinya tana tsaye sai dai aga ta heta kuwwa ta faɗi ƙasa tana sambatu aiko makaranta ta rikice ko ta ina sai ihu ake yi.

Ana cikin hakan sai ga wani Malami da vice principal sun shigo bakin Gate ɗin Hostel ɗinsu saboda labari yaje garesu cewa makarantar ba lafiya, sai ko gashi sun taradda abunda ya firgitasu agurguje aka ɗauki Prefect ɗin mai suna Rukayya aka nufi clinic da ita don har lokacin cikin mayen bugun jinin take sai mashalo take yi, Dije kam malamin yasa aka kawo masa ruwa a kofi yayi mata addu'a ya tofa mata ta yi firgigit ta miƙe kamar wata mahaukaciya sabon kamu tana waige waigen faɗin

"A ina nake? me ya kawoni nan? don Allah Aunty kiyi haƙuri WALLAHI ba da gangan na zubar da ruwan ba, don ALLAH ki yi haƙuri kar ki dakeni"

Wasu daga cikin Ɗaliban da ke tsaitsaye suna kallonta suka fara faɗin

"Ai na faɗa maku baƙaƙen aljanune da ita kuka ƙi yarda ai to yanzu dai gaskiya ta fito"

Hannatu tana kuka ta ratso students ɗin ta zo gaban Dijen ta tsaya tace

"Khadijah sannu"

Dije ta waiga ta kalli Hannatu tace,. "Me ya kawoni nan Hannatu??"

Malamin ya ƙura mata kallo yana nazarinta, sannan ya sa aka ta yiwa sauran masu aljanun addu'a suna tashi ɗaya bayan ɗaya, bayan komi ya lafa ya dawo wurin Dijen ya tambayeta minene asalin abunda ya haɗata da Ruƙayya, Dije ta zaro ido tace

"Wace Ruƙayya?? Ni fa banyi faɗa da kowa ba". Yace ba kiyi faɗa ba kika ji mata rauni har kika tsige mata tsoro ɗaya? Gashi a sanadin hakan kin janyo ta suma zaki faɗa ko sai na saitaki yanzu?"

Dije ta fashe da kuka tace,. "Ni fa WALLAHI Malam ba wanda nayi faɗa da shi ka tambayi Hannatu ka ji"

Malamin ya kalli Hannatu yace, "Au kenan da ke aka haɗu aka jiwa yarinyar mutane ciyo ko?"

Hannatu ta fara rantsuwar ita kam bada ita ba a tambayi kowa zai faɗa, daga nan ta yi bayanin yanda duk abun ya faru, Malamin yasa
wasu Prefects ɗin su rubuto masa sunan Dijen da duk wanda aka yi abun gabanshi tun farko, yace da su su kawo masa su gobe idan an tashi assembly, sannan aka kori kowa ya watse Dije ta miƙe da ƙyar suka nufi Hostel ɗinsu, don ranar kam gaba ɗaya labarin ake ta yi duk faɗin school ɗin inda wasu da yawa sunji daɗin abunda aka yiwa Rukayya saboda muguntarta, sai tsiraru ne suka ji tausayinta tare da jin haushin abunda Dijen ta yi mata cikin bainar nasi, yayin da wasu da yawa suka fara jin tsoron Dijen don gudun kada su ma ta yi masu abunda ta yiwa senior Ruƙayya.

Dije dai kam duk da ta yi mugunta amman hakan bai hanata jin tsoron makarantar ba, saboda tashe tashen aljanun da ta ga ana ta yi ranar ya firgitata sosai, musamman da dare ya yi ta kasa bacci har kowa yayi bacci ita ido ƙyamas zuciyarta cike da jin tsoro, aiko tana kwanarsu kwance kan gado ta ji takun tafiya ƙwass! Ƙwass! Ana tafiya da talkami ƴan'tsini ana karkaɗa awarwaro suna ƙara kuma direct wajen gadon da take kwance aka nufo, cikin tsananin firgici da tashin hankali ta sha jinin jikinta sai kawai ta ji an fisgi gadon da take an jijjigashi da ƙarfin tsiya, ana walili da gadon kamar fanka tare da ita anata zagaye ana faɗin

"Ba ke bace kike ƙarya da mu ba to gamu munzo me kike soooooo! me zamu yi makiiiiiii!"

Dije saboda tsabar tashin hankali sai addu'a take zubawa fili, sai dai kam in ta kamo wannan ta suɓuce ta saketa ta sake kamo wata haka ta dinga yi har ta ji anyi jifa da ita tun daga kan gadon har tsakiyar dogon ɗakin nasu, ba shiri ta ƙwallah wata arniyar ƙara tana faɗin

"Wallahi na daina bazan sake ba na tuba ku yafe mani wayyo Baffahna"

Tana cikin surutan ne ta ji an dafata ta zabura da sauri za ta zuba da gudu taji muryar Hannatu tana faɗin

"Ni ce Khadijah lafiya kike wannan uban ihun cikin daren nan?"

Dije ta tsurawa Hannatu kallo tuno abunda taji da kunnuwanta yasa ta ruƙunƙumeta tana faɗin

"WALLAHI mu bar makarantar nan aljanu ne da ita kasheni zasu yi Ni dai gida za'a kaini bazan zauna ba wayyo ALLAHna WALLAHI na daina bazan sake ba, an kashe kowa mu ne kawai muka yi saura"

Hannatu ta riƙo hannunta tace,. "Kalli ki ga? ga kowa nan lafiya ba abunda ya samemu kema tsoro ne kika ji tashi muje mu kwanta"

Wata senior ta zo ta riƙata ta tashi tsaye ta kaita kwanarta suka kwanta tare tana ta tofeta da addu'o'i saboda ba ƙaramin tausayi ta bata ba.

Aiko tun daga ranar Dije tasha jinin jikinta da lamarin duniya don ko malamin da ya tarasu don yiwa kowa hukunci bata ɓoye ba ta sanar da shi ba wasu aljanu ƙarya ce itace,. Amman kasancewar ganin irin ta'adin da ta yiwa Prefect ɗin yasa ba'a yarda da zancenta ba, an dai yi mata gargaɗi sosai akan kada ta sake in kuma ta sake za'a koreta makarantar bayan anyi mata horo mai tsanani, tsoron hakan yasa Dije ta sha jinin jikinta da kowa.

Ranar da aka yi visiting Hajiya Mama da Surry suka zo mata Visiting tare da uwar siyayya da abinci mai rai da lafiya da suka kawo mata, bayan zuƙa zuƙan namomin da aka soyo mata daban tare da wanda aka tsatstsago mata cikin miyar tumaturin da aka ciko mata wani ƙaton ƙaramin bokiti.

Sun sha fira sosai inda har ta gabatar masu da Hannatu Hajiya Mama ta yi ta murnar ganin Dijen ta fara rage ƙiriniyar da take yi, shiyasa ta yiwa Hannatu kyauta tare da ƙara nuna mata ta dinga fahimtar da Dijen abunda ya dace, da kuka suka rabu Dijen tana ta faɗin ita dai a kaita wurin Baffah'nta ta fasa karatun, da ƙyar Hajiya Mama ta zille mata suka tafi suka barta tana ta kukan ita garinsu take so ta koma ta fasa karatun bata son zama likitar.

Dije a hankali ta fara rage rashin jin nata saboda ita kullum dare da tsoro take kwana matuƙar ba tare da Prefect ɗin nan take ba, shiyasa kacokam ma ta koma kwanarta don tafi jin natsuwa idan tana tare da ita, saboda Senior Aysha ba dai addini ba sannan uwa uba tana da tausayin na ƙasa da ita sosai gata da natsuwa, don kuwa ita ko shirgin sauran ɗalibai bata shiga, iyakacinta karatu tare da zuwa masallaci da kullum jam'i baya wuceta saboda addini ya ratsa jikinta sosai.

Sannu a hankali shaƙuwa ta shiga tsakaninsu har itama Hannatun ta dawo wurinta suka yi zamansu hankali a kwance, idan zata je masallaci tare suke zuwa haka ma abinci bata jin ita senior ce da su take bajewa su ci abinsu, wanki ma itace take yi masu su iyakacinsu ɗaurayewa su shanya, ta kamasu ta kwance masu kansu ta tsantsara masu kitso mai kyau don tana jinsu tamkar ƙannenta na jini, musammam ma dai Dijen da yawan gashinta yasa take ƙara sonta saboda duk ta yi mata kitso sai an dinga zuwa kallonshi.

Gata iya gata Senior Aysha tana nuna masu hakan yasa Dije ta kwantar da hankalinta ta fara jin daɗin zaman makarantar, duk da wasu da yawa ma akan abinda ta yiwa Senior Ruƙayya Yusuf yasa suka daina shige mata da nufin cin zarafinta ko su sakata wani mugun aiki.

Don ko da aka yi hutu Dije ƙaguwa ta yi da ta dawo makaranta saboda mutuncin Senior Aysha da kuma ƙawarta Hannatu.

Watan Dije biyar a Yola da aka yi wani hutun second term Hajiya Mama ta shirya ta da uwayen tsaraba suka nufi ƘIRIU waton garinsu Dijen Baffah ɗiyar Inna Hasiya kanwar Usmanu mijin Hansai.


Ina yinku sosai mutanena😅🤝🏻



Akafta😛







D/AUTA Ce😊

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Ɗaukaka da baiwa ALLAH sai ya baka in ya so, babu Malami ba boka zaka zamo mafifici ko da maƙiyanka basa so, ilimi nagarta ke saka ɗan'adam sahun farko, babba ko ko yaro adalci ke saka ka yo ƙarko, daina hanzari magana jari salonta na ɗauko aha😉duniya rawar ƴanmata na gaba sai ya yo baya, inda lokaci zamani ba shi ɓoye baiwata🥴*




*Lamba ta 36*



Tun daga farkon shiga garin Dije ta fara hango mutanen da ta sani, aiko sai faman murna take yi tana ɗaga masu hannu, kafin kace me yara da abokan Dijen da ƴan makarantar allonsu duka sun biyo motar suna kuwwar faɗin

"Ga Dije, ga Dije, Dijen Baffah ta dawo ƘIRIU"

Direba da ƙyar ya samu wajen da ya raɓa ya yi parking saboda cincirindon yara da matasan ƴanmata har ma da wasu samarin duka, kowa fatanshi ya fara yin ido biyu da Dijen, saboda labarin da suka ji cewa Dijen ta yi aure gidan masu kuɗi.

Aikam itama Dijen cikin ƙaguwa ta ɓalle murfin motar ta fito bakinta a washe tana faɗin,. "Wayyo daɗi gani na dawo garinmu"

Aguje ta zanƙara da gudu ta yi cikin gidansu inda taci karo da Inna rik'e da zane tana ƙoƙarin yafawa yana zarmewa, saboda tsabar saurin taje ta ga Dijenta da taji anata ihun faɗin gata ta zo.

Suna cin karo Inna ta zaro ido cike da mamakin ganin Dijen tare da buɗe baki saboda tsabar farin ciki ta ma rasa me zata faɗa, Dije kam tsalle ta yi ta ruƙunƙumeta tana faɗin

"Wayyo ALLAHna daɗi kasheni gani ga Innata, yi huhu ina Baffahna ALLAH yasa yana gida"

Ta saki Inna ta yi cikin gidan aguje sai dai dole ta ci ƙaton birki saboda ganin ɗakin Baffahn a rufe, cike da jin haushi ta ɓata fuska ta nufo Inna da ke ƙoƙarin dawowa cikin gidan tana faɗin

"Bari inje in dubo Baffahna Inna idan mutanen sun shigo ki basu ruwa kafin ina dawo"

Inna ta yi saurin faɗin

"Au! Ki ce ba tare da mijin kaɗai kuka zo ba? To ki jira mana
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment