Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ihun jin daɗi, ta saki Inna ta zo gaban Baffahnta ta riƙo hannunshi tana faɗin

"Ashe ko da gaske kai ne Baffahnah wayyo daɗi kasheni Ni Dije"

Usmanu ya hararota ya ce "ashe dai har yanzu da sauran hankalin?"

Tana dariya ta saki Baffah ta ce

"Yaya Usmanu ya zu fa na girma kai ma ka sani ai"

Surayya ta kai su Inna har falon sannan ta dawo ta ce da su Baffahn su shigo a gaisa kafin a kaisu muhallin da aka tanadar masu, Safwan dai tsaye kawai yake hannunshi a aljihu yana kallon Matarshi wadda ita har kullum bata gajiya da abun dariya, haka ma shagwaɓarta da wautarta suke ƙara dulmiyashi cikin ƙaunarta, waɗanda a cen inda aka fito yake ganin shirmenta amman sai ga shi yanzu sun yi masa rana, don kuwa salon ba ƙaramin burgeshi yake yi ba.

Bayan sun zazzauna ne aka sake sabuwar gaisuwa Dije baki yaƙi rufuwa saboda murna, Hansai kam sai yi take yi tana satar kallon falon saboda ganin tamkar ba a duniya take ba, don ko ita kanta Inna ta jinjina irin wannan daula da Dijenta ta ke ciki, shi kam Baffah ba ma maganarshi ake yi ba don sai hamdala yake yi cikin zucinshi akan wannan ni'ima da Allah ya wadata Dijenshi da ita.

Bayan an ƙare gaiigasawa ne Dukansu aka kaishi masaukinshi, Inna da Hansai aka kaisu wani ɗakin baki da ke cikin sashen Dijen, Baffah da Usmanu kam takanas Safwan ya yi masu jagora zuwa ɓangarenshi, inda aka kaisu wani ɗakin alfarma da aka haɗashi tamkar ɗakin wasu sarakuna don kuwa ya sha ado ta ko'ina sai ƙamari ke ta shi.

Sannan aka kawo masu abincinsu da aka tanadar masu kala kala, bayan sunyi Sallah ne suka fara lodawa cikinsu suna jinjina irin wannan uwar gara da aka tanada donsu kawai, Usmanu ya buɗe ƙafafuwa sai jan girki yake yi yana faɗin

"Ashe Baffah shiyasa kake ta farin ciki saboda kasan inda ka kawo ƴarka?, To Wallahi a ja kunnenta duk tsanani ta ci gaba da yi masa biyayya, don ko watarana ta yi masa shirme ya kaita ƙofar gida ya ce ya ce ta fi gida, to ta ce masa ita ba inda zata je don taga wurin zama, yana kaita tana dawowa har sai ya gaji don kanshi ya haƙura ya ƙyaleta"

Baffah nama cike da bakinshi ya ce "ba ma zata aika shirmen ba bale har akaita ƙofar gidan, don haka ka godewa ALLAH ka godewa Dijengalata don sanadinta ne kake cin wannan naman"

Haka suka dinga firarsu da suka saba cikin raha da tsantsar farin ciki da jin daɗin ganin Dijensu ta yi dacen aure.

Inna Kam da Hansai su ma suna inda aka saukesu Hansai tare da yaronta sai jan gara suke yi Inna kam cike da jin nauyi take tsakura abincin, Dije tana kallonta cike da jin daɗi ta ce

"Inna ki saki jikinki don ALLAH ki ci abincinki, ba fa kowa daga Ni sai ku ko Surayya ta barku ku ji daɗin cin abincinku cikin nutsuwa"

Inna ta maka mata harara tace "don ma kin ci sa'a na zo? Ba yanda banyi da Baffah'nki da Mijinki ba akan a barni ba sai na zo ba suka ce dole da ni za'a yi tafiyar, Ni ban saba da wannan rashin kunyar ba ta ƴan zamani, zuwa gidan Suruki har da zube ɗuwawu a cenye abincin Suruki, kai Ni Hasiya wannan zamani ina zaka da mu? Kin ga Inna Tumba har ALLAH ya yi mata rasuwa bata taɓa tako ƙafarta ɗakina ba" cewa da Mahaifiyarta da ta haifeta ma'ana kakar Dijen.

Dije tana dariya ta ce

"Cabɗi to ai Ni Inna duk wanda ma zai auri ɗiyana dole ne ma ya yi man nawa ɗakin a gidanshi yanda ya yiwa Mahaifiyarshi"

Inna da Hansai suka zaro ido, Dije ta ƙyalƙyale da dariya ta ce "ALLAH kuwa zama zan yi yanda ta zauna idan aka muzgunawa ƴata in fito mu raba gari Ni da Uwarshi WALLAhi"

Inna ta ce "laaa! Na ga aya ashe Dijen har yanzu ba ta yi hankali ba, to ai sai ki janyo a tattaroki tare da ƴar a watsoku waje da kayanku kusan na yi WALLAhi"

Dije da Hansai suka dinga dariya Surayya ta shigo da wasu sauran kulolin itama ta zauna aka ci gaba da firar da ita anata dariya.

Da ƙyar suka ciyo kan Inna ta ci abincin sai dai ta ƙi cin sauran abubuwan a gaban Surayya da Hansai, saboda surukutar da ke tsakaninsu, ganin haka yasa Dijen ta ja Hansai ɗakinta suka bar Inna nan ita kaɗai sannan ta cisgi garar itama cikin ɗar! ɗar! don kada a risketa bata sani ba.

****

Zee kam a ranar bata kwana gidansu ba don kuwa Baaba Asabe ta kwasheta da kayanta suka nufi gidanta, suna shiga tashin farko ta ce da ita

"Bani wayarki"

Zee ta ce "ai Ni tun ranar da na bar gidan ban sake ganinta da idona ba, tana cen Yola a falona ban sani ba ko ya ɗauke mani ko kuma ma an sace oho"

Baabaah Asabe haɗe da fuska ta ce "to je ki kai kayanki ɗakinsu Inna Dela ki dawo ki ji"

ZEE ta zaro Ido waje ta ce "Inna Dela fa kika ce Gwaggo?"

Kai tsaye ta ce "eh ita nace ko a cikin halittar jikinki akwai abunda su babu irinsu jikinsu?? "

Zee ta girgiza kai tare da sosa kai murya ƙasa ƙasa ta ce "ƴan aiki ne fa Gwaggo, Ni dai don ALLAH ki barni ko ɗakin waje ne zan zauna amman ba ɗakinsu Dela ba"

Baabaah Asabe ta katsa mata wata arniyar tsawa ta ce "za ki je ki kai kayan ko sai na haɗaki da buloli yanzu?"

Zee ta zabura aguje ta nufi inda ɗakin na ma'aikatan gidan yake saboda tsabar tsoron Baabaah Asaben da take yi, tana tafe tana gunguni Baabaah Asabe ta ɗaga murya ta ce

"Ai da kin tsaya ki nuna man banbancinki da ƴar aikin, to ai gara su basu shuka tsiyar da kika shuka a gidan mazajensu ba amman ga su a matsayin yan aikin, to ke in Baki yi a hankali ba yan aikin ma sai su fiki daraja a idon duniya, don ko wannan bankaɗa da kika janyo aka yi wa zuri'armu kawai hakkinmu ya isheki ballantana haƙƙin ɗaukar rai da kika so ki yi, in banda ALLAH ya tarfawa garinki nono da yanzu kin janyo muna bala'in da bamu san inda zamu jefa kanmu ba, don haka WALLAhi Ni banu wani ragi tsakanina da ke a gidan nan don yan aikin ma sai sun fiki daraja a wurina"

Har Zee ta ajiye kayan ta fito bata daina sababin faɗa ba, haka ta zaunar da ita tana ta tsara mata abunda zata yi a gidan tun daga safiya har dare, hankalin Zee bai ta shi ba har sai da ta ji wai har da wanki zata dinga yi kullum, wankin ma kuma na samarin ƴaƴanta da suka balaga wasu ma har suna zancen aure amman ace har da su zata dinga yiwa wanki,cike da ƙuncin zuciya ta kwana tare da cin alwashin muddin ta ji za'a kasheta WALLAhi dole ta tsere ta bar mata gidanta, don bazata zura ido aiki ya kassarata ba tunda daman cen ita ko undies ɗinta wanke mata ake yi, ba abunda ta iya in banda dafa indomie ko shi don watarana in an dafo mata tace bata yi mata daɗi ba, Mahaifiyarta tace ba mai sake dafo mata wata in tana so ta je ta dafa da kanta, to da hakan ne ta iya dafata saboda Daddynta ya ajiye mata masu aikin da suke yi mata duk abunda take so, to yanzu ga shi Baabaah Asabe zata sakata shiga uku.

Don kuwa tun da sassafe ta tadota daga baccin da ta koma na bayan asuba, ta fito ta kaita wajen tulin kayan wanke wanke ta ce ta fara idan ta gama ta je ta share gidan lungu da saƙo, cike da fargaba da tsananin tashin hankali ta ke ƙarewa ƙaton gidan kallo, tana nazarin ko rabinshi aka sakata sharewa ai an so kasheta bale duka, sai ga muryarta a saman kanta tana faɗin

"Zaki fara wanke wanken ko sai na fara sauke maki bulalata a jikinki?"

Zee jiki yana rawa ta fara harhaɗa kwanonin Baabaah Asaben ta ce da wata matashiyar ƴar aikinta ta nunnuna mata yanda zata yi, tana tsaye har aka nunawa Zee komi ta fara m wankewa tana hawaye sannan ta bar wajen, ta dawo falo ta zauna zuciyarta cike da jin daɗin yanda ta yi nasarar da Daddyn Zee ɗin ya gano kuskuren da ya tafka akan tarbiyyar ɗiyarshi, tare da jin daɗin amincewar da ya yi akan ta zo da ita hannunta ta zauna don bai san ƙudurinta akan Zee ɗin ba, da wataƙila ba zai yi saurin amincewa ba duk da kuma yasan ba zata yi mata ta daɗi ba, amman bai taba tunanin irin wannan azabtarwa zata yi mata ba.

Zee Kam haka aka yini ana aiki wankin samarin ma sai da ta yi sai dai su ma kansu ba da son ransu ba don dai Mahaifiyarsu ta yi masu jan kunne da kashedi sosai akan duk abunda suka ga ta saka Zee iyakacinsu Ido, Dole Suka zura ido suna kallon yanda take ta yi masu wankin, cikin ƙankanin lokaci hannunta ya yi ja ya saluɓe aiko ta fara yarfa hannu tana kuka, ganin haka yasa aka canza mata wani aikin ko da dare ya yi ta kwanta ko'ina nata ciwo yake yi, da ciwon jiki ta kwana kan tabarma tana haki tana juye juyen wahala.





Sorry Zee😢 Wai ko dai in zo in gudu dake ne🙊 gidan mum Irfaan ko gidan Daughter Rufaida ko wurin ƙanwata Asiya? Ki yi shawarar inda kike son zuwa kafin in dawo🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️🤣





Akafta😊










D/AUTA CE✍🏻


*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*



*Lamba 68*



Daren ranar Dije da Inna sai hira suke ta zubawa, don ita Hansai tun da ta ji cikinta ya ɗauka ta baje abunta sai sharar baccinta take yi ita da yaronta, ganin dare ya miƙa ne Inna ta ce da Dijen ta tashi ta je wurin Mijinta, Dije tana zumɓuro baki ta ce

"Anan zan kwana Inna mu yi ta firarmu Ni da ke Inna, sabida ALLAH yaushe rabon da mu ga juna an daɗe fa? Ni dai don girman ALLAH Inna ki barni in kwana abuna anan ɗakin"

Ta ƙare maganar tare da zubowar wasu ƙwallah, Inna ta gyara ta yi kwanciyarta tana faɗin

"To Ni dai bacci nike ji idan ke baki gaji da firar ba ki ci gaba ai akwai aljanun dare suna saurarenki zasu tayaki yin firar"

Dije ta zaro ido tuno abunda ya taɓa faruwa a school ta yi saurin kwanciya bayanta ta ƙudundune tana faɗin

"Inna ki yi man addu'a kar su kamani don ALLAH"

Inna ta miƙe zaune cike da mamaki ta ce "zaki ta shi ki je wurin Mijinki ko ko so kike yi ya ɗaukemu waɗanda basu san abunda suke yi ba?"

Dije ta miƙe tana kallon ƙofa tace

"To mu je ki rakani WALLAHI tsoro nike ji"

Inna ta riƙe baki cike da mamaki ta ce

"Tunda kike gidan baki ji tsoro ba sai yanzu da kika ga mun zo ko? To ya yi insha ALLAHu gobe tun da sassafe mu zamu bar maki gidanki tunda so kike yi ya ɗaukemu mutanen banza"

Dije ta miƙe ta fito Inna ta rufo ɗakin zuciyarta cike da nauyin kada Safwan ɗin ya ga sun riƙeta, aikuwa Dije cikin sanɗa ta ke tafiya tana waige sai jin ta yi anyi caraf da ita, ba shiri ta yage baki da nufin fasa ƙara taji bakin Malaminta cikin nata, gano shine yasa ta ƙara ruƙunƙumeshi jikinshi tana faɗin

"Mu je ɗaki tsoro nike ji"

Cike da jin daɗi ya sake manneta jikinshi suka yi ɗakinshi, ganin da gaske tsoron take ji yasa ya fara tambayarta abunda ya tsoratata, cikin murya ƙasa ƙasa ta yi masa bayanin yanda suka yi da Inna, cikin dariya ya ce

"ALLAH ya biya Inna da gidan Aljannah don Ni ta kyauta man, saboda tun ɗazu da na dawo wurinsu Baffah nike ta juye juye Ni kaɗai akan gado, dole na fito falo na zauna ina kallo nan ma na ji ba daɗi na kashe ina tunanin yanda zan yi in ce ki zo, ashe Inna tasan ƙishina shiyasa ta koro man ke waje"

Dije ta tureshi cikin fushi ta ce "tunda haɗe man kai kuke son yi ai ku je ni ma gobe wurin Hajiyarmu zan kwana "

Safwan ya janyota jikinshi ya ce "ai Hajiyarmu ma ba zata so ki bar Mijinki shi kaɗai ba yana kewa ba"

Haka ya hilaceta ya gwangwaje abunshi tare da sassafta murya wurin sambatun da ya saba, don gudun ya tafka abun kunya gaban surukai.

Tun da Sassafe aka kammala masu komi na breakfast ɗinsu tare da taimakon wasu yan aiki biyu da Hajiyar ta ƙaro masu, bayan sun karya ne aka sake wata sabuwar gaisawa sannan Safwan ya kwaahesu zuwa gidansu su gayar da Hajiyar, tarba ta mutumci Hajiya Mama ta yi masu fuska cike da fara'a tamkar cewa da man cen ƴan'uwanta ne, Inna da Baffah suka yi godiya sosai akan yanda take kulawa da Dije tamkar itace ɗiyarta ba Safwan ba, Inna da Hansai da Dijen sun daɗe gidan tare da Hajiya Mama sannan Safwan ya dawo da su Baffah da ya je kaisu yawon ganin gari, marece sakaliya ya ɗaukesu ya kaisu gidan Mijin Surayyy, inda itama ta yi masu tarba mai kyau tamkar kar su rabu saboda kirkin Surry ba ƙaramin burge su Inna yake yi ba, sai gaf da magriba suka dawo gidan inda suka taradda an haɗa masu abincin dare mai rai da lafiya, tuwon farar shinkafa da miyar agusi ta ji zuƙa zuƙan namomi tare da lafiyayye ferfesun kajin turawa masu manyan tsokoki, bayan sun ci abincin ne aka koma yin firar bankwana saboda tun da sassafe zasu juyawa inda suka fito, tun cikin daren Safwan ya tanadar masu duk abunda zai ba su ya basu, Hajiya Mama ma da nata kalar tsarabar Surayya ma da tata, haka suka yi ta godiya kamar ba gobe, don kuwa su kansu sun san ba ƙaramin arziƙi suka yi ba,saboda bancin sutura kuɗi tsabarsu dubu ɗari Safwan ya baiwa Baffah, Inna dubu Hamsin Usmanu da talatin Hansai ashirin yaronta goma, bayan suturar da aka cikasu da ita da turaruka da sabulai kala kala, yaron Hansai kanshi ledar kayanshi daban aka siyo mashi masu ɗan karen kyau.

Tun cikin daren Dukansu suka saka Dije tsakiya suna yi mata nasihohi tare da jan kunne akan ta ninka wa mijinta da Mahaifiyarshi biyayyar da take yi masu, haka ma ƴan'uwaanshi ta riƙesu tamkar yanda zata riƙe nata, in ma da hali su fi natan don kawai ta sami zaman lafiya da kwanciyar hankali a gidan aurenta, anan ne take sanar da su gumurzun da aka yi da Zee akan kashe sun da ta so yi tare da ƙudurinta da ta yanke akan muddin Zee ta dawo to ita zata bar mata gidan, cikin fushi Usmanu ya ce

"WALLAHI kika kuskura kika bar wannan gidan akan baƙin shirmenki sai na saki jiki na lakaɗa maki shegen duka"

Inna tana harararta ta ce "to bari ki ji da kyau muddin kika taka ƙafarki kika bar gidan nan bada izinin Mijinki ba to ki sani ban yafe maki ba"

Baffah ya yafito Dijen ta zo gabanshi ta zauna tana zimɓoro baki yana dariya ya ce

"Shin Ina Dijengalata?? "

Hawaye suka zubo mata ta ce

"Gani Baffah".

Yace "to ki ajiye komi ki yi zaman aurenki tsakani da ALLAH, ki sa a ranki duk duniya babu wanda ya isa ya yi maki abunda ALLAH bai yi maki ba, haka ma kaf mutanen duniyar nan idan ymza su taru akan sai sun kasheki to basu isa su kasheki ba har sai kwananki ya ƙare, don haka ki ɗauka cewa duk abunda kika ga ya sameki daga ALLAH ne, abunda ma ya kuskure maki shi ma daga ALLAH ne da kin yi hakan shikenan kin ci maganin matsalarki, ALLAH ya saukeki lafiya ke da ƴar uwarki kuma ya baku zaman lafiya a gidajen aurenku"

Dije ta rufe fuska cike da jin kunya ta ce "Ameen" cikin maƙoshi, haka suka dinga nusar da ita abubuwa da yawa masu amfanarwa sannan ta saki jiki ta dawo dai dai aka ci gaba da fira cikin raha da annushuwa.

Dije ta ce su gayar mata da Gambo da su Ladiyo, ta ɗauko sako ta bayar ta ce akai masu ace in jita, don kuwa su Ladiyo kowa dubu bibbiyu ta bada akai masu Balan duduwa dubu biyar tare da Duduwar itama dubu biyu, sannan saƙon Maigari da Matanshi na shadda da atamfofi, Malaminta na makarantar allo ma da saƙonshi tare da ɗalibanta na makarantar da ta baiwa sababbin goma goma ta ce a raba masu su yi mata addu'a, abun dai masha ALLAH gwanin burgewa Dukansu kowane zuciya cike da tsantsar farin ciki da jin daɗi, tare da yi wa ALLAH godiya da ya baiwa Dije miji ɗaya tamkar da goma kuma ya haɗasu da mutanen kirki.

Tun cikin daren su Hajiya Mama suka zo suka yi sallama da juna shiyasa tun da sassafe suka fara shirin barin garin, Dije sai kuka take ci ana lallashinta har motarsu ta ɗaga ta faɗi ƙasa tana ta kuka gwanin ban tausayi, sai da Malaminta ya yi mata jan ido sannan ta fara shiga taitayinta, don ya yi mata alƙawarin in dai har ta bar kukan to itama zai kaita idan cikinta ya yi ƙwari ta je ta ganosu, sannan ne ya samo kanta ya koma aikin ban baki tare da daɗin baki kala kala.

Sati ɗaya a tsakani takardar samun aikinshi ta fito inda kai tsaye aka postershi Abuja, tare da zunzurutun albashi mai tsoka da kyautar sabuwar mota da gida a garin Abuja, mutane da yan uwa sai murna ake yi masu don Lawi kanshi sai da ya zo ta ya murna tun daga Gombe har Yola tare da Amaryarshi da tuni itama ta kusa zama Mama, don kuwa ɗauke take da cikinta ɗan wata biyar itama kyakkyawar bafulatana da ita masha ALLAH, kwanansu ɗaya a gidan suka koma cikin kewar juna, saboda jinin matar Lawin mai suna Maryam da ya haɗu cikin lokaci ƙanƙani da na Dijen Baffahn, saboda itama ba laifi akwai barkwanci da son wasa da dariya gata da saurin sabo.

Lokacin da aka ɗibar masa da ya cika ya fara zuwa aiki, fiddo da wasu dattijai biyu suka dawo gidan suna taya Dijen Baffah zama, atakure ya yi sati ɗaya ya dawo Yola cike da ɗokin Matarshi, don ba ƙaramin sabo ya yiwa kanshi da ita ba, shiyasa ya ji gaba ɗaya zama garin bai masa daɗi ba, dole ya kwashi Matarshi suka nufi garin Abuja a gidansu da aka basu, don ya so har sai ta haifu sannan su dawo nan ɗin , to amman ya ga hakan bazata samu ba don sabon da ta yi masa kanta, ga shi kuma shi matan banza basu gabanshi don ko na kwarai ɗin baya kula shirginsu bale har na banzan.

Aunty Ummi da su Husnah sai murna suke yi Dijen ta dawo kusa da su, shiyasa kullum suna tare basu wannan wurin shaƙatawa basu wurin ciye ciye da tanɗe tanɗe da lashe lashe, kafin ka ce me idon Dijen sun ƙara buɗewa cikin garin Abuja, don kuwa ita kanta tasan wurare da yawa.

Da zama ma ya yi daɗi sai ga shi da koya mata driving, tana jin tsoro tana fargaba haka yake koya mata ita duk da bata so, saboda bala'in tsoron da ta ke ji amman a hankali ko wata biyu basu rufa ba a garin ta fara iyawa, don ya ce da ta iya zai siya mata tata idan ALLAH ya sauke ta lfy, ko don ta fara zuwa makarantar da take kwaɗayi ba tare da takura ba, don saboda busyn da yake yi a wurin aikin nashi kullum, gashi kuma yana son ta yi karatun don shine babban gatan da zai mata a rayuwa, saboda akwai rayuwa akwai mutuwa in mune yau ba mune gobe ba, Yana da kyau mace ta dogara da kanta ko don ranar da kika rasa mai tallafa maki ki kula da kanki da yaranki da iyaye da ƴan uwanki duka.


****

ZEE Kam tun bata saba da aikin wahala ba har yanzu ya fara zame mata jiki, don ta yi ta tserewa tana zuwa gidajen yan uwa ana dawo da ita wurin Baabaah Asaben, don kowa cike yake da haushinta ba kaɗan ba musamman ƙin Aminu da ta yi tare da abun kunyar da ta janyo masu, Mahaifiyarta kanta da ta je gidan take korota ta fito tare da yi mata kashedi da gargadin cewa duk ta yarda Daddynta yasan halin da take ciki a gidan gwaggonta sai ta tsine mata, tana kuka take komawa yanzu har ta haƙura don kanta ta daina gudun, ganin hakan yasa Gwaggon ta fara sassafta mata daga matsin lambar da take yi mata, don kuwa ta ladaftu sosai kuma ta gano irin kuskuren da ta so aikatawa, ta yiwa ALLAH godiya da yasa Ruma bata bari ta aikata mugun abun da ta yi niyya ba, ga shi ta rasa Safwan ɗin kuma Aminun ma ta rasa shi don kuwa yanzu haka ƙawarta Sadiya yake aure, don Ruma ya so aura ta nuna masa amincinta da Zee bazata iya aurenshi ba, Sadiya kam hannu biyu ta karɓeshi yanzu haka da ƴarsu tana nan mai sunan Mahaifiyarshi.

Zee ta shiga damuwar rashin jin Safwan ɗin da kullum take tsumayin zuwanshi gareta ya ce ta dawo, amman shirun da ta jini yayi yawa ne ta fara tunanin binshi da kanta, don laifin da ta aikata masa ko ma wanene dole ne ya sallamata, kasancewar tasan numbarshi akanta yasa da Ruma ta zo ta ari wayarta ta kirashi, kasancewar baya da layin Rumar a lokacin shiyasa daga baya ya bi miss call ɗin da ya gani kusan goma sha bai ma san an kira ba, sai dai jin murya Ruma yasa ya yi saurin faɗin

"Wacece ??"

Jikinta yana rawa ta ce "Rumasa'u ce ƙawar Zee don ALLAH ka yi haƙuri da abunda ta aikata ita ce ta kiraka ɗazu da naje wurinta ta ari wayar ta kiraka baka ɗaga ba, saboda WALLAhi yanzu Zee ta canza sosai kuma ta yi nadamar abunda ta aikata"

Cike da mamaki ya ce

"Daga ke har ita kada ku sake nemana matuƙar kuna son kanku zaman lafiya"

Ƙittt! Ya kashe wayarshi gaba ɗaya cike da jin haushinsu duka, Dije da ke shigowa ɗakin da tiren coffee'nshi ta ajiye tiren akan stool ta ɗauki cup ɗin ta zauna tana kallonshi tare da nazarin yanayi shi, sannan ya zura hannu da nufin ya karɓi kofin ta riƙe gam idonta a kanshi ta ce

"Wa ya taɓo man Habibyna? Don haka na fita na barshi ba plss ka yi haƙuri ko ma mene saboda zama cikin mutane sai da kai zuciya nesa Mijina"

Cike da jin daɗin kalamanta ya duƙo ya kurɓi coffee'n sannan ya ce, "waɗannan ba irin mutanen da kike tunani bane, ki share da su kawai don na riga da na shafe babinsu a rayuwata"

Dije ta miƙa masa cup ɗin ya karɓa ya dinga sha a hankali har ya shanye, sannan ta karɓi cup ɗin ta ajiye ta kalle da kyau ta riƙo hannunshi ta haɗe da nata ta dunƙule waje ɗaya ta ce

"Wacece ta kiraka?"

Cikin diriricewa ya ce

"Ruma ce ƙawar Zee take rokona akan inyi haƙuri in yafe wa Zee wai ta yi nadamar abunda ta aikata"

Dije ta ji wani ɓacin rai ya ziyarci zuciyarta, amman ta yi dubarar ɓoye damuwarta ta ce

"To kai kuma me ka ce?"

Ya ɓata fuska tamkar a lokacin sannan ya sanar da ita abinda ya ce da ita, Dije ta ɗauko hannunshi ta ɗora a saman cikinta da ya fara turowa kaɗan, ya bita da kallon ƙarin ba'asi sannan ta kashe masa ido ɗaya ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment