Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

iya binsu ba, matuƙar sheɗan yana buga ganganunshi saman kanka, na gode sosai da taimakon da kika yi mani aka dawo da ni, kuma ki sa a ranki cewa kina da ƴar'uwa saboda yanzu Zee ta ɗaukeki tamkar ƴar'uwarta ta ciki ɗaya tunda har na gano ke ɗin alkhairi ce garemu ni da shi"

Tana ƙare faɗar maganar ta miƙa masa wayar ta fice da sauri tana kuka, ya bita da kallo sannan ya sauke ajiyar zuciya yace

"Babyluv sannu da namijin ƙoƙarinki, lalle ke alkhairi ce ga rayuwata, ina ta ya ƴaƴana farin cikin samun uwa ta gari irinki, fatana kawai a yanzu ALLAH ya sauke man ke lafiya ki bani Babyna a hannu in ɗauka"

Dije ta goge ƙwallarta ta saita natsuwarta ta ce "Insha ALLAHu ƴaƴa har sai ka ce in tsaya haka nan in huta , don in na Fara watso maku su sai ka rasa da hannun da zaka riƙe sauran"

Safwan ya fashe da dariya cikin dariyar ya ce "au watsosu ma zaki yi don salon mugunta?, To bari ki ji ko da jefosu zaki yi ta yi duk bayan minti biyar Habibynki ba zai taɓa rasa hannun da zai karɓesu ba, ke dai kawai ki natsu ki sako man su sannu a hankali ina karɓewa cikin farin ciki ba tare da gajiyawa ba ko ƙosawa"

Haka suka yi ta firarsu mai cike da barkwanci da raha har dukansu suka daina jin damuwar rashin ganin juna, sannan Dije ta daƙile firar dolenta don bata son ta shiga haƙƙin Zee, ba don ya so ba suka yi sallama cikin kewar juna tare da kwaɗayin ganin junansu, saboda mugun sabon da suka yi wa juna da kawunansu.

Har ga ALLAH Safwan ya ji daɗin yanda Zee ta dawo macen kirki, shiyasa cikin dauriya da kai zuciya nesa ya mu'amalanceta har lokacin barin garin ya yi ya tattara kayanshi ya koma Abuja, wurin Matarshi da ya ke jin a duniya kaf ba ya da matar da zata kamo ƙafarta ma bale ta kamota, ko da ko akwai ɗiyan lu'ulu'u da murjani a cikin.


****

Haka rayuwa ta yi ta shurawa sannu a hankali har cikin Surayya ya isa haifuwa ta haifo ƴarta mace masha ALLAH da ita.

Cikin zumuɗi Dijen ta yi ta murnar zuwa Yolar sai dai idan ta tuna da zata ga Zee sai jikinta ya yi sanyi, dole dai haka ta daure ta matsa masa ya barta ta biyo su Aunty Ummi suka nufo Yola, saboda a lokacin shi ana tsaka da aiki don during working hours ne, cike da jin daɗin yarinyar Dije ta fara santi tamkar ta sace yarinyar take ji saboda sonta da take yi, Hajiya Mama da su Surayya sai dariya suke yi mata ganin yanda ta maƙake yarinyar bata son kowa ya ɗauketa, don har goyeta take yi sai Hajiya ta yi faɗa take sauketa, Zee ma kullum tana zuwa da ita ake komi shiyasa Dijen ta rage kishinta da take ji aranta, saboda ganin yanda ta ke ta haba haba da ita tamkar cewa babu abunda ya taɓa shiga a tsakaninsu, haka ma da yanda take ta janta a jiki tana nuna mata cewa ai an zama ɗaya babu zancen wata kishiya shiyasa itama ta ajiye komi suka fara ɗasawa, wanda hakan ba ƙaramin daɗi ya yi wa Hajiya Mama ba, ta ƙara godewa ALLAH da har ta jajirce Safwan ya dawo da aurenta, don tasan dole ne sai ya nemi wani auren tunda har ya saba da mace biyun, kuma da wacce ba'a san halinta ba gwara wadda daman cen an san halinta sai a ci maganin matsalar.

Aka yi taron suna lafiya cike da ƙayatarwa yarinya ta ci sunan uwar Mijin Surry ana yi mata laƙabi da ilham, bayan suna Safwan ɗin ya zo ya yi kwana biyu sannan ya kwashi Matarshi suka koma Abuja. kawosu ita da

Sannu a hankali itama Dijen cikinta yana ta miƙawa har ya kai watannin haifuwa, Hajiya Mama ta matsa masa akan dole ya dawo da ita wurinta ta haifu, amman ya nuna shi dai ya fi son idan ta haifu sai su dawo yolar, saboda cen ɗin tana samun kulawar manyan likitoci a Asibitin da take awo, sai da Hajiya Mama ta yi masa jan ido sannan ya kwasota da himilin uwar siyayarta da ta jaririn da za'a haifo masa, don daman cen shi rabuwa da ita ne ba ya so saboda ko da take da titsetsen cikinta idan jarabarshi ta motsa tasan ta yanda zata faranta masa har ta gamsar da Habibynta.

Shi yasa ko da suka zo Yolar ya kasa ya tsare gidan Hajiya Mamar ya ƙi barin garin har sai da korashi saboda yanda ake ta nemanshi a ma'aikatar ta su, saboda muhimmancin da yake da shi dole ne wani abun sai da shi.

Satinta ɗaya a Yola ta fara jin sign na naƙuda, Hajiya Mama tana bata kula sosai da sosai don itama ɗin har nurse's ta samo mata masu duba mata ita har gida ba sai anje Asibiti ba, Zee kanta kullum tana gidan ana renon cikin da dakon zuwan haifuwar, sai ko ga shi cikin ikon ALLAH wata ranar juma'a Asubar farin ta fara naƙuda, jikin Hajiya Mama yana rawa ta saka direba ya kwasheta da kayan da duk za'a buƙata suka nufi wata babbar Asibin da ke garin yolar, cikin nasara kwata kwata bata yi minti goma da shigarta labour room ba ta haifo santalelen yaronta Mai kama da Ubanshi sak, fari jajir har wani yalo yalo yake yi saboda tsabar farinshi, ga shi ƙatoto da shi masha ALLAH tamkar ba haifuwar Dijen Baffah ba.

Farin ciki wajensu Hajiya Mama da fiddo da ma Zee ɗin abun ba'a magana, saboda har rige rigen ɗauka ake yi tsakaninsu su biyu, Surayya ma rufe ido ta yi tace tunda da ita yaron yake kama itace zata riƙeshi, Hajiya Mama dai sai dariya take yi masu idonta akan ɗakin da Dijen take tana ta baccin sauke gajiyar naƙudar da ta sha.

Ango ƙarni kam daman yana kan hanyar zuwa Yolar sai ga kiran Fiddo ya shigo wayarshi cikin kuwwa da ihun murna take sanar da shi an samu Baby boy, ba shiri shi ma ya buga wata ƙatuwar kabbara ya ce

"ALLAHU Akbar? Alhmdllh! Shikenan na zama Baba, Little sis kina da tukuici mai tsoka a wurina, to ya ita Mamar boy ɗin lafiyarta ƙalau dai ko?"

Cikin murnar albishir ɗin da ya yi mata na tukuici ta ce "fine take big bros bacci ma ta ke yi yanzu haka"

Baki a washe ya ce

"Ok Ina Kan hanya daman ganin na kusa ƙarasowa garin ki shafa man kan babyna"

Cike da jin daɗi fiddo ta koma ɗakin tana dariya ta ce "Wayyo daɗi Ni ce na yiwa yayanmu albishir ya ce in tsumayi tukuicina"

Surayya da ke ta faman murnar ta sameshi a wayar da nufin ta riga kowa sanar da shi ba shiri ta kashe wayar tana harararta ta ce

"Ai WALLAHI kin ƙware da mugunta yanzu don salon yaudara shine kika fice waje kika rigani to ai dole mu raba koma minene"

Zee sai dariya take masu Hajiya Mama ta kira cen garinsu Dijen ta sanarwa da su Baffah, sannan ta dinga kiran mutane yan'uwa da abokan arziƙi tana ta sanarwar haifuwar, kafin ka ce me Asibitin ta cika da yan taya murna kowa baki har kunne.

Angon ƙarni ma ko da ya zo ya taradda mutane ciccike sai tayashi murna ake yi, sai washe baki yake yi amman idonshi suna cen wajen dubo ta ina zai hango kyautar da ALLAH ya yi masa?, Aiko sai ga shi ya hango babyn hannu wata dattijuwa tana tofeshi da addu'o'i.

Cikin sauri ya nufeta ba kunya ya saka hannu ya karɓe yaron tamkar ya yi ihu saboda daɗin ganin yaron a hannunshi, ba tare da tuna da inda yake ba ya kaiwa yaron kiss a goshi da baki, sannan ya hankalta da mutane bakinshi ya ki rufuwa saboda dariyar kanshi da jin daɗin ganin ɗan shi,sannan ya miƙa yaron yana tambayar Hajiya Mama Dijen ta yi masa nuni da ɗakin da take hutawar, ya nufi ɗakin zuciyarshi fess da farin cikin hangota kwance har a lokacin tana ta baccinta, ya tsaya jikin gadon ya shafo kanta tare da duƙowa ya yi mata kiss sannan ya riƙo hannunta, cikin sauri ta buɗe idonta ta saukesu a kanshi ba shiri ta washe baki da murmushi akan fuskarta ta ce

"Habiby"

Ya riƙe hannunta duka biyu ya ce "sannu da ƙoƙari kin ji? ALLAH ya biyaki da gidan Aljannah, naga yarona Masha ALLAH har ya fiki kyau"

Ta ɓata fuska tare da turo baki ta ce

"Saura ƙiris in fara kishi da shi yasin"

Yana dariya mai cewa cike da zallar ƙaunarta tare da shauƙin sonta da ke ɗibarshi, ya duƙa ya tsotso leɓenta sannan ya ce

"I love You so much my heart desire, ke mahaɗina ce idan ina kusa da ke kina sakani susucewa, don haka kada ki janyo in yi abunda za'a ga na yi rashin kunya"

Dije ta yi masa wani fari da ido ta rausayasu sannan ta ce "ina sonka Habiby"

Cikin zurmawa da salonta ya ce "ina son matata kuma ina son kasancewa da abuta a kullum a koda yaushe kuma a kowane lokaci, amman yanzu sai na yi zaman jira kenan ko? Kwana nawa ne ma ake yi wai?"

Dije ta rufe fuska cike da jin nauyin maganar ta ce "kwana dubu uku ne ake yi ai nasan Habibyna jarumin gaske ne zai iya yin fiye da kwanakin ma "

Ya zaro ido waje baki buɗe ya ce "A wannan karon kam dole ne kowa sai ya gano ragwantakata, cabɗi ki ce in mutu kawai kafin zuwan lokacin"

Dije zata yi magana wata Nurse ta shigo tana dariya musamman ganin yanda suke riƙe da hannun juna gam gam tace

"To luv bird's zaku iya tafiya gida tunda har ta gama hutun, sai ku je cen ku ƙarasa soyayyar"

Dukansu suka kalli juna suna dariya Safwan ya saka hannu aljihu ya fiddo kuɗi bai ma tsaya lissafi ba ya miƙa mata yana faɗin

"To ga goro a tayamu da du'a'in dawwama cikin farantawa juna"

Ta karɓe tana jin daɗi ta fice bayan ta gama zuba masu addu'o'in.

Haka aka tattaro da maijego da jinjirinta da masu zuwa ta ya murna aka nufo gidan Safwan, saboda Hajiya Mama ta ce akai Dijen ɗakinta saboda danginta idan sun zo ta ji daɗin tarbarsu, kuma duk wanda bai san muhallinta ba ya gani, amman ta saka wasu dattijai masu kula da ita waɗanda za su yi mata komi kamar a gabanta, cike da jin daɗi Safwan ya fice bayan ya saukesu ya faɗa shaguna yanata lodo kaya har na hauka, bayan waɗanda suka sissiyo a Abuja sai da ya yiwa Dijenshi set biyu na jakunkuna masu samfurin akwati tsadaddu masu shegen kyau, kowace jaka maƙare da kaya na alfarma sannan ya yi wa boy na shi set guda shi ma tsadaddun kaya, Zee ma da nata set sannann ya yi wa su Hajiya Mama da su fiddo su ma, ya sa aka kwaso masa kayan suka nufi gidan Hajiya Mama ya zubesu gabanta, duk da ta ji daɗi amman ta yi masa faɗan almubazzaranci ba kyau, yana dariya ya ce

"Duk abunda na yi maku Hajiya ai kun fi ƙarfinshi wajena, amman insha ALLAHU zan kiyaye a gaba, don ko wannan don naga khadija ko lefe ban yi mata a lokacin aurenmu ba"

Ta sauke ajiyar zuciya ta ce To ALLAH ya rufa asiri ya ƙara buɗa maka kuma ya baka ikon sauke ɗawainiyar gidanka gaba ɗaya "

Ya ce '"Ameen"

Sannan ta ce idan duhun dare ya shigo ya zo ya kwashi kayanshi ya kaiwa Matanshi, sannan ta yi masa godiyar na su da ya siyo masu tare da saka masa albarka, da addu'ar kariya daga sharrin ko mi ƙankantarshi.

Dije kam tana cen ita jaririnta sun sha wanka sai ƙamshi suke yi, Surayya ta haɗa mata tea mai shegen kauri ta shanye saboda saukowar ruwan nono da wuri, sannan dattijan suka baje wajen da aka keɓe don kawai irin wannan lokacin, anata hidimar dafe dafe da dama mata kunun jegon da Hajiya Mama tasa aka dako tun lokacin da aka yi haifuwar.

Ko da ya dawo gidan ya taradda Zee da su Surayya ɗakin sunata firarsu suna shewar jin daɗi, Dije riƙe da kofin kunun tana sha a hankali saboda zafinshi, ya ƙaraso cikin ɗakin ya kalli Zee da ke goye da yaron ya ce

"Naman boy Daman cen kin iya goyon ne?"

Tana dariya ta juya kanta baya ta kallo yaron ta ce

"Ka ga alama don kuwa ga yarona nan yanata baccinshi don shi ma yasan Uwa ba wasa ba ce"

Gaba ɗaya suka fashe da dariya wajen dariya har Dijen ta ƙware da kunun da ta cika bakinta, sai ga shi da kaiwa wurinta ba shiri yana bubbuga bayanta yana hura mata kai tare da faɗin

"Sannu baby sannu"

Hankalinshi bai kwanta ba har sai da ya ga ta dawo normal sannan ya fara dungure mata kai ya ce ,. "Idan kin san ba zaki natsu ba to ki koma wani gu sai kin shanye kunun ki dawo don bana son wasa da lafiya"

Dije ta yi masa wani kallo cikin marairece fuska sannan ta riƙe kunnenta ta ce

"Am sorry habi....."

Ta kallo Zee ta yi saurin datse cikon maganar, Zee tana dariya ta ce "biby"

Surayya da fiddo suka fashe da dariya saboda yanayin da Zee ta yi maganar tana marairece fuska tana lanƙwashe wuya tare da murguɗa baki, sannan ta kalli su Surry ta ce

"Ku zo mu basu waje tunda a gabanmu ma ba za'a yi muna kawaici ba"

Su Surry Suka fice ɗakin suka barsu sunata kallon Zee cike da dariyar da ta suƙesu, Safwan ya kalli Dijen ya ce

"To Ni yanzu ya zaku yi da ni? Babyna na zo gani na taradda an wani duƙunƙuneshi a baya, ƙarshe ma ga yanzu kin janyo an fice da shi bamu gaisai ba"

Dije ta ɗauki kunun ta kurɓa sannan ta haɗiye ta ce "kun fi kusa ka je ka karɓo tunda baka godewa kulawar da yake samu ba"

Ya kalleta da kyau ya ce "haka ma zaki faɗa?"

Ta sake kurɓa kununta sai da ta cika bakinta sannan matso jikinshi ta janyoshi ta riƙo kanshi ta tallafo ido cikin ido ta goga hancinta da na shi sannan ta nufi bakinshi kamar wani sakarai ya buɗe bakin ta juye masa kunun sannan suka fara zuƙe kunun tare har suka shanye, sai ga shi sun buge da dulmiya cikin wata sabuwar duniya sun manta shaf da cewa ba su kaɗai suke ba har sai da suka ji kukan yaron sannan suka dawo hayyacinsu.

Sai ga fiddo ta zo rungume da shi ta ce tsohuwa ɗaya daga cikin dattijan ta ce ta ba shi nononshi ya tsotsa, Dije ta zaro ido waje ta ce

"To Ni ina nasan yanda zan bashi ??"

Safwan ya karɓi yaron Fiddo ta fice ya sakarwa yaron kiss sannan ya kalleta ya ce

"Oyo bari Abban boy ya koya maki riƙe man shi anan"

Ta karɓa ta rungumeshi ya ɗaga rigarta ta ƙasa ya fito da nonuwan, cike da zallar maitarsu a fili ya shafosu duka ta yi saurin lumshe ido, sannan ya ɗago kan yaron ya saita bakinshi ga ɗaya aiko yaron ya fara tsotsa zumui zumui tsut! tsut! Ta cije baki tana faɗin

"Da zafi Habiby kuma ma WALLAhi ba komi a ciki don ALLAH ka bari har ruwan ya zo a hakan zafi kawai zan sha"

Yana ƙumshe dariyarshi ya cire nonon a bakin yaron ya karɓeshi ya ajiye sannan ya je ya rufo ƙofar ɗakin, ya dawo yana wata dariya ya yi durƙuso a gabanta ya sunkuya ya kai nonon a bakinshi ya fara tsotso cikin mugunta, ta fara tureshi amman hakan bai hanashi tsotse ɗaya tas ya saki ya kama ɗayan ba, sai da ya ɗauki lokaci yana zuƙo nonon sannan ya saki, Dije tana hawaye wahala ta ce

"Shi dai mutum ya kamata yasan ya fara girma, a gaban yaro ko kunya baka ji ba kake wannan halin?"

Yana dariya ya sake ɗauko yaron ya ajiye a gabanta ya saita bakinshi ya saka masa nonon, yaro ya ci gaba da tsotsa har da su sauke ajiyar zuciya, Dije ta bi shi da harara ta ce

"Yasin zaka janyo in horashi tunda akanshi ne ake yi man mugunta"

Yana dariya ya ce "wuta bal bal cin zalin yarona ko a bayana ne ku wa"

Ta murguɗa masa baki tana cije leɓe saboda zafin da take ji yana ratsata, haka yaron kam ya sha iya son ranshi sannan ya koma bacci, Safwan ya karɓeshi ya kwantar da shi ya zauna suna firarsu mai cike da nasu salon son, har sai da suka ji ana ƙwanƙwsa ƙofar ne ya buɗe ya fice su Surry suka shigo suna yi mata tsiya.

Ko da dare ya yi Safwan ya kawo masu kayansu Dukansu sunyi farin ciki ba kaɗan ba, musamman Dije da har sai da ta yi kukan daɗi saboda ganin himilin kaya kuma wai duk nata ita da yaronta, ba shiri ta rungumeshi tana kuka tana yi masa godiya.





Mai jego muma dai kam mun tayaki murna😊





Akafta🤪









D/AUTA Ce✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*ALHAMDULILLAH!!!!*



*Lamba 71*





Dije da yaronta suna samun kulawa sosai tamkar a gaban iyayenta ko ma fi, don ta ɓangaren cima mai daɗi bata da wani aiki sai na cin daɗi, saboda har rago biyu ya sa aka yanke aka soye mata wani bayan an sarrafa sauran kala kala aka tasata gaba ta yi ta kwasar gararta, kwana biyar da haifuwarta ne ƴan'uwanta suka diro Yola ƙatuwar Bus cike da mutane har da masu zuwa ganin ƙwam, don kuwa izuwa lokacin Dije ta yi wata daraja da ƙima a idanuwan yan garin nasu, saboda mutumci da Safwan ya siya mata a wurinsu ba tare da ma ta sani ba, wanda ya janyo har su kansu Inna da Baffah yanzu sun zamo wasu mutane masu daraja a cikin garin na su ta sanadin hakan.

Dije murna baki har kunne saboda jin daɗin ganin ƴan'uwanta da abokan arziki a cikin gidan aurenta, sai haba haba take yi da su cikin mutuntawa tare da girmama matsayinsu a wurinta, wuri na musamman aka keɓe masu ana ta basu kulawa ta ɓangaren abinci da abinsha sai sambarka suke ta yi da sa albarka, Dije kam farin cikin fal ranta bakinta ya ƙi rufuwa saboda ganin Abokanta na ƙurciya, waton Ladiyo Jummala da Lanti da Mune sai Hansai da ta zame mata tamkar ƴar uwa tuni, saboda auren Usmanu da ta ke yi sannan kuma ga shi tana kyautawawa Innarta shiyasa ta ke jinta ta daban a wurinta.

Mutanen garinsu Dije kam sai mamakin ganin yanda ta koma ƴargayu suke yi, don tuni ta sade da su ba zaka taɓa ganinta ka gano cewa wai tashin ƙauye ba ce, ta burgesu sosai musamman yanda ta ke nuna masu kulawa babu ƙyama bale nuna wariyar launin fata, ganin haka ne su Surayya da Zee da ita kanta Fiddon suke ta Nam nan da su su ma.

Tun ana gobe suna aka watsawa aka fara hidimar bikin don kuwa gidan cike yake fam da mutane ana ta hada hadar bikin, tsakanin soye soye da dafe dafe bayan wanda aka kai wani guri ayo ammsn duk da hakan mutane sai ɓarkowa suke yi.

Ranar suna maijego da yaronta da ya ci sunan Mahaifin Safwan ana kiranshi da Sayyid shi ma kanshi ya sha gayu bayan an ɓata lokaci wajen tofeshi da addu'o'in kariya daga sharrin mutum da na aljan, don farinshi yasa ko wa ya ganshi dole ne ma sai ya maganta, musamman yan ƙauyensu Dijen da suke ganinshi tamkar ba Dijen ce ta haifoshi ba, saboda ganin yanda yake tamkar ɗan indiyawa saboda kyau da fari.

Dije tare da su Surry da sauran mutane sai ɗaukar photuna ake yi cen na hango wata tawagar mutane ta doso Dijen ko da na duba da kyau na hango Shaharrun marubutan nan masu ji da kansu da amfani da lokacinsu wajen farantawa al'umma irinsu

Hannah Suhana (Hajiya Duduwa)da Billy s fari Ayusher Muhammad, tare da Ummi Garkuwa, Nimcyluv, Maizafafa, Oum Mumtaz, Ummu Najma, Salaha Muhammad, sai Mmn Musaddiq, Firdausi mrs shugaba, Ameera Adam, Mmn Shaheed, Mmn Maleek, Autar manya, tare da Ummu Ja'afar.

Ganin yanayin takunsu yasa ta gano su ɗin ba ƙananun mutane ne bay yasa ta sa aka tanadar masu wurin zama na musamman, sannan ta je rungume da Sayyid tana gaisawa da su ɗaya bayan ɗaya sannan kowacensu ta gabatar mata da kanta cikin raha da wayewar kai irinta Marubutan, sannan suka dinga ɗaukar photuna da ita tare da Baby, sai ga shi na hango ana rigimar karɓar Sayyid tsakanin ƙannena biyu Billy s fari da Hajiya Duduwa, ko wace ta na faɗin ita ce zata ɗauka sannan dai Ƙanwata Ummi Garkuwa ta raba gardamar wajen shiga tsakiyarsu ta riƙe yaron aka fara ɗaukar photuna.

Tana cikin marubutan ne Fiddo ta zo tana haki ta ce ta zo ga wasu gungun mata cen su zo suna nemanta, Surry ta ce ta je ita zata ji da su aiko ta saki jiki ta dinga lodo masu abinci da abinsha da maƙulashe ko wace ta ci ta sha sannan ta cika mas ledodinsu na kayan bikin kala kala.

Dije ta je ta sauyo wasu kayan cikin wani arnen tsadadden less wanda yaji shuwari stone ta ko'ina sai walwalniya suke yi, ta fito tana takun ƙamshi ta nufi inda ake nemanta, sai ko ga Maryam Omee ta yi saurin zuwa wurinta ta rungumeta tana faɗin

"Oyoyo Dijeta Barka da arziƙi"

Dije ta saki baki tana dariya tace "yawwa Barka dai Auntyna" duk da bata ganota ba amman ganin zallar ƙaunar da ta nuna mata yasa ta ji itama ta kwanta mata a rai, Omee ta waigo bayanta tana kallonsu Mmn irfaan da ke tsaye suna kallonsu ta ce "mun yo tattaki ne takanas daga group mabanbanta saboda kawai mu tayaki murnar zuwan wannan rana mai cike da farin ciki a garemu duka, saboda haka yanzu zan yi maki bayaninsu filla filla"

Ta nuna Mmn irfaan da ke tsaye tana wara idon ta ina zata hango Zee ta ce

"Wannan itace Mmn irfaan sai wannan Mmn ss, Ummu Afrah, Fati Ghana, Oum Suhail, Hauwa Zubair, Deejerlee, Mum Sayyid, Sa'ar Bukar, Faeexe, Najida Aliyu, Daughter Ummi Khatsina, Rufaida idris, Hamida Ƙaura, Jamila Haidara, Mmn Ra'ees, A'isha Yola, "
gano hakan yasanMmn Heedaya, Zainab Garba, Aunty Sady,Rahina, Glam By hajia sumy,Ummu Rauda, A'isha kishoor, Amrah barrister, Mmn Beaty, Mum of 3full H, Ummu Muhammad, Aisha S yamm, Subai'a Hussaini Gwandu, Hannatu Umar, Saratu Nakura, Zee MD, Hannatu Ahmed, Ummu deedat, Firdausi Muhammad sani, Rukynamango, A'isha Muhammad, azrarrfa8, Fatima sani mmn Masoyi, Princess N, Nakura, Ummin Sadiq, Ummi Sajida, Mmn meenat, mmn Yusuf, Hannatu Garba, mmn inty&Anwar, Shafaatu Aminu, Halima Gwani, Mmn Moh'd, Tamasu, mmn basma, mmn Hafsa, mrs Kamal, Aisha mada, Ummu Aisha, Ummu Haidar, Fatima Bello maimaita, mmn Abdu, Nasmie mafara, i lv u mum,Mummyn Nasrin, Jamila Isa, Aunty Islam,mmn Husnah,Mummyn annur, mmn shuraim, Ummul adnan,Amina Abdullahi.

Cikin sauke numfashin wahala Omee ta dafe goshi ta ce "wai ALLAH yasin muna da yawa in nace in ta zayyanosu zamu kwana anan bamu tantance ba,don haka don ALLAH ku yi haƙuri saura abun ne da yawa...."

Tana cikin maganar ne maganar ta tsaya saboda hango Asiya Umar A ya yarda, da tayi ta shigo gidan cikin gayunta tana wara idon ta ina zata hango idon sani, Omee ta washe baki tare ta dafe goshi ta ce

"Wayyo rimatyna ta ƙasaro"

Dije ta yi dariya ta ce dasu gaba ɗaya tana yi masu sannu da zuwa sannan ta jasu suka yi ciki inda ta yi masu masauki a ƙaton falon nata, Dukansu suka shishigo kowace tana samun wurin zama inda wasu ma har ƙasa suka zube abunsu saboda yawa su yasa falon yana so ya yi masu kaɗan.

Nan fa aka shiga yi masu tarba ta musamman, don su yawansu bai hana kowacensu ta yi ƙat ta yi hani'an ba saboda anyi komi a wadace.

Ana cikin cin abincin ne naga ɗiyar ɗakina Mmn irfaan da Daughter Rufaida da ƙanwata Asiya Umar sun haɗa kai suna ƙusƙus, sai ga shi naga suna ta zarmewa da ɗaya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment