Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ni kuma bazata taɓa jin daɗin zama da ni ba, sai ta bar gidan nan da ƙafafuwanta ba tare da ta shirya ba"

Dije ta yi saurin kwantawa saman kafaɗarshi cikin muryar kuka ta ce

"Ni dai ka yi haƙuri don ALLAH Malam saboda Hajiyarmu bazata taɓa cewa ka yi abunda bai dace ba kai ma ka sani?"

Safwan ya shafo kanta cikin tausayinta ya ce "wai waye malamin? Ni fa bana son wannan sunan na fara gajiya da shi, don bazan yarda ki mayar da ni tamkar wani tsoho ba, amman ki daina kukan nan bana sonshi"

Ya ƙare maganar tare da goge mata hawayen da ke ta kwaranya akan fuskarta, saboda zafin dawo da Zee ɗin da ya yi har cikin zuciyarta bata ji daɗin hakan ba, amman bata son ta nuna ne don kada aga rashin kyautawarta, amman ta ci alwashin duk ranar da ta dawo ita kuma a ranar zata bar gidan don bazata zauna ba ta kasheta a banza ba, Dijen ta ɗago fuskarta tare da saka hannu ta share hawayenta sannan ta ce

"Mu je mu ci abinci"

Ya bita da kallon mamaki ya ce " Ke kina jin yunwa ne?"

Ta ɗaga masa kai, ya ce "magana za ki yi" cikin siriryar murya ta ce "Eh" sannan ya miƙe suka fito ɗakin har zata cire hijabin da ke jikinta ya ce ta barshi fita za su yi, ta biyoshi a baya suka shiga Mota kai tsaye ya ja suka fice.

Basu zame ko'ina ba sai wata haɗɗaɗiyar Restaurant yasa aka yi mata odar abinci kala kala, Dije ta ƙi ci ta ce dole sai dai su ci tare, ba don ya so ba ta dinga ciyar da shi yana ci itama yana bata tana ci har suka yi ƙat! Sannan ya biya Bill suka nufi wata plazar suka sissiyo kayan tanɗe tanɗensu da maƙulashe sannan suka dawo gidan, duk da a ƙoshe su ke amman hakan bai hanasu sake cin gasashiyar kazar da suka siyo ba, tare da korawa da abun sanyaya maƙoshi, bayan sun kammale ne suka je suka yi wanka suka kwanta, duk da hannunshi da ke ciyo bai hanashi sakin jiki ya sake angwancewa da matarshi ba, saboda a yanda yake ji ko kaɗan ba zai iya haƙura da ita ba a wannan lokacin, haka suka raba dare suna farantawa juna har sai da ita kanta ta ji tausayinshi saboda yanda yake ta shan shagalinshi ba tare da ya yi duba da ciyon da ke hannunshi ba.

Ko da safiya ta waye Dukansu cikin farin ciki da ƙarin ƙaunar junansu suka ta shi, bayan sun yi break ma haka suka sake komawa cikin duniyar ma'auratan sannan dukansu bacci mai ƙarfi ya yi awon gaba da su.

Kiran wayar da ake ta yi masa wani bayan wani ne yasa ya yi saurin falkawa daga nannauyan baccin da ya ke yi, cikin yin wani uban tsaki tare da jin haushin da bai sakata a silent ba, ya miƙe ya ɗauko wayar ganin baƙin numbobi barkatai yasa ya yi saurin zaunawa, sai ga wani kiran ya sake shigowa da sauri ya ɗaga, sai ga wani ƙanen mahaifin Zee yana sanar da shi gasu cikin gidanshi sun zo suna son yin magana da shi.

Cikin jin haushi ya kalli Dijen da ke ta baccinta hankali kwance, ya yi wani murmushin jin daɗi saboda ni'imar da ya kwasa a jikinta, ya yi mata wani kiss a iska ya hura mata sannan ya miƙe ya je ya yi wanka ya saka doguwar jallabiya baƙa ya ja talkamanshi plat ya fice tare da janyo ƙafa a hankali don kar ta tashi.

Ganin baƙin motoci biyu tare da dattijan mutanen yasa ya shiga cikin natsuwarshi, ya isa wurinsu suka gaisa sannan ya yi masu jagora har sashenshi inda babban falon tarbar baƙinshi ya ke, bayan sun zazzauna ne aka sake gaisawa sannan suka sanar da shi sun zo akan su ji ba'asin abunda ke faruwa, don yanzu haka Mahaifin Zee yana kwance asibiti hawan jininshi ya ta shi, saboda abunda ya ji da kunnenshi da wanda ya saurara a gidan Tv..

Saboda ƙarin jawabin da su Ruma suka zo masu da shi na cewa Zee tana hannun ƴansanda, sannan da labaran da aka gabatar a gidan TV dangane da case ɗin masu ɗauke da rahotannin tabbatar da faruwar hakan daga bakin Safwan ɗin da kuma su Surayya da Ruma da sauran ƴan'uwanta duka da aka ɗauka, a daren jiya wanda kuma a ranar aka watsashi a gidan television, wanda ya watsu cikin mintuna ƙalilan tamkar tashin bom ta ko'ina labarin ake yi, sai dai ba'a nuna fuskokin kowa ba don Safwan ne da kanshi ya ce kada a bari fuskokinsu su bayyana saboda tsaro, amman duk da hakan labarin ba ƙaramin shiga zuciyar mutane ya yi ba, musamman wanda yasan ita Zee ɗin da su Safwan ɗin su ma, shiyasa mutane suke ta kiranshi don kawai su ji tabbaci wasu kuma don su jajanta masa.

Ba tare da jan wata doguwar magana ba Safwan ya bayyana masu abunda ya sani da wanda ya ji a bakin Surayya da kuma Ruma, sannan ya yi masu jagora har falonshi na ciki inda aka yi abun wanda har lokacin akwai warin fetur ɗin duk da ya bi iska sosai, cikin sanyin jiki suka dinga bashi haƙuri don sanin da suka yi tabbas Zee bata da gaskiya, sannan suka nemi alfarmar a basu Zee su koma da ita gida saboda Mahaifinta da ke unconscious, ya ce sai dai aje gun Hajiyarshi duk abunda ta ce shikenan, dole suka ɗuru mota suka nufi gidansu Hajiyarmu, bayan an gaisa ne suka fara bata haƙuri kan abunda ya faru sannan suka nemi alfarmar inda hali suna son a janye wannan case don ALLAH kada a bari ya je kotu, ganin girmansu yasa ta ce da su ba komi insha ALLAHu ba za'a je kotu ba indai har itace ta haifi Safwan, cike da jin daɗi suka baro gidan suka nufi Police station ɗin sai dai duk yanda suka so a basu belin Zee hakan bai samu ba, don shi kanshi Safwan ɗin sun nuna masa tunda aiki ya zo hannunsu ko ya janye su bazasu janye ba, don case ɗinta ba ƙaramin case bane bale har a yi gaggawar kasheshi cikin ƙanƙanin lokaci, dole suka haƙura suka koma ba tare da ko ganinta sun sami damar yi ba, don a zahirin gaskiya Zee tana cikin mawuyacin hali saboda yanzu haka tana Asibiti maƙale da oxcegyn saboda azabar da ta sha a hannu ƴansandan.

Tsawon sati biyu dangin Zee suna ta sintiri tsakanin Gombe da Yola akan su samu a kashe case ɗin, da ƙyar suka yi nasarar karɓota a hannunsu bayan uwayen miliyoyin kuɗin da suka narka saboda kawai a kashe case ɗin ba sai ya je kotu ba, don shi Safwan kallonsu kawai ya ke yi saboda shima kanshi da kalar na shi takun a ciki, don gurinshi na son ta gane kuskuren da ta aikata, don har lokacin bai cire takaicin dawo da itan da Hajiya Mama tasa aka yi ba, shiyasa ya nemi alfarmar Hajiyar akan a barta ta je gida har sai ya nemeta, haka ko aka yi sun karɓota aka kaita wurin Hajiyarmu ta bata haƙuri sannan ta baiwa Safwan da Dijen haƙuri suka kwasheta aka nufi Gombe da ita, inda ita kanta ta ji ina ma ace akwai wani garin da zata je ba cen Gomben ba, don tasan muddin ta je cen dole ne ta fuskanci ƙalubale ba kaɗan ba wajen ƴan'uwanta musamman masu goyon bayan Aminu.






To fa sai hkr Zee😊





Akafta🙌🏻







D/AUTA CE✍🏻

*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*



*Lamba 66*



Zee durƙushe ƙasa tana kukan fitar hankali gaban gadon da Mahaifinta yake kwance gorar ruwa saƙale a hannunshi, ya yi shiru yana sauraren sautin kukan nata, zuciyarshi cike fal da wata sabuwar damuwa don abunda ta aikata da saƙon da Safwan ya isar masa ba ƙaramin dukan zuciyarshi suka yi ba, duk da ko an sanar da shi cewa ya mayar da ita a matsayin matarshi, amman har wannan lokacin bai dawo cikin natsuwarshi ba, wata ƙanwar Mahaifinta ce mai suna Baabaah Asabe ta katsa mata wata uwar tsawa ta ce

"Zaki ta shi ki bar ɗakin nan ko sai kin iyar da kashe muna ɗan'uwa ne?"

Zee ta miƙe jikinta yana rawa dafe da bakinta tana toshe kukan da yake fitowa tana kallon Daddynta bata son fita, cikin wata sabuwar tsawar Baabah Asabe ta sake cewa

"Ki fita na ce ko sai na fiddaki da ƙarfi ne?"

Zee ta dinga ja da baya tana gunjin kuka za ta fice Daddyn ya ɗaga hannu ya yafitota alamun ta zo wurinshi, da sauri ta dawo jikin gadon ta tsaya tare da riƙe kan gadon tana toshe kukan da ke ta fitowa a bakinta ta ce

"Don Allah Daddy ka yafe mani nasan na yi kuskure ka yafe man......."

Ya riƙo hannunta hawaye suna zuba akan fuskarshi ya ce, "me yasa kika aikata abinda zai janyo muna surutu a bakin mutane?"

Zee ta riƙe hannunshi gam ta durƙushe ƙasa ta ce "plss Daddy ka yafe mani abun kunyar da na janyo maku don ALLAH"

Baabaah Asabe ta fisgota da ƙarfi ta fiddata ɗakin sai da ta yi nesa da ɗakin Daddyn sannan ta wurgar da ita cikin fushi ta ce

"Na ƙara ganinki a ɗakin nan sai na baki mamaki WALLAHI, abun kunya kuma da kike so ayi haƙuri kanshi ke me ya hana ki yi haƙurin a lokacin da kika ji ɓacin ran da ya janyo kika yi wannan rashin hankalin?, Yanzu in Banda ALLAH ya taƙaita wahala kinsan iya adadin rayuka nawa zaki saka cikin ƙunci?? Bayan waɗanda zaki yi sanadin barinsu duniya? Ko ko an faɗa maki cewa idan kin kashesu ke ƙyaleki za'a yi?, To buɗe kunnuwanki da kyau ki ji gidana zaki dawo da zama daga yau har zuwa lokacin da Mijin naki ya ga dama ya nemeki, tunda don kinga Yaya Mani ya sake maki da yawa ne shiyasa kike ganin dai dai kike da kowa, to har abada na gaba yana gaban kuma ba zai taɓa dawowa baya ba, don gashi cen yanzu kin baro mata gidan tana jin daɗinta da mijinta ke kuma ga ki nan kunci zai kasheki tare da Iyayenki, to Ni dai WALLAHI wannan karon bazan zuba mako ido kina yin abunda kika ga dama ba, dole ne a nuna maki cewa ƴa ce ke kuma haifarki aka yi akwai na gaba da ke har gobe"

Tana ƙare faɗar maganar ta koma ɗakin Daddyn inda ta taraddashi sai shar ƙwallah yake yi, da ban baki da lallami ta samu ta shawo kanshi da ƙyar ya yi shiru, cikin nadamar irin damar da ya baiwa Zee a farko yake ta baiwa yar uwarshi haƙuri akan abunda ya aika akan Aminu, don itama tana cikin mutanen da suka yi fushi da shi akan auren sai dai don ance hannunka baya ruɓewa ka yanke ka cire inji hausawa fa, don kam a wannan zamani da muke ciki sau nawa aka yanke hannun aka jefar? ALLAH dai yasa mu fi ƙarfin zuciyarmu.

Zee ta daɗe durƙushe anan tana kuka har sai da Ruma ta zo ta ɗagata suka shiga ciki, inda suka taradda mahaifiyarta itama sai kukan take cisga gwanin ban tausayi, saboda takaicin abinda Zee ta aikata wanda tuntuni take nusar da Daddynta akan sangarcin da ya yi mata don ko kaɗan baya so a kyareta bale a nuna mata laifin da ta aikata ta gyara, to ga irinta nan yanzu ta janyo masu abun gori wurin mutane, Zee ta je ta rungume Mahaifiyarta tana wani irin kuka mai cike da ban tausayi, Mahaifiyar ta tureta har sai da ta faɗi ƙasa, sannan ta miƙe tsaye tare da nunata da yatsa ta ce

"Babban kuskuren da zaki aikata shine ki sake zuwa kusa da ni, don haka ki je tunda kin isa da kanki ki aikata duk abunda kike so, duniya ce wanda bai zo ba ma jiranshi take yi, kuma ta ishi kowa riga da wando har da zanen ɗaurawa"

Tana ƙare faɗar haka ta shige ɗaki abunta har da su dantse ƙofa, Zee ta sake fashewa da wani sabon kuka Ruma ta dinga bata haƙuri, amman ina yanayin da take ciki yafi ƙarfin ban haƙurinta, dole ta zura mata ido tana kallo zuciyarta cike da jimamin abun a ranta, tare da godewa ALLAH akan ƙoƙarin da ta yi wajen hana Zee cika burinta akansu Safwan da abunda zai faru ALLAH kaɗai yasan iyakacinshi akan matsalar.

****

Dijen Baffah kam ita da Malaminta sai cin amarcinsu suke yi hankali kwance, don ma masu zuwa jaje suna takurasu amman duk da hakan bai hanasu baiwa juna kulawa ba, cikin ɗan lokacin daga shi har ita sun sauya saboda natsuwar da suke samu da junansu, don shi Safwan ko tuno Zee baya son yi a ranshi, saboda ya riga da ya shafe babinta a rayuwarshi duka kuma yasa a ranshi duk runtsi ba zai sake zaman aure da ita ba, igiyar auren ce dai ta yi ta sha zamanta lafiya ko ita don ba ya iya saɓa umurnin Hajiyarshi ne da tuni ya cikasa mata ukunta ta huta.

Safwan kwance a falon Dije yana mayar da reply ga masu yi masa jaje ne ta fito ɗakinta cikin sanɗa ta zo bayanshi ta tsaya, sannan ta yi saurin duƙowa saitin kunnenshi cikin ɗaga murya ta ce

"Habiby!!!!!!"

Ba shiri ya zabura tare da jefar da wayar cikin firgicin da ta sakashi, Dije ta dafe ciki tana ƙyalƙyala dariya tana nunashi da hannu, cikin dariyar shi ma ya miƙe da nufin kamota ganin haka yasa ta fara gudu tana dariya, shi ma ya biyota yana faɗin

"Babyluv ki tsaya tun baki janyowa kanki aiki ba"

Dije ta dinga gudu sunata zagayen falon har ya ci nasarar cafketa suka faɗa kan kujera tare suna mayar da numfashi, Dije tana kyalƙyala dariya tace

"Don Allah Malam ka yi haƙuri ba zan sake ba"

Safwan ya cusa kanshi cikin wuyanta yana shinshino ƙamshinta idonshi a rufe ya ce

"Tunda baki tausayin kanki ai nima bana gajiya"

Dije ta yi sauri zaro ido tare da marairece fuska ta riƙe kunnuwanta duka biyu ta ce

"Am sorry my luv"

Idonshi a lumshe ya fara yamutsata tana zillewa tare da bashi haƙuri amman duk da hakan bai hanashi yin abunda yake so ba, bayan ya kammala ne ya koma faɗin

"Ke kika janyoni don haka dole ne ki yi haƙuri da halin Mijinki, faɗa man me kike so in yu maki ni ma wanda zan faranta maki tukuicin farin cikin da kike sakani?"

Dije ta zumɓuro baki wa je ta ce

"Baffah'na nike son in je in gano kwanan nan sai mafalkinshi nike yi"

Safwan ya zaro ido waje ya ce "canza wani don bazan lamunci doguwar tafiya da ke ba a yanzu, don ban sani ba ko na yi ajiya a jikinki ki zo ki jaza man jinya ba"

Dije ta ɓata fuska tace

"To Ni dai shi kaɗai nike so tunda na riga da na zana jarabawata da sai in ce ita, sai kuma in zaka kaini in fara karatun nursing ɗin tun yanzu"

Ya miƙe ya nufi ɗakinshi yana faɗin "in dai karatu ne har sai kin ce kin gaji amman tafiyar da kike so ce nake tantama, amman idan na yi shawara zan sanar da ke abunda na yanke"

Dije ta yi saurin miƙewa ta biyoshi tana faɗin "Don Allah ka barni inje WALLAhi na yi kewarsu Inna raboda da cen tun lokacin da Hansai ta haifu fa"

Ya yi saurin juyowa ya ce "to ke ma idan kin haifun ai sai ki je ba wani abu bane ba"

Dije ta fara kumbura fuska tare da rufe ido ta ce ",to Ni ina na isa yin cikin ma?"

Ba shiri ya fashe da dariya tare da dawowa inda take tsaye ya rungumota yana kallonta ya ce

"Baki isa ba ko?"

Ta ɗaga masa kai tana rufe ido, ya sake yin wani murmushi ya ce "Ok tom ya yi mu je in aunaki in gani in har da gsk baki isan ba"

Dije ta zare jikinta ta ce "A kaini Asibiti dai likita ya aunoni ai shi zai gano ban isa ba"

Ya ƙara janyota jikinshi ya sakar mata wani kiss a wuya ta zabura tare da kai masa wata kalar harara, ya yi dariya sannan ya ɗago fuskarta ido cikin ido ya ce

"A ganinki akwai wani likitanki bayan Ni Malaminki? To buɗe kunnuwanki ki ji, kinga waɗannan abubuwan sun ƙara cikowa"

Ya ƙare maganar tare da damƙo dukiyar fulaninta ta yi saurin lumshe ido, ya bita da kallo cike zallar ƙaunarta da sha'awarta da kullum take ɗibarsa, ya sake matso hips ɗinta ya ce

"Shi ma wannan ya ƙara buɗewa alamu sun nuna ni ɗin ba ƙaramin jarumi bane, don haka daga yanzu ki ɗauki kanki dai dai da matsayin mace mai ciki, saboda haka ba inda zaki je amman in har su ɗin kike son gani zasu zo har gidan nan ki gansu insha ALLAHu"

Dije ta yi saurin buɗe idonta tare da yin wani tsalle ta maƙalƙaleshi cike da tsantsar farin ciki ta ce

"Wayyo Habibyna shiyasa nike bala'in sonka"

Baki sake ya ce

"To bi a hankali kafin ki sanar da ni irin bala'in sona da kike yi don bazan lamunci a yi man asara ba"

Dije ta rufe idonta tace

"Wai da gaske cikin ne da Ni?"

Yana dariya ya ce "idan kina tantama ki bani nan da sati biyu zaki gasgatani"

Ta yi saurin barin wurin ta shige ɗakinta tana dariya wai ita kunya, ya bita da kallon ƙauna sannan ya shafo kanshi ya shige nashi shima saboda magriba ta kawo jiki kuma yana so ya sami jam'in SALLAH a Masallacin da ke manne da gidanshi, wanda bai wuce sati ɗaya da buɗashi ana sallah a ciki ba.









Tsuntsayen soyayya ayi a hankali kar ƙone wajen cinta da zafinta😝








Akafta👩🏻‍🦯







D/AUTA Ce ✍🏻
*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*



*NA HADIZA D/AUTA*




*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*



*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*



*Lamba 67*


Zancen Safwan ya tabbata don kuwa sati biyu bai cika ba Dije ta fara laulayi mai ɗan karen zafi, don kuwa ruwa ma idan ta sha sai ta amayesu, ga shi a lokacin Safwan ya fara zirga zirgar neman aikinshi, inda aka yi dace aka nemeshi Abuja interview, shiyasa ya mayar da ita wurin Hajiya amman ko da yaushe suna maƙale a waya har ALLAH ya dawo da shi, sannan ya kwashi Matarshi suka koma gida yana ci gaba da renon abarshi, don kuwa duk abunda take so baya jin nauyin dattijuwar da ke taya Dijen aiki yake zagewa kitchen ya yi mata, ko ba daɗi ta cinye tana santi daga baya kuma ta amaye tass!, Haka suke abu ƙaɗan ya ce sai sun je Asibiti an dubata don baya son ta zauna cikin gida da wata matsala a tattare jikinta, shiyasa duk wani abu sai ya nemi sani tare da shawarwarin ƴan Asibitin, duk da wani zubin yana biyewa son zuciyarta ya yi mata duk abunda ta ke so saboda kawai ta yi farin ciki, don ba ƙaramin jin jiki take yi ba, cikin haka ne Safwan ya tura direba ba tare da ta sani ba ya ɗauko su Baffah da Inna da Hansai da Usmanu don Gambo ta ce ita ta yi tsufa ba zata iya yin wannan doguwar tafiyar ba, duk da har a ranta ta so ace ta je ta dubo jikallenta, amman yanayin jikinta na tsufa yau lafiya gobe ciyo yasa ta haƙura ba don tana so ba.

Dije cike da mamakin ganin gidan wasu ƴan'uwansu Safwan da su Surayya a kitchen sai hidimar dafe dafe da soye soye suke yi, in sun sauke wannan su ɗora wancen gida ya runtume sai zuba ƙamshin garar da ake ta haɗawa su Inna ake yi, duk abunda aka yi sai an kawo mata ace ta ɗanɗana ta ji in ya yi, cike da mamaki take tambayarshi wai halan wasu baƙi ne zai yi masu muhimmanci shiyasa ake ta wannan hadahadar?, Yana dariya ya ce

"Ke dai ki ci ki ƙoshi ki sha maganin amanki ki je ki yi wanka ki tsalo kwalliyarki cikin sababbin ɗinkunanki"

Cike da jin daɗi ta fara cin wani dambun nama tana ci tana kaɗa kai alamun ya yi daɗi sosai, hannunshi riƙe da plate ɗin tana ci yana yi mata dariya, bayan ta ci abunda zata iya ci ne ya bata magani ta sha sannan ya je ya taimaka mata ta yi wanka, wanda ko shi ɗin sai da suka ɓata lokaci sosai sunata wasarsu ta ma'aurata, tare suka yi wankan suka fito sannan suka shirya cikin taimakekeniyar juna, kafin ka ce me sai ga su dukansu sun fito shar! Abunsu kowane sai tashin ƙamshi yake yi, duk da ta yi rama amman hakan bai hana kwalliyar ta yi kyau ba, don kuwa fatarta ta washe sosai ta yi haske dai dai jikinta, haka ma ta ƙara yin kyau masha ALLAH dukiyar fulaninta sun ƙara cikowa sosai a ƙirjinta, waɗanda a kullum baya gajiya da lalacewa akansu yana santin yanda suke ta ƙara hawa tamkar an hura masu iska ga taushi tamkar balombalom, dole ba don ta so ba take sakin jiki ta barshi ya yi abunda yake so don duk da ciyon ta wannan ɓangaren baya ɗaga ƙafa, a cewarshi wai duk wani maganin da zata sha bai kai wannan tasiri a jikinta ba, da wayo da lallami yake samun abunnda yake ƙulafuci, don idan ma ta ce zata yi tirjiya ma ba haƙura zai yi ba shiyasa take ta danne zuciyarta tana faranta masa, amman ita sam bata son damuwa a wannan lokacin da zai barta na tsawon watanni da tafi sha'awar hakan fiye da yanda yake manne mata akan biyan buƙatarshi.

Bayan sun gama kimtsa komi da ko'ina ne Safwan ya kawo falo ya ce ta zauna ta jirashi minti biyar kacal zai je ya tarbo baƙinshi ya dawo, aikuwa cike da mamakin da son ganin waɗanni baƙi ne haka?, Ta zauna tare da su Surayya suna kallo a falo suna fira jefi jefi, don ko ita ya ja kunnenta sosai akan kada ta sanarwa da Dijen zuwansu Baffahn ya fi so ta gansu unexpected, ai kuwa suna nan suka ji saukar motoci, Surayya ta yi tsalle ta kalleta ta ce

"Yau fa manyan baƙi ne da mu a garin namu"

Dije ta yi wata dariya tare da cewa "ai kam ga shi na ga alama don ko mu mun sheda da waɗannan manyan baƙi"

Surayya ta nufi hanyar fitq falon da sauri tana murna duk da itama cikin ne a jikinta, Dije ta bi ta da kallo ta ce

"Aunty Surayya dai ba'a girma ba har yanzu, da cikinki kike wannan uban rawar jikin ki je ki janyo muna jidali muna zaman zamanmu"

Surayya ta ɗaga murya kafin ta ƙarasa ficewa ta ce "ai sawun Giwa ya take na raƙumi wannan abun murnar dole ne mu nuna farin cikinmu"

Dije haka kawai ta ji ta kasa ɗauke idonta a ƙofar da ake shigowa falon, saboda jinta da take yi cikin ɗokin ganin su wanene waɗannan baƙin, ai kuwa sai ga Surayya riƙe da Abba yaron Usmanu wanda aka yiwa Baffah takwara da shi, cike da mamaki ta zaro ido cen sai ga Hansai bayan Surry, a zabure ta miƙe Baki a sake zata yi magana kenan ta hango Inna a bayan Hansai, aiko ba shiri ta fasa wata uwar kuwwa ta nufosu aguje tana kururuwa sai ga Baffah ta hango da Usmanu tare da Habibynta, cike da tsantsar mamaki ta dinga rufe ido tana budewa tare da murzasu tana faɗin

"Wayyo ALLAHna shin mafalki nike yi ko gaske?"

Hansai ta riƙo hannunta cike da jin daɗin ganinta ta ce

"Ido buɗe ne mune muka kawo maku ziyara"

Dije ta ruƙunƙumeta tana murna ta saketa ta nufi Inna ta faɗa jikinta tana
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment