Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ne,Dan shi mutum ne wanda baison ciwo,tunda mahaifinsa alhj dikko yay ciwo agabn sa ya mutu saiya saka abun a ransa shisam baison yaga ana ciwo ko shikansa takamasa.

A hankli ya dau cup din kunun yay bimillah ya kurba yanata Jin surutan mahaifiyar sa dabaiya karewa sai hirar rufaida kawai take masa tana ta famar tsara kalar rayuwar da zata bata in ta dawo zama da ita..
Ayanzu haka burinta da zakuwarta baifi taji ance mata hadiza ta aikta abunda takeso din ba,inhar kuwa hadiza ta rabu da Auren bukar da ko itanan da zata iya bata tallafin kudi ta tada rayuwarta itama,,tace du du hadizar nawa take?ai ba Wani tsufa tayi ba,xaka samu dakadan ma ta girme jasmine in an bincika..Wani cak ta dauke hirar ganin ko kurba biyu masu kyau baiyi ba ya aje cup,ta juyo a tsime tana hararsa "waime haka zaidu?
Yace mama wallh banajin dadine
Tace A'a fito dai ka fadi gaskiya Jasmin ta fini iya abinci shisa Inna baka nawa kake cinshi kamar kana tauna kashi,baice mata uffan ba yay yar dariya,,abincin ya Kara jawowa gaban sa,yanata kallon abincin..
"kada kafarta ta ta shigayi ba kaga mahaukaciya tana tanata magana ba ai dole ne kayimin dariya,..cikin sa ne ya soma yin kugi Jin zafin kunun dayake ratsa hanjin sa,memakon ya rika Jin motsin acikin sa saiya somaji akansa kansan ya soma Wani irin juyawa yanajin jiri mai tsanani,can ya miqe a zumbur kamar an tsakure shi ya rike kansa cikin Wani yanayi hjy mama sanda ta razana itama ta mike,hankli tashe tace,"lpyarka kuwa zaidu?..yana kkrin daga hannun nasa kawai Taga xufa ya feffetso masa yuuu ata kansan kamar wanda aka watso masa ruwa.."Wani irin ihun ta fasa ta hau sauke salati tana kallon sa
abunda take ta suspecting aranta ya bayyana mata a filin,'..tace Wayyo Allah ni hasiya na shiga uku,bukar zai kashemin Dana..
Ta damkosa da uban karfi ta zaunar dashi"..jirani anan zaidu,karka yadda ka barnan maza jirani,bai ma gama tusa duwawunsa akan kujerar ba ta nufi kitchen da uban sauri jingina kansa yayi Dan baisan Meyake ji akansa ba alokacin,tsintar kansa kawai yayi yana fidda wasu ruwan hawaye ga kansa na masa Wani irin juyayi ga halin rudanin data tasomasa a bazata gaba daya sai yajishi a cikin rudani

A birkice Hjya mama ta isa kitchen din tana daga ruwan maganin ta tafashe da Wani matsancin kuka,cikin kukan dake fitowa harda sheshhka tace "Wato bukar saida yay kwanan buzu akan Dan uwansa zaidu ko?..Ashe bukar zai iya hallaka ni nima tunda ya iya yin Hakan akan Dan uwansa....

Toh bari zaidu yasha ya warke Duk Inda bukar yake a duniyan nan sainaje na same shi nima ya kashe ni...

Cikin wannan rudaddiyar yanayin ya shigo ta same ya sheik a gurfane a kasa yanata kakarin amai,da uban sauri ta fado gabansa tana dafa kafadun sa..tana cewa
Sannu zaidu yanzu zaka warke insha Allah,ni Nan da kake Gani nafi karfin bukar, wallhy karyan malanta yakeyi waye ubansa inba tsohon matsafi ba?
Yo ko ubansan ne ya taso bai isa ya kashe min kaiba.
Bukar bai isa yaymin asrar ranka ba zaidu..bai isa ba.

A sama sama yaa sheik yakejinta Dan bakaramin wahala yakesha da ciwon kansan Nan ba,a rikice ta dago fuskar sa ya durkusa gabanta yana fuskantar ta Babu jira ta bude kwanan shan ta soma kamfatar ruwan tana watsa masa tun daga tsakar kansa har fuskr sa..

Babu abunda yake saukewa sai Ajiyan zuciya,sanda ta jikashi tsaf sannan ta Kai masa ruwan har bakinsa cikin muryan tashin hankli da rikici tace "zaidu budemin bakin ka...yana kokrin kau da Kai ta daka masa tsawa a birkice tace wallhy Sai in faffala maka Mari anan zaidu, kasan dai ba tsoronka nakeji ba ko?,Wani Kukan ta Kuma fashewa dashi"..banda iskanci anmaidani bagidajiya an raina ilimi na,inba Reni ba
Inhaifeka aciki na sann kace zan baka abunda zai cutar da Kai?dakai da bukar din ma Duk halinku daya baku mutunta maganata,...zaidu ka bude bakinka ka amshe maganin Nan...kariya ne zai kareka daga sharrin bukar...ko sai ya kashe ka? Wayyyo Allah na shigga uku wayyo ni hasiya zaidu zaimin asarar haihuwa,Ihu kawai take,yaa sheik ya rasa abunda yake masa dadi baima San sanda ya dau maganan ya shanye Dukka ba,"..Wani cak ta tsayar da ihun ta tayo kansa tanai masa sannu kamar ba ita tagama masife shi ba..yana gyara zaman sa aksa ta yayumo kofin kunun tazo da shi gabansa
Gaba daya ta rikita shi saida ya shanye,
Tsaban ta rikita shi baima San Meyake ji ajikinsa da xuciyarsa ba kawai ya kwanta akan cushion ya lumshe Idanun sa yanata surutan datakeyi...
Wanda shi Sam ba so yakeyi ba,baison wannan dabiar nata na zargin mutum musamman inbataji ba batagani ba..

A lokacin ita kuwa Inda za'a bata qur'ani dafawa zatayi tace bukar ne yake taba mata da...

Har sanda jikin san ya lafa yay sauki sannan ta dena bambami,jinshi kawai take tana kwabarta akan ta dena irin haka,ta dena zargin yayan sa da wann sigar,yana cewa yasan yaa bukar bazai taba masa Wani abu mummuna kamar wannan ba, bama jinshi take ba banda takaici da jimamin baqar zuciya irinta bukar Babu abunda takeyi,to lallai ya zame mata tilas ta Kare danta zaidu,Dan tagaji da Jin wa'azukan sa da nasihohi sa masu kashe jiki,aranta tace ita ba Shashasha bace da har zata zuba ido wa katon jahili yana tsafe tsafen sa akansu har aje amata asarar da..

Yaa sheik ya gama mata nasiharsa tsaf Amma bata fasa kulla abunda ke zcyrta ba,Shiru dai ta masa Jin ya Nace da cewa baison ta kawo maganan zargin yaa bukar akan wannan abun kwata kwata ma ya hanata tunkarar sa dashi,yace mata inma gaskiya ne saidai ta Kara tunxirashi yay musu wanda yafi Hakan,yace kawai ta kyale shi..sunfi awa biyu ahaka har bacci mai Nauyi ya safce shi ta dade tana zaune a kusa dashi tanata kallon sa harsai da baccin nasa yayi nisa sosai

Tare da sauke Ajiyan xuciya ta miqe tsaye a gurguje ta haura sama ta dauko jakarta,ta sauko yauko jiran driver batayi ba ta rinka lallabawa har bakin titi ta tare abun hawa ba'a sauketa akoina ba sai gidan Wani boyayyen mutum daga cikin dangin mahaifinta wanda ya mutu tun shekarar da zaman Auren ta da mahaifin yaa malam ya kare..
Shima babban Malami ne wanda yasan addini bana wasa ba saidai shi a bilma ya zauna tare da kanurai yakan bada magani sosai Dan bazara taba mantawa shiya rinka kareta daga sharrin sihirin mijinta mahaifin yaa malam

Tunda ya rasu yayan sa suka dawo birni,dake a yanzu sune sukayi gadon abun sosai,gaba dayansu sun shahara sunyi suna sosai wajen bada maganin sihiri aljanu,jifa,karya kala kalan manakisa na aljanu Babu wanda basu iyaba..
Kawai dai wasu mutanen Sukanji tsoron zuwa wajensu sabida tsoron aljanun dake yawan mu'amala dasu,Duk dama tasan tun tale tale zuriar gidansu basa sihiri ko aikin bokanci..

HjyTana shiga gidan ta fashe ma yaran da kuka dakema sun manyanta sosai kuma suna sonta
Tace musu danta bukar ya haukace yana neman ya hallaka ta,kawai kuka takeyi tasan inbayi Hakan ba Hala sumadin hakuri kawai zasu bata suce tayi tawakkali,ita Sam bazata iya ba,so take ayi ma ahalinta
Katangar karfe da muguwar xuciyar irinta bukar,
musamman ma akan xaidu wanda ta bukaci ayi ma zaidun ta saukar qur'ani atayata da addoi da sadaqa..

Kudi mai uban yawa ta bude jakarta ta dire agaban su tace insun Kare zata Karo wasu,ita dai kawai atayata kare zuraiarta daga sharrin danta yaa malam..

Babu kalar nasihar da basuyi mata akan karta tsame yaa malam a adduar ba,kuka take ta tuma tace sammm Babu ruwanta dashi,ma duniya ta Mikasa sabida yaje ya ga Duk abunda take guje masa wanda shekara da shekaru tasan ta iya baqin kkrinta wajen jawoshi Amma yanzu jii take kokadan bazata iya ba...
Gudun kar zaidu ya farka yaga bata Nan yasa tayi maza ta sallamesu ta koma gida,samu kuwa tayi yanakan baccin sa,a sadade ta shiga ciki sannan ta dawo ta hau tattara wajen ta kimtsa tsaf ,daya daga cikin hayakin da aka bata ta zuba maza maza a kaskon wuta ta kawo Dede setin kujeran dayake kwancen ta ajiye masa shi yana hawa kanshi yana shaqa...


Haka ya rinka mafarkai Wai ana binsa da wuka za'a kashe Sa,acikin mafarkin ya rinka Kare kansa da adua ya shafi almost 2hrs yana baccin,sai can around 9:30am na safiya ya farka yanamai Jin kansa wasai,da guzarin sa wanda tamkar bashi bane dazu dayake Jin tsananin kasala da azaban ciwon kai..
Tashi yayi ya zauna Jin ko ina shiru ya saka Kai ya fice a falon ya nufi sashen sa,bai wata wata ba ya fada wanka
,fitowar sa keda wuya ya tarda tarin miss call of cause na can abuja yafi na ko Ina yawa,sai na imad guda daya,sauran Duk daga wajen aikinsa ne a gurjuge ya shirya kansa tsaf
Cikin wata dakakkiyar shadda dark blue colour ita bamai gare bace Dan haka asalin shape din jikinsa mai dauke hankli da nuna jarumtarsa a fili wanda tuni ta fallasa kanta wajen kara masa kyau da kima ta fito rass..

Cikin gaggawa ya koma sashen hjy mama ya same ta xaune agaban tv da waya akunnenta tana magana da hjy jasmine, Jin motsin sa yasa tayi saurin tura kullin magungunan data karbo yanzun Dan batama son ya San dasu,hayaki ne wanda za arika sakawa a sashen sa na can,wanda zaina kareshi daga sharrin Duk Wata muguwar halita musamman ma aljanu da mayu,sauran Kuma na yaransane,jira ma take inta fita ta aika sauran ma hadiza tsoronta Kar bukar wata rana ya kashe su..
Katse wayar tayi sanda sukayi sallama dashi Dan yace mata yana sauri Amma yau bazai dade ba zai dawo duba da Ita kadaice agidan sai yar aikin da aka barta dashi maman Abdul,datake Dan debe mata kewa,yana ficewa ta cigaba da shimfida ma hjy jasmine dokoki altho bata sanar da Ita komi ba,kawai dai umarni tabata akan tana da bukatar a tsare mata yayan ta da jikokinta daga sharrin mutum da aljanu...Kuma ta gargade ta da kyau akam maza ta gaya ma keeyan ya
nemeta awaya dake tasan shidin ya iya karatun qur'ani bana wasa ba,Dan shine yafiye yin saukar qur'ani agidan dama...but dake basu cika zama a Nigerian ba yasa abun baiyi Wani qarfi sosai ba..

Bayan sun gama discussing akan haka suka bingire da hirar dawowar imad,tanata bawa hjy jasmine dariya sabida kowa yasan yadda take da imad tamkar sa'oin juna komi saiyace ita,ita kuwa bata gajiya dashi ayi fada a shirya,kin dawowar sa Nigerian yasa tayi fushi tace bazata kara masa magana ba,Amma ayanzu Hakan ji take Inda zata so abuja da da mararin son ganinsa azuciyarta zata iso..

Sun dade suna hira Inda hjya jasmine ta zayyana mata dukkan abunda yake afkuwa a bangaren su hjy goggo a sabon gidansun...

Ajiyan xuciya hjy mama ta rinka saukewa Jin Wai harsuna shirya shagalin bikin murnan dawor su abujan,Duk sun gauraya da yara anata kashe kudade ana siye siyen banza da wofi,ga Aina'u ga kanwarta zarah data tsani yanayin rayuwarsu, ita sam ba irin rayuwar datake so ma yayan zaidu bakenan,son ranta ace su shikar kamilallun yarane maso son kiyaye addini kamar mahaifinsu..
Amma Sam Wai bazakaga sun nitsu Suna abu kamar na masu hankli ba sai in mufrad yana Nan ko mahaifinsu yana saka musu Ido?
Aranta tace toh lallai zata dau kyakkwan mataki Dan jiya taga illar zuba Ido kabar yara Suna tabewa awajen wanda baisan darajansu ba,sosai taga illar yin sanya a wajen hadixa.

Har suka kammala wayar bata dena mita ba,Wani haushin su hjy adadan take ta ji aranta tace"...Gaba daya sunzo sun dasa ma yayan zaidu kwadayin duniya,Suna cusa musu ra'ayin da bazai ficce su ba..
Da haushin haka aranta ta karace zamanta,sai can da ta idar da sallan azahar sannan ta Dan kwanta rama bashin baccin da ake binta wanda tun jiya batayishi ba...





*™✓SHADE OF RUFAIDAH*


_BY_
_SURAYYAHMS_


_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_


BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.


Part1:chapter 26


7:am
Anguwar gangare

Tun bayan ficewar umma hadiza agidan yakumbo take fama da jikin rufaidah wanda Tunda ta farka laulayi kawai takeyi da kyar ma ta Sami tayi sallah tadan kwanta bacci mai Nauyi ya Kara daukarta,Banda juye juye da wangale wangalen cinyoyinta Babu abunda takeyi,har Yau kasarta be dena mata tsami da zugi ba,saidai ata ciki ciki kawai takejin radadin abun, dan Koda taje tsarki ta leka kasarta bata ga komiba sai dan kumburin da wajen yayi,daga Nan bada wani dadewa ba yakumbo ta Sabi mayafin ta itama ta fice ta nufi kasuwa yin musu dan siyayya,dubu sha biyar din da hadizan ta bata ta rabashi gida biyu mai yawan ta boyeshi a gindin setin samiran ta kwalli daya dake tsakar dakin wanda tadanyi jere dashi akas,Wajen masu saida abincin gwari ta nufa direct tadan tarkato musu abunda baza'a rasa ba,yar shinkafar su wanda baifi kwano hudu ba,wake,surfaffen garin masara,da flour,dake ma tanada garin gero da tarkacen sauran ragowar hatsi data samo wajen kale a gida,sai Yan sabulun wanka da wanki da sleepas da Kuma brushi ta hada mata harda man shafawa wanda tasan dai dole Rufaida ta bukace wayannan..

Bayan ta kammala da Nan ta biya har lambun gangare Inda akecema Gidan arha,anan shima ta sissintsinta musu kayan miya da sauran tarkacen su Maggi da manja harda dan kifi da Dan abun sha'awa Abunka da Abincin marar lpya..

Niki Niki ta shigo gidan hannunta dauke da kayan abinci tana tafiya dakyar sabida Nauyi da gajiyar jikin tsufa a kofar daki ta ajesu tayi sallama tare da leka cikin dakin tana mai kallon saman gado,sauke ajiyan xuciya tayi ganin Rufaida Takoma bacci still sai juye juye take da alaman bakin dadin baccin takeyi ba
Kusan minti biyar yakumbo tana tsaye daga wajen cikin rasa ta yadda zata soma tunkarar lamarin rufaida Dan gaba daya yanayin jikin rufaidar na kashe mata jiki..

Abunka da believe irin na tsofaffi already ta riga ta gama sawa aranta cewa Rufaida ta riga ta san da namiji by now,ita Sam bata wani gamsu da labrin cewa attempt bane kawai jinsu takeyi aranta tace Wani irin abu kenan namiji zaiyi da jikin rufaida ace haryanzu bata dena dingisawa ba?yarinyar da akace tayi kusan sati a Asibiti?Ance mata wai shigar karfine toh tayaya kenan rufaida zata kufce batare da ta rasa budurcinta ba?,,ita tun jiya da hadiza ta gaya mata abunda ya afku take saka Idonta sosai akan yanayin tafiyar rufaidar tana Kuma lura da Duk Wani motsawarta Wanda har ayanzu bata gamsu da cewa rufaida ta dawo cikin hayyacinta bama bare ajega samun sauki, Kuma tabbas bata cire tsammanin cewa ba a bawa kasarta da jikinta kulawar daya dace ba,yo meye ma asibiti suka iya?ita dama can bata yarda da maganin asibiti ba tafi gane na gida na zallan itatuwa,yo bakaken fatan ma da suka bijire ma na Allah ai yanzu dawowa sukeyi a Hujajan, inaga Kuma ance turawa dama can sume sukasani banda neman kudi da Suna bare har ace sunyi ma rifaida magani?mita kawai take yi aranta Dan Aganinta ko dingishin da Rufaida takeyi aynzu ya isa ya gamsar da kowa yasan cewa bataji ruwan zafin jinya ba.

Bisaga wannan tunanin data dingayi a xuciyarta ta juya ta shiga debar kayan abincin tana kaisu cikin dakin,sanda ta shiryasu tsaf sannan ta taho a gjiye ta zauna bakin gadon kusa daf da rufaida,kallo tabita dashi sannan ta shafa goshin ta daya jike da zufa jin yadda ko inanta ya dau dumi da alaman zafin zazzabin dake jikin tane yake neman tsanantawa,.

Minti biyu bata kara xaune awajen ba rufaida ta soma bude gajiyayyun idanunta data kullesu gam gam suke mata Wani irin Nauyi da duhu kanta na mata Wani irin Azaban ciwo..

Wani malalaciyar ajiyan xuciya ne ya kufce mata ayayin da taja numfashi me qarfi cikin yanayin da bazata iya banbancewa ba, a hankli ta shiga furta Allah acikin zuciyarta tana kokrin samar wakanta nitsuwa
Batayi aune ba taji an dan tallafo kafadun ta,yakumbo tagani tana ta Kallon ta duk tausayinta ya cike kwayar idanunta na tsufa kallo daya zaka mata kasan ta damu sosai,a nutse rufaidar ta maida mata kallo itama, Jin jiri na shirin debarta yasa ta sulale a kasale ta jingina da jikin yakumbo tare da kankameta tana sauke wasu gajiyayyun numfashi dake saukowa daga can kasar xuciyarta a hankli,sun dade a haka batare dasun cewa juna uffan ba harsaida rufaida taji kamar ta Dan samu nitsuwa,idanunta da sukayi Lui sukayi sanyi ta shiga warasu kadan a hankli ta kamo hannu yakumbo ta hada da nata ta rike, cikin sanyin yanayi ta shiga karema lungu da sako na dakin kallo wanda ya zamto mata tamkar mafarki kasancewarta a raye Kuma a Nan kusa da wanda zata taimaketa sabanin kwana biyuncan daya wuce datake kallon mutuwa da azaba agaban ta karara.


Dan kadan ta motsa jikinta ta Kara lafewa ajikin yakumbo tare da sakar mata jiki tana dada narkewa ajikintan,kanta
yakumbo ta shafo kadan tace rufaida "ya jikin?..Adan takaice ta dago ta kalleta,kallo daya ta mata,sann ta sauke kanta can kasa cikin yar siriyar muryanta dabai Wani fitowa da kyau tace da sauki yakumbo,shiru ne yabiyo baya,can tace yakumbo umma na fa?..karde ..sai Kuma maganan ya dauke mata difff..
Wani Shiru tayi jin yadda maganan ya tokare mata makwaro..."yakumbo dake lura sosai da yanayinta tace 'rufaida ki kwantar da hanklinki,hadiza ta riga ta koma dakin mijinta Amma tace zatayi mana aika daga Nan ma zamuji inkomai ya daidaita ko?"..silent hawayen daya riga ya sauko mata ta shiga sharewa tace Toh Allah yasa haka
"..Allah yasa baba ya yafe,ni bana son umma takasance cikin fargaba saboda ni,..
yakumbo dake Dan shafo gadon bayanta tace Ameen rufaida karki damu karki Saka komi aranki, insha Allah Babu abunda zai same hadixa".Dan shiru tayi snn taja Wani karamin Ajiyan xuciyar tace fitsari nake ji yakumbo kitemaka min inje inyi,tana gama Furta Hakan sai ta kuma sauke hawaye,Nan yakumbo ta dago tana kallon fuskarta canta tallabo habarta tana mai karewa rudaddiyar yanayinta kallo,cike da yanayin lallashi da saukar da murya tace Rufaida ta,ki fadamin gaskiyar yadda kikeji ajikin ki Karki boyemin komi kinji?yaji miki ciwo sosai ko?Da uban sauri rufaida ta sauke kwayar idanun ta kasa tayi shiru,ayayin da kwakwalta ya riga ya fassara mata manufar tambyar da yakumbo tayi, kusan minti biyu ta dauka ahaka bata iya dagowa ba Jin wani uban nauyin furta Wani kalma game da hakan daya gama baibayeta yana cusa mata fargaba
...batare da ta kalleta ba can tace "ummm Anta min jinya a Asibiti fa ykmbo,kawai dai bana jin dadin jikina nane,sai inrika Jin kafana yana min tsamitsami,musamman ma innai fitsari Duk sai inji zafi zafi inajin Wani zugi kamar na kaikayi..

Yakmbo dake kan kallon sunkyayyen Kantan tace "yo a'ina ma Bature yasan yadda ake kulawa da mace dama?kawai sun barki babu isashen jinya,har Wani ciwon ma yaje ya Kara makale miki a gindin mara..tana kaiwa nan Taja numfashi sama cike da saka wasu abubuwa dayawa aranta wanda bata furtasu a fili can tace..nide yanzu ki Dan miqe Muje bayan gida in Gani,tun kafun rufaida ta motsa ta amsa harta dafo kafadunta yanayin lallabi da lallashi tace,insha Allah zaki warke tass rifaida, kibani Nan da kwana biyu zakiga har Kin ware kina takawa akan kafafunki,shiru rufaida tayi batace mata uffan ba ta sunkuyar da kanta Nan yakumbo ta miqe tsaye tabi ta gyara mata kwanciyar ta fice..
Wani bin kofar da Ido tayi A hankli ta sulale ta Jinginar da kanta akan matashin Kan sannan ta lumshe idanunta tsammm can sai kuma ta bude idon firgit Jin muryan yakmbo daga ta bakin kofar tana mata magana
"..tace rifaida kidan jirani kadan bari na zaga Nan baya na dawo,..Ina xuwa..gyada kai tayi tace toh sannan ykumbo ta fice a Gidan cikin sauri ta fantsama jeji..Kara Lumshe idanuntan tayi tayi lamo tana sauke Ajiyan xuciya tuni hotunan Duk Abunda suka afku da Ita ya shiga dawo mata cikin idanun ta,ahnkli ta rinka Jin wanni irin bakon yanayin da bata San dashi ba yana shigarta yana raunana mata xuciya da gangan jiki.


Gaba daya takanji duniyar yyi mata fadi da zafi,Babu Wani takamammen kwanciyar hankli ko Wani digon walwala a zuciyarta da kwakwaltan da already a cike yake da tunani kala kala har bata San Inda zata ajiye xuciyartan taji Dan dama dama ba..

Tunanin yadda zata soma tattara pieces din rayuwarta ta dawo cikin hayyacin ta shiyafi damunta wanda aynzu shi yafi rike mata kwkwalwa da zuciya har aranta take Jin kamar bazata iya sakashi a ranta nan kusa ba..

Tasan nata rayuwar ya riga ya Kare, kimtsatsen rayuwarta data Dorawa kyakkwan buri ya riga yayi Gamo da Wani mummunan tabon da bazai taba gogewa ba,dafe kirjinta tayi zuciyanta na mata Nauyi matuqa,sam Sam bata yarda da cewa zata iya sake leqawa waje bama bare ajega ta soma tunanin leading normal life Irina kowa..

Aranta tariga tasan cewa Komin boye wannan abun da zatayi aranta to tabbas wata rana saiya fito fili,inaga mutane sunji cewa ta kashe mijinta taci naman Mutum?
Wasu maqudan hawayen da suka makale mata ta shiga saukewa Suna saukowa bisa kuncinta da uban yawa kamar an kunna ruwan tamfo,kuka mai sanyi ne ya kufce mata wanda yake saukowa da ciwo bisa makoronta tana fetsar da Wani irin yankakken numfashi mai tafe da wahallen turirin damuwa da kinci,ko Yaya zata tunkare rayuwarta na Nan gaba da wannan muguwar qaddarar nata oho?Ita kanta tasan Gina Wani rayuwar ba abu mai sauki bane musamman ma in xancen abunda ya afku da ita yashiga kunnen magulmatan mutane,"..hawaye ta rinka saukewa wnda Babu adadin su tanajan sheshekar kukanta mai saka tausayi, acikin brain dinta kokri take taga ta daure din,she is alwys trying to put her thoughts behind Amma Ina sai taga kamar bazata taba mancewa ba,she has being trying so hard tun acan Vegas a Asibiti take kkrin dannewa Dan harga Allah bata son tana tuna komi,Sam Sam take son tayi nesa da tuno baqar azaban da ukubar data fuskanta abaya wanda yake azaban tsorota yake rikitata yake bala'in cusa ma xuciyanta da kwakwanta da ruhinta tsananin damuwa.

Around 8am saiga yakumbo ta dawo hannun ta dauke da tarkacen itatuwa da saiwowi Suma a kofar kitchen din ta jibge su,batayi wata wata ba ta shiga kitchen din tadan shashare ta hau hura huta a murhu,dake ma itacen Kara ne bai Wani bata wahala na ya tashi,ruwan kunu ta soma dorawa yanayi tana gefe tana daka kimba da kanufari da masoro,ruwan na tafasa ta Debi kadan ta jikasu sauran ta dama garin geron ta yayi kyau shi baiyi ruwa ba shibaiyi sololo ba Daga nan Cikin Dakin ta nufa dashi ta ajiye agaban rufaidar tana mai umarta ta data miqe ta sha,da kyar Rufaida ta miqe ta zauna qamshin kunun daya Gama bule wajen shi yabata karfin gwiwar Jin kamar zata iya sha,dayawa yakumbo ta zuba a cup ta Mika mata tace mata ta Daure tasha daga Nan bata fice a Dakin ba har sanda taga hakan ya faru,sanda taga kaiwarta baki na uku snn ta fice ta koma kitchen abunta,itama Dan sauran kunun daya rage ta shanye tass sannan ta Kara hada wuta da manyan itatuwar dayake Wajen tuni wutar ya hau ci babban tukunyar ta doraye ta Dora sannan ta cikashi da ruwa mai tsafta..bayan ta Gama hakan taja saiwowin data kawo ta shiga tsince su kowanne da irin mahadin shi ta shiga waresu.

Zama tayi agabann murhun ta rafka uban tagumi Jin Rufaida bata motsa ta ciki ba,hakan yasa ta jefa kanta cikin tunanin umma hadiza,aranta tace "ko Yaya ma take ciki oho?..tagumi tayi cikin yanayin dake Saurin fallasa damuwa taja Wani qarfaffan numfashi,Kan ta Kara nitsawa cikin tunanin can daga cikin daki ta soma jin motsi alaman kakarin amai miqewa tsaye tayi cikin sauri ta nufi dakin, tun kan ta isa baqin kofar saiga rufaida ta wawuso a guje bata zube a koina ba sai a tsakar Gidan rike da cikinta dake Wani irin juyawa,Wani irin zazzafar amai ta shiga fitarwa daga bakinta wanda tamkar hanjin cikinta ne suke shirin yoyewa ta bakintan suyo waje,
Ta Dade tana aman harsanda ya zamto yawun bakinta kawai ake Gani,cikin sauri yakumbo ta kawo ruwan sanyi ta hau wanke mata fuska sauran ta bata tana tayata kurkure bakinta
,wani gagarumin nishi takeja a

Please Login or Register in order to submit comment