Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fahjr harta kammala ta fito da zimman tare shi awajen motsa jiki,cikin shirinta tsaf ta fito cikin wata arniyar sport wear white colour ta kamfanin puma Wanda ta kwama ajikinta shima bata kyalesa hakanan ba sanda ta feffetsa masa turaren sihiri, rigar sanyinsa irin mai hular Nan ne Dan haka bata daura Wani Abu akanta ba ta tufke attachment din ta kamasu sama da ribbon, saidan wandon ta wanda yadan kama dirin jikinta ya mata cas cas ta saka white and black canvas booth ma kafafunta Wanda ya mata masiffar kyau,wani balain son kalar datasa din takeyi har cikin zuciyarta dan komi datakeyi saboda imad takeyinsa by now Babu abunda bata sani akan yanayin rayuwarsa ba,his favorite colours his fav food Duk Wani abunda yake so da abunda baiya so hatta abubuwan da yakeyi da Inda yake zuwa tsaf sanda tanemi masaniya akansu

As part of her plan na samun shakuwa dashi yasa yau din dole ta yi sammakon fitowa wajen motsa jiki ta sameshi dantasan motsa jikin kusan al'adansa ne,saidai Duk da haka harta fito waje bata dena Jin fargaba ba sakamakon yadda Wani bangaren zuciyarta nata yake zargin cin karo da mufrad awajen saidai da abun mamaki yau bata gansan ba..

Da yar karamar sallama ta shigo ganinsa zaune akan waist mill machine kanshi akasa daga Ganin irin zamn dayayi kasan hanklinsa ya riga yayi nisa ta Wani wajen Dan harta karaso daf dashi bai wani lura da sautin takunta ba,tsayuwa tayi na kusan mintina uku tana famar aikain kallon sa,as expected kayanjikinshin all white ne Babu surkin Wani kala ajiki wanda hakan ya balain Kara mai kyau da gwajiini a cikin idanunta tanajin Wani irin sonshi da shaawarsa na mamayarta har cikin kokon zuciyarta da ruhin ta,dafa kafadunsa dayaji anyi ya sashi katse tunaninsa ya juyo suka hade ido da Zarah wacce already ta tarbe sa da wasu irin sihirtattatun Murmushi mai kumshe da tarin manufofi,turaren jikinta Dana shi ya gamutsu ya sauya ma yanayinta nitsuwa mai rikitar da gangan jiki murya mai sanyi da taushi ta kakalo ganin yadda ya kafe kwayar Idonta da kallon da shikansa Bai San yanayi ba, tana murmushin tace mai hi?..ba yabo babu fallasa ya Kau da idonsan yace mrn batare daya motsa ba koya nuna rudewarsa a fili ba sabida shi mutum ne mai sanyin nitsuwa da kamun Kai...

Harta zauna gefe da shi bai kara kallon ta ba Nan da nan ta shiga drawing conversation tanayi tana jan aji cikin nuna masa ita sam batayi tsammanin ganinsa anan bama.

She was just acting normal tana Kuma balain watching salon kalaman ta Inda tasan dai bazai taba cewa bibiyarshi takeyi ba
A hankli harta soma drwing attention dinsa kanta da irin hirar game din da ta dinga yimasa while shikam Bai fiye son tankawa ba all his tot nd worries naga kan tunanin datazo ta samesa yanayi na rufaida.

"He dream about her yestade,daya farka saiyaji hanklin sa ya bala'in tashi aransa yanajin mugun sha'awar ganinta da sanin halin datake ciki.
He just can't get over the girl,Duk halin da ake ciki yana makale da Ita azuciyarsa,shiyasa Duk gargadin da yaa sheik ya masa akan ya mance da ita aransa sai yanajin kamar bazai taba iya ba,bayajin samun nitsuwa a zuciyarsa daga ya kwanta shikadai rufaida ce zata shiga fadowa aransa da zuciyarsa saiya rinka Jin kamar baida Wani babban burin daya wuce sanin halin datake ciki ayanzu.

Har Zarah ta Gama barbadenta tayi waje Bai Wani bata fuska sosai ba altho she is convince maganinta yana samun kusanci dashi yadda take bukata she just one is a matter of time kafun shidakansa ya soma bibiyarta
Da soyayyarsa so Duk Wani abunda zai mata ayanzu bawai damunta yakeyi ba tasan dai dolene ya shigo hannu,he was on call with yaa sheik hakan yasa yyi xcusiing dinta ya nufi hanyar dakin sa da wayar a kunnen sa,Babu yadda baiyi yaa sheik ya barsa ya taho kanon ba Amma haka yaki masa fir yace masa yabari kawai shi zaizo abujan jibi inyaso zasuyi magana cos he is kind of busy now da wasu abubuwan haka imad ya tsinke wayar badon yaso ba dan Wani irin mugun Nauyi yakeji aransa nason tambayarsa halin da rufaida ke ciki
Wanda ya kasa iya furta masa a fili.

Daga Nan Bai kara fitowa ba yafada wanka yama Gama mancewa da wata Zara daya bari a waje,ita kuwa Zara cikin salon makircinta sanda ta jawo hanlin shukra kanta Duk dama bawani sake musu fuska takeyi yau saita tsinci kanta da bata labari tanata cewa tuntuni tare da imad take wajen motsa jiki,aranta tasan muddin shukra ta san da haka toh tamkar da kowa ya sani ne..

She just want ppl to start picturing her real intention akan imad tana so asan da cewa lallai akwai Wani kulalliyar Ajiyar romance dake shirin tashi da zafin zafinsa a tsakanin su wanda takeso ta zafafasa banawasa ba.

Nazli is busy da i don't care attitude dinta ta Dade tana sharban baccinta batama San me akeyi agidan da sassafen Nan ba

Shukra ce dai ranar da kyar ta samu ta nitsu tunda ta tabbata da cewa ba dawowa yaa sheik zaiyi yau ba take bushasha Duk da bata kwanta da wuri ba Bai hanata farkawa da wuri ba kaf tabi ta tashe su da gulman Zara da imad data debo mutanen gidan sunata mamaki wasu kuwa basu dau maganan da Wani muhimmancin ba wani sabuwar gagarumin shirin aka shigayi kamar na jiya kowa na kille da dokin ganin sa..


Haka kawai xuciyar zara yake bata cewa akwai wani sabuwar abu muhimmi Wanda ya shafe rayuwata game da haduwarta da IMAD,Wanda by far bazata iya tantance shi ba,wato haka kawai jikinta da zuciyarta yake bata shidin nata ne wani sabon al'amari ne mai karfi a zuciyarta dake yawan alakanta su Wanda a wannan lokacin bazata iya cewa menene shi ba akalla hanklinta dai ya kwanta da kalamn mutanen gidan koba komi sun tabbatar mata da ta karbu awajen su saura shi Dan tabbas yadda taga ake kaunarsan Nan baza a taba kin masa auren Wanda ya yace yaso ba,..


Haka Aina'u ta fice agidan batare da sun hadu ba sai ta waya datake gaya mata komi,zarahn ce still ta dada karfafa mata gwiwa akan magani zaiyi aaiki akan muffy tunda har ya soma kusantarta is just a matter of time shizai soma bibiyarta harsai ta gaji dashi.

Duk yadda ai'nau taki cusa Hakan aranta haka Zara ta ladabtar da Ita harsanda tayi Imani da zancenta ta Kuma yarda da Hakan kwarai da gaske.

Yauma normally akayi breakfast mufrad ne kawai bayanan acikinsu sabida Wani early morning meeting din daya fita a presidential villa
Bai dawo ba sai wajen 11am Nan ma shiryawa kawai yayi suja fice da imad basu kara dawowa ba sai can dare...


Daga ta bangaren rufaida kuwa tunda su maman Iman suka bar gidan ta kasa samun nitsuwa a xuciyarta Duk dama yakumbo tayita rarrashinta da kalamai Masu taushi masu Kara karfin gwiwa da karafafa zuciya saidai Hakan baiyi Wani tasiri akanta ba, can bayan ishai datayi sallah tadanyi karatun qur'ani sannan taji nitsuwa ya Dan sauko mata kwanciyarta kawai tayi batare da ta kula yakumbo ba ta takure kanta waje guda akan gadon tare tarin tambayoyi da bukata masu dumbin yawa a zuciyarta wanda har iyanzu takejin nauyin furtasu waje

Haka daren ya Kare yakumbo bata fahimce yanayin rufaida ba,Dan ko cikin dare taji motsinta sai taji kamar ba baccin takeyi ba inta leka ta gani saikuma taga idanunta a rife

Washe gari da asubahin fari lokacin iskan asuba ya cilla yakumbo Wani duniyar rufaida ta zame daga Kan gadon cikin sanda ta sabi doguwar hijabin ta tayi waje.

Duk da yanayin jikinta na yadda take fama da rashin cikakken nitsuwa da lpya Bai hanata nausawa cikin anguwa ba danjin kanta take kamar wata zautacciya Wanda xuciyarta yake shirin tsinkewa da damuwa da kunci,a wannan yanayin datakeji bata bukatar Wani abunda zai karya mata gwiwa,atleast not a shaming party,Duk dama Hakan kusan dolene Amma bazata iya bowewa aranta jiya ta matikar tsorota da yanayin fassarrar dataji anmammta ita da iyayenta a abakinsu maman Iman wanda bata da aufi tasan aduk sanda aka Furta mata Hakan zataji zafi da ciwo axuciyarta bana wasa ba,jiya har kasa iya runtsawa tayi, cikin zurfin tunanin data yi tayi taga ya dace taje ta same malamin islamiyar su Wanda ake kira da malam sheik Abdul jabbar mohd sule,which she is sure zai saurareta batare datayi judging dinta ba,snn da alaman shine kawai zai iya gaya mata abunda zai iya tallafawa rayuwanta a halin yanzu datake matukar bukatar kwakwaran mafita..

Agaban masallacin da mallm Abdul jabbar yake jan salla ta nemi lungu ta rakube rike da kanta dayake mata Wani irin tsananin ciwo kamar ba sanyin safiyar Allah ba

Hanklinta kwance ta cigaba da kallo har aka watse dake tasan malam yakan tsaya ne harsai ya kammala karatun qur'anin sa sannin ya wuce gida

Sanda wajen yayi shiru bakajin sautin komai sainashi sannan ta tattara sauran karfin gwiwarta ta shiga takowa a hankli harta iso bakin masallaci.

Sanda ta iso daf sannan taji ta kasa iya daga kafafunta awajen tsayuwa tayi tsam tanamai lumshe idanunta batare da shirya ma Hakan ba Jin yadda karatunsa yake mugun ratsa mata cikin kunne yana mai shigan jikinta kamar iska mai tsananin sanyi.






*™✓SHADE OF RUFAIDAH*


_BY_
_SURAYYAHMS_


_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_


BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.


Part1:chapter 33


Kara matsowa kusa malam abduljabbar yay cikin Mamkin ganinta yace koba rufaida bace?kanta dake a can kasa ta dago ahnkli ta dan kallesa ayayin da take kkrin tare tulin ruwan hawayen dake bulbula daga cikin kwayar idanunta wanda ita kanta tasan bata isa ta tsare sa ba,cigaba da kallonta yay har saida sautin muryan ta Mai tsananin sanyi da rauni ya kufce ya fito daga can kasan tantanin makwallonta tare da sakin wata yar karaman dirin numfashin ta Mai tafe da rawa rawa,cikin yar sheshekar kukan datake kkrin danne rurinsa ta daure tace Assalamu alaikum malam katashi lpya?"Lpya" kawai.. yace ynata kallonta duk jikinsa a mugun sanyaye da yanayinta dayake lura daga Nan Wani karamin shirune ya gifta a tsakanin su,baice uffan ba itama bata kara iya ce masa komi ba,kallon yanayinta kawai ya dingayi already jikin sa ya riga ya basa rufaida ba lpya ba,ita kuwa alokcin abubuwa dayawa ne suka shiga damunta suna ruda mata tunaninta game da zuwanta datayi Nan saitanajin kamar bai Dace ma ta fito a wannn yanayin ba

Wani irin rudani ne ya gauraye fuskarta da zuciarta wanda yake kokrin kulleta mata Kai ta hanyar cunkushe mata zuciyarta da karfaffan waswasi

Tunani take aranta tana sakawa tana warwarewa"..shin A Inda mummunan labarin ta ya baza koina a anguwar su tasan dai da kyar ne in shima baiji labarin cewa tayi kisan Kai ba so What if he also choose to misunderstood her now?wajen wakenan zataje ya tallafa mata wajen taso da qarfin imaninta dayake neman gushewa?
tasan dai bazata taba iya komawa ga kawu zaidu aynzi ba,Sam bata son ta Kara jawo masa Wani matsalar da mahaifinta yaa malam,Wani irin karayar zuci ta dingaji ayayin datake wannan tunanin Wanda ya haddasa mata Jin mumuman rauni a zuciyarta Wanda bazatama iya fasalta kalar ciwon dayake tafe dashi ba,Wani irin cunkuso da ciwo ta dingaji a Kan kirjinta da zuciyarta,sai tay wani jimm Babu wani shiri sai taji hawaye zirrrrr nabin kuncinta suna saukowa har kasa bisa kumatunta hartana Jan shessheka sautin kukan nata ne yake fitowa a fili..

Cikin yanayin damuwa malam Abdul jabbar ya hau rarrashinta da kalamn sa masu sanyi yana mai bata haquri yace:

"Kiyi haquri ki shigo daga ciki malama rufaida, ai Koma menene matsalar taki bai dace ki tsaya anan kina kuka ba ko?..Dan Allah kiyi haquri ki shigo ki zauna ki nitsu inbawai har kin yanke ma Allah hukunci ba ne
Jin tayi masa shiru yasa yace malama rufaida kinaji kuwa?
A Babu shiri ta gyada mai kai batare da cewa uffan ba tabi umarnin san ta shigo daga cikin masallacin tana Dan goge hawayen dake manne akan fuskarta, can nesa da shi akan tabarma ta nema waje ta zauna,tana zama ta kife kanta akan kafafunta tana famar sauke nannauyan Ajiyan zuciya..

Malam dake kkrin sauraran damuwrta Bai wani jira Jin ta bakinta bama yahau mata nasiha da wa'azi masu bala'in shiga jiki da ratsa Imanin mai Imani Wanda acikin furucin san ne kadai yasa ta fahimce cewa ashe shi baima sanda labarin abunda ya afku da Ita da aketa bazawa acikin anguwar jiya ba.

Hakn ya Kara bata damar Jin zata iya fayyace masa damuwarta ta fuskar neman kofar mafita da sauki,tana hawayen ta shiga rero masa kadan daga cikin abunda ya afku da Ita bata iya boye masa komi ba sabida raunin datakeji da Kuma yarda dashi datayi ganin shi bamai saurin fassara bane tana Kuma kyautata zaton bazai tona mata asiri ba.

Malam Abdul jabbar yakasance mutum ne mai rauni da tsananin tausayi,
shima sanda ya zubda hawayen sa sosai agabanta Jin irin ukubar rayuwa da ta fuskanta a hannun mijinta Wanda har ya jawo tayi sanadiyar daukan ransa a wannan yanayi

Saidai shi baiyi mamakin jin yadda tace mutanen anguwan sun juya kan maganan ba,Dan wannan din tamkar da dabiar Dan Adam ne na dindin din,wato ya aibata mummunan qaddarar Wani sannan shi yana mai kafafa da nasa laifukan.

sosai malam ya tausaya mata duba da karancin shekarunta duka duka rufaida batafi sa'ar yar kanwarsa maryam dake karkashinsa ba,tunanin yake ta yadda yarinya karama kamar rufaida zata iya dokar kalubalen dake tattare da irin wannan qaddarar shiyasa yashiga bi da kalamansa cikin hikima yana saukakawa yanamai dangata ko Wani matsalarta da ayoyin alqur'ani da kissosi na manzon Allah saw dan ma kartaji kamar da ra'ayinsa kawai yake furta mata wayannan muhimman shawarwari ko danta ji dadi...

Sunfi minti arbain rufaida tana shiru anajin nasihohin sa wanda Kamar yadda tayi burin samun karfin gwiwan daga gareshi Hakan yakasance har fiye da yadda take zato ma, Dan sosai malam ya nuna mata cewa komi arayuwa mai wucewa ne in har ta dage da addua da karatun qur'ani ta Kuma yarda da Allah tasaka sauki a lumaranta ta mance da maganganun mutane,shida kansa ya mata alkwari cewa muddin ta samu saukin jikinta toh koshi zaina zuwa har gidan yakumbo yana koya mata karatu Dan dama baifi surori kadan ya rage mata ta kammala saukan qur'aninta ta ba.

Sosai rufaida taji sanyi aranta atleast she got sumone else dat totally understand her pain and is ready to help her regain her strngth,basu wani Dade ba malam yace tayi marmaza ta tashi ta koma gida tun kafin gari yay haske mutane su fara tsareta da gulmace gulmace

godiya sosai ta rinka masa Dan har yawan hawayen datakeyi saida taji shaukin yinsa yadan ragu kyawawan kalaman sa masu mugun sanyayawa Wanda taji dirarsu a zuciyarta tamkar saukar ruwan sanyi ta mike tsaye tana famar godiya,shikuwa sai bata haquri yaje yana dadda jadadda mata akan ta dage da kusantar kanta ga Allah.


Cike da godiya tayi masa sallama ta dauki hanya direct ta nufo gida dakema ta Dan killece dskarta bata bude shi dau awaje ba duk da haka daidaikun mutanen dake wajen sai kallonta Suke suna gulmanta, basu dai tunkareta ba dake ma kanta a kasa yake take tafiyarta Kuma cikin sauri da dauke kai bata tsaya kula uban kowa ba harta isa kofar gida

Sallama tayi Jin koina shiru ta fadi tsakar gidan kirjinta ne ya bugga atake ta nemi waje ta dakata Jin sautin muryan yakumbo a daki tanata faman masifa saidai bata San da watakeyi ba.

Kirjinta ne ya buga Duk tunaninta Kar ace mata ummanta tane ta dawo,cikin sanda ta shiga karasowa tana takawa a sace harta ta dafa kofar dakin,Nan da nan ta gane sautin muryan Wanda takeciki,daga Nan ta tsaya itama tana saurarinsu..
Daga ciki taji yakumbo tana masifa tana cewa
Ashe mutum bazai huta da maganan rifaida ba?Fisabaillah da sassafen Allah tun gari Bai Gama waye ba anzo ana tare ka gulmace gulmacen banxa da wofi to wallhi nidai Babu ruwana Allah na Gani nayi wadar da irin wannan rayuwar taku

Dagata dayan bangaren muryan matar mai anguwane yake tashi cikin isa da iko tana mai dakatar da kalaman yakumbo cikin salon tsananin raina mata wayo

"Ai ke kam dama haka matsalarki take,gaki Nan dai kin manyanta Amma rikicewar tsufan Nan yanaso ya zautar dake kina abu kamar karaman yarinya wacce bata mallake hanklinta ba"Nina ce miki gulma ya kawo ni gidanki?mutanen gari dai da suketa debo matsalar jikarki suna damun mu dashi shine Nace bari inzo dakaina in magance mana komai ..Cikin tsareta da sauri yakumbo tace toh sannu Aminatu yar sarkin yaqi,wato kinxo ki magance mana komi,yat dariya yakumbo tayi da zafin haushin ce mata datayi wai bata mallakin hanklin kanta ba,tace toh sai kuma akayi Yaya Amina?nikam anya kanki daya kuwa?yarinya da uwarta da ubanta araye kyace wani andameki da matsalarta?ko daga cikin iyayen nata akwai Dan uban dayaje gidanki yanemi temakonki ne inda akwai ai saike fito fili ki fayyacemin dan ni bana aikin yaranta
bana kafa hujja da rade raden mutanen anguwa..

Cike da dacin rai da izza tace
"Abun da rufaida tayi Sam bai dace ba Niso nayi ma inzo in sameta a cikin dakin Nan shiyasa ma nayi sammako na taho,yakumbo boyeta da kukeyi bashi ne fa mafita ba,wannn Abu data aikata na kisan Kai ya shafe mu duka,yarinya tabi ta batama suna Duk garin kano a baredede da damu? Toh wallhy inku bazaku iya sakata agaba ta amshi kuskurenta ba ta mu zamu iya,ai gamunan muzamu iya ladbtar da kowacce shegiyar yarinya Dan bazamu taba bari ire iren ta Suna yawo anguwa Suna gurbata wa sauran yan matan mu tarbiyan su ba..

Shiru yakumbo tayi aranta tana ta mamakin yadda matar mai anguwa take tada jijiyar wuyarta akan abunda kwata kwata bai shafe ta ba..
Rufaida dake manne da kofar dakin tanajnsu Babu abunda kirjinta yake sai bugawa,gaba daya ta maida hanklin ta wajen son jin kalar amsr da yakumbo zata bayar,Kan ta hankara kawai taji an bankade kofar ta ciki,yakbon ce ta fito waje a harzuke ta debo talkamna matar mai anguwa batare da ta lura da Ita ba ta koma ciki. Dakin ta watsa agaban ta tace

"Ke Amina Kisaka kafafuwanki anan ki kama hanya kibarmin gidana ko in gurje mummunan bakinki..
Matar mai anguwa ta mike tsaye zatayi magana yakumbo ta daka mata tsawa a gigice Wanda yasaka rufaida shigowa cikin dakin a rikice,da sauri ta isa gaban yakumbon tana mai rirrike ta ganin yadda tsaban bacin ranta yake tafarfasa a fili..yatsun hannun ta har Wani rawa rawa suke tana nuna su akan fuskar matar mai anguwa
A zafafe cikin tamfatsen masifa tace"Harke Amina kina da bakin zuwa gidana Dan ubanki kina gaya min baqar magana akan rufaida?yarinya inbaki sani ba da raina aka haifeki,nasan komi akn rayuwarki in kura na maganin zawo to taiyi maknta mama,
karkiga Wai kin auri mai anguwa kina Wani bunkasa kina hura hancin waike kin mallake sa,waye baisan cewa uban ki matsafi bane ne kakanki kuma gasurkumin boka..

Ke Amina Daga yau Na haramce ki da shiga tsabgar rayuwar rufaida inyaso kisa mijinki ya koreni anan anguwar dadin abun harki mutu baxayi gindin haihuwar yar data Kai rufaida ba..

Da Wani irin kukan kura matar mai anguwa ta mike har jikinta na bari,..

"Wani kike gaya ma wayannan maganganun yakumbo?mani like wa gorin haihuwa?
Wasu maqudan hawayen takaici da tsananin zafin maganan yakumbo take suka yanko mata cikin rasa kalar xagn daya dace ta sauke akan yakumbo kawai ta shiga tabe bakinta tana kada kanta araunane...

Can dai ta dauki takalmamta ta riko a hannu tana mai kallon setin rufaida

Tafi minti biyar tana kallon rufaidar da Wani irin mugun Ido a kuma ayanayin daya jefa rufaidar Jin mummunan tashin hankli da fargaba..
Hawayene suka shiga sauka a idanunta Babu kakkautawa,matar mai anguwa ta tabe baki cikin tsananin fushi"Uhm yarinya banga laifinki ba,ace barewa tayi gudu yarta Kuma tayi rarrafe?uwarki ma haka take, mafadaciya makira Wanda tafi kowa salon iya munafurci,hakama wann tsohuwar Wanda kukayi gadon mugun hali da bakin zuciya awajenta,kinje kin kashe mijinki kina tunanin mu zamu kyaleki anan anguwar kina yawo kina abunda kikaga dama ko?toh wallhy bazata sabu ba saidai in bani bace matar mai anguwa.

Saina saka an ladabtar dake an koya miki tarbiyan da gidanku suka kasa baki,shashar yarinya kawai,da aihuwar irinki gwara in mutu a juya,Allah ya hanani gindin haihuwar Indai irinki zan haifi..
Allah ya raba ni da Mai baqar zuciya irinki Allah wadar da tarbiyan da aka baki,dangin marasa mutunci, kwadayayyu Kuma dolene agaya muku laifinku ko kunaso koba kwaso..
Da so nayi muyi magana ta fahinta domin ki gaya min mtsalar ki Dana iyayenki Amma harni ce za'acin mutunci ana min gorin haihuwa akanki?toh wallhy saina nuna muku iyakarku a anguwan nan zaman anguwar Nan saiya muku daci..
Tana dasa aya yakumbo ta juyo da ita tana kwallon cikin kwayar idanunta da already a hargitese yake da tsananin bacin rai Dan in akwai abunda ta tsana baifi kamata gorin haihuwa ba

Yakumbo tace
Inkin isa kije ki aikta Duk abunda kika Furta anan Amina
Tsayuwar rana faduwarsa ga fili gamai Doki saura sukuwa,shiru tayi Jin yadda rufaida ta rirriketa da zimman sassaita ta,'..kiyi hakuri umma Amina
Allah ya huci zuciyarki laifin danai muku kuyafemin,abunda ya afku Dani qaddara ce bason raina ba,dan Allah kuyi min adalci kudena zargin iyayena akan Duk abunda ya afku Dani,laifi nawa ne bana su ba,in zaku aibata no zaku aibata basu yakumbo ba kiyi hakuri Dan Allah in ranki ya baci

Cike da isa da izza matar mai anguwa ta juyo a hatsale
Bazan yi haqurin ba
Maqirar banza sai Kun kwaso ma mutane tijara sannan kuzo Kuna makale murya Kuna abun tausayi.

Rufaida kin ban mamaki,to wallhy ki maxa ki kyara halayenki tun wuri Dan kuwa kin aikata mummunn laifin da bazai taba gogewa atarihin rayuwarki Dana anguwar Nan ba.

Cikin dauriya Rufaida tana tare ruwan hawyenta tace Toh kuyi haquri kuyafemin,caraf yakumbo tace karma suyafeki.
Su sakaki a wutar jahannama in su suka halicce ki
In masu kikayi wa laifin su kashe ki mugani,dadin abun kowa zai Gani a kwaryan cin tuwonsa,Kuka ne ya kufce mata tace karya Amina takeyi wallhy dantaga bani da komi ne tazo har gidana tana zagina tana cimin mutunci,suje suyi wa ubanki wannan barazan gulman mana in ba tsoro ba?kawai Dan anrainnin wayo kowa saiya kwaso sharar bakinsa yana watsa min?angani tsohuwa kekuma karamar yarinya toh Duk wanda yake tunani ko yake ikirarin zai kuntata ma rayuwar wani Dan yanaganin yafisa abun duniya karshe shi zai zamto abun tausayi Kuma wallhy saikin tozarta kanki da muguwar halinku Amina.

Abun da ya afko rufaida kwata kwata bai shafeku ba, Yan mata nawa ne a anguwar Nan wayanda suke aikta mugayen abubuwan Allah wadar? Har Yan mata masu siyar da kwaya an kama su,ga karuwai ga yan daudo da gwartaye da Yan luwadi,Amma ai ban tabaji anje har gida ana titsiyesu ba sai Akan nawa da qaddarace ta afka mata tayi kisan kan,dan tsaban Kun raina min wayo?Allah saiya sakamin ya sakama rifaida,yarinyar Nan bata taba muku komi ba sai Allah ya mana sharia akan muzanta da kuke faman yi.

Tsaki matar mai anguwa taja ta kama hanyar ta tayi waje,ita kuwa yakumbo sai sauke hawayen ta take tana jin tsananin zafin abun aranta,
Cike da sanyin jiki rufaida ta juyo tana share kwllar idanunta da suke zubowa daddaya
Muryanta adan dishe tace"kiyi hakuri yakumbo,
Dan..batama karasa ba yakumbo ta tsareta a fusace da yar masifa tace
Ke dalla rufamin baki wani hakuri zaki ban bayan kin kama kinfice waje sassafen nan danki jawo mana masifan mutanen anguwa
Ba kallon ki da sukeyi bane a anguwar yasa suke zuwa nan watsa gulma?Wajen malamin mu naje fa yakumbo?..waye kuma malamin Ku?
Bayan kaf anguwan nan babu mai hankli jahilan banza magulmata wallhy in ba tashi tsaye mukayi ba sai sun binne mu da ranmu.
Masifa yakumbo ta cigaba da yi,rufaida bata kara ce mata uffan ba har sanda ta danyi sanyi,sosai ta fahimce cewa damuwa ne da tsoro take son ya fara damun zuciyar yakumbo,tuno sallan fajr da batayi ba yasata fita waje cikin sauri ta doro alwala tazo ta aiwatar..
Tana idarwa

Please Login or Register in order to submit comment