Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mufrad kuwa baice komi ba sanin shi miskiline yasa Babu wanda ya daga hanklin sa akan haka har aka soma cin abinci.

A hnkli malak take jujjuya spoon dinta acikin abincin at first zaka dauka ta koshi ne but tunani kawai take akan yadda Zara ta tuttula ma kowa abinci kamar wasu mayunwata itama sosai tasoma gane kalar zarar sai taga kamar bata mata ba...

Hirar America shiyabi ya dauke musu hankli kowa najin hirar da ake musamman da aka sako zancen case dinsu da rufaida

Hjy goggo ce ta nace da masa tambaya akan zancen kisar Kan da akace rufaida tayi,sama Sama yake musu bayani danyariga yay alkwari da zuciyarsa cewa bazai taba bude asirin rufaida awaje ba bare ma dayasan mata da karamin kwakwalwa da son jin gulma shidai saice musu yake self defence ne
Kuma mijin nata shine baida gaskiya

Tuni hirar yaa malam ya Kara zafafa awajen hjy adada da hjy goggo sunata barbada akan halayyar yaa malam da sukaji ance Wai yanayi ma yayan cikinsa auren dole,fade fade Babu abunda basuce akan haka ba,kawai su fito suce akan kwadayin abun duniyane yaa malam ya jefa yarsa acikin ukuba basa iyawa sabida yadda sukaga mufrad da hjya jasmine sun dauke wuta Sam Sam suka ki su bada fuska acikin hirar tuntuni da ake maganan su suka ja bakinsu sukayi shiru sunki suce komi.

Ba Wani cin abincin sukayi ba imad ya fara cewa ya koshi,
Anan ne ma sukaji cewa ai gidan doc mehra yayi breakfast dinshi

Ana kammala komi Aina'u ce ta soma xamewa ta haura can sama tsabar batason ma Zarah ta sata yin Wani aiki

Hakan kuwa Zarah ta zama uwar jagora wa masu aiki har sanda aka kammala tsaftace wajen tas

A Lokacin daidai motar daya kawo kayan imad da Dan tsarabar da yayo musu ya iso,Nan d nan nazli tabi bayan keeyan suka je da masu aiki aka tattaro trolleys dinsa manya guda uku da babban travelling bags trolley kawai yace akai masa sama sauran jakunan haka ya damka ma mahaifiyarsa yace tsaraba ne,daya jakar nata ne ita daya,sauran kuma yace tasan yadda zatayi dashi araba a tsakanin mutanen gidan,cikin Jin dadi ta rinka saka masa al'barka.

Mufrad ne ya dauke hanklin sa suka haura sama can dakin da aka Kai kayansan cikin masa bayanin yadda yaa sheik ya tsara masa nashi sashen a cikin gidan cewa da akayi saiya kawo mata kafin abashi site din ya rinka sakashi dariya,slowly zakuwarsu akan zancen auren nasa saiya soma shiga zuciyarsa ya soma jin kamar zaiyi tunani akai kawai


Daga falo kuwa Tsabar murnan da akeyi a babban falon site din hajya adada aka baje kaya aka hau rabawa,Bai Wani dauke su lokaci ba sabida kusan komi yasa anyi packaging dinsa da sunan Duk wani ahalin dake gidan hatta su Anty meera akwai nata sunan saura sauran da suka rage aka bawa malak da su hjya goggo sannan aka debi jewwries da turare aka damka ma Zarah akace taje can su raba da Aina'u.

Komi cikin raha da jin dadi aka gabatar,
Anty meera da hjy jasmine suka koma can daki,aka bar hjy adada da su hjy saddika Wanda har ayanzu hirar case din rufaida kawai sukeyi acikin laluben duhu don kuwa haryanzu harsashe suke basu fahimce asalin abunda ke tafiya ba.

While acikin zuciyar Hjy goggo harda kyashin jikinta da takeyi tanajin mugun zafin rashin kasancewar su da Ita aganinta haryau hasiya itace silar rabata da danta gashi Dan jikarta ma tana shirin janyeshi da jarabar dan tsohon mijinta, Hakan yana matukar cusa mata baqin ciki aranta,
Yo meye mahadin zaidu da Dan cikin hasiya ai ubansu ba daya ba,meyasa za a saka mata jikanta agaba da damuwa..

Tunda akace rufaida ta kashe mijinta take ta mamakin yanayin tarbiyan da aka basu..,anata tunanin aiga mata nan birjik akan musu auren dole Amma bata tabajin ance ga wata ta kashe mijinta ba sukam ma ada can Duk auren dolen aka rinka musu Kuma suka zauna da maxajensu lpya suka hayayyafa
Kawai dai baqin zuciya da muguwar zuria irinna hasiya.

Koda can ma ai ta fahimce kamar ba aslin son dikko hasiya takeyi ba kudi kawai tagani ta biyosa,hira kawai sukeyi hjy goggo tana ta saka wayannan abubuwan aranta hjya Adada kuwa damuwarta baifi taga anyi gaggawan yaface Duk wani zumuncin dake tsakanin zaidu da dayan Dan hasiya ba..

Aganinta basu da mutunci ko darajar da zasu hada xuria dasu sabida matsalar su ta karamcin ilimi da wayewa ga talauci,sosai da sosai hjya siddika take Goya mata baya itama aranta ko kadan bata son abunda zai hada zuriarta da harkan karanci da zubda mutunci bare ajega karancin ilimi da wayewa,sun Dade suna hira akan lamarin su rufaida Duk dama bawani saninsu ko sanin rayuwarsu sukayi ba,haka dai suka tayi Suna tofe tofensu aranar Babu abunda basu tofa akansu ba...

Daga cikin babban falo malak ita kadaice a zaune da wayarta a hannu ta daddanawa Duk hanklinta nakan wayar tana famar karanta Wani littafi
Mai taken Ajalin so da surayyahms ta wallafa,daga Ganin yadda take sauke Murmushi kasan book din ya mugun tafiya da Ita..

Da wannan fara'ar akan fusknta ta dago caraf suka hade ido da shukra data shigo tana tafiyar rigima malak batayi kasa a gwiwa ba tace mata "Hi..
Kallo Shukra tabita dashi bata amsa ba sanda ta nemi wajen xama ta zauna a kasaitance ta Wani harde kafafunta Wanda kafin ma ta Gama aikata hakan malak harta bada banza ajiyanta ta dauke kanta ta mayar kan wayarta tanamai cigaba da abunda takeyi, tmakar bata San da halitta awajen ba"..ganin hakan yasa shukra ta rude gaba daya ta rasa yadda zatayi ta soma fidda maganar dake bakinta harga Allah itadai tana son tayi kawance da malak
Sai can ta daure cikin kadadi tace
"ummm Ya Daddy Mehra?Fatan yana lpya,malak batace komi ba itama har tadanja lokaci,batare da kulawa ba ta ce
Lpyar sa lau,ya school?cike da rolling eyes da Jin takaicin Jan ajij malak shukra tace oh dama kinsanni ne?a nitse malak ta juyo ta dasa mata dara daran eye balls dinta dats speaks confident tace "u're yaa sheik dougher I guess..shukra tace yeah,malak ta tabe baki,"he is my dad's best friend nothing wrong in knowing u guys right?..cikin Jin dadin Jin haka shkra tace yeah but har me kenan kika sani akaina?murmushi malak tayi ta Dan Kai da Kai kasar wuyarta tace Nothing..not even your names.
Shukra zatayi magana ta Kara tsareta"..I have Neva been to kano,nd i guess you just moved to abuja right?..cikin rasa kyakkwar amsar da zata bayar tace yes tare da miqa ma malak din hannu a tsaye ta mike tana kallonta "I am khadija zayd matazu..pplarly known as shukra and you?..sanda ta Kare mata kallo sannan ta Mika mata hannun ta sukayi musabaha tace I am malak mehra..da Wani irin salon aji ta karashe Furta hkan Wanda yasa shukra kwace hannun ta cikin sauri so what are you planning to study?..Kai tsaye malak tace information technology,and u? Shukra tace I'm studyn law at nsukka halama gobe na wuce schl daga Nan ta soma zuba tana bayanan da ba a ma tambayeta ba
"Actually We came to meet our grandma sai kuma ga dawowar uncle mad Hakan yasa mu dole muka tsaya tarban sa,so dama uncle mad yasanki ne?dnt tell me u're his pet girlfriend su mama since baki wani girma ba..dariya sukayi atare kowa da yanayin fassarrar sa a takaice malak ta maida mata amsa tace"yes I'm still young for marriage so how old are you?saurin shanye mgnan shukra tayi Dan tambayar bemata ba da kyar ta furta I'm almost 17...malak na shiru batace mata uffan ba,can itama tace am 16..Ashe kusan daya muke,shukra ta tabe baki kasar wuyarta tace nope,nifa har yanzu bana kula guys..u know lokacin Abu ayishi yanzu kuma lokacin karatuna ne I won't spare any minutes Ina cusa kaina wa namiji,Neva,a hnkli malak ta dago Jin ance"cusa Kai wa namiji?abun ya bata dariya,cikin yar muryanta dabaiyi kama da ta damu da zancen ba tace hey,Ba acewa Hakan cos Allah zai iya jarabtarki dabin wani namiji Shukra tace noo noo pls Allah ya sawwake
I can't imagine myself to look like Anty xarah,god forbid,cike da rashin fahimta malak tace "Who is dat?ban fahimce ki ba who is zarah?Aikuwa Nan aka motsi Inda yakeyiwa shukra kaikayi,atakaice sanda sunfi awa guda tana tsinka ma malak labarin Zarah filla filla shafi shafi harsai da takai karshe sannan ta dasa aya..
Mamaki ne ya Gama cikke xuciyar malak tayi shiru tana jinta batace mata uffan ba,she is just wondering yadda akayi shkra tasan dukan wayannan abubuwa,baki ta tabe lallai toh saka idon yakai makura,batun Zarah kuwa bai Wani bata mamaki ba Dan tuni ta soma gane take takenta,wayartane yay kara ganin new number yasata sawa a handfree batakai kunnen ta ba tanayin sallama muryanshi mai dadi da taushi ya tsareta
Yace c'mon taho ta waje Ina jiranki,tunkan ta amsa cikin tsananin mamaki shukra tace uncle mad?atake Malak ta miqe tana mkin yadda akayi ya samo number ta hakan yasa tafice cikin sauri batare data kula shukra ba.







*™✓SHADE OF RUFAIDAH*


_BY_
_SURAYYAHMS_


_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_


BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.


Part1:chapter 29


Malak tana ficewa a falon Shukra ta hau bin bayanta da Wasu muguyen harara daga nan itama tashi tayi ta fice fuu cikin jin haushinta tayi Sama can ta haura dakinta Wanda akayi sa da tulin kayan duniya tsarin sa tsarin Yan gata irin Disney princess din nan yasha ado harta jikin bango tana shiga dakin tayi super ta fado kan faffadan Italian bed dinta dayasha kwalliyar pink bed sheets da trow pillows,kwanciya tayi tana famar juye juye aranta feeling so annoyed and ashame dan kwata kwata Batayi tsammanin zatayi ta zuba farrr kamar ankunna engine agaban malak ba So Wat will dat girl think of her now?...

Ita kanta tasan Tana da zargi da son hada gurmi a zuciyarta game da mutum shiyasa gaba daya takejin kanta a matukar dore ynzu

Ita Gani take batayi daidai ba Cike da takaici ta cije labbanta cikin tunanin kalar fassarar da malak zatayi mata makira Magulmaciya,mai saka Ido ko cheap?Wani tsaki ne ya kufce mata tuna Wani uban Jan aji da shasshareta da malak keyi alokacin da Idonta ya rufe akan gulma tana famar xuba mata labarai babu tsayawa, Sosai ta soma Dan da nasanin tunkarar malak da hirar she tots ko malak zata biye mata ne su hada Kai yau agidan su kuntatawa Zarah but sanin cewa ta kwafsa yasa atake aranta ya cunkushe ta soma jin haushi da tsanarta arnta tana cewa halama Duk layinsu daya da Zarahn, Dan da alamar itama malak din son uncle mad din take,Wani dore fuskanta tayi aranta tana bambami tana cewa wallhy basu isa ba,mikewa zaune tayi tana huci "tabdi jam wallhi dukansu bazasu same uncle mad ba uncle imad yafi karfinsu shiba class dinsu bane wannan nazarin ne ya cigaba da huruwa yana zafafa aranta kusan shine ma ya dauke mata hankli ya dakatar da ita daga saukowa kasa zuwa waje.


Bangaren Aina'u kuwa tunda ta zame daga wajen cin abinci ta haura sama ta shiga dube duben dakin ko zataga muffy amma bata gansa ba,atake taji ranta yay mummunan baci zuciyarta yahau tafarfasa yana mata Kuna Wani irin gajiya da fushi ta soma Ji aranta game dashi

Cike da takaici take ciza yatsanta tana nazari ita kadai da zuciyarta,All this while mufrad yana Nan agarin abuja amma banda yawacen yawacen meeting dinsa acikin abujan Babu abunda yakeyi Kuma haka tayi haqri dashi dakema ta lura kamar dawowar su da Zaran yasa yake jajjan baya da ita a tunaninshi Hala zarahn tafi dauke mata hankli,hakan yasa sai yayi banza da ita baiya ma son kwana agidan and sometimes zaizo din but still acikin sauri zai Kara fita yace mata zaiyi wani abu awani wajen,abun mamaki sai gashi jiyan nan da imad ya dawo wai har yawaiwaye shi, ai tanajin hjy saddika da safe tana cewa ai tare ma suka kwana..

Cikin tsananin takaici take jeka ka dawo a coridor zuciyarta a cunkushe tarasa abunda yake mata dadi can saiga Zarah ta hauro sama cikin tafiyar yanga hannunta Niki Niki da kayan tsarabar su tare da yar fara'a akan fuskarta,Suna hade ido Zarah ta tsaya durus ta dan dakata tace "Sis ya naganki haka whats wrong?dada dore fuska ain tayi tare da sauke karamin Ajiyan zuciya tana kallonta tace Nothing, Muje tacan dakinki muyi magana banason magulmatan gidan Nan su jimu,atare suka juya suka shiga dakin Zarah dake ma Duk a waje daya ne,ko zama basuyi ba zarah ta hau nunnamata kayan tsaraba cikin rawan jiki gaba daya ta rasa nitsuwarta dake Duk designers ne wanda tabbas tasan da kudi mai yawa aka siyesu, bracelet na mandarina duck dats so shiny ta dauka ta makale a hannun ta tana murmushi, ita kuwa Aina'u tagumi ta rafka Dan damuwar ta mijinta ne ayanzu ,ynxu hakama haushin imad din takeji na balbaleta kamar ta kashe shi haka takeji,Wani tunani tayi saita juyo cikin sauri Tace zarah Kin lura da wata karamar yarinya datake wani mammakale ma saurayinki kuwa?cikin Jan aji ta tabe bakinta kamar ba zugi take so tayi ba..tace "Baifa kamata ace kina barinsu waje daya ba fa,wallh kwanan nan saikijii ana zancen laka masa ita ke kinsan munafurcin gdan Nan kuwa? tsaye Zarah ta mike a hujajan kamar an tsokanota tace "Ina yar waccan ficcikar yarinyar Wanda tasaka Wani abaya?tun kan ain ta dago taja Wani dogon tsaki "Mtchww ai nafiki ganin ta..you know wat sis ni bazanfa tsaya sanya ba,im so glad ur family are already pressuring him akan batun auren nan so kawai ya aureni mu huta"....tsaye ain ta miqe tun kan Zarah ta karasa magana ta tsare ta tace toh wat are you planning to do now?u have to act fast,ke wallhy daga yaa sheik ya dawo zamu bar gidan nan mukoma asokoro Kuma kema ai can zakibini tunda kowa yasan dai Waje na kikzo hutu,u have to speed up ur game fast zarah,tun anan kisamu ki ja hanklin sa or Did u think abubuwa zasu tafi miki daidai harya soma kulaki inmuna can su Suna Nan da irin wayannan Yan kusuri tsomen?
hmm jiya jiya yazo Amma har anbiyosa gida da yarinya..thy are just fooling us ingayamiki.

cikin nazari mai kama da rashin hankli Zara tace no way,no way bazai taba yuwa ba,kinga malam fa cewa yay abun nan zaidan ja lokaci kafin ya shigesa I have to get myself more close to him yana kallon cikin Ido na yana shaqar qamshi na,maybe in 2_3weeks sai kiga komi ya kammala Amma ai dolene in San nayi kafin Nan, tana gama Furta Hakan tana sauke Ajiyan zuciya fuuu ta wuce gaban wardrobe ta bude ta fidda Wani sabbin kaya,golden atamfa ce mai kyau da tsada wanda aka baza mata dinkin bubu tasha zaren design daga sama har kasa tana Wal wal tana sheqi da haske,ganin haka yasa Aina'u tayi saurin mikewa tsaye tana kallonta da mamaki"
Zarah wannan kayan Kuma fa?
Batare da kulawa ba zarah tace canza kaya kawai zanyi, Bata hankara ba taji har an fauce kayan cike da dore fuska ain tace 'whats wrong with kayan jikinki?..Zara xatayi magana ta tsareta a zafafe c'mon waike so kike kowa yasan kinxo neman namiji agidan Nan?dazu fa har dariya su nazli suke miki..hade ranta tayi cikin rolling eyes tace Aina'u pls spare me da maganan su nazlin Nan to in sunyi min dariyar saime?..damuwa ta batasu bane,hanklin gayen Nan nake bukata and you know kyakwar sutura itace hasken ya mace I want him to fall for me by simply admiring me..dariyan takaici ne mai karfi ya kufce ma ain batare da ta shirya masa ba, cikin dariyar tace ohh ahakan ne zai falling miki?tsaki mai kauri taja,Zara ki bude idonki ki dube shi da kyau acikin lawyoyin ma shina ajin farko ne gashi
kyakkwan namiji hadadde by now yasha arangama da irinki dubu Banda ma wayanda suka fiki a komi da komi Wani wawan suturanki ne zai sashi ya fallen Miki?c'mon In zakki kimtsa kawai ki kimtsa ki Dan kkakara turaren Nan naki kije waje ki same sa u can start a conversation or talk abt something else Zarah kada ki soma yarfa kanki agabansa pls know ur limits I beg you,ta karashe tare da hade mata hannun alaman roko..

Sauke Ajiyan xuciya Zara tayi cikin rashin sanin abincewa Nan dai ta sallame komi da alaman ta dauki shawarar ainaun altho ba a yadda taso kominta ya tafi ba,iya abunda ainaun ta kikkitsamatan kawai ta rike sannan ta hau kikkimtsawa can ta kama hanya tayi waje..


Anguwar bayan gari
Old maguwa site kano.


Karfe 1 da rabi bayan sallan azahar umma hadiza ne a kwance atsakar gidanta Inda ta baza babban tabarma a baranda kamar mai shan iska tana lura da masu shige da fice,yau takasa ta tsare ne danta dakatar da magulmatan anguwan su da suketa kaikawo tun safe a tsakar gidan kowa da kalar salon munafurcin sa suna famar mata tambayoyi akan kisan kai da sukaji ance yarta rufaida tayi..

Saidai wannan karon sun balain shan mamakin karfin hali irinna hadiza Dan kuwa bushe idanunta tayi tasss ta shiga bawa kowa amsa daidai da shi batare da nuna fargaba ko jin tsoro ba..
Hasalima in ga kalleta bazakace tana cikin damuwa ba,na ciki na cinta Amma haka tabi ta danne dukannin damuwar ta da kuncinta wanda har Yanzu tana jn zafi da radadin halin da rayuwar yarta rufaida ya shiga ciki

anan ma take dada Jin yadda labarin ya bazu aranta tana mugun shan mamakin yadda gulma ya karade gari cikin Dan kankanin lokacin da baikai ace har Yan nesa ma sunji ba..

Saidai ayau da Wanda take magana da shi da Wanda bata taba muamala dasu ba Dik sune agidanta,kusan kowa a anguwar saida ya shigo gidanta Jin Karin bayani akan zance
"Daga an shigo sai kaji ana sanya muryoyin tausayi na makirci "ayya hadiza Ashe auren dole akayi ma rufaida wannan mummunan al'amari yaje ya afku?Ai munji ance auren dole akayi mata shine taje ta kasa zama ta kashe mijinta,kwanaki yansanda aka zo aka tafi da yaa malam Ashe abun kenan?tou ita Kuma rufaida maiya kaita kisan Kai,au rayuwa ai yar haquri ce Kuma mai kudi kuka aura mata halan?

Umma Hadiza batacewa uffan saidai tajisu amma bata cika musu burinsu najn gulma game da abunda ya afku da rufaida,Abu daya kawai ta sani aranta shine ta Kare martaban yarta,Duk wanda ya kawo mata baqar magana acikin xancen sa itama takan tsayane ta dubi wani Abu mai muni daya faru dashi shima saita mayar masa da amsar sa daidai shi Inda zai masa ciwo da zafi wasu har sukan kasa yin haquri atake sai su nuna ransu ya baci suyita zage zage

Yanzun Nan ma rahamatu yar gidan malam dalhatu mai kantin breadi ta fice a zuciye tana zage zage tana kumfar baki,Kwata kwata yarinyar bata da mutunci,ubanta ne dillalin gulma uwar ta ma haka,kowa yasani gulma ne rayuwarsu, gaba daya lokutansu da karfinsu akan sakawa rayuwar mutane ido ya Kare,Wanda ake xargin tsabagen iya saka Ido da aibata yayan mutanen dasukeyi dinne ya jawo yarsu rahamatu ta lalace ta zama karamar karuwa a layi Amma Duk da haka basa gani Kuma basu fasa ba,a shekaru dai rahamtu bazata wuce ashirin ba Amma ayanzu haka aurenta biyu tana fitowa,ita tsaban son hada gurminta yau sawunta yafi kafa takwas a kofar gidan yaa malam tsaban sonjin rahoto but tunda umma hadiza ta gasa mata baqar magana ya mata ciwo saita ta fice a Gidan a zuciye tana karade anguwar Duk Inda ta zauna saita hau zage zage

"Ai kwara ni da kanin miji na ake zargina,zargina fa akeyi Wai nayi cikin shege ma kanin miji na ni ban kashe uban kowa ba
Amma yau har matar yaa malam ne zata cakka min baqar magana akan wata shashar yarta data dabawa miji wuka a ciki?..

"baqar zuciya da Muguwar tarbiyar data basu shine ya fito fili,yaran Dan sunga Suna da kyau sun bi sun debo kwadayin duniya sun daba a kokon zuciyansu,iyayen ma kwadayin abun duniya yasa sun sayar da mutuncin yayansu wa masu hannu da shunu hahahahaha ayyuriiiiiiii tooh ai sheikenan karyan kyau Kuma ya kare
Daga yau Zamuga uban da zai aura musu yarsu dataje ta kashe mijinta,Kai duniya ace yar yarinyar Nan har tasan tayi kisan Kai?Dama can ni ban yarda da shiru shirun rufaidan tan nan ba ai daga Ganin rufaida baqar mugunta da taurin zuciya ne da Ita irinna uwarta,ga jiji dakai haka zata wuce agaban babba bazata tsuguna tagaishe sa ba sunajin kansu yayan malami gasu waisu Yan boko,daga sun gama a aura musu masu kudi..
hehehehe yau munga karshen draman madalla da asirinsu ya Tono ga yarsu ta janyo musu abun kunya..

Aranar Babu wanda ya huta da wannan hirar musamman ma da umma hadiza taki Sam ta nuna damuwarta dan iya danne matsalarta tayi fuk danta Kare martaban yarta Wanda kwata kwata mutanen anguwa basuyi tsammani ba,lungu da sako zancen kenan wasu Sukace hadizar ce mai dore ma yayanta gindi suke tafka iya shege,ai hadiza shegen girman kai ne da Ita tanajin kanta matar Wani babban malamin tana so tayi ma mutane iyeyi da jan aji da walakanci,shirun umma hadiza akan zancen ya balain sosa ma magulmata rai bana wasa ba,barinma matar mai anguwar dake itace babban jakadar Duk Wani saka Ido da gulma Dan in anje an debo agidanta ake fara saukewa taji tanaji ta kushe Wanda Bai gamsheta ba,har karawa mata matsayi take depending on yawan gulman da kake kawo mata,yau da ba a samo mata cikakken rohoto akan case din rufaida ba har kukan takaici snda tayi,in aka tambayeta sai tace "hadiza ta rainata ne,bata darajata a matsayin uwa Kuma matar shugaba,gaba daya ta daga hankli ta da tsaban baqin cikin rashin samun cikakken rahoto akan batun rufaida,sonjin gurmi yabi ya hanata sakat,taso ace hadiza tayi magana Dan tabbas tasan lamarin Nan babba me, almajiri ya riga ya gaya mata cewa yau har fada umma hadiza sukayi da mijinta akan rufaida
Amma Wai har Yau itace zata sako hadizan agaba tana magiya tana son taji asalin Kan labari daga bakin matarnan ta rarraina mata hankli
Yo Inde batun kisa ne ai tuni sun riga sunji,dalilin yin kisan da sauran rahoton shi suke matukar muradin sonji Wanda har iyanzu Babu wanda yaji zancen daga bakin hadiza,Abun nan yana matukar Sosa musu rai..

Wasu ma gani suke kamar hadiza ba jinsu take ba,Amma inba haka ba wanni irin makirci da bugun ciki ne yau basu gani ba,mata sai kace dutsi
Daga anyi magana Iya kaci tace musu qaddara ne ya jawo lamarin Nan kuma Babu wanda yafi karfin qaddara
Daga Nan kuma saitaja bakinta tayi shiru bata kara ce masu komi,komin jidan makirici da iya shan ciki haka zaka gaji ka barta,Duk kokarinsu haka sukayi abanza suka kyale ta..



Bangaren rufaida kuwa yau Banda bacci da jinya Babu abunda jikinta yakesha gaba daya jikintan yayi lagwas Babu sauran karfi Dan ko taci abincin amai kawai takeyi..

Around 5 na yamma Ykmbo ne zaune a Tsakar gidan ta rafka uban tagumi ga tarin wanke wanke agabanta ta rasa ta Inda zata soma tunkarar yanayin jikin rufaida wanda haryanxu tausayi kawai yarinyar take bata Gani take ciwon Nan harda damuwa

Ta Dade awajen cikin tunani kafun ta kammala ayyukanta ta tashi takai komi kitchen ta kimtsa su,dakin ta nufa ganin rufaida nakan bacci yasa ta dau mayafin ta saba akai ana daf da gabanin magriba tayi ficerwata Dan dama akwai wasu abubuwan bukata datake so tayi amfani dasu .


Kiraye kirayen sallahn magrib yasa Da kyar rufaida ta bude lumsasshun idanunta da suka riga sukayi ja duk sun kumbura tsaban kukan datayi

Wani Nauyi idanun suke mata,ahakan dai ta shiga warasu ta shiga sauke su a hankli akan bugun kwanon dake dakin tana famar kallon sama can can tana sauke nishi mai zafi kamar wacce zata dauke ranta a take.

Wani kakkarfan Ajiyan zuciya ne ya kufce mata,a hnkli ta runtse idanunta tayi tsam da shi tana fesar da numfashi cikin dada son karfafa imanin dake cikin xuciyanta musammn game da hukuncin data soma yankewa ayanzun na dagewa da ibada dakai kukanta wajen Allah da

Please Login or Register in order to submit comment