Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Wani tambayar
,shhhh ta furta tana kallon cikin kwayar idanun rufaidar da pleading eyes da alaman tanajin tausayinta sosai,but it's seems like thy are being watch in a control room,matar tana sana da cewa Duk Wani motsin su ana kallo.
Cikin sigarr rarrashi ta Dan shafa kanta still bata ce mata uffan game da tambayoyin datayi mata ba,maganin data shigo dashi kawai ta bude ta miqa mata tace mata tasha,a Babu yadda ta iya ta amsa ta sha din, daga Nan ma amai ta dingaji daya tsananta mata sai ta mike ta nufi toilet kafin ta dawo tazo ta tarar da dakin babu kowa alaman har matan ta fice abunta.

cike da sanyin jiki ta karasa zuwa kan gadon,kwanciya tayi a sulale Cikin tsananin rasa abunda ke mata dadi,Wani lumshe idanunta tayi cikin tsananin rudani tabbas yau da Ita ba musulma bace da tuni ta yanke hukuncin kashe kanta kodanma ta huta da azaban rudanin datake ciki

Haka tayi ta zama acikin wannan yanayin,by 7pm ta shiga alwala tazo ta samu har an aje mata abincin ta,kwata kwata bata iya ci ba haka ta dinga kwaxa amai, da misalin 10pm na dare,tsantsar azaba da gajiya ne yasa bacci mai nauyi ya mata bazata bacci ya dauketa,Wani irin juyi take cikin baccin daga Gani kasan ba dadinsa take ji ba,after like 30 mint Wani sabon ihun ya tayar da Ita..
A mugun razane ta farka rike da kirjinta dayaketa bugu kamar zai fita bakinta dauke da kalmar innalillahi wa inna ilaihi rajiun..

"Wayyo Allah na..
Wayyo Allahna
Sai kuma numfashi da uban nishi mai mugun tada hankli da kada ruwan ciki dayake biyo baya.

As usual jikinta na rawa rawa ta iso har bakin door din ta kasa kunnunwanta
Tana dada Jin ihun

Zama tayi abakin kofar ta jingine bayanta kadan tana kkrin cusa kanta a tsakankanun cinyiyonta Jin tsabar yadda zuciyarta yake bugawa da azaban tsoro..

Dan kadan ta motsa jikinta da alamar tana shirin gyara zamanta sai kiiiiiiiiiiii taji alaman budewar kofar a mugun firgice ta miqe tsaye tamkar wacce zatayi tumbul taci da kasa Tabi Ta matsa da mugun sauri tayi can da baya

Wani irin bugun balai kirjinta yake sai diffff difff diff numfashinta yake sauka kamar wanda zai dauke gaba daya,gani tayi kofarta ya Budu kadan Amma har yanzu babu wanda ya shigo ciki,tafi mintina arbain cikin tsananin tsoro tana tsaye tana ta kallon kofar,ganin kamar babu motsin kowa anan kusa yasata tayi mastering courage da kyar ta fara karasowa gaban door din ahankli a hankli...

Tafiya take tanajin yadda bugun kirjinta yake mugun karuwa,tsayuwar cak tayi a bakin door din dan da kyar take iya motsa hannun ta dake famar rawa Kar Kar kamar wacca aka zubawa kankara

Lekawa kadan tayi ganin babu kowa yasata taji relieve,sai ta dubi kofar da kyau, da alamar tun safe da matar Nan tazo fita ne ta manta ta barmata kofar ahaka a bude,she dnt even notice,sai taji Wani irin haushin rashin sanin Hakan ne yakamata,ai da tuni ta ficce waje ta nemawa kanta hanyar guduwa agidan saidai Duk abunda zai faru ya faru...

Kara lekowa tayi ahankli tana famar zaro idanun ta waje Wani zuru zuru tayi da idanun tamkar wata babban barauniya,cikin dabara ta sulalo jikinta ajikin kofar ta fice dama ta dade da burin son sanin me ake aikatawa ma mata agidan Nan kuma Nan din ma ina ne?sai kawai ta yanke hukunci aranta cewa koma menene ma ita guduwa kawai zatayi..

Tafiya ta somayi a sulale tanamai maida hanklinta ga Inda tafiye Jin waccan ihun,Wani irin tsorone yake kassara mata gabobin jiki,ko inanta karkarwa yake Amma Sam bata fasa ba,thank goodness kafafunta babu takalma bare ajiyo Wani motsinta

Kimanin kofuna 5 ta wuce wanda taga dukansu irin nata ne wanda take ciki saidai harta wucen bataji motsin kowa ba,tsayawa tayi cak a kofa na shida Jin yadda gabanta yayi mummunan fadi,daf kofar data tsayan taji Wani abu kamar alamar motsi motsi

Firgita tayi Kamar dai zata je jikin kofar atake sai taji kafafunta sun mata nauyi,ta dade a Hakan sannan tayi mastering courage ta karasa daf da daf,hannun ta dake rawa rawa takai jikin kofar sannan ta aje kunnen akai tana jiyo sautinsu haka ta dinga jiyo me ake cewa

"It's a gang rape"..

"Wayyo Allah, gabanta ne ya wani irin bugawa da tsananin qarfi,take kanta yayi kara kamar wanda aka dandatsa mata shi da katon guduma..

Dauke numfashinta tayi chak ta kuma yi tsitttt tana kan Jin conversation dinsu,wanda sukeyinshi cikin izgili da mugunta can ta shiga girgiza kanta a firgice tuni idanunta suka kawo ruwa cikin ranta tace..."Ciniki?
" siyar da Ita?
Innalillahi Masu siyar da mutane ne

Bata masan lokacin data janye jikinta daga jikin kofar a mugun firgice ba,daga kafafunta tayi alaman zata bar wajen Wani azaban karane ya razanata mai dauke da tsananin ciwo da azaba wanda ya fito daga cikin dakin,tunma kafin ta sauke numfashin ta dake shirin barin jikinta kafartan ta yaja ta da jiri ta fadi tim akasa,tabi ta tashi agigice,...."kuyi min rai". ...Dan Allah ku kyaleni...wayyo Allah na..na shiga uku...mutuwa zanyi
Dan Allah kubarni
Wayyo Allah na shiga uku..Allah ka dauke raina in fita daga wannan azabar

A rikice rufaida ta soma ja da baya idanunta sun wanke fuskarta da uban hawayen tsoro sautin ihun ya gama cike mata kunnenta da kwalwakta,itama ji take kamar ta kurma ihun saidai bazata iyama bude bakinta ba sakamakon barin dayakeyi karkar,da kyar ta miqe tsaye
Cikin tsananin sauri ta juya ta cigaba da tafiyarta gaba cikin neman hanyar da zata tsiratar da kanta gaba daya hayyacinta baya jikinta

Batako yi nisa ba tasoma jin alamar wani motsi,tsayawa tayi cak,zuciyanta na difff difff ji take kamar kurwanta zai fito waje,Jin kamar mutum ne yake shirin tunkarota yasa ta Firgita ta deba a guje saidai bata iya tantance inane kofar dakintan ba,Nan danan ta mannu da bango cikin tsananin razana ta dauke numfashinta gaba daya,ji kawai tayi an finciko ta daga Nan sai bata karasanin meya faru ba sai washe gari data farka ta tsinci kanta awani rufaffen daki a shimfedeta akan gado..


A hankli ta shiga wara idanuntan da suka kumbura sukutum sukayi Wani luiii da su tamkar na wacce take shirin gangarar mutuwa.

Gabobin jikinta da zuciyarta gaba daya sun nakasa da azaban razanar datayi ji take kamar ta dauke numfashinta ace mata batama duniyar..

Saidai ganin matar Nan akanta datayi ne yake shirin daidaita mata hankli,da kyar ta iya bude bakinta sautin maganan ta ya shiga fita a karkarye
,"k .u..yi ha..k..uri
Da..n Alla..h kuyi hak...uri,wallhy ban muku komi ba..
Ku kyaleni na tafi gidan mu,wayyo Allah na umma na wayyo umma na shiga uku wallhy kasheni zasuyi..

Matar batace kala ba saima kallonta datakeyi ganin bama a hayyacinta take ba.

Wani irin kukan azaba da tsananin razana takeyi jikinta na tsananin karkawa,da dukkan zuciyarta take kukan tana magiya tana mai rokon amata rai..

Can matar ta taho kusa da ita,batare da cewa komi ba ta dagota ta zaunar da Ita,kallon 2 snds ta mata sann..tace
"..Ke, kiyi shiru...ina rufaida bata ma gane me ake furta mata kukan kawai takeyi
"Ki yi shiru mana
Wai so kike akamaki?
Shirun tayi atake sakamakon tsawar da matar ta daka mata
....
Dan shiru tayi sannan ta kara fashewa da Wani irin razanannen kuka mai tsuma zuciya da karya garkuwan jiki,ta cigabayi a hankli,
can sama sama numfashinta yake harbawa kamar wanda zata shide, sheashekarta ma da qarfin sa yake saukowa Dan hatta idanunta bata iya budeshi tsaban yadda ruwan hawaye ke ambaliya akan fuskartan yana gangarowa
,cikin tsananin rawan Murya da azaban razana ta kalle matar da Wani irin salon magiya "Please I want to go home ...
Dan Allah ki fitar Dani anan
Ai..ai...ai naji abunda akeyi acan dakin,sanda ta Wani jaaaa nunfashi ta kara fashewa da kuma sannan ta cigaba wallhy
Bana son ayimin fyade,ni ban taba kwanciya da namiji ba,and
..and..Its asif it's a gang rape,Bayan Nan kuma naji sunce sayar dasu kukeyi Nima kenan Haka za'ayi min?
Na roke ki da girman Allah ki fitar Dani agidan nan
Inkinsan darajar iyayenki ki taimaka min,Ni Wallhy tsoro nakeji,Hala ma mutuwa zanyi ko..kukan ta cigaba da yi asif she is crying her last tabi ta rude gaba daya,kallo daya matar tabita dashi sann ta dauke kanta ta miqe tsaye tana mai cigaba da kallonta cikin Wani yanayi mai wuyar fassara,A hankli Tace ki saurareni yarinya ki fahimce cewa Anan babu mai kubutar dake,saidai inkika bani hadin kai zan iya taimaka miki,Jin Hakan yasa rufaida ta miqe tsaye itama tana bin matar da kallon rudani
Tace.."babu mai kubutar dani?,hawayen da suka makale a idanunta tuni suka gangaro,sai tayi sauri ta sulale kasa kan gwiwarta
,"Dan Allah ki tausaya min,kefa mace ce,ya zakiji in akace ni yarki ce ko kanwarki ko wata yar uwanki?ki duba halin danake ciki,Dan Allah ki fitar Dani a gidan nan na koma gidanmu,"..kiyi min rai ki taimakeni na koma wajen umma na..
Matar ta taso Adan kufule nace
Bakiji menace miki bane? ta tambayeta sounding pissed Rufaida tana shiru bata dagoba tukun ta cigaba da kukanta kanta akasa,a hankli ta shiga kakkame jikinta ta mamaye kanta cikin wani yanayin kunci gwanin ban tausayi,can Matar tace"I'm willing to help u but you have to cooperate..ki dena wannan kukan naki Dan baida amfani, kisa aranki cewa Babu yadda zakiyi ki kubuta anan gidan,Kisani Duk Inda kikayi ana kallonki,ko yanzu ma sunsan Inda muke inma baki sani ba..Kuma yanzu haka ina mai tunasar dake cewa kin jefa kanki ne acikin babban barazana, meya fitar dake a dakinki?

Anan Rufaida ta dago kanta da kyar cikin shesheekar kuka tana famar girgiza kai tace
...NI fa Guduwa zanyi..

Wani Dogon numfashi matar taja tana kan kallon ta very closely...
Ganin yanayin ta da abun tausayi,d girl is absolutly terified ita haka kawai taji aranta tana son taimaka mata

Kofar fita ta nufa ta dan leka waje kadan,tafi 5 mints awajen abkin kofar sannan ta kulle kofar da keys sai ta dawo ciki cikin sauri,zama tayi a Inda rufaidar ta kife kanta da gwiwa babu abunda yake tashi sai sautin kukan ta da saukar numfashin ta mai qarfi.

A hankli ta shiga shafa mata kai sannan ta soma peting bayanta tanamai rarrashinta batare da tace mata uffan ba..sunfi minti goma haka Amma babu abunda ya sauya a bangaren rufaida kuka kawai take zuciyarta cike da ambaton Allah

"Wani Huhhhhhm matar ta sauke Ajiyar zuciya da kamar bazatayi magana ba cen kuma sai tayi
Tace
Yarinya mai sunanki
Da kyar rufaida ta Dan dago tace
Sunana rufaidah
Idonta taf da ruwa Tace Allah sarki rufaida..
Toh ke Meya ya hadaki da Mutum kamar alhaji bature
Har kika yadda kika aure sa wato Kinga kudi ko?rufaida tace.."A'a...ta dakatar da ita cikin sauri da iya gaskiyar dake cikin kwyar idanunta,"nifa ban sanshi ba,ko ganin sa bantabayi ba,wallahy mahaifina ne yayi min auren dole,kuma haka yay ma sauran yayu na..

Runtse Ido matar tayi sannan ta bude a hankli
"Auren dole?
Kina nufin bada son ranki kika zonan ba?..gyada mata kai Rufaida tayi, da sauri"..I'm sorry..matar tace muryanta dauke da tsananin tausayin ta

Nan ta gyara zamanta tana duban ta very closely,.."Tace,
Yawancin matan da kikejin ihun su anan gidan mafi akasari kwadayin su Dana iyayensu ne ya jefo su...To ke maisa iyayenki basuyi bincike akan alhaji ba?kinsan shi waye kuwa?...cikin karajin mummunan fargaba rufaida ta girgiza kanta tace A'a,ai shi baba babu ruwansa,baiya bincike,cikin jinjina kai matar tace tabb
"Toh Alhaj bature da kike gani shi asalin tsohon Dan safara ne.,rufaida ta dago a rude "bangane ba?safarar me,matar tace ina nufin Baida Wani sana'a a rayuwansa daya wuce saida mata da yara kanana,wanda za'a na sana'ar karuwanci da su Dan ana kawo masa kudi,Duk wanda ya kawota Nan to sana'ar da zaa dorata kenan,kuma babu mai kufcewa Hakan,in harma jininku ya hadune ya turaki aikin bauta agidan wasu ko kasuwa ko kamfani depending on wanda zai siyekin..
A mugun firgice rufaida ta miqe tsaya Jin abunda matar ta furta wanda yake barazanar buga mata kwakwala
Magana zata furta matar ta miqe tsaye cikin dakatar da ita da Wani irin yanayin warning a muryanta
Tace" don't even try it,He is very wealthy and well connected,har cikin jamian tsaron kasar nan yana da ido da kunne,a Duk Inda kika shiga saiya sa an kamoki,shiyasa ma nake gargadin ki daki kama kanki ki nitsu tun kafin ki jawo ma rayuwanki kisan wulakanci da axaba
Dafa kafafunta tayi ta juya da Ita Suna fuskantar juna
"Ai kinji irin ihun da sauran matan sukeyi ko?If u dare try to run away,zai saka kattin maza su dagargaza gindinki till ure numb,inkina da rashin kunya da taurin kai kuma su kara maki da duka in most cases thy will use electric shock on ur vagina inbaki iya riqe azabar ba ahaka zaki mutu aje abawa karnuka namanki suyi bidiri.

So now will u cooperate or no?





*™✓SHADE OF RUFAIDAH*


_BY_
_SURAYYAHMS_


_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_


BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.


Part1:chapter 10
*The devil serve my breakfast.*


A mugun firgice rufaida take kallon bakin matar ayayin da koinanta ya shiga karkarwa mai tsanani koinanta ya nuna alaman firgitarwa,bude bakinta tayi da niyyar bada matar amsa atake sai kuma taji Wani irin nakason zuci ya mamaye ta,firgice ne ya rinka bin jinin jikintta har izuwa sassan gabobin jikinta sai tayi lagwas jikinta babu kwari tamkar wata nakasashiya, cikin yanayin rasa me zatayi da rayuwarta ta sulale kasa rigib ta kifu a kan gwuwarta,Wani irin razanannen kuka mai tsananin tsuma zuciya da shiga jiki ne ya kufce mata wanda bata shirya masa ba

"Wayyo Allah na...
cikin Wani mayuyaci hali Ta riko kanta tana jujjuya shi cikin tsananin daburcewa da zaucewa mai haukatar da gangan jiki,da qarfi ta furta
"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun..
Wani irin rawa
Koinanta yakeyi jikinta na shaking tamkar wace aka jonawa electric shock,alamun karayar zuciya da nakasa ne ya gama bayyana ayanayin ta musamman muryan ta daya dishe ya kakkarye ya kuma fita daga na mutum mai sauran hankli
,hannun ta da kafafun banda azababben bari babu abunda sukeyi, kamar wata tsohuwar datayi shekaru dari haka ta nakasa gaba daya ta kasa iya amfani da sassan jikinta gwanin ban tausayi..

Wani irin runtse idanunta tayi tana kuka mai zafi cikin yanayin tsumayi kanta na rawa alaman tana cikin yanayin tsananin neman temakon gaggawa daga alkaryar wannan mummunan qaddara dayake shirin tunkarota...

Matar ne ta matso kanta tana mai cigaba da cewa
"Rufaida,ba kukan fa zakiyi ba
Just get up and hear me out ki tabbata kin saurari abunda zan fada miki da kyau
Har yanzu rufaida bata dago ba tayi mata alaman tana sauraruntan da kai..Tace washe gari da safe Zamu fita wajen sa tare da ke"..u were being watched daxun da kika fice so he is suspecting you now.."idan ya tambayeki meyasa kika fito din,karki amsa masa".
In kuma ya matsa sai kice baki da lpyane ..Ni kuma zan sha bakinki ince masa Kina neman sane,did u understand?...
Rufaida ta gyada kanta,kamo yatsun hannunta matar tayi cikin nuna damuwarta tace
But u have to remain very calm agabansan in ba haka ba zai tabbatar da cewa guduwa kike son kiyi kamar yadda suke harsashe daga Nan kuma bazan iya kareki ba

Ahaka suka tsayar da maganan,kowa dai yay shiru after like 4hrs sai gashi har kirar asubahi ta riske su,fita waje matar tayi na mintina kadan kafun ta dawo tazo ta samu rufaida harta idar da sallah sai famar kuka takeyi wanda zai tabbakar maka cewa takai kukanta wa ubanginta ne
Maganganun da sukayi jiya ta kara maimaita mata
So Bata jira rufaidar ta amsa ba tayi saurin dagota tsaye suna fuskantar juna hannunta ta kawar gefe ta shiga share mata hawayen dake kan bulbuluwa daga idanunta"...u have to act very well in har kinason rayuwarki..
Ki daure...a tsorace rufaida ta gyada kanta,cikin tsananin sanyin jiki ta shiga share hawayentan a matukar sanyaye wanda Da kyar suka tsaya,matar tace "muje?...ta gyada kai...sun fara tafiya kenan taga rufaidar taja ta tsaya Nan da nan matar ta juyo tana binta da kallon tuhuma?cikin sanyin yanayi tace"..meyasa kikace nayi Hakan?dame Hakan zai kareni wajen kubutar dakaina daga Nan gida?shin in na amsa cewa guduwa zanyi kashe ni zaiyi?..matar tadanyi shiru can tace 'a'a..bakashe ki zaiyi ba,Amma zaki kwashe azaba irin na wayancan matan,da sauri rufaida ta kalleta sai kuma ta kaudakai gefe bata kara cewa uffan ba

Fita sukayi a dakin matar tana gaba ita tana biyota a baya after like 15 steps saiga wata stairs agaban su,Nan ma basu dade akai ba suka billa cikin wata hadaddiyar falo mai kyau da tsari saidai bame girma ba.

Mutum suka gani a zaune,wearing suits top da bakin wando Duk kanshi ya ccinye da sanko ga Wani uban bald head dayake rabza sheqi tamkar anshafai mangayda,Wani irin faduwa gabanta ya karayi bata kuma dago kanta sama ba,kasa ta cigaba da kalla har suka iso gaban mutumin wanda shikadai ne awajen kuma basai an gaya mata ba sosai jikinta ya bata cewa shine mijin nata wato Alaji BATURE..

Wani hade ransa yayi Cikin harshen yaren da bata tabaji ba ya dakawa matar tsawa,Nan danan matar ta shigayi masa magana da alaman bayani take kanyi masa muryanta harna rawa rawa tana cikin hakan sai ya maida hanklin sa gaba daya ya koma kan rufaidar Juyowa yyi da Wani irin salon kallo mai tafe da tsantsar mugunta...
Still yaren ne a bakinsa,it's actually sound like a local slangs na baqaqen chadians,meaning
"kinki ki fadamin gaskiya Fatima,Shin meye yarinyar nan tasani game Dani? Guduwa zatayi ko?
Wat u did u ask her about jiya Dana aike ki wajenta?

Matar wanda itace akecewa Fatimar cikin harshen yaren tace "Na rantse maka alhaj iya gaskiyar kenan na fada maka"The girl is totally innocent,"
wannan kalman kawai ta fadi a fili cikin harshen turanci kafin ta juya ta cigaba da yare,"bayanai ta rinka masa cikin kissa irinna mata,tace masa yy duba da yanayin lamarin Yau kwanan rufaida sha hudu bata gansa ba kuma bata fahimce komi game da su ba,she guess dats why she is outside jiya tace kuma Ina mai tabbatar maka dacewa ba abunda kake Zato bane,she can't even run away cos she is helpless zazzabine ajikinta sosai,kuma da alamu batama San kai waye ba..

Wani shiruu yy alaman yna nazari akan abunda ta furta can dai yace hmmm,Sai ya maida mata wasu kalamai masu nauyi masu nuna alamar rashin amincewarsa da ita,daga karshe kawai ya sallameta yace abarsa shikadai da rufaidar.

Matar bata so Hakan ba ta fice tundaga yanayin tafiyarta yy murmushin fahimtar komi da suke ciki,wani haushi yakeji aransa

"So who is dis girl da har fatuma zata min karya akanta?
Tunda suke da Ita bata taba nuna Jin tausayinta ga wata ba bare ajega ta tsaya mata but why dis bitch?,a zuciyarsa yaketa raya Hakan ayayin dayake matsowa kusa da Inda rufaidar take tsaye..

Wani irin rawa jikinta yake tsaban tsoro, ji take kamar zata saki fitsari Wani kuuuuu hanjin cikinta yake bada sautin curewar da yayi da tsananin fargaba

But she knew she have to calm down a Dan dole ya zama ta nema makanta nitsuwa da sauki,she just can't imagine herself being totured with gang sex,da Dalilinta na son sanin me matar Nan zatayi nan gaba wanda zai kubutar da Ita...she is desprate..tana mutuwar son taga ta gudu tabar gidan.

Wani irin shuumin kallo yake mata har ya iso daf da gabanta,ganin kyaunta da hasken fatar jikinta masha Allah,tuni ya somajin rudewa da azababben Kwadayi,hakan yasashi rawar kafa sai famar lashe bakinsa yake kamar tsohon maye..

Wayar sa ya dago ya bude snn ya tura saqo,ya rubuta
"meye sunanta? Ya tura sakon ma fatima Dan shi baima sani ba,ko ince abubuwan dayawa bazai iya riqe Sunayen su ba,so within some scnd sai gashi har an maido masa amsa..."Rufaida"..kawai aka rubuta sai yy murmushi,kansa nakan wayar can ya dago fuskansa dauke da Wani irin munafukin Murmushi da yake marar fasaltuwa
.yace Hajiya rufaida
"AMARSU ta ANGO!..kinyi fushi da ni ko?tsam tayi da jikinta cikinwa yanayin kin dago kanta bare ta kalleshi,ya kara matsowa kusa daf,Wani Firgita tayi taja da baya Jin alamar hannun shi daya sauke akanta yana shirin shafamata kai,Hakan yasa ta dole ta Dan dago ta kalleshi sai sukayi Ido hudu da juna sunfi minti uku ahaka sannan ta dauke idanunta ta sadda kanta can qasa...yace rufaida?
"U cried ne?..Kukan me kikayi?..da kamar bazata amsa shi ba,but the man himself is looking like a phsycopath
Gaba dayansa tsoro yake bata,yy mata kama ne da irin mutanen Nan masu ciwon kisa ko ciwon mugunta, Dan kwata kwata bata gane yanayin sa ba ayanzu,he seems nice,happy and dangerous at same time,dauriyar da bata San dashi bane ya taso mata ta shigo sauke Ajiyan zuciya tana fidgeting yatsunta kanta haryanxu na kallon kasa,while trying to control her breath ta Dan dago
A hankli tace
"Ina kwana na?
Umm dama Bani da lpya ne jiyan saina fitta..Jin ta furta Hakan so confident and clean yasa shi sake wata yar karamar rudadiiyar dariya Yace wow
"Ayya am sooo sorry.. idanunsa stiff akanta kamar mayen da yake jiran go ahead domin ya hadiyeta ya cigaba da magana.

"Zo ki zauna muyi Dan hira ko?sai ya jawo hannunta abazata kuma da Dan qarfi ya turata gaban Wani kujera mai kamar dinning table saidai shi ba babba bane 4 chairs ne kawai biyu na kallon biyu,Adan dolenta ta zauna he care not about how she is trembling silently,sanda yaga ta nitsu sannan shima ya zauna ya kuma cigaba da mata kallon kurilla can Yace .
"Amarya Yakamata ace kinsan waye mijinki ko?bamu haduba tun bayan biki,na barki ne kidn huta dake mahaifinki yace bai shirya ba ya bada ke...yanzu kin amince Dani a matsayin mijinki?saiya fashe da wata muguwar dariya,irinta shashanci irin mai cin rai din nan,cikin yar dariyar yace
"Ai dolenki..
To ya kikace ?ya kamata musan juna ko?She cudnt hide her fear ta dago cikin sauri da kaduwa,muryanta na Dan rawa rawa
Tace alhaji"..ban ban fahimce ka ba?saita dan kuresa da ido,wani mugun yanayin razana ayanayinta tana mai maganan xuci"Meyake nufi da yakamata tasan shi?Wani mugun yawo ne yabita magwaronta wanda ya sauko mata har kan dokin xciyarta
Yay babakere

Lura da Hakan yasa sai bai amsa ta ba miqewa tsaye yayi yana cewa kiyi min afuwa nidai
"Nasan na tauye maki haqqinki shiyasa ma Nace Fatima ta kawoki da safen yau xanmiki bayani..,sai yadan juyo,amma
Jiyan wai Ina xakije?

Atake kuma ahnkli tace mai "babu".

Ya yatsina fuskar sa
"C'mon girl Tell me...ko har kin gaji da gidana ne?

Nan ta dago kanta da sauri dan sosai jikinta yake ta bata Wani abu mummuna game dashi,da kuma irin tambayoyin rainin hankli dayake mata da alaman so yake ya samu kwakwar dalili ko Wani tabbaci daga bakinta sabanin abunda Fatimar ta gaya masa dazu..

Fahimtar Hakan datayi yasa ta dade danne zuciyarta ta kuma bisine tsoronta ta kalle sa da kyau..tace
"Lpya ne bandashi
"I'm stuck.tun ranar aka kawomi nan,akace min kanada wasu matan da yara ya bangansu ba?Gidan yayi min shiru dayawa kuma banajin dadin jikina shiyasa ma danaga door dina abunda shine sai nafito..

Harta dasa aya baice mata uffan ba,Wani Irin kallon daya mata ya nuna alamar rudewrsa akanta he didn't expect this absolute courage from her sabida already ya riga yasan she is hiding something frm him ita da fatima,it's posble tajiyo Duk abunda suke ciki..
Tabe bakinsa kawai yayi aransa yana dada lura da Ita

Ganin abunda ta zabar makanta kenan tayi wasa da haklinsa yasa syima ya sake jikinsa ya shiga shararo mata karya yana cewa ai iyalansa basa Nan ne amma ya mata alkwarin cewa gobe gobe zasuzo daga Nan kuma zata fara normal rayuwanta a matsayin amaryan sa,Nan ma ya babbata hakuri
Yace ai yakan sa a killace ta ne sabida akwai maza masu lura masa da komi nashi anan gida kuma baiyarda dasu sosai musamman akan mace ba

He made this up sabida ko zai sata yarda cewa Hala masu aikin sa ne suke kawo mata dan Babu yadda za'ayi ya amince musu cewa ta fito har waje Amma bataji labarin meke faruwa agidan ba

He knew she knows and she is just hidding it kuma ya fahimce cewa kamr Fatima ne ta gargade ta.

Har ya gama babatun karairayin san rufaida bata dago ta dubesho ba kallon kasa kawai ta cigaba dayi na tsawon mintina batace dashi uffan ba..

Can da ya gaji sai ya miqe ya karasa gaban wata hadaddiyar microwave nan ya shiga warming abinci, shinkafa ne da Wani irin miya wanda bata sanshi ba it's seem like a continental soup
Bayan ya dumu saiya bude fridge dinsa ya dauko Wani abu kamar naman rago a lullube haka a yar lede ya

Please Login or Register in order to submit comment