Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kunna wayar ne.
Sun jima suna hira kafin ya ce mata zai kira video call anjima.
Aishatu ta ajiye wayan tana kallon Rabi'ah ta ce“Wai ina kika da'de haka¿â€
Rabi'ah ta zauna kusan Aishatu tana yamutsa fuska ta ce“Wlh cikina ya mur'da bari na tafi dare ya fara sai wani jiqon kuma. Ke kam bakya jimawa da waya.â€
Ta qarashe mgnar tana 'daukan wayan tana dubawa baqin ciki kamar zai kashe Rabi'ah da kishi.
Aishatu tai dariya ta ce“Wlh idan duk sati zan ce Ma'aruf ya siyamin waya zai siya min, sbd son da yake min, yanzu haka ya ce zai biyo min da wata rantsatsar Samsung Galaxy.â€
Rabi'ah ta ce“Allah ko? Tabb ai ke kam kin fimu morewa, Allah ya qara dan'kon 'kauna, ni kam na fasa auren wancan banzan can mai jiji da kai ba wani abin hannu yo kyau zanci dan ubansa.â€
Aishatu ta duma mata duka abaya ta ce“Wlh ki rufawa kanki asiri ba ruwana ah toh. Ai ni da kaina nasan Ma'aruf ya ha'du ga bai gajiya ashimfi'da sai dai kai ka gaji ga iya romantic kamar zan mutu nakeji sbd dad'in abin. â€
Rabi'ah ta matse qafafunta tanajin wani yammm jikinta tsabar jin son inama itace. Aranta ta ce“Wlh sai na aureshi naji abinda kikeji.â€
Takaicin jin labarin ya saka Rabi'ah miqewa ta ce“Toh ni na tafi insha Allah nida shigowa wannan gidan sai bayan aurena.â€
Aishatu ta ce“Wayyo ni babbar 'Kawa pls kiyi Ku tsayar da mgna kar azo ayi biki cikina ya tsufa na kasa ta'buka abin azo agani wajan auren 'kawata.â€
Rabi'ah ta ce“Nan kusa 'kawata karki damu bye.â€
Aishatu ta rakota ta saka Nura direba ya tafi ya kaita gida.
Ita kuma ta dawo ta fara kallonta Tv tana jiran Ma'aruf ya kirata.
*Tchad*
Ja'afar yana fitowa daga sallar isha, yay shirinsa cikin wata 'danyar shaddah mai kyau, maroon colour wadda Ma'aruf ya 'dinko masa, sosai tai masa kyau sai baza 'kamshi yake.
Yahuza ya kalleshi ya ce“wai ina zuwa ne kana 'kyalli sai ka ce ango?â€
Ja'afar ya shafi sumar kansa, ya 'dora hula wacce tai masifar masa kyau ya 'dan tauna le'bansa na 'kasa bai tanka su ba, ya zaro wayarsa ya fito yana latsawa. Jikin 'kofar gidan ya tsaya, ya dannawa number Rahma Kira.
Lokacin Rahma na wajan Abie 2 da farko, da ta shigo ba wata mgna suke sosai ba, amman bayan yaje yay sallar isha yazo, ya shiga bata lbri, yadda yake bata labarin wani makaho ya sakata dariya har takai ta riqe hannunsa tana 'kyal'kyalata dariya.
“Wayyo Abie 2 karka saka cikina ya qulle...â€
Dai-dai lokacin wayanta yay qara.
Duk number ba suna, jikinta ya bata Ja'afar ne.
Cikin rawan jiki tai picking call 'din ta manna wayar kunnenta tare da sallama.
Ja'afar daga can ya amsa sallamar yana lumshe idanunsa, cikin shaukin 'kaunarta ya kirata.
“My Qalbi! Muryaki sanyi ga da'di fiye da sarewa,gaki da tausasa murya. Wlh ina sonki,
so wani abu ne mai kyawu, kuma wani yanayi ne da mutum zai so ya dam'ke. So shi ne yanayin da kan sa ka ji ka a raye.
My Qalbi ina fatan kin fahimci cewa zan so ki har karshen rayuwata, sabida ba kin kasance budurwata ka'dai ba, ke ce Aminiyata, 'yar balarabiyata je t'aime. Ga ni nan tafe gareki tauraruwar mata, ki fito domin tarban masoyinki.â€
Rahma batasan lokacin da da'din kalaman Ja'afar suka sakata mi'kewa ba, ta fara taku cike da wani irin salo tamkar tana gabansa, murya atausashe cikin harshen French, ta fara maida masa martanin kalamansa.
“Habiby nah! Ina son jinka a kusa da ni, ta yadda numfashi na da naka zasu gauraya, ta yadda zan ke juyo sautin bugun zuciyoyin mu na fita a tare. Ina so mu kasance a tare har abada, Ina Son Ka!
Ana gane kyawun shuka ne idan har an gama ta da taki.
Tayaya za a gane sama idan har babu 'kasa?
Kamar haka ne, farin cikina zai yi wuyar bayyanuwa matuƙar ba ma tare da juna.
Na kan shiga damuwa a dukkan lokacin da na duba gefena ban gan ka ba.
kullum na kwanta bacci, na kan yi mafarkin ka zama uban ‘ya’ya na, ni kuma na zama mata a gare ka. Sai dai na san iya mafarki ba zai wadatar da ni ba a bisa kulawar da nake tunanin samu daga wajenka. A saboda haka nake fatan mafarki na ya zama gaskiya nan kusa idan ubangiji ya amince mana Ina Son Ka! Habiby nah, Allah ya kawo min kai lafiya.â€
Ja'afar dukkan illahirin jikinsa rawa yake, tsabar ru'dewa da kalamanta, sosai yake jin 'kaunarta fiye da komai aduniya.
Manyan kyawawan idanunsa masu lumshewa ya bu'de yaja dogon numfashi ya ce“My Qalbi 'yar balarabiyata ina sonki ganinan tafe bye.â€
Ya katse kiran.
Idanunsa ya firfito da su waje sakammakon ha'da idanu da sukayi da Ibtisam, tsaye gabansa dukkan illahirin jikinta zanzana yake wata irin zufa ta wanke mata fuska tamkar an zuba mata ruwa.........!
2/12/22, 20:44 - Buhainat: _*DATTIJON ARZIƘI*_

25&26

_*My Sisters Don Allah Don Darajar Annabi Karki Karanta Idan Baki Biya Ba, Na Ku'dine Idan Kinga Yana Yawo Na Satane Ga Hanyar Da Za Ki Samu Naki Akan.😟👉ðŸ¼300N +22796515805*_

Wani irin azababban numfashi,wanda yake dab da barin gangar jikinta. Ibtisam ta janyo shi da qarfin tsiya, tamayar da shi mazauninsa, da kyar ta ha'diye wani yawu mai 'dacin gaske, still idanunta cikin nashi.
cikin fitar haiyaci tana nuna shi da yatsarta jikinta na kyarrrma ta ce.
“Ja'afar! Kanada wacce kake so anan Tchad? Me yasa baka fa'damin ba ka canza ni amatsayin abokiyar rayuwarka? Har na tako 'kafata nazo wajanka, na za'beka . Tabbas ka nunamin halin maza, kuma ka koyamin hankali ka tashe ni a bacci, tabbas na gode sosai Ja'afar ina maka fatan alkahiri.â€
Ta qareshe mgnar tana danne kukanta ta sakar masa 'kayataccan murmushi ta juya zata tafi, wanda dakyar take ganin gabanta, wani irin jiri ya kwasheta, luuuuu zata zobe, Ja'afar yay saurin tarota ta fa'do jikinsa, ya riqeta yana fa'din.
“Ibtisam me kike hakane za ki jima kanki ciwo fa!â€
Kallonsa tai da kyawawan idanunta masu girma da suka rine lokaci 'daya sukayi jajir, ta sakar masa murmushi ta ce“No! Bazan jimu ba, jeka sai ka dawo bye.â€
Ta qarashe mgnar tana janye jikinta, anasa ta nufi kewayan su cikin jarumta, take tafiyar wanda bata wani ganin kirki, amman hakan jikinta yake motsawa tamkar tarwa'da, wanda zaka 'dauka da gayya takeyi, sai dai haka halittar tafiyarta take.
Ja'afar jikinsa ya yi sanyi, ya kafeta da idanu, yanajin sonta sosai, amman ya kasa ya bita ya rarrasheta.
Kansan ya sanya ya fita agidan ya bu'de motar Ma'aruf ya shige yaja ya tafi wacce daga can zai biya ya ajiyeta agidan sai ya dawo a taxi.
'Bangaran Rahma kuwa, lokacin da ta bar wajan Abie2 ta la'be tana zubama Ja'afar kalaman soyayya, cike da shauki Abie 1 na dab da shogowa yaji komai da take fa'dama Ja'afar.
Hankalin sa ba 'karamin tashi yay ba, sai da ya jira suka gama wayan, wanda numfashinsa yake barazanar 'daukewa, amman tsabar jarumta irin tasa, yay surin ri'ko hannunta, cikin fizgo numfashin sa wanda yake barazanar barin ruhinsa ya kirata.
“Ummina! Waye wannan? Yaushe kuka ha'du? A ina yake? Yaushe ya lalata miki rayuwa da soyayya haka?â€
Rahma ta kalleshi da 'kananun kyawawan lumsassun idanunta, fuska ba walwala tana qoqarin 'kwace hannunta, ta ce“
Shine za'bina sonsa nake idan ba'a aura min shi ba, komai zai iya faruwa damu, sabida muna son junanmu, Allah ne ya ha'damu...â€
Wata irin cakumowa Abie 1 ya mata ya matseta jikin bango ya 'daga hannunsa zai wanka mata mari Abie 2 ya riqe ya, yana fa'din subahanallahi! Abdul Majeed da kanka? Haba! Idan rai ya 'baci hankali ke nemoshi.â€
Ya qarashe mgnar yana kamo hannun Rahma da Abie 1 ya nufi falon dasu, ya zaunar da su.
Sai lokacin Rahma ta saki wani irin rikitaccan kuka ta riqe qafafun Abie 2 ta ce“Don Allah ku auramin Ja'afar kar na rasa raina wlh zan iya mutuwa ko mubar gari ni da shi...â€
Abie 1 ya furta.
“Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Ummi kina cikin haiyacinki kuwa?â€
Abie 2 ya kama hannayen Rahma ya ce“Ok ok! Munji zamu aura miki, yi yaushe kuka ha'du da shi?â€
Rahma ta tsagaita kukanta ta ce“Yaune Allah ya ha'damu.â€
Abie 1 and 2 suka tsirawa junansu idanu cike da abin al'ajabi jin wai yau amman ta haukace musu hakan?
Abie 1 zai magna Abie 2 ya katse shi ta hanyar cewa“Ok ba damuwa bari yazo mu tattauna idan munji asalinsa mun yaba da hankalinsa ba damuwa.â€
Ya 'karashe mgnar yana kamo fuskar Rahma ya ce“Kalleni 'diyar albarka.â€
Rahma ta kalli Abie 2 da guntin hawayenta.
Idanunta ya gwala sosai yana leqa qofofin hancinta, ya dawo ya cire mata hijabi, amman daga sama ya janye iya kanta, ya bu'de tsakiyar gashinta.
Mugun firgita yay sakammakon ganin abinda ya fara zargi.
Ayatul kursiyyu ya fara tofa mata da Amanar rasulu.
Ya gama ya jamata hijab ganin yadda jikinta yake 'bari ta cakume Abie 1.
Abdul Majeed ya sakata cikin jikinsa shima addu'ar yake tofa mata, tana wani irin zanzana. Abie 1 ya ce.
“Barta haka aikin babbane miji da matane akanta ayanzu bataji bata gani akan Ja'afar barta kar tai bacci har yazo ina son na fahimci meke faruwa gamone ko aiko mata akayi.â€
Abie 1 ya sauke 'katuwar ajiyar zuciya ya ce“Ya Allah ka dubeni ka kawomana sauqi cikin wannan musibar da take kunno kai.â€
Rahma ta janye jikinta tana hararensu ta ce“Sbd na za'bi wanda nakeso kuka laqabamin ciwon aljannu?â€
Abie 2 ya ce“Kiyi hkr je ki kawoma ba'kon naki abin motsa baki kafin ya iso anan za'a sauke shi.â€
Ya qarashe mgnar yana 'dauke wayar tata.
Cikin murna ta mi'ke tana fa'din.
“Ngd Abie2.â€
Ta fice.
Abie 1 ya bita da kallon mamaki.
Hannunsa Abie 2 ya riqe ya ce“Kabi asannu ayanzu zata iya maka mummanar tsana idan ta gano baka sonta da Ja'afar, sam bata haiyacinta mugayen she'danune akanta, ka bari muga yaron insha Allahu komai zaizo da sauqi zan rabata da wannan she'danu cikin kwana qalilan insha Allahu zata dawo Rahma sak.â€
Abie1 sosai ya shiga tsananin tashin hankali, amman jin abinda Abie 2 ya fa'da sai yaji ya samu nutsuwa da kwanciyar hankali ka'dan, ya jinkina kansa ya kasa cewa komai.
Wayar Rahma ta 'dauki ringing.
Abie 2 ya 'daga da sauri dan yana zargin Ja'afar ne.
Ai kuwa yaji yay sallama ya 'dora da harshen French, ya na fa'din.
“Tauraruwar zuciyata ga ni nazo ina 'kofa.â€
Abie 2 baice komai ba ya mi'ke ya fice.
Rahma falo ta isko Raiyana da Jaddatu and Hanan iman.
Zama tai can gefe tana ka'da 'kafa 'daya kan 'daya, ta girgizawa ba wanda ta kalla acikinsu bare ya samu arzi'kin mgna.
“Latifa!â€
Ta kira cikin 'dan 'daga murya wanda yake ba halinta bane.
Latifa ta iso aguje jin yanayin murya Rahma.
“Uwa 'dakina ga ni, barka da hutawa.â€
Rahma ta jinjina kai ta bu'de 'dan 'karamin bakinta ta ce“Abubuwan motsa baki za ki harha'do ki ha'do da bottle na faro gida kwalin drink 'daya, ki tabbatar jero duk wani abinda zai gani yaji sha'awar cinsa, sai ki kai 'bangaran Abie 2 bari naje na canza kaya.â€
Ta 'karashe mgnar tana mi'kewa ta kalli Jaddatu ta ce“Jaddati ya dai kallo haka kamar na canza?â€
Bata jira me zata ce ba ta nufi saman.
Latifa kuwa ta mi'ke ta nufi kitchen, domin cika umarnin uwar gidanta.
Jaddatu ta ce“Kai wannan abin ba na wasa bane, Rahma batada lafiya wlh ko shakka babu aljanu sun shafeta.â€
Raiyana ta ce“A'a Ummi wlh Rahma lafiyarta lau, qila wasane irin na jika da kaka...â€
“Ke! Raiyanatu ki min shiru banson hauka, kece amatsayin Uwa ya kamata ki gano wannan yarinyar ta canza har ubanta da take masifar so ta daina shiga lamuransa, ta daina walwala bata son shiga sabgoginmu kice tana lafiya?â€
Hanan taja dogon numfashi ta ce“Wlh batada lfy bari Abienta yazo.â€
Raiyana taji hankalinta ya tashi karfa su 'bata mata shirinta tun ba'aje ko ina ba.
Amman sai ta cije tace“Ai kuwa idan hakane bamuga ta zamaba Ummi.â€
Jaddatu ta kalleta ta watsar ta ce.
“Ai naga yanzu atsaye kike.â€
Rahma ce ta fito cikin wata rantsatsiyar Abaya blue mai adon stones ta mata mugun kyau sai baza 'kamshi take, tana sauri sbd ta manta wayarta acan.
Da kallo suka bita har ta 'kullema ganinsu.
Abie2 yana fita ya saka aka bu'dema Ja'afar 'katon gate 'din ya shigo da motar ciki.
Bayan yay parking ya fito yana kallon irin girman gidan da tsaruwarsa.
Amman kasancewarsa mutum mai masifar kamun kai da basar da abu kallo 'daya yama gidan ya kawar da kansa, ya sake danna kiran Rahma.
Abie 2 ya 'daga da sallama yana isowa wajansa ya katse kiran ya basa hannu.
Ja'afar ya rusuna cikin girmamawa ya gaishesa.
Abie 2 ya yi matuqar mamaki ganin Ja'afar baqar fatane, ba ma shi ba shine yaron da ya ta'ba bugar masu mota, toh me hakan yake nufi? Shi dai alokacin yaga basu nuna sun San juna alokacin ba.
Fuska ya Saki ya amsa gaisuwar ya Kamo Ja'afar ya miqar da shi, ya ce“Ja'afar ko? Sannan kaine kwanaki ba'ama fi sati biyu ka bugi motar muâ€
Sai lokacin ma Ja'afar ya tuna.
Kai ya jinjina cikin girmamawa.
Abie ya ce“Tin yaushe kuka ha'du da Rahma sannan zan maka tambaya tsakaninka da Allah me kamata wanda idanunta suka rufe akanka, har bata son kasancewa damu yanzu?â€
Ja'afar ya ce“Ni kuwa me zan mata? Wlh ban mata komai ba, ni asalima yaune Allah ya ha'damu amman sai mukaji kamar daman can mun jima, kuyi hkr don darajar Annabi Abba Ku bani Rahma na aureta karku bi cewar ba jansin mu 'daya ba.â€
Abie 2 ya ce“Dan Allah sunkuyo ka'dan naga kanka.â€
Kasancewar Ja'afar dogon namiji ne ingarma, Abie 2 bazai iya ganin kansa sai ya rankwafo.
Ja'afar bai musa ba, ya sunkuyo da kansa.
idan ba idanunsa suke masa gizo ba tabbas abinda ya gani akan Rahma shine akan Ja'afar, toh idan hakane waye ya yi aikin nan? Me hakan yake nufi? Abie ya shafi kan Ja'afar, aransa ya ce“Ina buqatar dogon nazari da wurudin dare na kaima Allah kukana ya nunamin abinda nake son gani acikin baccina.
Azahiri ya Kama hannun Ja'afar ya ce“Muje ciki.â€
Abie 1 na zaune ya buga tagumi suka shigo da sallama.
Kallonsu yay yana amsa sallamar, ya mi'ke tsaye.
Abie2 ya ce“Karkace komai insha Allahu komai zai warware basa hayyacinsu, dan haka mubasu lokaci qalilan mu bisu da abinda sukeso ka cije ka daure karka mu sa musu.â€
Abie 1 ya koma ya zauna.
Ja'afar ganinsa da kamar Rahma sosai afuskarshi ya gano mahaifinta ne.
Ya zube yana gaishesa.
Amsawa yay ya nuna masa wajan zama.
Ya zauna.
Latifa ta shigo da sallama ta dire babban tray da ta shaqo da abubuwan motsa baki da ruwa and drink.
Ta tsiyaya a cup ta beqawa Ja'afar ta tafi.
Abie 2 shi kawai yakema Ja'afar hira yayin da A 1 ya sadda kasan zuciyarsa tamkar zata tarwatse yakeji.
Rahma ta shigo cikin sauri tana mai fito da damuwarta kan fuskarta, sbd tasan Ja'afar ya kirata.
Tiris taja ta tsaya ganinsa zaune.
Wani irin farin ciki ya baibayeta sai lokacin ta saki fuskarta har batasan lokacin da ta kirasa.
“Habiby nah oyoyo.â€
Dukkansu suka 'dago suka kalleta.
Ja'afar ya sakar mata tattausan murmushi, abinka da aikin jinnu bai damuba da gaban iyayanta yake cikin zazzaqar muryasa ya ce“Oyoyo My Qalbi.â€
Zo zauna kusa dani gasu Abba nasan bazasu hanamu auren juna ba.â€
Abie 1 idanunsa sunyi masifar yin ja kansan yayi wani irin mugun sara masa atake jijiyoyin kansa suka fito sukayi ra'dau² wani irin jiri yaji yana 'dibarsa azaunen, bakinsa 'daci yaji maqoqwaronsa take ya bushe, hakan ya saka ya kwantar da bayansa akujeran ya runtse manyan fararen idanunsa da suka zama kamar gauta. Ahankali 'dan 'karamin jan bakinsa yake motsawa, ya shiga kiran sunan Allah.
Rahma ta iso ta zauna kusa da shi tana sakin tattausan murmushi, suka qurama junansu idanu.
Abie2 ya ce“Ikon Allah! Wannan wane mai 'daukan alhakin ne yay wannan abin mai ha'darin gaske?â€
Abie 1 ya bu'de idanunsa cikin dauriya ya ce“Pls Abdulmajid kayi wani abin tin ban rasa raina ba.â€
Ya miqe tsaye ya zuba hannayensa cikin aljihun wandonsa ya nufi hanyar fita.
Rahma yaji ta rungumeshi ta baya tana kyalkyala dariya ta ce“Abie Ngd zaka auramin Ja'afar ko¿â€
Murmushin yaqe yay ya cireta ajikinsa ya lakaci hancinta ya ce“Eh jeki zauna Abie 2 ka kula da kasancewarsu har ya tafi.â€
Ya juya da sassarfa yabar falon.
Cikin farin ciki ta dawo ta zauna suna firasu su uku, Abie 2 na qara musu 'kwarin guiwa sbd yasan idan Allah ya yarje masa matuqar daman ba 'kaddara aurensu bace ahaka toh tabbas zai rabasu da shai'danun aljannun nan.
Abie yana fita ya shige wata narkekiyar mota qirar Jeep 2021 ba'ka shi 'daya ya fizgeta ya nufi gate yana zuba uban horn. Megadi sanye da uniform, ya wangame masa gate jikinsa na rawa, ya sulala motar aguje ya fice daga gidan.
Security's 'dinsa na ganin haka suka shiga mota suka rufa masa baya.
'Bangaran Ibtisam ranta ya yi masifar 'baci atake taji matsanecin son da takema Ja'afar ya riki'de yana zama tsana mai zafin gaske dan ya gama yaudarata.
Bayi ta shiga ta ci kukanta ta gode Allah ta fito ta shiga 'dakinsu kamar abin arzi'ki ta bu'de Jakarta ku'din da Ja'afar yake bata ya ce“Ta dinga siya abinda take so ta kwashesu dukkansu ta 'kirga ta ga tsaf zasu isheta komawa Niger.
Hamdala tai ta 'kullesu jikin kallafinta ta 'daura a'kugunta ta sanya dogon hijab, ta goge lambobin da suke cikin wayarta baki 'daya ta ajiye wayan sama Jakarta dan tai al'kawalin bazata tafi da komai na Ja'afar ba.
Fitowa tai Baba mai taxi na zaune Falmata na masa fifita yana con abinci, sbd zafin da aka fara. Bintu na zaune.
Ibtisam ta rusuna cikin 'boye damuwarta ta ce“Baba zan amso magani nan kanti cikina na mur'dawa.â€
Baba me taxi ya ce“Subahanallahi ai kuwa tsamki ba da'di leqa ki gayama Ja'afar sai kizo muje asibiti zaifi akan wannan maganin katin ban sonsa.â€
Cikin murna da alamun nasara ta amsa da “Toh Baba.â€
Ta miqe ta fara tafiya Falmata na cewa.
“Sannu Ibtisam tsamki ba da'di Allah baki lafiya.â€
“Ameen†ta amsa ta fita.
Cikin sauri ta fice tana addu'ar karta gamu da Yahuza ko Harisu.
Ganin ta karya kwanar gidan ta sanya gudu sosai take gudu na uban mamaki, har ta kawo bakin titi ta samu taxi ta shiga tana maida numfashi ta ce“Babbar Tasha zamuje.â€
Me taxi yaja suka tafi.
Su na dab da isowa tashar motar, wanda Abie shi kuma yake zuba uban gudu ba qaqqautawa, sam baima san Inda zaije ya samu nutsuwaba, sam bai lura da mai taxi na gabansa ba, sai da ya qureshi ya furta “Ya Salam!â€
Ya na qoqarin taka baurki yana zuba horn dan mai taxi ya kauce,tinda burkisan yaqi taku sai ji kake Kauuuuuuuuuuu ya bige mai tasan ta baya, motar ta kife 'kasa tana gangarawa gefen titi, lokacin mai babbar mota kuma yana dab da isa wajan motar me taxi wanda jama'a suka kwashi salati ana ihuuuuuu.
Abie tsabar firgita jikinsa rawa yake Idanunsa ya firfito waje yana fa'din.
“Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!!

_Afuwan ina busy ne kwana 2 mu ha'du gobe insha Allah._

_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
2/12/22, 20:44 - Buhainat: _*DATTIJON ARZIƘI*_

27&28

_*My Sisters Don Allah Don Darajar Annabi Karki Karanta Idan Baki Biya Ba, Na Ku'dine Idan Kinga Yana Yawo Na Satane Ga Hanyar Da Za Ki Samu Naki Akan.😟👉ðŸ¼300N +22796515805*_

Idanunsa ya runtse cikin tashin hankalin marar misaltuwa. sbd babu wata hanya da zai iya ceton rayukan wa'danda suke cikin taxi daga babbar motar da take neman isowa gab da su.
Jama'ar da suke bakin titin kowa kiran sunan Allah yake.
Cikin hukuncin Allah, babbar motar na gab da isowa wajan taxi Allah ya basa ikon take burki da 'karfi, yana sharkafa uwar zufa. Jin motar ta tsaya bai bi ta Kansu ba, yay hamdala wajan Allah.
Abie jin tsayuwar motar cak, yay saurin bu'de idanunsa yana 'dago kansa, yaga mutane har sun fara zagaye motar harda securities 'dinsa, wanda sukai saurin zuwa wajan tin kafin 'yan sanda su iso.
Abie cikin rawar jiki ya bu'de motar ya fito yana fa'din.
“Alhamdulillah! Ubangiji kasa bayinka wa'danda suke cikin motar nan, ba wanda yaji mugun rauni.
Wlh ummina yau kin sakani cikin wani hali.â€
Can kuwa an samu an 'daga motar.
An bu'de Ibtisam kwance cikin jini kanta ya yi mugun buguwa bata ko motsi hannunta da 'kafarta kamar sun karya. Me taxi kuwa da ransa ras sai dai ya karye a hannu goshinsa ya jimu sosai, haka bakinsa ya 'dan tsage.
Abie na isa yaga halin da ake ciki ya qara rikicewa ganin Ibtisam kamar ta mutu.
Arikice ya furta.
“Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Abbas ku kamasu muje asibiti.â€
Ya 'karashe mgnar cikin fitar haiyaci, ya ya sunkuya ya cicci'bi Ibtisam cikin jini aguje ya nufi motarsa.
Su Abbas su ka 'dauki me taxi wanda yake jin jiki sosai, suka nufi motarsu.
Da mugun gudu ya bar wajan, yayin da su Abbas suka rufa masa baya.
Kai tsaye *Hôpital général*
Ya nufa, tin ahanya ya kira Dr Salis, yay masa bayanin komai.
Su na isuwa daman an fito da gadon marasa lafiya, aka 'dora Ibtisam da me taxi aka nufi emergency dasu.
Sosai likitocin suka duqufa ceton ran Ibtisam da take cikin mawuyacin hali.
Haka 'bangaran me taxi ma.
Abie ya kasa zaune ya kasa tsaye acikin tashin hankali yake, idan Ibtisam ta mutu ya kashe mutum.
Kallon Abbas yay yana sauke numfashi ya ce“Ta ina za'a fara neman iyayan yarinyar nan? Ya Rabbi!â€
Abbas ya ce“Yalla'bai insha Allah komai zai zo da sauqi ka kwantar da hankalinka.â€

'Bangaran Ja'afar da Rahma, suna zaune a falon, hirasu suke cikin walwala da annushuwa. Abie 2 ya ma Ja'afar tambayoyi akan shi na inane, Ja'afar ya masa bayanin rayuwarsa da komai wanda da ahaiyacinsa yake bai fiye mgna ba Sam bare ya tsaya bada dogon tarihin gidansu dan a basa mace, tabbas Ja'afar bazai ba hakan.
Abie 2 ya jinjinawa Ja'afar sabida yana son namiji mai takaici da neman nakansa. gaba ya saka su cike da tarin tausayinsu.
Dai-dai lkcn da hatsarin ya faru lokacin gaban Ja'afar da Rahma suka buga atare, sai da suka mi'ke tsaye suka dafe 'kirji kusan atare suka fa'di.
“Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!â€
Abie 2 ya raqesu yana tambayar.
“Me ya faru daku atare haka?â€
Rahma ta rungume Abie 2 ta ce“Wlh gabana yay mummunan fa'duwa Abie2.â€
Ja'afar ya ce“Nima gabana ya fa'di, bari kuka Qalbi insha Allah babu wani abunda zai mana shamaki da mallakar junan mu kinji?â€
Kai Rahma ta 'daga lokacin da take kafeshi da 'kananun kyawawan idanunta masu lumshewa, wanda suke qara masa 'kaunarta.
Abie 2 ya ce“Kaga Ja'afar yanzu dai muje mu rakaka ka tafi gida dare ya fara, sannan pls kayi qoqarin yin sallar tsakiyar dare ka karanta Qur'ani mai girma.â€
Ja'afar ya sosa kansa ya ce“Tom Abba sai da safe.â€
Ya 'karashe mgnar ya na kallon Rahma.
Har wajan mota suka rakoshi ya kalleta ya ce“Qalbi sai na kiraki anjim Ok?â€
Rahma ta shagwa'be tana langwa'bar da kai gefe, ta ce“Ok Habiby na ina jiranka bye agaishe min da su mamah.â€
'Yar hararata yay ya ce“Tana Niger zan fa'da mata ta waya.â€
Murmushi suka sakarwa juna suna 'dagawa juna hannu har ya 'bacewa ganinsu ya nufi gate.
Su na dab da shiga ciki wayar Rahma da take hannun Abie tai qara ya beqa mata.
Ganin Abie ne ta 'daga tana murna ta ce“Abie nah Ja'afar yanzu ya tafi.â€
“Ok ban Abienki idan yana kusa.â€
Beqama Abie 2 wayar tai.
Sallama yay masa.
Abie ya ce“Abdulmajid an sami matsala, tsautsayi ya gifta na bige mota taxi me motar da wata yarinya, sun jimu yarinyar tana cikin wani hali, duk na rasa nutsuwata.â€
Abie 2 ya ce“Subahanallah! Kuna wane asibitine?â€
Abie ya ce “Hôpital général kazo da Rahmatullah kar afa'dawa Ummi hankalinta zai tashi.â€
Abie 2 ya amsa da“Toh insha Allah.â€
Rahma ta ce“Abie me ya sami Abiena¿â€
Hannunta ya Kama ya ce“Muje Yahaya ya kaimu wajan abinki ya buge motar me taxi sosai sun jimu.â€
Kuka ta sanya tana fa'din.
“Wayyo Abie nah Allah yasa komai yazo da sauqi.â€
Ja'afar yana fita ya nufi gidan Ma'aruf. Ya na zuwa bayan ya shiga yay parking, ya fito ya nufi ciki domin basa makullin.
Ma'aruf na zaune daga shi sai 3 quarter ba ko Riga jikinsa, shi da Aishatu suna aikin nasu na video call, ya cikata da zancan batsa, tana dariya.
Knocking 'din 'kofar da yaji anyi yasan bai wuce Ja'afar.
“Maman Babyna ina zuwa zan amshi key 'din mota.â€
Aishatu ta ce“Humm kai kam akwai sauqin yarda, baka tsoron ya gudu da motar?â€
Hararenta yay ya ce“So what? Ai yana cin ribata bazai ta'ba guduwa ba sannan wannan ba lusarin namiji bane mai budurwa zuciya wannan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment