Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yana knocking.
Ma'aruf yana na'de cikin bargo suna video call da Aisharsa.
Dariya ya kwashe ya ce“Ban gani ba da kyau, cire komai malama tare kike da mijin ki.â€
Aishatu daga can ta 'kyal'kyale da dariya ta ce“Wai ba kace fita zakayi ba?â€
“Yes naji Ana buga 'kofa amman sai kin nunamin abubuwana.â€
Ba yadda ta iya ta shiga nuna masa komai yana dariya, ya ce“Wlh badan sonki ya rufemin ido ba, da ba abinda zai hana na qaro 'yar duma-duma, na dinga shafa manya 'duwai...â€
Cikin masifa ta ce“Ga hanyar nan jarababbe kawai.â€
Ta tsinke kiran tana sakin kukan kishi.
Ma'aruf ya bushe da dariya ya mi'ke ya sauko ya saka kaya dan ba uwar komai ajikinsa.
Falon ya fito yaje ya bu'de 'kofar.
Ja'afar tsaye can nesa.
Ma'aruf ya ce“Ka iso? Meye sunanka?â€
Ja'afar ya ce“Ja'afar.â€
“Ma Sha Allah, shigo toh na kintsa zamu fita.â€
Ja'afar bai musaba ya shigo. Ya nuna masa wajan zama ya zauna shi kuma yaje ya shirya.
Mamaki Ja'afar yake namiji da lafiyarsa kamar wannan wai sai anyi driving 'dinsa, da zuwa siyo masa duk abinda ya keso ko kai masa.
Bai jimaba ya fito cikin shigar suit ba'ka'ke, sun masa kyau sai 'kamshi yake.
Makullan motar ya bama Ja'afar ya amsa ya mi'ke suka fita.
Motoci ne biyu 'dayar arufe Jar suka shiga.
Tin layinsu ya gano Ja'afar babban direba ne sosai hakan yay masa da'di yasan komai zai kammala cikin satittika.

*Gabon*
Abdul Majeed zaune cikin falo ya na mgna alamun mgnar ta sirrice, ya nutsu sosai yana sauraron bayanin, kafin shima ya fara mgna.
Kusan 20 minutes kafin ya gama wayan ya mi'ke ya kira security 'dinsa ya ce“Shirin tafiya Espagne an gama shirya komai jirgi nan da awa 1 zai 'daga.â€
Cikin girmamawa ya amsa ya fara ha'da kayansu.

Aishatu zaune ta 'kurama Tv idanu, amman ranta Sam ba da'di.
Wai ita Ma'aruf zai gayama mgna dan tana ramammiya?
Knocking 'din 'kofar akayi, ta 'kwalawa uwani kira.
Aguje ta fito cikin girmamawa ta ce “Ga ni hajiya.â€
“Dan Allah uwani wai inada rama sosai ne halan?â€
Uwani ta 'kunshe dariyarta ta ce.
“A'a hajiya bawai sosai ba, amman ai bakida laifi.â€
Aishatu ta ce“Humm ai daman nasani masifarsa ce kawai, jarababbe je ki bu'de 'kofa.â€
“Toh an gama.â€
Uwani na bu'de 'kofa Rabi'ah ta shigo tana taunar cihngam.
Aishatu ta ce.
“Uhmm! Ina aka fito da rana tsakiya?â€
Rabi'ah ta zauna tana yatsina fuzka ta ce“Kinji haushin kanki, kin manta yau bikin Zaliyah?â€
Aishatu ta ce“ni wlh na manta daman kuwa ban zuwa, an 'batamin rai. Wai ke! Sosai nakeda rama?â€
Rabi'ah ta fashe da dariya ta ce“Au yanzu abun atare dake baki saniba?â€
Ai wlh kin fiye tsunburewa, ki faso gari hajiya....â€
“Ya isa! don Allah malama! Ta shi kije banson buro uba 'yar ba'kin ciki kawai.â€
Rabi'ah ta ce“Wlh bazan tafi ba sai Ac ya gama kaimin karki min iskanci kinji ko.â€
Aishatu ta mi'ke cikin 'bacin rai ta ce“Tinda gidanku ne sai ki zauna.â€
Ta nufi bedroom 'dinta ta rufo 'kofa.
Rabi'ah kwanciya tai saman kujera tana dariya, ita tasan me take kisimawa aranta...

★★★★★★★
*Bayan kwana 9*
Rahma sosai tai wani irin shaquwa da dattijon nan, da ta mayar da shi tamkar Abienta, ya murje ya goge ya yi wani irin kyau, baida aiki daga ci sai Sha sai ibadah, Rahma gefensa na zaune ko bazata masa mgna ba, yana tsintar kansa cikin farin ciki.

'Bangaran Ja'afar da Ma'aruf sosai sun saba ya siya masa kaya na zamani harda takalma, da waya wanda dakyar Ja'afar ya amsa, ganin Ma'aruf baiji dad'i ba sosai.
Ya basa albashinsa na sati wanda yawan ku'din sun tsorata Ja'afar, ya ce bazai amsa duka ba, dik yadda Ma'aruf yakai da naci Ja'afar yaqi a uku ya raba ya amshi kaso 'daya.

Can Tahoua Ibtisam ta na cikin tashin hankali, sbd afarko, yaqi batun Jamilu Laraba harda kukanta, ta rasa ya zatayi, har wajan mahaiyarsa Dadah taje ta ce bazasu ma Ibtisam auren dole ba.
Tanko ya saurari Ja'afar sunyi mgna akan ya kwantar da hankalinsa shi zai aura ma Ibtisam.
Amman dare 'daya Tanko ya ce ya fasa yaba Jamilu Dadah ta goyi baya, yanzu haka an sanya ranar aure sati biyu masu zuwa. Yaan musu gyaran gida an shafasa da siminti, anyi forge gidan ya dawo tsaf
Ibtisam ta rame tai ba'ki hankalinta atashe kullun cikin zazza'bi take.
Ja'afar baki 'daya baida nutsuwa da kwanciyar hankali, sabida Baaba sunyi mgna akan ya fawwalawa Allah lamarin, kar ya kuskura ya zuga Ibtisam ta bijirewa iyayanta.
Hakan ya saka Ja'afar ya rage waya da Ibtisam, duk da yana cikin damuwar rashin jin muryata, ko ta kira shi bai d'agawa, idan ma ya d'auka hkr yake bata akan tai biyayya, har hawaye yake a 'boye dan ba qaramin so yake mata ba.

Misalin 3 na dare wanda ya rage yau sauran kwana 2 'daurin aurenta da Jamilu.
kwance take kamar an tsinketa ta mi'ke ta bu'de 'kofa ta 'dauki wayar da Laraba ta tirsasata take 'daga kiran Jamilu.
Buta ta 'dauka ta shiga bayi.
Number Ja'afar.
Ya na cikin tsakiyar bacci yaji ringing 'din wayar.
Lalubo wayar yay ya bu'de gajiyayyun idanunsa ya bu'de wanda suke cike da bacci, ya kalli screen 'din wayar ganin Ibtisam gabansa ya fa'di yay saurin 'daga kiran.
“Baby lfy me ya faru bakiyi bacci ba?â€
Ibtisam ta fashe masa da kuka ta ce.
“Mon amour kai har bacci kakeyi kaga yadda na koma sabida rashinka ko wata ka samune a can?â€
Ja'afar ya dafe goshinsa da tasan me yakeji da batace hakan ba!
â€Yi hkr fa'damin me ya sameki?â€
Ashagwa'be ta ce“Ni ba mafarki nayi kazo shine na kiraka naji. Don Allah Mon amour me sunan garin da kake a Tchad?â€
Ja'afar ya ce“Me yasa kika tambaya, ko nan zaku zauna da mijin naki?â€
Kuka ta sanya masa harda shashe'ka.
“Sorry yi shiru Ndjamena muke, baby wlh ina ta addu'a kinga yaune kawai bacci ya rinjayeni tinda muka shiga halin nan zaune nake kusan kwana, ina fa'dawa Allah wani bin sai asubah nake baccin da bai fi awa biyu ba na tafi wajan aiki. Don Allah ki nutsu ki rabu da iyayanki lfy, yadda nakeji akanki nasan wani banza bazai shiga min gonataba da garaje, Allah yana sane da kowa da komai kije ki amince karki musu ayi auran kinji Babyna.â€
Cike da farin ciki ta ce“Allah yasa ni matarka ce Sahibina, ina sonka bye kayi bacci lfy na gayamaka bana son Baba jimilu bani ba kaima yakusa haifarka.â€
'Kitt ta kashe wayar baki 'daya ta buga tsalle ta ce.
“Ndjamena.â€ðŸ’ƒ
Komawa ta yi tai kwanciayarta.
★★★
Bayan kwana biyu
Abien Rahma sai da tai da gaske ta damesa da koke² yay shirin tahowa, sbd uzururuka sun tisasa gaba sai 'kasashe yake wucewa.

Ja'afar sanye da Riga da wondo na sanyi kalar blue, masu taushi, ya 'dora ba'kar rigar sanyi mai wula asaman kayan. Wani irin fitinannan 'kamshi yake tashi ajikinsa, wanda ya baibaye motar baki 'daya. Sai dai fuskar nan ba walwala sabida damuwar da yake ciki, 'batan Ibtisam yau kwana biyu anyi Neman duniya an rasata, ana zargin shi ya saka a saceta, ga fitinar Laraba ta addabi iyayansa.
Tsaki yaja yana tura hannunsa cikin sumar kansa yana shafawa
Gudu yake sosai sbd zai biya wani waje ya 'dauki Ma'aruf ya kaisa Airport, zaije Gabon.
Wayarsa ta 'dauki ringing.
Kallonta yay yaga ba suna, yaqi 'dauka.
Kusan kira biyar hakan ya saka ya 'daga tare da sallama.
“Hello Mon amour kazo ka 'daukeni ina tashar mota.â€
Motar saura ka'dan ta ku'buce masa tsabar tashin hankali. Gangarawa yay bakin titi.
Cikin tsawa ya kira “Ibtisam! wa ya kawoki tchad tin daga niger? Nace uban wa yakawo ki? Wlh idan baki gayamin ba nazo zakiyi nadamar sanina arayuwarki.â€
Ibtisam daga can atasha tana ri'ke da wayar sai da taji kamar ta Saki fitsari mugun tsoronsa ya shigeta tin kafin ya akasance awajan.
Gigitaccan kuka ta Saki tace“Don Allah Mon amour kazo zan maka bayani wlh ni 'daya na shigo mota bazan 'boyema komai ba.â€
'Kitt ya katse kiran ya kifa fuskarsa saman tiyarin motar ya fesar da wani irin 'dumamanmen numfashi, ya 'dago yama motar key ya juya ya koma baya sabida nan tafi kusa da tasha.
Ibtisam hankalinta ta she ta du'ke nan tana kuka, cike da tsoron kar Ja'afar yaqi zuwa bayan taci uwar wuya ahanya.
Mai taxi da ya bata wayarsa kasancewar yanajin hausa ya ce.
“Qanwata 'yan gidan naku basa zauwane?â€
Kai ta girgiza ta ce“Kayi hkr jira muga ko yazo sai abaka ku'din katin da ka saka awayanka nai kiransa.â€

Ja'afar waige² yake cikin Tasha kasancewarta mai girma, can 'bangara da aka saukesu ya nufa.
Du'ke ya hangota jikin taxi kamar ma fa'dane yake mata tana kuka, har mutane sun fara taruwa Ana tamabayarsa.
Ransa yaji ya 'baci da sassarfa ya isa wajan, yaji mai taxi na fa'din.
“Ashe batada ko sisi ta saka na siyi katina na bata kira ko kwartontane ma....â€
Cikin zafin nama Ja'afar ya rufe msa baki yana masa 'kas'kantaccan kallo.
“Ya isheka malam! Katin nawa ka saka awayan?â€
Ya qarashe tambayar yana sakar masa baki.
“Sosai Ja'afar yay masa kwarjini yana son ya masa tijara ya kasa, ya ce“Na jaka 'daya.â€
Jaka biyu Ja'afar ya mi'ka masa.
Ya maida kallonsa wajan Ibtisam wacce tinda taji muryasa ta mi'ke ta kafesa da ido tsoransa ya hana tai masa mgna.
Wani mugun kallo ya watsa mata tai saurin sadda kanta tana wasa da yatsun hannunta hawaye na kwaryan saman kyakkyawar fuskarta.
Ahankali ya 'karasa wajanta ya tsaya dab da ita.
Ji tayi bugun zuciyarta ya tsananta, ga wani fitinannan 'kamshinsa da baibaye mata hanci.
Take jikinta ya 'dauki 'bari.
Kama hannunta yay ba tare da yace mata ufan ba, ya fara tafiya.
Binsa take kanta a 'kasa.
Sai da taji ya bu'de mota ya zaunar da ita, ya rufe ya zagaya,ya shiga ya fizgeta yabar tashar.
Har sukayi nisa bai cemata uffan ba, haka bai kalleta ba.
'Dagowa tai ta kalleshi, wani irin girma ta ga ya qara,ya qara kyau fatarsa ta murje.
Fashewa tai da kuka ta fa'da jikinsa ta zagaye hannayenta bayansa cikin kukan ta ce“Kamin horon komai banda shariya kai ka'dai na zaba akan kowa karka gujeni pls Sahiba kamin mgna ko sau 'daya, bazan ta'ba iya jure rashinka ba Mon amour.â€
Ta 'karashe mgnar cikin shashe'kar kuka tana shigewa faffa'dan 'kirjinsa, ta 'kan'kameshi sosai, kamar zai gudu.
Wata irin wahalalliyar ajiyar zuciya Ja'afar ya sauke, ya fesar da zazzafar iskar bakinsa waje.
Cikin fushi ya ce“Sakeni matsa.â€
Sakinsa tai cike da tsoro ta rakub'e tana kuka.
“Kiyi shiru malama.â€
Ha'diye kukan tai ta saka kanta tsakanin cinyoyinta.
*Restaurant Amandine*, ya biya ya mata takeaway.
Kai tsaye gida ya wuce da ita.
Key ya saka ya bu'de 'kofar kewayansu.
Fuska ba walwala ya ce“Shiga muje.â€
Ibtisam ta shige sum-sum cike da tsoronsa.
Jarka ya nuna mata da ruwa yace“Wanke hannunki.â€
Ba musu taje ta wanke.
Kitchen ya 'dauko plate, 'dakin ya bu'de ya ce ta shigo.
Tass ashare an sanya ledar 'daki ga katifarsu 'katuwa, 'kamshin turaren hakki na tashi.
Abinci ya juye mata a plate, ya ce.
“Zauna kici.â€
Ya nuna mata katifa.
Zama tai kanta 'kasa.
Akwatinsa da Ma'aruf ya basa ya bu'de ya ciro wata abaya ja mai shegen kyau, wacce ya siyo mata tin farkon zuwansa da zummar ya kai mata.
Ajiye mata yay ya 'dauko mata soso da sabulunsa ya ce“Kina idar da cin abin kije kiyi wanka, bari na 'dora miki ruwan zafi, ga mai ki shafa ki sanya wannan rigar, sai ki kwanta. wallahi idan nadawo baki fa'damin gaskiya ba zaki raina wayona, na tafi.â€
Ibtisam ta jinjina kai ta ce“Ya Ja'afar karka rabu dani don Allah.â€
Harara ya zuba mata,ya ce“Oya ci abinci malama.â€
Cikin rawar jiki ta 'dauki spoon 'din ta fara cin jalof 'din shinkafar da 'katuwar cinyar kaza.
Le'bensa na qasa ya tsotsa ya zura hannayensa, cikin aljihun wandonsa ya fito ya shiga kitchen ya kunna resho ya cika tukunyar da ruwa ya 'dora ya fice ya rufeta ta waje, ya shiga motar ya fizgeta aguje yabar layin ya kira Baba Tsalha yana masa bayanin komai, ya ce idan yakai uban gidansa airport ya dawo zasuyi mgna.

Rahma zaune kusan Jaddatu cikin shirin fita take, ta mannawa Jaddatu kiss akumatu.
“Wlh Rahma kibi asannu yanzu tarbar Abien naki ma sai kin kwashi mutumin nan kunje tare?â€
Raiyana ta ce“Ummi ai baya komai daughter muje lokaci ya yi fa!â€
Hanan ta ce.
“Ummi baza ki jeba ne?â€
“A'a wlh ina nan iman mu zauna ko?
Iman ta ce“Naqi Abie zanje na kawo.â€
Rahma tai siririyar dariya ta mi'ke ta sungumi Iman ta ce.
“Muje. Latifa!â€
Aguje ta iso ta zube.
“Allah shi temaki uwar 'dakina maganin kukana, fa'di na cika 'ya daga Allah.â€
Rahma tai murmushi zatayi mgna taji murya Jaddatu ta ce.
“Mu kuma ubanki shi temakemu kike nufi kome? Na ce bayan aikin harda qira da ro'ko ya kawoki munafuka.â€
Ta 'karasa mgnar tana 'daga sanda ta wurgoma Latifa, tai saurin kaucewa tana fa'din.
“Ya Allah kana gani dai ni bansan me na ma Jaddatu ba?â€
Hanan dariya sai da ta zube saman carpet.
Raiyana ta gintse tata dan dakyar ta Sha wancan Karon.
Rahma ta sauke Iman tana dafa goshinta ta ce.
“Ya Salam! Jaddati me kike hakan? Wlh bana jin da'di Sam ba girmanki bane, kince tabar miki wasa ta bari toh me ruwanki da ita yanzu?â€
Jaddatu ta tafa hannun tana shirin sanya kuka ta ce“Rahma bare yafini wajanki?â€
“Ni ban ce ba mgnar gaskiya nakeyi. Latifa je sama ki gyaramin bedroom da falo, 'bangaran Abie na gyara na gaji sosai.â€
Raiyana ta kalleta ta ce“Au ya bar miki key ne?â€
Rahma ta ce“Daman wajena wannan yake naje 'daukar abu naga ba gyara ba'a gyaraba shine na gyara ammi. Jaddati kiyi hkr mun tafi.â€
“Bari uban naki yazo Rahma tinda Latifa ta fini.â€
Rahma bata sake mgna ba suka 'dunguma suka fita.
Zaune yake sanye da shaddah ruwan sararin samaniya, ta Abie da Rahma ta basa, yaji qaran ta'ba qofa.
Rahma ta shigo da sallama tana riqe da hannun Iman.
Amsawa yay ta ce.
“Abie 2 muje toh mun makara fa!â€
Kafa'da ya ma'kale.
'Kananunkyawawan idanunta ta zaro tana kwa'be fuska ta ce“Pls Abie 2 Allah zanyi kuka.â€
Murmushi yay ya ce“A'a 'diyar albarka kar kiyi kuka wlh kome kikeso zan miki. Kalli Iman na mana dariya fa!â€
Rahma ta matso tana rik'e da hannun Iman ta be'ka masa hannunta 'dayan, ta marerece.
Ya gane nufinta sai yay murmushi ya ma'kale kafa'da ya mi'ke da kansa, ya ce “muje toh.â€
'Kwalla ta taru a idanunta ta ce“Sai na fa'dawa Abiena mai sona Abie2 baya sona.â€
“Don Allah 'diyar albarka kiyi hkr.â€
Ya qarashe mgnar yana kamo hannun nata.
Kallon juna sukayi lokacin da suka sauke ajiyar zuciya atare.
Da sauri ya Saki hannun yana lakatar dogon hancinta.
Iman tai dariya ta ce“Sunyi fa'da ina musu dariya.â€
Rahma ta ce“Ai kin kyauta tinda ni bai sona bai 'daukana 'yarsa ba.â€
“Me nayi miki toh baby.â€
Baki ta zum'buro ta ce.
“Baram-baram.â€
Dariya yay ya bu'de 'kofar ya fito.
Suka biyo bayansa.
Su Raiyana suna cikin mota har sun gaji da zaman jira.
Gaba kusan direba yake zaune.
Yayin da Rahma tana gefe iman saman cinyarta. Rainaya gefe Hanan atsakiya.
Motarsu gaba ta securitys bayan tasu haka suka fita.

Babban titin ambassadna, danja ta tsayar da su Rahma.
Sai kallon titi take.
Bayan an sakesu Yahaya cira aguje.
Akuma lokacin motar Ja'afar bayansu ya 'dauko Ma'aruf, Sam baisan ya akayi motar ta ku'buce masa ba, ya daki motar su Rahma, daga baya ji kake garammmmmmmmm...........!
_💃ðŸ»Yar Ajin Tubarkallah🥰_

*DATTIJON ARZIK'I* N300 katin MTN ta wannan number *+22796515805*


BA'KAR FATA
Autar Manya

TSINTACCIYA
Nimcyluv

SULTAN
mss flower


Gaba É—aya 800
Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman Fidelity Bank, masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 za ku tuntuɓa. To show evidence of payment 08142105218


*Real Ladingo+22796515805* For more information😇

_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
2/7/22, 07:46 - Buhainat: _*DATTIJON ARZIƘI*_


*BY*
_Rahma ladingo Ummu Fareesa😘_

*🔥FITATTU HUƊU🔥*


_*HOME OF QUALITIES WRITERS ASSOCIATION*_

```TABBAS ASIRI GASKIYAR ME SHI NE.😔 HAJIYA KU SHIGO PAID GROUP NA TATTIJON ARZI'KI AYI WANNAN TAFIYAR DAKE, BABU KE BAYIN DA NASANIN BIYAN N300. ```


*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*


_*cнapÑ‚er 20 Last free page💃ðŸ»*_


Ja'afar cikin zafin nama da 'kwarewar shi, yay saurin Janye motar baya, tin bugun farko da ya mata, yay baya da sauri, cikin ikon Allah bai shiga sosai ba.
Amman motar ta bugu.
Ba binda yake fa'da sai.
“Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Allah yasa yadda bamuji ciwo ba wa'dan da ke cikin motar ma basu ji ciwo ba.â€
Yay saurin yin baya sosai yana kallon yadda ya bugi bayan motar ya lo'ba sosai, addu'arsa Allah yasa ba wanda ya ji ciwo acikin motar da ya buga 'din.

Su Rahma ba 'karamin tsorata sukayi ba, lokacin da Ja'afar ya bugi bayan motar tasu, wanda take gefen 'daya ya lo'ba, “Innalillahi wa'inna ilahir raji'un!â€
Shine su Rahma suke maimaitawa dukkanun su.
Jin yadda aka bigi motar su daga baya wanda har far 'din baya na hagum ya fashe take dukkansa ya zube tsakiyar titin.
Security's da suke biye da su hankalinsu ba 'karamin tashi yay ba, aguje suka qaraso wajan dab da motar su Ja'afar,
Sukayi parking suka fito ganin har yanzu mai motar yaqi fitowa ya bada hkr, ga shi jama'ah sun taru sosai.
Rahma ta ru'de tana rungume Raiyana da Iman. ta le'ka Abie 2 jikinta na 'bari ta ce“Abie 2 bakaji ciwo ba ko?â€
Abie ya ce“Fatan kema jijjigar motar bata saka zuciyarki ta tab'u ba?â€
Hanan ta ce“Wannan wane irin jakine ya bugemu a mota amman bazai so ya bamu hkr ba?â€
Rahma ranta ya 'baci ta ce.
“Ai kuwa rashin mutunci ba abinda yake cikin tsarina bane amman wlh sai naga me yake taqama da shi. Ya bugi motar mu amman mu yake jira mu fito ko me? Kodai macace a motar ina zuwa.â€
Ta 'karashe mgnar tana qoqarin bu'de motar dan ta fita.
Abie 2 ya ce“A'a 'diyar albarka zauna bari zan duba muga ko dai yaji ciwone, ayi masa uzuri.â€
Yahaya direba ya ce“Eh hakane kam hajiyar gida kiyi hkr 'barna ce an Riga an mana ita.â€
Raiyana ta ce“Hakane amman kowaye bai kyauta ba, kamar da niyya akayi.â€
Abie 2 ya girgiza kansa, ya bu'de motar ya fito Yahaya na bin bayansa.

Ma'aruf kuwa tsabar tsoro da ru'dewa yasa ya rufe idanunsa ya toshe kunnuwansa, yana kiran sunan Allah, dan ji yake yau sun gama mutuwa zatonsa sun shiga motar sosai sam sai lokacin da Ja'fara ya masa mgna yana 'ko'karin bu'de motar.
“Oga muje muba masu motar hkr don Allah, mune da laifi.â€
Ma'aruf ya kalli Ja'afar ya ce.
“Su basu san tsautsayi ba ai nima an kashe min far 'din mota...â€
Securities ne suka katse masa magana suna 'kwan'kwasa glass 'din motar.
Ja'afar bai tsaya sauraren Ma'aruf ba ya bu'de motar ya fito.
Tsaye suke fuskar nan ba fara'a, sun game rai.
Ja'afar aransa ya ce“Tabb ashe ba hausawa bane, ni kuma ban iya larabci ba.
Cikin harshen français ya ce “Kuyi hkr wlh ku'buce min tai bansa ya hakan ya faru ba.â€
Abbas ya ce“Amman shi ne bazaka fito bada hkr ba kun ha'dawa mutane gosulo?â€
Ja'afar ya ha'diye 'bacin ransa, dan yasan shine baida gaskiya, ya ce“Kuyi hkr...â€
Ma'aruf ya ce“Kar Allah yasa su hkr, ai muma an mana 'barna.â€
Abbas ya harzu'ko zai kaima Ma'aruf duka, Abie 2 ya ce“A'a ku dakata! Me yake faruwa ne harda bugu? Ai mugodewa Allah abinda ya tsaya anan, ba wanda yaji ciwo Allah ya kiyaye gaba.†Ma'aruf ya ce“Bayan ka turo acimin mutunci a baina nasi ni za'a Mara? Ja'afar ya ce“Haba! Me kake hakane? Wannan babban mutum ne, duk abinda zakayi ka guji yiwa babba magana gatsal.â€
Rahma tana kallon komai ta can, ta bu'de motar aharzu'ke ta fito ta dimfaro wajan.
Tana zuwa ta Kama hannun Abie 2 ranta a'bace ta ce“.
Abbas tinda basuda mutunci kuyi duk abinda ya dace sannan gyara mana motar mu kamar yadda muka fito da ita...â€
Ja'afar ya kalleta ya kauda kansa, baisan me ta ce da larabci ba, amman ya mayar mata French ya ce“
Don Allah kiyi hkr ba da gangan bane...â€
Da sauri ta waigo ta kalleshi taja tsaki ta maida masa da French ta ce“Anqi a hkrn kun rainawa mutane hankali, ashe ko Arab 'din ma basaji, duk wanda ya ce zai ta'bamin Abie sai naga bayansa...â€
Abie 2 ya rufe mata baki ya ce“
Abbas muje Ku kuma Ku tafi Allah kiyaye gaba.â€
Ja'afar yarinyar tai mugun ba'kanta masa rai yaji ya tozarta, amman ya danne 'bacin ransa ya ce“Merci beaucoup papa.â€
Ma'aruf bai ce komai ba, sbd yay nisa wajan kallon Rahma da nazartar ta idan zai fara, ga dai Raha Abdul Majeed Abdulwahab Marocco amman ba damar saceta.
Raiyana tana kallon duk abinda yake faruwa.
Murmushi mai taushi tai, aranta ta ce“Anzo wajan.â€
Zaunar da ita Abie2 yay mazauninta yaja kumatunta ya ce“Baby rigima! Mu gode Allah babu wanda yaji ciwo.â€
Rahma ta turo baki batayi mgna ba, ya rufe motar ya isa mazauninsa Yahaya yaja motar yabar wajan.
Yayin da su Abbas ke biye da su.
Ja'afar na driving cikin 'kwarewarsa yana fesar da zazzafan huci, yana mamakin me yama yarinyar? Ya ga hkr yake basu, idan ba dan shine baida gaskiya ba su isa ya basu hkr ba, koda kuwa za'a tara masa mutanan tchad baki 'daya ba wai kallon suna larabawa ba.
Tsaki yaja yana fa'din.
“Shiyasa na tsani yawancin masu ku'di basuda adalci...â€
Ma'aruf ya ce“Hummm! Har ni?â€
Ja'afar ya ce“Ka gyara gaskiya bansan naga mutum nawa babba rashin kunya, wannan zai kusa haifarka fa, koma ya haifar kake neman masa rashin kunya.â€
Ma'aruf da yake yana son shirya iya shege ya ce“Na bari Ja'afar Ngd da shawara, yarinyar nan tanada jin kai, ko dan ta ga tanada kyau.â€
Ja'afar bai tanka masa ba ya ta'be baki, shi kam baiga kyau ba, haushinta ma yake ji, kyawun mace 'daya yake gani cikin 'yan matan duniya Ibtisam 'dinsa.
Kusan tare su ka shiga airport, Ma'aruf sai message yake da wata number yana dariya.
Ma'aruf bai fice minti 15 jirginsu ya 'daga zuwa Gabon, Ja'afar ya juya zuwa gida.
Su Rahma sun shafe 25 minutes kafin jirgin su Abie ya iso. Abie 2 ya mi'ke ya 'dan zagaya ya dawo.
Su na zazzaune wajan da ake jiran matafiya sai ga shi shi da security 'dinsa, sanye da wata narkekiyar shaddah me mai'ko.
Rahma ta mi'ke cikin matsanaicin farin ciki ta ruga aguje.
Hannayensa ya ware mata cikin tsananin farin ciki ta fa'da saman faffa'dan 'kirjinsa, ta 'kan'kameshi tana sakin wani irin numfashin, ta ceâ€Abiena Rabin raina, I miss you so much.â€
'Kan'kameta yay ya shafa bayanta, bakinsa dab da kunnenta murya atausashe ya ce“
Miss u too my baby ummina. Kinyi kewar Abie sosai ne¿â€
Luf tai ’Kirjinsa tana 'daga kanta alamar Eh.
Rainaya ta iso ta ce“Toh Iyayan soyayya uba da 'yarsa Abien Rahmerh barka da zuwa.â€
Rahma ta janye jikinta ta Kama hannun Abie tana murmushi.
Amsawa yay fuska sake ya 'dauki Iman Hanan ta turo baki gaba tana fa'din.
“Yaya Abdul ta 'yarsa yake da matarsa baiga 'kanwarsa ba?â€
Abie ya rungumeta yana murmushi ya ce“Ban isa naqi ganin Ƙanwata ba.â€
Abie 2 ya ce“Yalla'bai barka da zuwa.â€
Abie 1 ya sakesu ya rungume Abie 2 sukayi musahaba.
Rahma sai murna take ta yi Abie biyu.
Motar su Abbas Abie 1 ya shiga Rahma ta ce nan zata shiga. Ai kuwa ahaka suka jera zuwa gida, Abbas na masa bayanin tsautsayin da ya faru.
Abie ya ce“Allah ya tsayar nan.â€

Ja'afar kai tsaye wajan gyara yakai motar, sbd far 'din gaba guda ya fashe, sai an saka sabo, daga can ya nufi gida.
Ibtisam bayan ta gama cin abincin ta fito ta leqa kitchen ta ga ruwan zafin har ya tafasa, ta kashe reshon ta juye abokiti ta, ta shige bayin, tai wankanta tass, ta fito.
Mai ta shafa na Ja'afar mai azabar 'kamshi, ta sanya Riga mai shegen kyau ta mata cif har 'kasa ta yane kanta da mayafin abayar, ta fesa turaren Ja'afar ta kwanta saman katifar tana fa'din.
“Mon amour ina sonka har na mutu. Yaushe zan tsaya na auri mutum kusan sa'an Babana, Anna Baba ku yafemin ban gudu dan 'bacin ranku ba.â€
Ta 'karashe mgnar tana sakin kuka abin tausayi.
Ja'afar tinda ya shigo yake jin shashek'ar kukanta.
'Dakin ya shigo ya ga ta ha'da kai da guiwa, tana rusar kuka.
Wani irin tausayinta yaji ya kamasa, amman yana son ya nuna mata kurenta.

“Kukan me kike tinda kin gudo?
'Dagowa tai tana kallonsa idanunta sharkaf da hawaye.
Zama yay ya ce“Fa'damin me yasa kika za'bi barin iyayanki da kowa sbd ni? Ko dan ki tozarta iyayanki?â€
Ibtisam duk da tana tsoron Ja'afar amman hakan bai hanata shigewa jikinsa ba, cikin kuka ta ce.
“Kasani ban ta'ba son kowa ba sai kai bazan iya jure rashinka na har abada ba.â€
Zazzafar iskar bakinsa ya fesar ya Sani Ibtisan son so take masa, tana qaunarsa matu'ka kamar yadda yake sonta.
Fuskarta ya riqe da tafin hannunsa biyu, ya jefa mata gajiyayyun idanunsa ma'abuta lumshewa.
Cike da kasala ya ce“Mon cÅ“ur kalleni.â€
Wani irin fitinannan sanyi Ibtisam taji lokaci 'daya ya kama sassan jikinta, sbd yadda yay mata mgnarsa mai wujijjiga mata zuciya da gangar jikinta.
Kallonsa tai ta yi saurin rufe idanunta ta kirasa“Mon amour pls muyi aure wlh ina sonka ka ji.â€
Ta 'karashe mgnar tana fashewa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment