Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

mutum 7 kowa da aikinsa Kama daga mai kula da lambu da mai kula su talato talato d'awisu jimuna tantabaru aku da sauran abin kiwo. Masu gadi mai wanki mai bawa flowers ruwa, dukkansu suka gashesa cike da girmamawa.
Fuskar shi sake dukkansu ya bek'a musu hannu suka gaisa. Cike da dattaku cikin muryasa mai taushi ya ce.
“Am! Yahuzaya anjima idan ummina ta farka daga bacci zaka kaita wajan shak'atawa, k'ila da amminta pls waje mai kyau ok?â€
Cike da girmamawa ya rusana yace “Ok Yallab'ai insha Allahu.â€
Kai ya jinjina ya nuna Abbas da Khaleefa cikin securities d'insa ya ce“Yauwa Abbas and Khaleefa ku jira ummina ta farka zaku fita da ita awannan farar mota.â€
Cikin girmamawa suka masa.
Ya shiga bayan bak'ar motar securities biyu suna gaban motar kusan direba.
Jarida Abie ya d'auka ya fara karantawa.
Tin kafin direba ya iso d'aya daga cikin masu gadin au 2 ya na sanye da uniform ya wangale musu k'atoton gate mai girman gaske, kalarsa golden.
Rahma da take tsaye ta k'urama motar Abie ido har lokacin da motar sulale ta fice daga gidan.
Wata irin wahalalliyar ajiyar zuciya ta sauke mai k'arfin gaske, hawaye na silalowa daga cikin k'ananun idanunta masu matuk'ar haske, wanda b'acin rai ya saka ya canza Kala.
Sosai hawayen ke zarya saman kyakkyawar fuskarta, ta rufe glass d'in window tana Jan labulen, taja k'afafunta dakyar ta koma ta zube saman Royal bed d'inta, tana sakin wahalallan kuka, mai tsuma zuciya.
“Allah sarki Abiena, Ya Allah kaima ya baka mata ta gari wacce zata kular min da kai tasan darajarka ta zauna dakai akowane hali, ya Allah ka saka Abie mai lafiya ne ba gaskiya bane abinda take fad'amaka, na tsani Raiyana tinda har bataga girmanka ba take maka rashin kunya.â€

Su na fita daga gidan Abie yacema direba.
“_*Hôpital de la Renaissance*_â€.
Direba ya amsa cikin girmamawa“Ok Yallab'ai.â€
*Niger*
💃ðŸ»TAHOUA lele birnin adar.
Unguwan ( *Geban zogi*)........... Billahi akwai k'ura😹ðŸƒðŸ»â€â™€ï¸


*DATTIJON ARZIK'I* N300 katin MTN ta wannan number *+22796515805*


TSINTACCIYA
Nimcyluv

SULTAN
mss flower

BAK'AR FATA
AUTAR MANYA


Gaba É—aya 800
Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman Fidelity Bank, masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 za ku tuntuɓa. To show evidence of payment 08142105218


*Real Ladingo+22796515805* For more information😇


_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu baðŸ™ðŸ¼.*_
2/2/22, 09:18 - Buhainat: _*DATTIJON ARZIƘI*_


*BY*
_Rahma ladingo Ummu Fareesa😘_

*🔥FITATTU HUƊU🔥*


_*HOME OF QUALITIES WRITERS ASSOCIATION*_


*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*


_*cнapтer 5&6*_


Gidane ginin jar k'asa mai d'auke da d'aki biyu k'wal, sai d'an filin da baida larewa.
Matashiyar budurwa ce ta fito daga band'aki rik'e da bokiti, alamar wanka ta yi, jikinta na d'igar da ruwa, sai turo baki gaba take tana game jikinta waje d'aya alamar sanyi take ji.
'yar kimanin shekaru 17 ahaife, kyakkyawa fara mai kyan sura ba laifi, komai na jikinta ubangiji ya tsara mata shi daidai ita, ba abinda yake mata kyau irin wushiryata da dimples d'inta idan tana murmushi, tanada gashi babu laifi yanada d'an yawa, gata mai yawan fara'a da son mutane, ga kirki.
Wata fara mata zata kai shekaru 40 alamunta zatayi fad'a tana bakacen masara da zasuyi girkin dare wajan sarrafa tuwan tsaki da ita.
Da harara tabita ta ce“Wallahi Ibtisam idan kika min jajen mura zakici ubanki tinda jarabarki bata k'arewa, daga wancan ciwon ki kwanta wancan, mu kullun kud'inmu wajan miki magani yake k'arewa, gaki ba wani tsayayyan saurayi mai zuciyar kulawa dake...â€
Tanko da yake shigowa cikin gidan yay caraf ya ce“Eh kekuma lashe money ba! Wlh Laraba ki rabani da mugun hali karki b'atamin yarinya, shiyasa Yaya Karime ta ce na turata wajanta, wlh na kusa d'auketa kiji da k'ananun 'yaran tinda baki iya mgna ba! Ya zaki dinga jayoma d'iya budurwa kamar Ibtisam jaraba? Kinsan tasirin bakin uwa jikin d'anta? Sannan kice kina son rayuwarta ta yi albarka? Kike mgnar saurayi Ja'afar ai namijin duniyane inace duk mafi yawan siyan maganin bawan Allah nan shi ke siya? Dan haka dan Allah ya masa bud'i na abin aure idan yaje bid'ar ya dawo zan basa Ibtisam, sabida nasan ba zata tozarta ba.â€
Laraba taja tsaki tana had'e gira sama da ta k'asa, ta ce“Ai kaji hamm wannan yaron mai bak'ar zuciya da girman kan tsiya kamar ba d'an Malam Adamu mai panpo ba, da Hansatu mai waina ba, yaron da zai shiga duniya zamu jira? Wlh da wannan gwara kawai taje wajan Yaya Karime d'in.â€
Tanko ya girgiza kansa ya ce“Allah ya sawwaqa.â€
Ibtisam ta ajiye bokitin tana langwab'ar da kanta gefe,ta shagwab'e fuska tana diddira k'afafunta cikin zazzak'ar muryanta ta ce“Baba ni dai Ku sakamun albarka, zata bini, ni ba inda zanje Cameron ta yi nisa ni dai ina sonku ba zanyi nesa daku ba.â€
Tanko ya ce“Insha Allahu albarka na tare dake.†tsalle tai ta shiga d'akin da yake mallakinsu ita da k'anninta, ta shirya domin zuwa wajan sahibinta.
“Tanko ni sai ka tsinemin nabi duniya kaji.†ko takanta bai bi ba ya shiga cikin d'akin domin d'aukar abinda ya kawo shi.

Unguwan Moray Gidane na jar k'asa shima, wanda yake d'akuke da dakuna hud'u acikinsa.
Na farko yanada kewayensa, daban yayin da sauran suke game a kewaye d'aya. Na Malam Adamu sai na inna Hansatu mai waina da na Sailuba Deluwa.
Gida sai shige da fice ake 'yan siyan waina, inna mai waina macace 'yar kimanin shekaru 45 kyakkyawace bak'ar buzuwa, mai shegen surutu da son kud'in tsiya, amman ta iya neman na kanta.
Deluwa tana gefe tana kallon ikon Allah, inna ta washe baki sai labarin tafiyar da Ja'afar zaiyi take fad'awa duk wanda ya shigo.
“Dan Allah Ku jira na k'arasa bawa Hashimu jinya yake bai jima awaje.
Ni kuwa Hashimu na ce Anya ta rasulu ba ciwon daji bane kuwa?â€
Hashimu haushinta yaji sosai yaga me ruwanta da lamarinsu daga zuwa siyan waina?
“A'aâ€
Kawai ya ce bai sake tanka mata ba, dan yana jin shayin Ja'afar da sai ya gayamata mgna, toh gayen ne ba sauqi mugun tsoron sa ake, shegen k'arfine da shi, ga saurin hannu, bugu d'aya idan yama sai ka kai k'asa.
har ta basa wainarsa ya tafi bai kulataba ta gama surutun .
Cikin sauri yake had'a kod'add'un kayansa, wad'anda suke wanke tass sunsha turare, ya zuba cikin jakarsa ta matafiya wacce ta d'an ji jiki.
Matashine d'an kimanin shekaru 28 bak'ine kyakkyawa mai manyan idanu masu haske, akwai dogon hanci, yanada fad'in fuska kad'an, wacce take zagaye da saje mai kyau.
labb'ansa bak'ak'e kamar mai shan sigari, yanada yalwatacciyar sumar kai da ta ido haka gira, yanada tsayi sosai ingarma namijine sosai yanada cikar zati, mai k'iran k'arfafa jikinsa duk a mummurd'e.
Ma sha Allah yanada kyau sosai duk da yana bak'i kyawunsa na musamman ne, ga kwarjini da farin jinin 'yan mata har mazan ma, nason abuta da shi, matsalarsa shi d'an ra'ayine, ko za'a mallaka masa duniya idan abu bai masa ba, toh an wuce wajan.
Sosai 'ya'yan masu kud'i suke rubibinsa da masa kyaututuka amman ko sau d'aya bai amsa ba bai kuma basu dama, Ibtisam har kusan kasheta wata yarinya tai zata taketa da mota akansa sbd itace zab'insa.
shiru² ne bai fiye mgna ba sam arayuwarsa, yasan neman na kasan bai k'arasa kartuba sabida rashin larewa duk yadda yake da masifar ilimi tinda ya yi (BAC) har sau 3 bai samuba ya watsar sabida zuciyar masifa yakeda, sam baison raini ko zaka mallaka masa duniya, ya sani sarai aikinsu ake siyarwa 'ya'yan masu kud'i shiyasa yake masifar jin haushin masu kud'i, sun tara sunacin gumusun suda 'ya'yansu bai ishesu ba ilimin nasu ma sai an siyar musu, shiyasa sam baya alak'a da mai kud'i.
Ganin karatun bai d'oreba ya shiga neman kud'insa sana'a kowace iri indai ta halal ce yi yake, ba ruwansa da girman kai, raini ne bai so.
Ya idar da shirinsa yana sanye da k'ananun kaya sun masa kyau duk da ba sabbi bane, amman sun amshi murd'add'an jikinsa.
Yana tsakiya da fesa turare ta fad'o d'akin kamar an jefota.
Jikinsa ta zube ta k'ank'ameshi tana sakin kuka mai cin rai.
Wata irin zazzafar iska ya feso daga bakinsa, yana ciza bak'ak'en lips d'insa, ya d'ago da kanta ya kafamawa kyakkyawar fuskanta, manyan fitinannun idanunsa, komai baice ba ya zagaye bayenta da hannayensa, yana bugawa asannu, alamar lallashi.
Kuka take harda shashek'a.
Wani irin fitinannan numfashi ya fizgo dakyat, ya fesar, cikin kamalarsa, da muryasa mai fitar da amon dad'i cikin tausasa murya ya kira“Mon cÅ“ur!â€
Wani irin zirrrrr yarrrr Ibtisam taji adukkan illahirin jikinta, wanda sai da tai saurin nutsa kanta tsakiyar faffad'an k'irjinsa.
Cikin shashek'ar kuka ta amsa“ Na'am Mon Amour.â€
Cikin kunnenta ya rad'a mata kina sona?â€
Kai tsaye tace“Har na koma wajan mahaliccina Mon Amour ina sonka.â€
Wani guntin smile ya saki wanda ya bayyana fararen hak'oransa, ya kuma k'awata masa kyawun fuskar ta shi, ya janyeta jikinsa ya kamo hannunta suka zauna gefen yamutsatsar katifarsa.
Ya ce“Abdan muna tare ko wata uku nayi idan na samo kud'in auremu zan dawo muyi aure sai mu koma ok?â€
Kai ta jinjina tana kwantar da kanta saman cinyarsa tana mak'ale da hannunsa cikin nata.
Ahankali ta shiga jero masa kyawawan addu'o'i yana amsawa da Ameen can k'asan labb'ansa.
Kod'ad'iyar wayarsa kira Itel ta d'auki ringing.
Ganin sunan ya saka shi d'aukan kiran yana sallama.
Ko me akace oho ya amsa da “Ok 15 minutes ina zuwa.â€
Ibtisam ta sanya masa kuka tana shigewa jikinsa.
“Pls my Ibtisam.â€
Dakyat ya iya furta hakan yana d'ago da kanta ya shiga shanye mata hawayen fuskarta da harshensa yana buga bayanta.
Kiss ya mata agoshinta, bayan ya zuk'e hawayen ahankali ya furta“Na baki amanar kanki Mon cÅ“ur, ki kularmin da kanki, zan kular miki da kaina.â€
Cikin kukan dake son taso mata ta ce“Namaka alk'awali duk runtsi Mon Amour zan rik'ema amanata.â€
Labb'anta ya sumbata ya mik'ar da ita, kud'in wajansa ya raba abiyu ya bata raba ya ce“Kiyi buk'atunki zan turo miki wasu da zaran mun isa lafiya na samu akin k'wadago mai kawo kud'i, sai ki sai waya da layi muna mgna kafin na dawo...â€
Ya k'arashe mgnar yana jan dogon numfashin uwar mgnar da ya yi dan dan ita kawai take saka shi dogon sharhi.
Ibtisam ta langwab'ar da kai gefe ta girgiza kai ta ce“A'a mon amour ka bar shi kaga wasu ma na kawomaka jiya aka kawoma Anna kud'in adashe sai na sato rabi na kawo maka....â€
Wani mugun kallo ya watsa mata, wanda yasa ta mak'ale sauran mgnar bakinta, ta sadda kanta k'asa tana wasa da yatsar hannunsa.
Janye hannunsa yay ya Kama harshen hijab d'inta ya d'aure mata kud'in wajansa, ya d'ago fuskarta cikin kakkausar murya ya ce“D'ago kanki kalleni.â€
Ya k'arashe mgnar yana tsura mata fitinannun idanunsa.
Ibtisam tsoronsa ya kamata sabida bai tab'a mata hakan ba.
Cikin rauni ta d'ago ta sauke k'wayar idanunta cikin fitinannun idanunsa.
Runtse Nata idanun tai tana fad'in.
Mon amour kayi hkr wlh ban tab'a satar mata kud'iba sai yau dan na baka.â€
Labb'anta ya kamo ya murza ta Saki qara tana k'amk'ameshi.
“Ni ba lusarin namiji bane da har zaki sato kud'i agidanku ki kawo min karki kuma tab'a abinda ba'a baki ba, maza jeki mayar dasu idan kika d'aukeso bana son munafukin mutum, nasani ba halinki bane kinyi dan nine, amman karki kuma, sannan banda kula samari ok?†Ya k'arashe mgnar yana zaro zoben azurfar hannunsa na k'aramar yatsarsa kasancewar zoben 2, ya kamo farin hannunta ya sanya mata a yatsarta, ya sumbaci yatsar me zoben, ya ce“Amanata kinji.â€
Ibtisam tace“Insha Allahu mon amour kuma zance Anna tai hkr na mata laifi amman bazan kuma ba. â€
“Yauwa matana muje toh.â€
Hannunta ya kamata suka fito har waje ya rakota ya ce“Ki kwance kud'in harshen hijib.â€
Hawaye ya fara bin kyakkyawar fuskarta ya had'e raina yana zura hannayensa cikin aljihun jeans d'insa ya ce“Ok na fasa tafiyar mu zauna acikin talaucin har iyayanki su gaji da jirana su aurama wani ke, daga nan ciwon zuciya ya kasheni ko?â€
Da sauri ta Saki murmushi tana girgiza kai ta ce“Mon amour fatan alkahiri inata jirnka kaj?â€

Wani sansanyan kallo mai tsayawa azuciya ya mata ya ce“Je t'aime mon cÅ“ur bye.â€
Da gudu tabar wajan tana sakin kuka.
Goshinsa ya dafe ya furta“Ya Rabbi!â€
Gida ya koma ya d'auko kayansa ya rufe k'ofarsa kasancewar k'annensa mazan duk suna school.
Cikin sa'a yanzu ba kowa sai inna da Deluwa da k'annensa biyu mata masu aure sunzo masa bankwana.
Sadiya da Ramla suka mik'e cikin farin ciki suka rungumesa kamar wasu 'yan yara.
Inna ta ce“Kufa baku hankali ni wlh wannan d'abi'ar ta turawa bata burgeni k'arti gotai-gotai ana wani rungume².â€
Deluwa ta ce“Haba! Hansatu me kike hakane? K'annensa Ramla uba d'aya Sadiya uwa d'aya uba d'aya meye idan ya rungumesu? Kina abu kamar ba ilimi.â€
Ja'afar ya kalli Deluwa Sam baiji dad'i ba shi fa duk yadda inna mai waina take uwarsa ce baison agayamata mgna, duk rabi gaskiya aka fad'a.
Fuska ba yawo ba fallasa ya ce“Toh Ku sakeni mana. Mom ina kwananku, ni na fito zan fice ayimana addu'a.†ya k'arashe mgnar yana ajiye jakar nasa ya isa wajan inna ya zauna kusanta ya kwantar da kansa cinyarta.
daman haka yanke sun San halinsa.
Deluwa ta ce“Allah ya tsare Ja'afar Allah yasa fitarka ta zama babban alkhairi.â€
Inna mai waina ta washe baki tana tura waina d'aya bakin ta ce“Ameen ya Rabbi amin Deluwa mmn Ramla.â€
Ta idar da magnar tana tauna wainar ta shafi sumar Ja'afar mai taushi ta ce“Bak'in buzuna, jarumin yaro wanda yasan ciwon kansa da neman gumin halak d'insa, Ya Allah ina rok'onka ka dubi d'ana ka saka wannan tafiyar ta zama silar arzik'insa tinda masu abun sun danne sun hanama 'ya'yanmu su k'arasa karatunsu dan karsu kamosu. Toh Allah ka dubemu muma Allah kasa yarona yaje garin da zai zama silar arzik'insa, ya Allah kasa ya nemi halalinsa duk abinda zai zame masa fitina acikin rayuwarsa Allah ka masa katangar k'arfe da shi, Allah kasa munada rabon wasu ci aijkinmu, Allah ka had'ashi da zuk'ek'iyar mace musha biki tinda dai Labara na min kallon banza bani ba had'a zuri'a da irin masifa barni da surutuna...â€
Ja'afar yay saurin d'agowa ya rufe mata baki da tattausan hannunsa yana had'e rai ya ce“Haba! Inna me kike hakane? Banson irin haka ni duk duniya Ibtisam nake so kuma zan fita neman abinda zan aureta, Ngd da addu'a amman ki cire ta had'uwa da wata sabida ba shi zai fitar daniba.â€
Inna sosai take shakk'ar d'an Nata sabida bai mgna biyu, tabbas tasan iya gaskiyar ya fad'a, itako kaf cikin 'ya'yanta tafi sonsa ko dan shine d'an farko.
Baki ta washe ta ce“Toh bak'in buzuna Allah ya tsare amman kasan ko bayan ka auri Ibtisama take kowa sai nima na zab'o kalata bak'ar buzuwa ka aura sabida kar amantada iri?â€
Kansa ya dafe shifa ya tsani zancan mace idan ba Ibtisam d'insa ba.
Dan mgnar ta wuce ya ce“Naji abar maganar ni zan wuce, Ramla Sadiya zan kiraku insha Allah, bari na biya wajan Baba panpo muyi sallama. Deluwa ta ce“Allah ya tsare Ja'afar akula da ibada akiyaye sabon Allah.â€
Sosai Ja'afar yaji dad'in nasihar wacce inna ma bata masa sai addu'ar ya yi dai kud'i.
Kai ya girgiza ya musu sallama har k'ofar gida suka rako shi inna harda kuka Ana fatar majina. Dakyat ya lallasheta ya tafi.
Dattijone bak'in buzu kyakkyawa fuskar shi mai cike da kamala, d'an kimanin shekaru 55 zaune saman kujera cikin rumfa wajan siyar da ruwansa masu baro sai cikawa suke.
Ja'afar yay ma masu baro sallama ya isa wajan mahaifin nasa wanda suke tsananin kama da shi.
Rusunawa yay yana gaishesa.
Malam Adamu ya fad'ad'a murmushinsa ya ce“Yaron kirki an fito?â€
Cikin girmamawa ya ce“Eh Baaba zamu wuce ayimin aikin gafara idan nayi ba daidai ba Baaba.â€
Malam Adamu ya shafi kansa ya ce“Ai kai Ja'afar idan nace ka b'atamin naso kaina, Allah ya maka albarka ya baka wajan kirki Allah baka halalinka, ya tsareka da dukkan abin k'i Allah ya had'aka da mutane nagari, sannan ka rik'e ibada aduk inda kake kaji tsoron Allah aduk inda kake ka rik'e amanar duk wanda ya yarda dakai ya baka Amana, toh ka riqe da hannun biyu, Allah baka abinda zaka nema na halak, munyi mgna da Tanko ya ce ko yaushe zasu jiraka tinda yarinya kai take so kaima haka, dan haka karka manta da amana kaji?â€
Ja'afar yay k'asa da kansa ya ce“Insha Allahu Baaba bazan canza daga yadda kuka saninba.â€
Addu'a ya sake masa ya basa kud'i yak'i amsa ya tafi cike da kewar mahaifin nasa.
Yana zuwa wajan da sukayi mahad'a su ukune masu tafiyar kai tsaye, tashar mota suka nufa, wacce zata kawosu madaoua, sabida bus d'in asuba ya barsu da ido biyu zasu shiga damagaram, amman yanzu sai dare.
Yanzu sai su shiga ta azuhur zuwa damagaram daga can su nufi diffa da asubah daga nan sai su zab'i wajan zuwa neman halak Cameron ko Tchad.
B'angaran Ibtisam tana zuwa gida ta mayarwa Laraba kud'inta ta ajiye b'oye wanda Ja'afar ya bata idan Batan yazo ta basa, fad'a saman yaluluwar katifarta tana kuka mai cin zuciya harda ihu take.
Labara na wanki ta ce“Wallahi ubanki zanci idan na shigo d'akin nan.â€
Ibtisam kukanta ta ci gaba tana kiran Ja'afar, sai da Laraba ta jibga mata kashi tai shiru.

*K'asar Tchad*
(Ndjamena)
Kamar yadda Abdul Majeed ya Saba zuwa asibiti duba marasa lafiya, ya rabawa masu k'armin k'arfi temako na kud'i wanda zai ishesu cin abinci da maguguna haka yauma ya yi, a _*Hôpital de la Renaissance*_
anata saka masa albarka da addu'ar gamawa da duniya lafiya, yayin da wajan ya kasance har 'yan jarida amman ya rok'i alfarmar karsu d'auke shi video, kasancewarsa mutum mai daraja haka kuwa akayi sun dai d'auki rahotannin jama'a da yadda 'yan uwan majinyatan suke kukan dad'i daman wasun acikin mawuyacin hali suke, sunzo daga garuruwa daban-daban.
Daga asibitin kai tsaye ya wuce ( *MOURSAL*) unguwan da ake gina masa tamfatsetsiyar asibitin yara wacce yakeso ya tallafawa marasa k'arfi iyayan yara, ciwo ko wane irine na yaro kyauta za'a masa magani.
Ko Rabin ginin ba'a gamaba dan kullun cikin d'aukan ma'aikata yake amman tuni ya sanya mata suna ( *RAHMA HOSPITAL TCHAD*) da ya lek'o komai na tafiya yadda akeso, daga nan ma ba gida ya nufa ba.
Misalin k'arfe 2 pm.
Jaddatu bayan sallar azuhur ta yi addu'o'inta ta mik'e ta fito falon ta ga wayam ba kowa.
“Latifa!â€
Ta Kira da k'arfi.
Latifa cikin sa'a ta jiyo kiran ta fito daga kitchen, daman bata tafi b'angara su ba, ta amsa kiran ta fito aguje.
“Jaddatu ga ni.â€
“Ke hau sama je ki dubamin Rahma lafiya, na tura Raiyana ta kirata tin lokacin da mukaci abinci bata zo ba, Abienta ya Kira sau uku ya ce baya samunta aduba masa ita, yi sauri kiramin ita. Saura kije kina gwalo idanu kalli banzan kalli wofi! karkizo ki fad'amin me take asaman tak'i zauwa taci abinci.â€
Latifa ta ce“Toh bari naje da sauri.â€
Tana shirin mik'ewa Raiyana ta iso bakinta d'auke da sallama.
Jaddatu ta amsa tana fad'in.
“Wai bakije kiran Rahma ba?â€
Raiyana ta zauna kusan Jaddatu tana matsar k'walla ta ce“Ummi!â€

*DATTIJON ARZIK'I* N300 katin MTN ta wannan number *+22796515805*


TSINTACCIYA
Nimcyluv

SULTAN
mss flower

BAK'AR FATA
AUTAR MANYA



Gaba É—aya 800
Via 6850917335 Na'ima Shu'aibu Sulaiman Fidelity Bank, masu tura kati 08167888934 ga ƴan uwa na Niger +22796515805 za ku tuntuɓa. To show evidence of payment 08142105218


*Real Ladingo+22796515805* For more information😇

_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
2/2/22, 09:18 - Buhainat: _*DATTIJON ARZIƘI*_


*BY*
_Rahma ladingo Ummu Fareesa😘_

*🔥FITATTU HUƊU🔥*


_*HOME OF QUALITIES WRITERS ASSOCIATION*_


*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*


_*cнapтer 7&8*_


“Wallahi bansan me na ma Ummi k'arama ba yau. nayita bugun k'ofa ta bud'e min tak'i na kira Abienta ina sheda masa ya kira awaya ta fito ta ci abinci, ya ce bai samunta.
Yanzu da na gama sallah na koma wajanta, wlh tana jina ina knocking k'ofarta, har sai da naji ta yi mgna amman tak'i bud'e min.
Ummi don Allah ya zanyi nasan laifin da na ma daughter? Wlh ban son b'acin rantaâ€.
Ta k'arashe mgnar tana sakin kukan kissa.
Jaddatu Rahamu ta ce“Ikon Allah! Kai! Gaskiya ba banza ba, Rahma bata nuna ma mutum irin wannan halin nata sai da k'wak'waran dalili, sai idan ak'asar turai da take karatu suka b'ata mana ita.
Ke Latifa! Zo nan Raiyana ku temaka min na hau saman na fito da ita da kaina.â€
Latifa ta ce“Innalilahi! Jaddatu ta k'ak'a za ki iya hawa beni har hawa biyu ahaka? Wlh ni dai ba zanyi aikin da na saniba, bari naje na dubota.â€
Jaddatu cike da jin haushin Latifa ta kwad'a mata sandar hannunta, tana fad'in.
“Mugun nufinki ya qare akanki, munafukar banza wato sakoni zakuyi na fad'o na mutu ko? Wlh yau sai kinbar gidan nan Latifa.â€
Raiyana ta danne dariyata ganin yadda zafin sandar da Jaddatu ta kwad'a mata ya gigitata, ta nufi hanyar beni tana fad'in.
“Wlh Jaddatu ko yanka naman jikina kike bazan bar gidan ba, idan ba waje aka fitar daniba, bazaki rabani da neman abinci na ba, bari na kirawo Rahma ita ce zata rabamu dake.â€
Jaddatu tana dogara sanda ta nufi hanyar beni, tana fad'in.
“Latifa shin ke mayya ce ne don Allah? â€
Matattaka Latifa ta fara takawa ta ce“Eh akan neman na kaina ba!â€
Raiyana ta rik'e Jaddatu ta ce“Ummi don Allah kiyi hkr bari na bi bayanta, insha Allah zamu fito da Ummi k'arama.â€
Da kyat Jaddatu ta zauna Raiyana ta bi bayan Latifa, tana kisima abubuwa dayawa acikin zuciyarta.

Tsaye take gaban shower ruwa masu d'umi suna sauka tsakiyar kanta, amman gashinta ya na lullub'e cikin hular leda bataso ya jik'e, idanunta a lomshe sai tagwayen ajiyar zuciya take saukewa, ajere-ajere.
Sosai take jin dad'in yadda ruwan yake ratsa kowane kafar hudodin gashin jikinta.
Murya Latifa taji tana bugun k'ofa tare da fad'in.
“Uwar d'akina don Allah ki bud'e ga Jaddatu can na k'ok'arin hawa beni.â€
Rahma jin abinda Latifa ta ce ya sakata saurin bud'e kyawawan k'ananun idanunta, masu tsananin lumshewa tai saurin janyo towel mai girma ta d'aura ta fito cikin sassarfa.
K'ofar ta bud'e.
Raiyana da Latifa tsaye, suna rarraba idanu.
Fuskar ba yabo ba fallasa cikin zazzak'ar muryata ta ce.
“Uhm! Tana ina Jaddatina? Keko Latifa hawayen me kike? Jaddati barazana take dan na sauka nasan halinta da son rayuwarta, kamar ba zata mutuba!ba zata hayo ba, ga ninan zuwa.†Latifa ta ce“Wlh sanda ta kwad'amin wai sai nabar gidan nan, don Allah zo ki rabani da ita.â€
Rahma ta dafe kanta ta ce“Oh! Ya Rabbi! Ok ina zuwa.â€
Ta k'arashe mgnar tana k'ok'arin juyawa, dan sun saka ta yi mgna sosai.
Raiyana ta ce“ daughter! Don Allah me na miki kike fushi da ni?â€
Rahma ta juyo ta saki guntin smile wanda ya k'awata fuskarta ta shafi fuskar Raiyana cikin sanyinta ta ce“Ammi ba komai fa, kawai yau ban tashi da yanayi me dad'i bane ba.â€
“Ayyah! Sannu toh ki shirya ki fito don Allah, Abineki nata kiran Ummi.â€
Kai ta d'aga ta juya ciki, Latifa ta zauna k'ofar d'akin ta ce“Aunty Raiyana kije zan jira ta fito muje tare, ita kad'ai zata rabani da Jaddatu.â€
Raiyana ta tafi tana dariyar mugunta.
Wayanta ta kunna ta shiga shirya jikinta, cikin mintinan da basu wuce biyar ba ta shirya cikin riga da siket kayan Indian, ruwan toka abinka da fara fata, sosai su ka mata kyau, ta fesa turare ta saki gashinta, saura gefen fuskarta sauran har tsakiyan banyata, ta yi kyau sosai kamar ka saceta ka gudu, sai baza k'amshi take.
Fararen hannunta masu zanen Jan lalle ta sanya ta d'auki wayanta, fuskarta ba wata walwala ta latsa number Abineta ta danna masa Kira, ta nufi k'ofar fiti.

Zaune yake tsakiyar manyan mutanen da suke gudanar da meeting, harda gwamna, yaji ringing d'in wayan da mafi yawanci da layin suke waya da Rahma, sam ya manta bai bar wayan cikin mota ba, yadda yabar sauran biyun.
B'oyayyar ajiyar zuciya ya sauke, lokaci da ya zaro wayan cikin aljihun gaban rigansa. Kallo d'aya yama kiran ya sanya wayan a silent, yana sauke wani irin fitinannan numfashi ya Kira sunan Allah cikin ransa, yasan Baby ummi na cike da kewarsa.

Rahma jin bai d'aga kiran ba, tai rau-rau da k'ananun idanunta masu mutuk'ar kyawu farare, ta bud'e k'ofar ta fito.
Kallon Latifa tai tana zaune sai zazzaro idanu take kamar tama sarki k'arya.
Da hannu tama Latifa nuni ta mik'e su tafi.
“Yauwa uwar d'akina maganin kukana, don Allah ki lallashi Jaddatu ta barni ina son zaman gidan.â€
Rahma tai murmushi suka nufi matattakalar benin.

Raiyana kuwa d'akinta ta shige ta zauna tana kiran number Auntie Saro.
Bugu d'aya Auntie Saro ta d'aga daga can tana fad'in.
“Toh uwar gajan hkr wani abun ko?â€
Raiyana ta ce“Humm Auntie bazaki saurara kiji da me nazo ba? Nifa kinga
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment