Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

fushi dani nafi Sonka akansa ai.â€
Tallafo fuskarta yay zaiyi mgna ya ga ta kafe jajayen 'kananun la'bbansa da 'kananun idanunta masu saka shi shauki,tana musmus da 'dan 'karamin bakinta, idanunta sun tara ruwa, harara ya zabga mata ta sadda kanta qasa tana wasa zabon hannunsa.
Akunnen ya ra'da mata.
“Idan na gane kina sonsa Babyna?â€
Da sauri ta 'dago rinannun idanunta ta kalli Abie sai tai saurin runtse idanunta, sbd yadda bugun zuciyarta ya tsananta kallon da Abie ya mata 'kwa'kwaluwarta bazata iya daukarsa ba, fuskarta ta tura cikin 'kirjinsa tana sauke ajiyar zuciya ta zagaye hannayenta bayansa.
Ahankali ta kirasa “Abienah!â€
Murmushi yay, ya saka mata babban hijab 'din da yazo da shi ya 'dauketa cak kamar baby ya mannata 'kirjinsa ya nufi 'kofar fita.
Kallonsa take ba ko 'kiftawa wani irin abu me girma takeji wanda ta rasa meye shi abun ji take tamkar bazata iya rayuwa ba Abienta ba gashi watarana gida mijinta zai badata.
Hawaye suka wanke mata fuska ta sanya tafin hannunta tana shafa sajan fuskarshi tana Jan dogon hancinsa.
Kallonta yay ya 'daga mata gira, ya ce “No! Bana son kuka bari zamuyi mgna zuwa dare OK baby ummina?â€
Ya 'karashe mgnar yana 'daga ma gira ya karkace kansa.
Rahma tai saurin goge hawayen sai ta tsinci kanta da sakin dariya tana jan gemunsa.
Duk inda ya gilma cikin asibitin kallonsu ake cike da sha'awa.
Baya ya zaunar da ita Meerah ta zauna kusanta shi kuma yana gaba kusan direba suka nufi gida, Rahma jinta take kamar ma batayi ciwo ba,ta shiga wani irin yanayi me da'di ganin Abienta baiyi fushi da ita ba.

A can Gabon kuwa, Nura na isowa bakin gate Aishatu ta ce“Yauwa Nura bari na 'dauko kayan sai mu juya ban 5 minutes. â€
Ta fa'da tana 'balle murfin motar ta nufi cikin gidan ta qaramin gate ta shiga.

Motar Ma'aruf ta kalla ta girgiza kanta ta ce“Ko me ya tsayar da shi, yanzu hka bacci yake hamm wannan mijin nawa 'dan hutune, Allah na gode maka alamun shiriya qarara sun bayyana wajan Masoyi.â€
Tai murmushi ta nufi hanyar da zata sadata da falon.
Ido biyu tai da takalmin mace a'kofar falon, taji 'kirjinta ya buga dammm! Da sauri ta mur'da 'kofar jin ihu ta kutsa cikin falon........!

_💃ðŸ»'Yar Ajin Ma Sha Allah🥰_


_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
3/12/22, 17:42 - Buhainat: ```D A```

```61&62```

_*My Sisters Don Allah Don Darajar Annabi Karki Karanta Idan Baki Biya Ba, Na Ku'dine Idan Kinga Yana Yawo Na Satane Ga Hanyar Da Za Ki Samu Naki Akan.😟👉ðŸ¼300N +22796515805*_

```Wow! 'Yan Paid Group nah wlh banda bakin yi muku gidiya sbd yadda kuke zumabin ruwan sharhi da comments billahi abin na matuqar burgeni, yana sakani nisha'di, hakan na nuna min kuna anfanu da saqonnin cikin labarin da darusan duk kuna 'dauka, My Habibaties ina yinku much love Jazakumullahu Khairan.💃ðŸ»â¤ï¸â¤ï¸â¤ï¸ ```
Babu editing
☹ï¸

Abun da idanun Aishatu ne suka nuna mata taqi yarda ta kifawa kanta mari, tana mintsinin hannunta, ta ji eh ita ce ba mafarki take ba, amman taqi yarda da hakan.
Cikin 'barin jiki ta qaraso dab dasu idanunta na neman rufewa, haka ta daure ta tsaresu da ido, eh tabbas Ma'aruf mijinta shine saman Rabi'ah 'kawarta aminiyarta wacce ta aminta, ta kamasu tirmi da ta'barya.
Baya ta matsa da sauri tana toshe kunnuwanta, daman kuka sam bazata iya ba adaidai wannan lokacin.
Cikin fitar hayyaci ta ce“Me ya kamata nayi musu?â€
Kai ta girgiza ta ce“Babu tabbas ko ba mgna ka zuba ido ta ishi me hankali. Haqiqa na tafka kuskur me girma na auren Ma'aruf sai abu na biyu aminci da Rabi'ah duk da kuwa ana garga'dina akan mugayan halayanta naqi sbd bana shedar abinda idanuwana basu gani ba! Tih wai tin yaushe suke aikata masha'a?â€
Zaune tai dabas can nesa dasu ta basu baya, jin yadda Rabi'ah da Ma'aruf suke zuba sambatu ya saka ta gigice ta 'dimauce ta haukace ta fita daga sahun mutane dishi-dishi take gani, kunnuwanta sun 'dauke 'dif idanunta sun rufe ruf komai ya tsaya mata, take taji cikinta ya mur'da taji wani abu kamar lema na binta gefen cinyoyinta daga hakan bata sake sanin inda kanta yake ba.!
Sai da suka kwashe tsawon 50 minutes suna abu 'daya kafin su samu gamsuwa.
Ma'aruf ya mirgina gefe yana maida numfashi, Rabi'ah gabanta taji yana mata azabar zogi dakyar take motsawa sabida caccakar da ya mata bata wasa ba, tasan badan qarfin magugunan da ta shaba ta matsa tabbas da ta jima da sakin kukan wahala.
Miqewa yay tsaye yana dafe kansa zuciyarsa wani iri ba da'di, ya kwashi kayansa ya nufi bedroom.
Watsi yay da kayan sakammakon ganin Aishatu babu rai cikin jini ya 'kurma wani irin ihu yana fa'din.
“Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Aishatu! Me ya sameki don girman Allah karki min haka.â€
Ya 'karashe mgnar yana cicci'barta zai nufi waje, sam ya gigice ya manta ba kaya ajikinsa.
Rabi'ah wacce tai mutuwar tsaye tsabar tashin hankali ya sakata sakin fitsari har wani irin amai yake taso mata, ya akayi Aishatu ta dawo? Yanzu Aishatu ta kamata da mijinta suna aikata masha'a?
“Wayyo Allah na shiga uku na lalace son zuciya 'bacinta! Ma'aruf tsirara kake ka saka kaya don Allah.â€
Ta 'karashe mgnar tana saka kayanta tai waje aguje sbd batajin zata iya kwana agarin nan yau sbd abun kunyar da tai babba ne, sai dai toh ina zata?
Ma'aruf haka ya maida kayansa cikin najasa ya 'dauki Aishatu yana kuka kamar yaro 'karami ya fita.
Nura wanda ya gaji da zaman mota ya fito ya shigo suna zaune me gadi ganin Ma'aruf da Aishatu cikin jini ya 'daga musu hankali.
'Kofa suka bu'de masa Nura da gudu ya nufi motar ya bu'de masa ya shigar da ita shima ya shiga yaja suka nufi hospital.

*Tchad*
Ibtisam lokacin da ta shigo falon duk suna falon Jaddatu Hanan Rayyana Laraba, duk ana fira.
Sallama tai suka amsa, ta gaishesu ta zauna kusan mahaifiyarta.
Jaddatu ta ce“Har kin dawo?â€
Ibtisam bata san me ta ce ba kai kawai ta 'daga Rayyana ce ta fassara mata sbd tana jin hausa.
Ibtisam ta kalli hoton Abie wani tam'kememe yana sanye da wata farar shaddah 'dinkin tazarce ya yi masifar kyau, 'kayataccan murmushi akan fuskarshi.
Idanu ta lumshe ta sake bu'de ta sauke idanunta akan na shi da Rahma fara'ar fuskarta ta kau, tai saurin kauda kanta tana jin wani irin zafi aranta, sam aganinta basu daceba sbd kyawunsu ya yi yawa duk da ta ga suna Kama, amman dai ta kasa yarda 'diyarsa ce duk da kuwa tasan zai haifetan.
Rayyana ta ganeta sarai da gangan ta ce“Ibtisam ya dai? Ko hoton Ummi da Abie ya burgeki?â€
Murmushin yaqe tai ta ce“Eh sunyi kyau miji da matane ko?â€
Rayyana taji gabanta ya fa'di tai saurin cewa.
“A'a babanta ne.â€
Ibtisam ta sauke ajiyar zuciya a'boye ta ce“Uhmm! Sunyi kyau.â€
Laraba ta zubama 'yarta idanu sbd abin nata yanzu ya daina bata mamaki tsoro yake bata.
Jaddatu ta kalli Raiyana tana riqe baki ta ce“Ikon Allah Rayyana wani munafurcin kike son 'kullawa kika sauya harshe?“
Rayyana ta miqe ta ce“A'a Allah bada hkr Ummi ba wani munafurci da akayi wlh.â€
Ta sanya kai ta haye bene.
Ibtisam ji tai bazata iya zaman falon ba ta miqe ta nufi bedroom 'dinsu.
Laraba tabi bayanta.
Tana zuwa ta rufeta da fa'da.
“Ashe ke bakida hankali sakarace shin ke mayyace ne Ibtisam ko me? Kina kallon mutum har matarsa ta gane.â€
Ibtisam ta ruqo idanu ta ce“Oh! Matarsa ce wannan 'din? Humm! Yo dame ta fini idan ba fari da da gashi da shekaru ba, wlh bata fini da komai ba...â€
Baki Laraba ta buge mata.
Ibtisam ta saki kuka ta ce“Don Allah ki rabu dani Anna idan bazaki tausaya min ba wlh tallahi ba laifi na bane ina sonsa ne bansan ya zanyi ba.â€
Ta fa'da cikin kuka tana shafa zoben hannunta tana kuka.
Laraba tagumi tai ta sakata gaba dan ta ga so take ta kashe mata aure da qarfin tsiya.
Cikin fusata ta ce“Wlh Allah idan kika kashemin aure ta qarfi Ibtisam bazan yafe miki ba, ki dawo hayyacinki.â€
Ibtisam ta rungume Laraba ta ce“Ki tayani da addu'a.â€

*Espanol*
Su na zuwa gida Meerah ta ha'dama Rahma ruwan wanka ta sake wanka, ta sanya riga doguwa green colour marar nauyi me qaramin hannu, tana zuba 'kamshi jikinta ba 'kwari, haka tai sallah ta fito falon wanda Meerah ta gyara ta kunna turaren wuta sai uban 'kamshi yake, ga wani irin sanyi me da'di.
Saman sofa ta zube tana kiran Meerah.
Gabanta zube tana mata sannu da jikin.
Rahma cikin sanyinta ta ce“Ina wayana? Abie ya fitane tinda muka zo banjin motsinsa ba?â€
Meerah ta ce “A'a yaje dai masallaci ya dawo ina ga yana can sama bedroom 'dinsa.â€
Meerah bata rufe baki ba sukaji qaran takunsa yana nufo falon.
Rahma ta 'kurama corridor d'in idanu, tana fa'din.
“Meerah jeki aikin ki pls kawomin apple bakina 'daci wlh.â€
Ta 'karashe mgnar tana langwa'bar da kanta, daidai lokacin suka ha'da idanu, da Abienta.
Tsura masa idanu tai yana sanye da jallabiya milk colour tai masa kyau gashin kansa sai sheqi yake, yana zuba wani irin fitinannan 'kamshi.
Laptop 'din hannunsa ya ajiye saman center table, ya zauna dab da Rahma ya kamo hannayenta ya sumbata, yana murza 'karamar yatsarta, ya hura mata iskar bakinsa saman idanunta.
Firgigit tai ta dawo hayyacinta.
Shagwa'be fuska tai tana turo 'dan qaramin bakinta gaba ta ce“Abienah kayi kyau wlh kamar saurayi Abie nah, kamar na qaroma 'yan mata uku ka cike hu'su har Ammi.â€
Ido 'daya ya kashe mata, yana gyara mata gashin da ya zube gefen fuskarta, ya sumbaci tsakiyar kanta mai fitar 'kamshi man da take anfani da shi.
Dab kunnenta ya ra'da mata “Ok kiyi ta kallon Abienki ai nakine ke 'daya Babyn Abinta Ummin Abienta, kul naji bana son wasu matan koda kuwa 'yan gold ne na yafe ruhina ta isheni.â€
Yadda yake mata mgnar bakinsa dab da kunnenta har fatar bakinsa na ta'bo fatar kumnenta kamar yana goga mata da gangan ya sanya Rahma ta 'kyal'kyale da dariya tana qamqame Abie tana saqalo hannayenta wuyansa ta tsira masa 'kananun kyawawan idanunta tana dariya.
Shima kallonta yake ya 'dora hannunsa saman kyakkyawar fuskarta yana shafawa yana Jan siririn hancinta, ya sumbaci idanunta, yana kallon fararen haqoranta casss.
Ahankali ya ra'da mata“Pls Baby dariyar ta isa kar ta 'kulle min cikin ki OK? â€
Kai ta 'daga masa tana sumbatar kumatunsa tana kallon bakinsa ya 'daga mata gira, ya ce“Babyna ce Meerah ta ha'domin coffee me da'di.â€
Ya qarashe mgnar yana janyo laptop ya kunna yana sake matseta cikin jikinsa. Sumar kansa ta shafa ta sumbata tana fa'din“'kamshi wlh me da'di Abienah.â€
Ta 'karashe mgnar tana sauka daga jikinsa.
Fizgota yay ta dawo jikinsa tana sakin dariya tana cewa“Abie Rabin raina ka karya min hannu wayyo zafi.â€
Dariya yay ya kamo hannun ya ce“Mugani Babyna sharri.â€
Rahma kallonsa take tana murmushi ta ce“Abie mgnar ammi wai me ta min ne wai nace karka rabu da ita?â€
Ido ya kashe mata ya ce“Babyna idan zan wuce bayan kin kammala shan maganinki dake zan wuce bana son karatunki ayanzu OK?â€
'Kananun kyawawan danunta ta zaro tana kallonsa, ta marerece fuska, ta tallafo fuskarshi tana kallonsa tana Jan dogon hancinsa ta ce“Am da gaske Abienah baka son nayi karatun gida zamuje?â€
Ra'da ya mata akunnen.
“Yes Babyna bana so ki hkr bayan bikin ki zan mayar dake wata 'kasar OK?â€
Goshinsa ta sumbata ta ce“Ok Rabin raina an gama nima wlh bana so daga yau kaje kawai ka amso takarduna ko?â€
Ta 'karashe mgnar tana kallonsa.
Gira ya 'daga mata ya ce“Allah ya miki albarka Babyn Abientah.â€
'Yar dariya tai ta janye tana fa'din “Abie bari akawo coffee me da'di.â€
Ta qarashe mgnar ta nufi hanyar kitchen, da 'dan gudunta, jikinta ko ina na motaswa yake.
Abie kai ya girgiza yana fa'din.
“Babyn Abienta yarinyar kirki.â€

Meerah kuwa tana famar wanke apple tana yankawa,Rahma ta shigo kitchen 'din, bakinta 'dauke da sallama.
Meerah ta amsa tana fa'din.
“Madam Rahma yankawa na tsaya yi.â€
Murmushi tai fararen haqoranta suka bayyana ta ce“Lah! Ba komai wlh, tsaya ina zuwa.â€
Kankana ta 'dauko da kanta ta wanke ta yankata fito da strawberry ta yanka mangwaro 'daya tajera tsaf ta ce“Kaima Abie.â€
Ta fa'da tana 'dora masa coffee 'din.
Cikin 10 minutes ta ha'dama Abie coffee me da'di sai 'kamshi yake ta zuba cikin wani irin cup na glass na shan coffee blue ne me shegen kyau, yanada 'dan girma, ta juye coffee'n aciki, ta fito.
Zaune yake yana amsa waya yana danna laptop.
Rahma ta zauna kusansa har jikinsu na ha'duwa, ta ajiye cup 'din saman table ta kwantar da kanta kafa'dar Abie, ta sanya hannunta 'daya ta zagaye damtse hannunsa wanda yake amur'de tamkar soja, ta sanya 'dayan saman fuskarshi tana ta'ba gemunsa zuwa sajansa, tana kallonsa tana murmushi.
Gira ya 'daga mata, yana sakar mata tattausan murmushi, ya janye wayar daga kunnensa ya ra'da mata.
“Baby barni na amsa waya, kalli kin riqe min hannun danna laptop. â€
Ya 'karashe mgnar yana sumbatar gefen kunnenta, yaci gaba da amsa wayar atsanake.
'Yar dariya tai tana zagaye hannayenta bayansa ta 'boya kanta cikin 'kirjinsa.
Yafi 12 minutes yana wayar kafin ya gama ya ajiye wayar yana rufe laptop 'din, ya kalli coffee'n yana murmushi.
'Dago kanta yay yana fa'din.
“Baby ummina wannan coffee ha'dinki ne ko?â€
Galala ya saki baki yana kallonta bacci take abinta cike da nutsuwa.
Kanta ya shafa ya sake maidata jikinsa ya mata yadda ya 'dagota ya sanya hannunsa ya rungumeta gam.
Coffee' ya 'dauka yana kur'ba, wani irin da'di ya gauraye bakinsa ya lumshe idanunsa yana ha'diyewa, ya sake kai cup 'din bakinsa, bai direba sai da ya shanye tass yana santin coffee'n lallai Babynsa kome nata daban yake.
Yanka apple 'daya ya 'dauka ya kai bakinsa, ya tauna yana kallon Rahma.
Strawberry ya 'dauki 'daya ya gutsira ya kai saitin bakinta ya matsa ruwan ya sauka saman 'dan 'karamin bakinta daidai wajan tsagar hakan yaba ruwan damar fara shiga bakinta.
Lashewa tai tana lasar baki.
Murmushi yay yakai sauran bakinsa ya cinye ya 'dauki yankan kankana guda ya ci, mangwaro shima yanka guda yaci.
Ya miqe da ita ya nufi corridor 'din zai sada shi da bedroom 'dinta.
Wani irin sansanyan 'kamshine ya tarbesa tin daga 'kofar yana bu'de 'kofar,ga wani irin sanyi mai ratsa zuciya da ganganr jiki.
Ajiyar zuciya ya sauko ya shige cikin bedroom 'din ya kwantar da ita saman royal bed 'dinta ya rufeta da blanket, ya sumbaci goshinta, ya kunna mata A/C ya juya ya fice daga 'dakin.
Falon ya dawo ya 'dauki laptop 'dinsa da wayoyin, ya kira Meerah.
Cike da ladafi ta rusana tana fa'din.
“Ga ni Yalla'bai.
“Yauwa ki 'dauke mata kayanta ki saka fridge har ta farka ta yi bacci, me kike girkawa ne?â€
Meerah ta ce“Madam ta ce“alfatat kawai take buqata na niqa naman rago na zuba wajan gasawa, nayi miyar hanta zallah, kaima ta ce shi zakaci kana son sa, sai lemon inabi shi ta taban umarni Yalla'bai.â€
Abie ya jinjina kai yana tafiya ya ce“Akwai hantar ne?â€
“Eh Yalla'bai akwai.â€
Bai sake mgna ba ya tafi.
Miqewa tai ta 'dauki tray'n ta nufi kitchen, dan cigaba da aikinta.

Bedroom 'dinsa da take kallon ta Rahma ya shige ya rufo 'kofar ya ajiye wayoyinsa da laptop ya nufi bathroom.
Bai jima ba ya fito ya kunna A/C ya haye saman lafiyayyan bed ya kwanta. Ba jimawa bacci ya kwashe sa, sbd daren jiya baiyi wani bacci ba

*Gabon*
likitoci tsaye akan Aishatu suna famar cefon ranta, wani irin jini take zubarwa abin akwai firgitarwa sosai.
Ma'aruf tsaye yake yana kuka mai cin rai yana leqe ta glass yadda likitoci suke tsaye akan Aishatunsa.
Duqewa yay yana fa'din.
“Astagfirullah Allah na tuba, yanzu da wani idanu zan kalli Aishana naci amanarta amamn ya akayi hakan ta faru? Wlh tin bayan mgna da na mata akan Aisha na wajan biki bansan me nake ba, wa zai fuskanceni wai zai yarda dani? Shin ya zan kira gida na sheda musu Aishata na halin mutuwa da rayuwa ciki wata 6 ana zubada jini! Ya Allah ka yafemin, tabbas alhakine yake bibiyata, ba'awa Allah wayo ban ta'ba zina ba amman na saka anayi ga ta inda Allah ya jarabeni..â€
Ya 'karashe maganar yana zube awajan yana wani irin kukan nadamar dukkan abinda ya aikata aduniya.
tinda yake bai ta'ba zaton zai riski rana me muni irin wannan ba, bai zata rana irin wannan zata ritsa da shi ba, ya yi nadamar zuwansa duniya, ya yi da nasanin abinda ya aikata ayau, ya rasa taya ya aikata zina, tabbas yasan yana aikata mugayan halaiya wanda ya tuba ya ji ya yi nadama, ko ada can ya tsani kusantar macan da ba tashi ba, bai ta'ba aikatawa ba, duk da kuwa yadda manyan 'yan mata suke bibiyarsa sbd Allah ya basa baiwar kalamai na saye zuciyar 'yan mata amman bai ta'ba zina ba, sai dai yasan yana dillancinta sbd Safarah da suke aciki ya tabbata ba mata duka bane suke aikatau idan sunje 'kasar larabawa dayawa zina sukeyi.

Zabura yay ya miqe tunawa akwai najasa ajikinsa, kallon likitocin yay ta glass yana zubar da hawaye, ya juya cikin zafin nama gudu².
Nura na ganin halin da yake yay saurin bu'de masa bayan mota ya shiga, ya rufe ya zagaya ya shiga ya tasheta ya fice daga hospital 'din.
Suna zuwa gida ya kalli falon inda komai ya faru ya runtse idanunsa ya nufi bedroom.
Agaggauce yay wanka tsarki ya sanya jalabiya ruwan toka, ya 'daukarma Aisha kayan sakawa ya fito suka koma hospital.
Rabi'ah tinda ta iso gidansu ta shige uwar d'aka tai wankan tsarki ta canza kaya ta takure a 'dakin tana kuka tanajin wani irin 'daci cikin ranta ta rasa me yake mata da'di ahalin da ta ga Aishatu ta tabbata ko zata rayu sai taji jiki, idan ta mutu yana nufi ita ce sila?

Su na isowa asibitin ya yi dai dai da fitowar doctors wanda yake kanta na goge gumi.
Ma'aruf aguje ya taresa yana tambayarsa “Doctor ya matata don girman Allah...? â€

_Rahmerh ladingo😉_


_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
3/14/22, 19:46 - Buhainat: ```D A```

```63&64```

_*My Sisters Don Allah Don Darajar Annabi Karki Karanta Idan Baki Biya Ba, Na Ku'dine Idan Kinga Yana Yawo Na Satane Ga Hanyar Da Za Ki Samu Naki Akan.😟👉ðŸ¼300N +22796515805*_

Doctor ya sake goge zufar goshinsa ya ce, “Muje office kayi gaggawar saka hannu za'a cire abinda yake cikinta kafin ayi biyu babu.â€
Ma'aruf kansa ya dafe yana fa'din.
Hasbunallahu wa ni'imal wakil LA haula wala quwwata inna billahil aliyul azim.â€
Jikinsa na rawa yabi bayan doctor yana kuka, suna shiga office 'din ya sanya hannu, aka gama komai aka shirya Aishatu aka shiga da ita 'dakin tiyata.
Ma'aruf sai lokacin ya yi tunanin zuwa kawai ya fa'dawa iyayansu.
Can gidansu Aishatun yaje ya fa'da, mahaifiyar ta shi ma tana can gidansu Aishar wajan bikin. wanda cikin lokaci qalilin gidan yanayin fuskokin su ya canza zuwa damuwa.
Mama Adiya ta shiga tashin hankali harda kuka ta shedawa su Munnira.
Munnira ta ce“Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Aishar dai mama?â€
“Eh ita dai muje muga halin da za'a fito da ita.â€
Hajiyar Ma'aruf hankalinta idan ya yi dubu ya tashi, ga Ma'aruf ya sakata gaba yana kuka.
Hajiya Ma'aruf ta kira Alhaji babba ta sheda masa abinda yake faruwa ya ce su fito baki 'daya suka 'dunguma zuwa asibitin.
Haka suka tafi hankalinsu atashe harda uwani me aikin Aishatu.
Kai komo kawai suke suna jiran fitowar Aishatu.
Ana kiran la'asar aka fito da ita, aka kaita 'dakin hutu.
Ma'aruf jin anyi nasara ciro yaron ita tana lfy sai dai jininta ya hau sosai tana buqatar hutu, dan har yanzu bata farfa'do ba. Dr ya ce akiyaye duk abinda zata gani ya 'bata mata ranta.
Koda suka shiga wajanta bata San wanda yake kanta ba.
Akaba su gawar yaron da ba'a gama masa halitta ba.
Ma'aruf yana kuka aka binne yaron da shi acan babban gida.

*Espagne*
Kiran sallar la'asar ya tashi Abie daga dadda'dan baccin da ya 'dauke shi.
Wanka yay ya fice masallaci.
Rahma kwance ta yi 'dai'-daya baccinta take shararawa.
Har Abie ya dawo daga masallaci, ya zauna a falon ya kunna Tv yana amsa waya ya ga shiru bata fito ba, ya miqe ya nufi bedroom 'dinta.
Kwance take tana sharara bacci.
Bathroom ya wuce ya ha'da mata ruwan wanka masu 'dumi.
Zama yay bakin bed ya janye blanket 'din jikinta, ya rankwafo yana kallon kyakkyawar fuskarta.
Ya sanya hannunsa ya gyara mata gashinta, wanda ya rufe mata fuska.
Anutse ya tattarashi ya 'dago kanta ya 'Dora saman cinyarsa ya kitse mata gashin a 'daya ya saka ribbon, ya sumbaci tsakiyar kanta, ya shafi gefen fuskarta, ya 'dora bakinsa kan kunnenta ya kirata“Baby Ummi! Oya tashi anyi sallah.â€
Ya qarashe mgnar yana cizon fatar kunnenta.
Idanunta ta bu'de tar tana kallonsa, ta turo 'dan 'karamin bakinta gaba.
Murmushi yay ya kwantar da kanta saman pillow, ya kamo lallausan hannunta ya miqar da ita zaune ya 'dauke cak kamar 'yar baby ya shiga bathroom da ita, ya direta ya ce“Oya wanka azo ayi sallah, aci abinci OK Babyna?â€
Kai ta 'daga tana shigewa jikinsa tai lamo, ta 'dago kanta tana kallon kyakkyawar fuskarshi, tana 'kif² da qananun idanunta masu matuqar masa kyau, da sanyasa shauki.
'Yar dariya yay ya ce“Uhmmm! Baby mage oya wanka lokacin sallah zai shige, idan kin gama kome sai ki shige jikin Abienki kiyi luf ba me hanaki Ok.â€
Janyewa tai ta amsa da “Toh Abie Rabin raina.â€
Hancinta yaja ya fita ya rufo mata 'kofar toilet 'din.
Kayan jikinta ta cire ta shige cikin ruwan 'dumin, wanda yake fitar da wami irin 'kamshi.

Abie yana fitowa falon ana danna doorbell 'din falo.
Ya nufi hanyar falon.
Yana bu'dewa suka ha'da idanu da Anee. Cike da girmamawa ta duqa ta gaishesa ya amsa fuska asake, yana fa'din.
“Anee an taso? Ma Sha Allah wuce sai ki shige tana 'dakinta.â€
Amsawa tai da “Toh Abie Allah qara girma.â€
Kai ya jinjina ya bata hanya ta wuce ya rufe qofar.
Zama yay yana kallon tashar CNN.
Meerah ya kira ta kawo masa dabino ya bata umarni ta dafa masa shayi.

Anee sanyin da'din 'kamshin bedroom 'din Rahma ya saka lumshe idanu tana fa'din.
“Uhmm! Habibty Rahma son sanyi da qamshi.â€
Ta qarashe mgnar tana zama tana jiran Rahma jin qaran ruwa a toilet.
Sosai Rahma tai wanka, ta 'dauro alwala, ta fito, 'daure da towel.
'Kananun kyawawan idanunta ta waro ganin Anee ta iso gareta tana fa'din.
“Oyoyo my Anee ashe za ki dawo?â€
Anee tai dariya ta ce“Dakata! Mage karki fa'domin ajiki ki jiqani da ruwna jikinki.â€
Murmushi tai tana goge jikinta da qaramin towel, ta ce“Daman kin samu babyn Abie zatayi hugging 'dinki ma.â€
Dariya sukayi.
Agaggauce ta shafa lotion ta saka riga da wando Pakistan orange colour sun mata kyau tsaf ta fesa turare ta yane kanta da mayafin ta tayar da sallar la'asar.
Tana idarwa bayan ta yi addu'a ta miqe ta zauna kusan Anee tana sauke numfashi jin kanta na ciwo.
Anee ta ce“Rafeek fa school ya iskeni sai munzo naqi wlh bakiga yadda ya damu ba, akanki Habibty ya ce yana kiranki baya sumunki, switch of.â€
Rahma ta dafe goshinta, tana kallon Anee ta yamutsa fuska ta ce“Wayan inaga Abie ya kasheta ne, pls kici ya ban lokaci kinga Chad zamu koma da Abie ya ce ba yanzu zanci gaba da karuta ba, ni ban iya musu da Abie na ba! Ya ce tarewa zanyi kwanan nan gidan mijina, so kinga abun ya tabbata babu damar naci gaba da alaqa da Rafeek duk da daman sanin matsayina ya saka ban sakar masa fuska sosai, kawai kimina fatan alkhairi wlh bazan qi za'bin Abie na ba, za'binsa tin bansan kaina ba nasan yanada dalilinsa mai qarfi na aurar dani da wuri.â€
Anee ta jinjina kanta ta ce“Gaskiya my Rahmerh kinada hankali da hangen nesa da biyayya wa Abienki Allah ya saka miki da khairan, ya kuma baki ladan biyayya insha Allahu bazakiyi kuka ba, amman zanyi kewarki idan kin tafi.â€
Rahma ta rungumeta tana buga bayanta tana zubar da hawaye dan har acikin ranta batajin son mijin nata kowaye, sai dai zatama Abie biyayya haka tana son karatunta hkr kawai tai dan ta farantawa Abie ransa.
Hawayen fuskarta ta goge ta ce“Anee muje muyi dinner. â€
Anee ta miqe tana fa'din.
“Nima yau nayi naki banci komai ba.â€
Murmushi Rahma tai tana cire mayafin kanta ta ajiye saman bed, suka fito.

Abie zaune yana cin dabino yana kur'bar shayi yaji motsinsu, bai waigo ba idanunsa kan Tv wayarsa ta 'dauki ringing.
Rahma ta kalleshi tana zama kusansa ta zare dabinon hannunsa takai bakinta tana kallonsa yana amsa waya.
Kallonta ya yi, yay saurin kai hannunsa wanda ta janye dabinon ya ta'ba goshinta ya ji zafi.
“Ya Salam! Baby ba lafiya.â€
Ya furta yana shafa gefen fuskarta, ya miqe yana fa'din.
“Eh Kamal aha'da su kamar yadda nace 'din pls anjima zuwa dare zan kiraka yanzu inada babban uzuri zanba baby magani.â€
Ya qarashe mganr yana tafiya.
Rahma da idanu ta bisa tana murmushi.
Hannun Anee ta kama suka tafi kan dining area.

Abienta ta fara zubama ta zubama Anee kafin tai serving 'din kanta.
Suna tsakar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment