Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

French ta maimaita mata abinda ta fa'di sbd tanajin French sosai.
Murya Abie ta daki dodon kunnen Rahma da Ibtisam.
“Baby me kike atsaye anan?â€
Rahma zatayi mgna idanunta suka sauka akan zoben diamond 'din Abie a yatsar hannun Ibtisam.
Cike da mugun kishin da bata san daliliba, ta damqe yatsar ta waiwayo ta tsare Abie da kyawawna 'kananun idanun ta ce“Abienah me ya kawo zobenka hannun yarinyar nan?â€
Ihun Ibtisam sukaji wacce ta dafe cikinta ta fashe da kuka ta sulale zata fa'di 'kasa sai lokacin Abie ya ankare da yarinya, tsaf ya karanceta.
Rahma ta tarota tana fa'din “Abie temaka mana wlh ta suma daman bata warke ba ku ka dawo?â€
Abie ya ce“ No! Matar wani zan kama? Meerah kamata, Baby wuce ciki ki huta umarni nake baki ban son musu oya zo mutafi.â€
Ya 'karashe mgnar yana wucewa ya fasa ma zuwa 'bangaransu Abien, dan dole sai ya ra'basu zai wuce.
Ibtisam jin abinda Abie ya ce ga Rahma na shirin sakinta ta bisa hakan ya saka ta..................

_Rahmerh ladingo😉_


_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
3/19/22, 18:59 - Buhainat: ```D A```

```69&70```

_*My Sisters Don Allah Don Darajar Annabi Karki Karanta Idan Baki Biya Ba, Na Ku'dine Idan Kinga Yana Yawo Na Satane Ga Hanyar Da Za Ki Samu Naki Akan.😟👉ðŸ¼300N +22796515805*_

_Afuwa wlh yau na tashi da wata irin mura ta maqoshi, sam komai baya min da'di, but nayi typing ga dai shi nan so bansan ko bazai maku da'di ba dan kawai dai ina son ragewa ga azumi na gabatowane shiyasa nai maku Ngd_

Ta riqe Rahma sosai tana kuka tana fa'din“Wayyo cikina aunty zan mutu, kaina marata.â€
Ta 'karashe mgnar cikin kuka, tana dafe cikinta.
Rahma macace me tausayi sai kawai ta ru'de hankalinta amugun tashe, ta ri'ko Ibtisam tana mata sannu kamar zatayi kuka, ta ce“Meerah temaka mu shiga ciki inada magani sai na bata idan baiyi sauqi ba sai muje hospital. â€
Ibtisam da'di ya cikata ganin Rahma zata tsaya tare da ita ta sha magani, ko banza ai ba zata bi balarabe ba.
Kafa'darta suka shiga suka nufi ciki da ita, tana kuka 'kasa² Rahma na mata sannu duk ta damu, dan tasan ciwon ciki ba da'di.
Abie kuwa bai tsaya jiran Rahma ba, ya wuce ciki.
Tsaye yake 'kofar falon doorbell ya danna sau biyu, Jaddatu tana zaune ta washe baki ta ce“Su takwara an iso, Latifa zo bu'de 'kofar.â€
Rayyana ta miqe cikin rawar jiki ta ce“Ummi bari na bu'de musu.“
Ta kalli Latifa wacce ta fito da saurinta zata nufi hanyar falon, ta ce“Latifa koma aikin ki zan bu'de.â€
Ta 'karasa mgnar ta nufi hanyar falon tana wani irin taku me cike da nutsuwa sai wani irin fitinannan 'kamshi yake tashi ajikinta.
Hanan ta kalli Jaddatu tana dariya ta ce.
“Dan Allah Ummi kiba Rayyana lafiya ki saka musu idanu ba ruwanki.â€
Jaddatu batace uffan ba.
Ahankaali ta 'dora hannunta saman handle 'din 'kofar, ta bu'de.
Idanu hu'du sukayi da Abie wanda shigarsa ta kusa gigita Rayyana, wai irin mahaukacin kyau ya mata ga wani irin kwarjini na musamman, duk da 'kamshin da yake tashi a ko ina bai hana Rayyana jin dadda'dan 'kamshin Abie na musamman ba!
Abie fuskar shi ba yabo ba fallasa yake kallonta, ya ra'bata zai wuce tai saurin fa'dawa jikinsa ta rungumeshi gam, cike da murnar ganinsa take fa'din.
â€Oyoyo Habiby sannu da zuwa ina Ummin mu ne?â€
Daidai lokacin su Rahma suka iso wajan.
Wani irin abu ne ya tokare 'kirjin Rahma ganin yadda Rayyana ta ru'kum'kume Abienta 'kam, tana zuba maza sannu da zuwa.
Zuciyarta wani irin mahaukacin bugu take wanda ada batajin hakan idan taga Rayyana da Abienta.
Dakyar ta iya 'ko'karin janye idanunta akansu daidai Abien na qoqarin 'ban'bareta daga jikinsa ta sadda kanta suna riqe da Ibtisam wacce baqin ciki da takaicin su Rayyana da zafin kishi ya sakata Sam ta manta 'karya ciwo take ta miqe tana hararansu afakaice ta ce“Aunty cikina ya lafa ma zan iya tafiya Ku sakeni.â€
Rahma daman sam bata cikin hayyacinta ta saki Ibtisam zata wuce Rayyana ta rungumota tana fa'din.
“Oyoyo ummina sannu da zuwa ya gajiya? Muje kiyi wanka kiyi sallah kizo kuci abinci.â€
Rahma ta dake ta qaqalo murmushi ta ce“ammi na sameku lafiya? Ya 'karfin jikin?â€
Ta 'karashe mgnar tana satar kallon gefen Abie taga wayam baya wajan.
Ajiyar zuciya ta sauke.
Meerah ta gaishe da Rayyana ta amsa cikin sakin fuska.
Suka nufi falon.
Ibtisam kuwa tuni ta shige 'bangaransu ranta amatu'kar 'bace.
Rungume da Jaddatu ta hango shi yayin da Hanan take kusansa zaune Iman na zaune acinyarsa sai 'kayataccan murmushi yake saki wanda ya bayyana fararen haqoransa dimples 'dinsa suka lo'ba.
Rahma ta lumshe kyawawan 'kananun idanunta tana jin bugun zuciyarta na tsananta.
Hanan ta taso aguji ta rungume Rahma tana fa'din.
“Oyoyo Ummina ta dawo.â€
'Yar dariya Rahma ta yi tana hugging 'dinta sosai cikin siririyar murya ta ce“Ammi na sameku lafiya?â€
“Alhmdllh! Baby Abienta.â€
Fuska ta yamutsa wanda daidai lokacin suka ha'da idanu da Abien ya 'daga mata gira ta kauda kanta tana ha'de face.
Da sassarfa ta isa wajan Jaddatu ta ra'ba gefenta har jikinsu da Abie na ha'duwa.
Sumbatar Jaddatu tai ta ce“I miss you Jaddati.â€
Jaddatu ta rungumeta tana buga bayanta, cike da 'kaunarta.
Abie ya miqe ya nufi saman bene cikin kuzari yake taka steps.
Rayyana ta miqe tabi bayansa.
Jaddatu ikon Allah take gani.
Rahma tana kallonsu sai ta rufe idanunta ta nutsa kanta 'kirjin Jaddatu.
Kayansu ne Ummi Adnan da Latifa suka shigo da manyan trolleys.
Jaddatu ta ce“Ku haura dasu sama.â€
Rahma ta bu'de idanunta wanda sukayi jajir ta miqe tana 'ka'kalo murmushi ta ce “Meerah muje sama.â€
Jaddatu ta ce“Toh Ku fito ba kuci abinci don Allah.â€
Kai Rahma ta 'daga zata wuce taji muryar Laraba wacce ta fito tana gaishesu da musu sannu da zuwa.
Rahma ta jinjina kanta ta ce“Ngd ina Ibtisam?â€
“Tana ciki wai kanta yake ciwo.â€
Rahma bata ce komai ba ta haura sama.
Dai dai 'kofar 'dakin Abie takejin mgnar Rayyana a falo dan wannan mgna ba bedroom bane.
'Kirjinta taji ya buga da 'karfi tai saurin wucewa.
Falonta ta shaqi wani irin 'kamshi me da'di ko ina fess ta zube saman sofa tana fa'din.
“Latifa iyayan gyara ko ina tsaf. Pls Meerah ha'damin ruwan wanka sai muje na nuna miki 'dakin da za ki zauna.â€
Meerah ta amsa da “Toh.â€
Ta nufi hanyar bedroom 'din Rahma.
Bayan ta cika mata bathtub da ruwan 'dumi ta zuba sabulu na ruwa da turarukan wanka masu 'kamshi, ta ciro sabon towel a ledarsa ta rataya saman abinda ake sarkafe kaya, ta fito.

Fitowa sukayi Rahma ta nuna mata 'dakin da yake face da nata ta ce“Shiga akwai komai na bu'kata bedroom ne da toilet ba falo ki duba idan kina bu'katar wani abun kimin mgna, idan kinyi wanka kin shirya kinyi sallah sai fita zuwa cin abinci.â€
Godiya Meerah ta ma Rahma ta shige ciki yayin da Rahma ta koma ciki.
Kwance tayi cikin ruwan tana sauke ajiyar zuciya ta lumshe idanunta.

'Bangaran Abie Yana shigowa falonsa, wayarsa ta 'dauki ringing ya zube man sofa yana amsa wayan, Rayyana ta shigo. Kai tsaye ta shiga bedroom 'dinsa ta ha'da masa ruwan wanka, ta fito har lokacin yana amsa wayan.
Kusansa ta zauna ta zare masa takalmin sa ta cire safan, ta kwanto jikinsa tana kallon fuskarsa mai cike da kwarjini uwa uba haiba.
Face ya ha'de ya matsar da ita gefe yana ciga da amsa wayansa.
Yana idarwa ya miqe zai shige ciki ta riqo hannunsa cikin zubar hawaye ta ce“Dan Allah Habiby karka haramtamin kanka naji na yarda zan zauna dakai daga nan har lokacin da kayi niyar kusantata bazan sake maka rashin kunya ba ko roqon ka bani haqqina don Allah ka yafemin laifin da na maka karka sakeni wlh ina tsananin 'kaunarka Habiby.â€
Ta 'karashe tana sakin kuka ta rungumeshi.
Bayata ya buga ya ce“Ok naji amman pls kibar takurani ina buqatar hutawa zamuyi mgna idan na nutsu OK?â€
Kai ta jinjina ta ce“Toh Ngd Allah ya qara hucemin zuciyarka dan Allah idan ka fito kazo kaci abinci na girka maka duk irin launin Abincin da kakeso.â€
Kai ya jinnina mata ya nufi bedroom, ta zauna zaman jiransa ta rabka tagumi.

Rahma tana fitowa daga wanka Ana kiran la'asar tai sallah ta miqe ta shirya cikin Riga da sikir coffee brown 'yan indai sunbi kyakkyawan jikinta sun la'be shape 'dinta ya fito sosai ta Saki gashinta har gadon baya ba tare da ta kame ba, ta fesa turare ta canza sarqar 'kafarta ta saka sarka da 'dan kunne na azurfa da awarwaro wanda Abie ya siyamata kwanan nan, sbd ta ce azurfa na burgeta.
Sosai tai wani irin kyau, na fitar hankali, takalmi mai ma'dauri ta fito.

Anutse take tafiya cikin sanyinta fuskarta Sam ba alamar walwala.
Gabanta taji ya fa'di lokacin da tazo dai-dai 'kofar falon Abie, wucewa tai abinta tana share 'kwallar da ta taru cikin idanunta.
Meerah ta hango zaune 'kasa kusan Jaddatu suna fira.
Tana wucewa hanyar dining area ta ce“Meerah kincin abinci kuwa?â€
“Meerah ta ce“Eh naci.â€
Jaddatu ta ce“Rahma lafiyarki kuwa? Abie 2 yazo miki sannu da zuwa ya tafi.â€
Murmushi tai ta ce“Wlh lfy lau Jaddati wayyo nayi missing 'dinsa bari naci abinci naje na gaishesa.â€
Ta 'karashe mgnar tana nufa kan dining area.
Kujera tajata zauna tana bu'de kululin.
Baki ta ta'be sam batajin zata iya cin wani abun.
Pizza ta yanka wacce taji 'kwai da hanta da koren tattasa ta tsine albasar ta zubar dan sam arayuwarta ta tsani alabasa.
Jug ta 'dauka ta tsiyayi fruit ta ajiye ta yanki pizza tai bismillah ta kai bakinta tana taunawa.
'Kamshin turarensa ya kawoma hancinta farmaki, ta lumshe idanunta tana sake kai pizzar bakinta.
Kujera ta ji anja ta kusa da ita an zauna muryasa dab da kunnenta ya ce“Babyna ke 'daya kike cin abinci bakya neman Abienki?â€
Ya 'karashe mgnar yana zare sauran fizzar hannunta yakai bakinsa yana 'daukar cup 'din fruit 'dinta ya kai bakinsa saitin bakinta da ta kur'ba.

Jin murya Rayyana na dariya ta ce“Ummina wai baccine kikeyi akan dining area?â€
Sai lokacin Rahma ta bu'de kyawawan 'kananun idanunta ta saukesu akan fuskar Abienta wanda ya tsareta da manyan shanyayyun idanunsa.
Sanye yake da fararen kaya na shan iska masu masifar kyau da laushi sun kar'beshi sosai, ga wani irin fitinannan 'kamshi da yake.
Diriricewa tai ta kauda kanta ta kalli Rayyana tana qaqalo murmushi ta ce“Ammi wlh maganin mura nasha Ashe wai bacci na fara bari naje na kwanta.â€
Ta 'karashe magnar tana 'ko'karin miqewa.
Tattausan hannunsa ya 'dora saman kafa'darta ya mayar da ita ta zauna ya rankwafo sosai jikinta yana mata wani irin kallo wanda ya sakata zaucewa asakalce ta Kira shi.
“Abie!â€
“Na'am My Baby oya sha.â€
Ya kafa mata cup 'din fruit daidai inda ya kafa bakinsa.â€
Tsintara kanta tai da 'dora hannunta saman nashi mai cike da gargasa tana shan fruit 'din suna kallon juna ta lumshe idanunta sbd bazata iya jure kallonsa ba, sai 'dumin hucin lumfashinsa yake sauka 'kofofin hancinta .
Ta tsinci kanta da zura hannun ckin tafin hannunsa ta nimqe sosai.
Rayyaan kuwa tana famar zuzzubama Abie girke² da ta yi masa.
Rahma bata ankare ba ta shanye sai da taji ya janye cup daga bakinta tai saurin bu'de idanu taji ya sauke mata la'bbansa saman goshinta, ya yanko pizza ya gutsira ya saka mata sauran abakinta.
Daurewa tai tana ci.

Rayyana ta zauna kusansa ta ce“HABIBY bismillah!â€
Rahma tai sauri ta miqewa tana fa'din. ammi zanje toilet.â€
Abie ya bita da idanu yana girgiza kansa wani irin smile akan fuskar shi.
Rahma ta 'dauki mayafin Hanan da yake ajiye saman kujera tana qoqarin saita kanta ta ce“Jaddati bari na gaishe da Abie 2.â€
Jaddatu ta ce“Yauwa da kin kyauta yazo dubaki kina sama.â€
Har zata wuce ta hango Ibtisma na leqe kamar ma kukane take, sai ta dawo baya ta nufi corridor 'din.
Kusanta ta tsaya da harshen French ta ce“Ibtisam lafiyarki kuwa?â€
Ibtisam ta share hawayenta ta ce“Uhmm! Babu lafiya wlh ciwon son wani yake neman kasheni ga shi inada miji ga Babana ya ce idan na kaso aurena babuni babu shi, wlh ina cikin masifa da jarabawa, don Allah Balaraba ki temaka min.â€
Ta 'karashe mganr cikin kuka.
Rahma baki ta saki tana kallonta ta ce“Ke bakida hankali kikeson wani bayan kinada aure? Toh wai wayema kikeso?â€
Ibtisam ta riqe lallausan hannu Rahma tana sha majina ta ce“Wlh balarabe babanki wanda naga kuna kama wanda dai kukazo dazu...â€
Rahma damm! 'Kirjinta ya buga fizge hannunta tai, ta ce“Na shiga uku! Abie kikeso? Toh wlh bazaki samuba kuji jiraba da masifa, ina zuwa.â€
Ta fa'da tana juyawa har zata bar wajan ta juyo ta Kama hannun Ibtisam zata zare zoben hannunta.
Ibtisam taqi tana fa'din.
Don girman Allah karki rabani da zoben nan kiyi hkr...â€
Rahma bata San ya akayi ba ta 'dauke Ibtisam da gigitaccan mari tana huci ta ce“Zan miki tijara mafi muni da ba'a ta'ba miki ba, ke wacece? Waye ubanki za ki kalli 'kwayar idona ki ce Abiena kike so? Wai ma kinada aure?â€
Wani irin Jan zoben tai cikin 'bacin rai ta zare shi daga hannun Ibtisam ta zura a yatsarta ta nunata da yatsa.
“Ki cire Abie nah aranki bazaki ta'ba samunsa ba.â€
Ta 'karaahe mgnar tana Jan tsuki tabar wajan.
Ibtisam hannu ta 'dora akai tana 'kurma ihuuun da ya janyo hankalin su Latifa suna kitchen.
Dasu Jaddatu wanda suke falo.
Aguje Laraba ta taho su Jaddatu na bin bayanta.

Abie Rayyana ta temaka masa wajan cin abinci tana zuba masa surutu bai tankata ba, abincinsa yake ci.
Ta tsiyayo masa fruit ta beqa masa cup ya amsa yana kaiwa bakinsa ya ji hayaniya kamar ihu da kuka ya miqe yana cewa“Lafiya kuwa wa yake mana ihu haka cikin gida?â€
Rayyana ta ce“Wlh ban saniba bari na dubo.â€.
Rahma kuwa fucewarta tai ta nufi fart 'dinsu Abie 2.
Abie anutse yake takowa wajan yana kallon yadda su Jaddatu su ka kewa Ibtisam tana birgima 'kasa, jikinta na wani irin 'bari tana fa'din “abamu zobenmuâ€.
Laraba ta ru'de ta kamota tana fa'din.
“Na shiga uku! Ibtisam aljanu kuma¿
Jaddatu ta ce“Subahanallahi aljanu¿ Latifa ki kirawo Abie 2 don Allah ya temaka mata da addu'a.â€
Abie iso yana kallon irin abinda Ibtisam take, tana kiran zoben su ya kalli hannunta ya ga babu zoben.
Kallon Jaddatu yay ya ce“Ina Baby ummi?â€
Jaddatu ta ce“Naga zata fita sai naga tayo nan tana wucewa naji ihun yarinyar nan ashe aljanu gareta ka temaka mata da addu'a.â€
Abie ya ce“Idan aka Baku zoben zaku tafi?â€
Ibtisam wani irin sanyi ya ziyarci zuciyarta, ta sake 'kandarewa kamar gaske ta ce“Eh balaraba ta mana duka ta mashe zoben.â€
Abie dariya taso ku'buce masa ya danneta ya ce“Rayyana kawomin ruwan zafi na tofa addu'a aciki axuba masu. Ki biyo min da wayar charger. â€
Rayyana jiki na rawa ta nufi kitchen.
Jaddatu ta ce“Kayi da yaren da zamu gane meke faruwane?â€
Abie zaiyi mgna da larabci ya ga ibtisam ta miqe zuwat tana atishawa tana fa'din mun tafi amman amaido mana zoben mu.â€
Abie ya ce“Ummina dan Allah kuje Ku zauna ta ce sun tafi.â€
Ya 'karashe mgnar yana tafiya.
Rahma kuwa tana fart 'din Abie 2 suna hirasu ta saki jikinta ta danne 'bacin ranta.
Abie 2 ya ce“ 'Diyar albarka Abienki ya min bayanin komai akan dawowarki tin kafin Ku taso hakan kuma ya yi daidai, nima ina son naga mijin 'diyar albarka.â€
'Dan murmushi tai tana rufe fuskarta da tafin hannunta.
Mal Adamu ya ce“Ina Baban naki muje sannu da zuwa yana sama?â€
Rahma kallonsa take dan batasan me ya ce ba.
Miqewa tai ta ce“Abie ina zuwa zan dawo anjima.â€
Karo sukayi da Abie a 'kofa ya riqota yana binta da kallo.
Cikin raunanniyar murya ya ce.
“My Baby haka kika fito bakiga kayan sun kamaki ba? Mayafin baida girma sosai, duk da ya rufeki.â€
Ya 'karashe mgnar yana janyota bayan 'kofar yana sumbatar goshinta ya 'dora bakinsa 'kasan wuyanta ya ri'ko 'kugunta sosai, ya sakar mata Sumba 'kasan wuyanta.
Fuskarta ya tallabo ya kai bakinsa dab da hancinta ya kirata cikin siririyar murya “My Baby! Menene wai kike fushi dani? Oya gayamin Baby.â€
Ya 'karasa mgnar yana 'dora bakinsa saman nata ya sumbata ya kamo lips 'dinta na 'kasa ya tsotsa second 5 ya saki.
Rahma 'Kala bata cemasa ba, da idanu take bisan zuciyarta na bugawa.
Qamqameta yay yana sauke ajiyar zuciya ya ra'dama akunnenta.
“Oh! My God! Babyna menene pls kiyi min mgna.â€
Kuka ta sakar masa mai sauti tana son 'kwace jikinta.
Matseta gam yay ajikinsa yana sauke ajiyar zuciya yana buga bayanta akaunnenta ya ra'da mata muje 'dakina ki zayyane min laifina muje 'kofar 'kasa OK babyna? â€
Kafa'da ta maqale tana dukan 'kirjinsa cikin kuka ta ce“Yanzu nakeso waccan yarinyar tabar garin nan bana son su sake kwana a Tchad, sannan kuma karka sake rungume ammi agabana,zuciyata zafi take sai naji kamar na ha'diye zuciya na mutu...â€
Murmushi yay mai sauti ya sumbaci la'bbanta ya kamo dogon hancinta ya tsotsa, ya kamo hannunta yana kallon zoben da ta amshe wajan Ibtisam.
Wani irin sanyi yake ratsashi tare da azababbiyar 'kaunar Rahma.
Zagaye hannunsa yay ya qamqameta ya ra'damata.
“Ok My Baby amman kinada fitinannan kishi, oya Ruhina rungumeni da kyau pls.â€
Rahma ta sanya hannayenta dukka biyun ta zagaye gadon bayansa ta qamqameshi sosai. Ajiayar zuciya suka saki atare suna sake qamqame junansu.....


_Rahmerh ladingo😉_


_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
3/22/22, 23:24 - Buhainat: ```D A```

```71&72```

_*My Sisters Don Allah Don Darajar Annabi Karki Karanta Idan Baki Biya Ba, Na Ku'dine Idan Kinga Yana Yawo Na Satane Ga Hanyar Da Za Ki Samu Naki Akan.😟👉ðŸ¼300N +22796515805*_


Ibtisan baccin'karya ta fara tana jin Abie na tafiya, bayan Jaddatu da Hanan sun tafi, Ibtisam fara juyi irin zata farka daga baccin.
Laraba zata tasheta, ummu Adnan ta ce“Aa kamata mu kaita 'daki har ta tashi da kanta.
Kamata sukayi suka kaita 'daki suka fito, Laraba ta sanyata gaba tai tagumi tana zubar da hawaye.
Ibtisam ta miqe tana dariya harda riqe cikinta.
Laraba ta 'dora hannu akai ta ce“Na shiga uku! an haukata min yarinya, bari na kira Tanko.â€
Ibtisam ta ce“Wlh da gan-gan nayi Anna, wanna shegiyar balaraba ni zata amshewa zobe ta mareni haka kawai dan muna gidansu.â€
Anna ta tafa hannayenta ta ce“Ikon Allah! Ibtisam me kikeson zamane? Sbd Allah aljanun 'karya kikayi? Toh wlh sai na gamaki da ubanki...â€
Rungumeta tai ta fashe da kuka ta ce“Dan Allah kiyi hkr, shi kenan ni ba mai fukantata sbd Allah? â€

Rayyana cike da murna ta 'dora ruwan zafin, sai wani bubbu'de hanci take miji ya sakata aiki, sai murna take ita MATAR so.😂Ga MATAR so can rungume da mijinta, suna zuba ruwan love.😹
Tana juye ruwan zafin a cup tana 'yan waqoqinta na shuwa arab, Latifa da Ummu Adnan suka shigo, Latifa ta gintse dariyarta, jin yadda Rayyana ta dage tana waqa.
Ummu Adnan ta ce“Lah! Auntie Rayyana ai yarinya ta samu bacci har kowa ya Kama gabansa, tana can 'dakinsu.â€
Rayyana ta ce“Ok shi kenan Allah ya 'kara mata lfy.â€
Ta fita daga kitchen 'din.
Latifa ta tintsire da dariya ta ce “Auntie Habiba matar nan batada kunya,kiga irin tuggun da ta shiryama 'yar me gidan amman wai take wani za'kewa, tana feleqe da bu'de hanci ita matar gida humm! Wlh banjin wai ya qeleta ne, sbd yadda yalla'bai yake son uwar 'dakina da uwa zai ci gaba da zama da ita...â€
Ummu Adnan ta rufe mata baki tana zunguranta akai ta ce“Bakyajin ngna ba ruwanmu muyi ayukan gabanmu, kinga yau kima ma'aikata girki can 'bangaran kitchen 'dinsu zanji da nan, sbd idan kin fara mitar mgna sai an kamamu za ki daina.â€
“Toh naji bari na kaiwa Jaddatu shayinta na gado sai na tafi.â€

Rayyana tana fitowa ta isko Jaddatu na mitar Rahma bata son mutane me ya kaita dukan 'yar mutane harda amshe mata zoben da Abie ya bata lokacin tana hauka.
Rayyana bata saka baki gudun hantara sama ta haye domin sake sabon wanka.😹

Banda ajiyar zuciya ba abinda suke saukewa, sunajin bugun zuciyoyin junansu, sun du'kule tamkar abu 'daya.
Abie ya janye dogon gashinta wanda ya zubo ya rufe mata fuska,ya sumbaci goshinta, bakinsa ya manna kan kunnenta cikin wata irin tsadaddiyar murya ya ce“My Baby Ruhin Abie kin daina Fushin?â€
Ya 'karashe tambayar tata yana sumbatar kunnenta cikin ja tsuit.
Ajiyar zuciya ta sauke ta 'daga kanta alamar “Ehâ€
“Thank u My Baby Ruhin Abie, muje ki kwanta ki huta amman karkiyi bacci OK?â€
Kallonsa tai cike da mayen sonsa wanda bata san tana masa ba, ta 'daga kanta.
Hannunta ya kama suka fice faga part 'din Abie 2.
Wata hanya mai yawan shuke-shuke suka bi hannunsu manne cikin juna.
Rahma kallon Abienta take tana jin idan ba Abienta bazata rayuba cikin jin da'di.
Tsintar kanta tai da zare hannunta cikin nasa ta rungumeshi ta baya ta saki kuka.
“Oh! Ya Rabbi! My Baby zo naji menene?â€
Ya fa'da yana juyo da ita,gabansa ya rungumeta yana shafa bayanta kusan kunnenta ya mata mgna me taushi.
“My baby Ummi menene? Pls fa'damin kinji.â€
Kanta ta tura tsakiyar 'kirjinsa ta lumshe idanunta tana sauke numfashi dan bata san me zata ce ba.
Numfashi ya sauke ya 'dauketa ca'dak kamar 'yar tsana ya mannata 'kirjinsa ya nufi wata kwana sai ga wata 'kofar glass kalar blue.
Yatsunsa ya saka ya danna wasu lambobi sai ga 'kofar ta bu'de da kanta, ya sanya kansa ya shige 'kofar da kanta ta rufe kanta.
Tsayawa fa'din tsaruwar wannan hamshaqin falon 'bata lokaci ne wani dogon corridor ya nufa kusan tafiyar 4 minutes sai ga shi wata 'kofar nanma lambobi ya danna 'kofar ta bu'de ya shige ta rufe kanta.
Steps ya fara takawa anutse.
Rahma ta shafi sajansa ta manna masa Sumba kan dogon hancinsa ta tura katan tsakiyar 'kirjinsa, hannunta saman gemunsa tana murzawa.
Abie sauke 'katuwar ajiyar zuciha ji yake kamar ya ha'dihe sbd 'kaunarta, da sonta.
“Babyna! I love you kinji.â€
Ajiyar zuciya ta sauke tana murmushi bakinta kusan kunnensa ta ce“Abie Rabin raina karka zautar da Babynka ta kasa gane matsayinka wajanta ta fa'da halaka sbd ina jin sonka ya banbanta da na baya Abie ina son na rayu da kai ya zanyi um?â€
Ta 'karashe mgnar tana cizon fatar kunnensa tana leqen fuskarshi.
Ya Allah! My Baby!â€
'Yar dariya tai tana kallon kyawawan 'kwayayen fitilun da aka 'kawata silin saman benen dasu tana cusa hannunta cikin sumar kansa ta ra'da masa “Abie Rabin raina Ummina da Ammi sunyi sa'ar miji ni kuma nayi sa'ar....â€
La'bbansa taji ya tura mata cikin bakinta, duka yana juyawa, yana hura mata wata irin 'dumammiyar iska mai fitar da dadda'dan 'kamshin bakinsa.
Lumshe idanu tai tana sauke numfashi, ta fara shan jajayen 'kananun la'bbansa cikin nutsuwa.
Key ya saka ya bu'de 'kofar ya shige.
Sanyi 'kamshi ya daki hancin Rahma amman bata bu'de idanunta ba anutse take tsotsar la'bbansa har ta janyo harshensa ya sauke numfashi yadda take Sha anutse tana ha'diye yawunsa.
'Kofar bedroom ya bu'de ya shige baya ganin gabansa sosai sabida yadda Rahma take shan bakinsa.
Saman Royal bed 'dinsa ya kwantar da ita ya mata rumfa da faffa'dan 'kirjinsa ya tallabo kanta yana shafa gashinta ya tsira mata idanu yadda take shan bakinsa tsakaninta da Allah, kallo 'daya zaka mata kasan tana jin da'din bakin nasa. Bai yi qoqarin tayata ba sbd kar ya rikitata.
Abinda yasan zai sakata bacci cikin nutsuwa ya fara qoqarin mata.
Ahankali ya zuge mata zip 'din rigarta ya tura hannunsa tsakiyar bayanta yana mata massaging hankali yana yawo da hannunsa 'dayan saman cikinta zuwa marata yana shafawa anutse yana 'dan mammatsa mata jikinta ta yadda zai fitar mata da gajiya.
Narke masa tai tana fitar da wani irin nishi still taqi fasa shan bakinsa ta qamqameshi tana amsar irin massaging 'din da yake mata.
10 minutes wani irin dadda'dan bacci ya 'dauketa, bakinta manne da nashi.
Wani irin numfashi take saukewa mai cike da nutsuwa.
Abie ya tsotsi tsinin harshenta ya zare bakinsa ahankali, yana lashe yawunta da ya 'bata masa baki, ya zame jikinsa ahankali ya gyara mata kwanciyarta ya tattaro mata gashinta ya 'daure mata ya 'kura mata ido bai ta'ba son abu kamar Babynsa ba, ko Ummul Aymana da ya mata sahihin so bai kai na babynsa ba, duk da son da ya mata ne ya shafi babynsa, sai dai ita baby bazai iya sadaukar da ita wa kowaba, kamar yadda ya yi na umminta,sbd yasan Tabbas ita ce sanyin idaniyarsa rayuwarsa jinsa ganinsa komai nasa, tabbas bazai ta'ba son abu kamarta ba.
Smile ya saki 'kasa² ya ce“Allah mai hikimomi bila adadin, wato ke 'din abokiyar rayuwatace shiyasa Allah ya hanani Ummul Aymana ya mallakawa Uncle Aliyu suka haifamin ke, suka mallakamin kyautarki, da aurenki tin kina tsummanki, wayyo 'kwai zai fashe Babyna, ya Allah ka jiqan Uncle Aliyu da Ummul Aymana.â€
Wasu guntayen hawaye ya goge akan fuskarshi yana mugun son bayin Allah nan.
Ya shafa fuskarta ya manna mata kiss akumatu, da lips 'dinta me jiqe da yawunsa ya ce“Ina sonki My Baby iyayan kishin Abienta, My Rahmerh Abienta take so tin bata san matsayinta ba,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment