Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ce masa.
“Abien Ummi tana mgna fa!â€
Jaddatu ta ce“Ke! Wlh bana son mgnar banza uwar me zata basa?â€
Abby yay murmushi ya ce“Haba! Rahmu kin 'dauko da zafi tsokanar Zahra ne fa!â€
Hanan da Haleesa suka k'yalk'yale da dariya.
Abie ya zauna kusan Jaddatu yana gaishe dasu Abby.
Jaddatu ta kalleshi ta ce“Abinci fa?â€
D'an mufmushi yay ya ce“Ai yanzu naci wajan Abie2.â€
Iman tai tsalaf ta ce“Abie d'azu naji Auntie Rahma tana cewa ta yi kewarka...â€
Jaddatu ta ce“Kakan kewansa tai da shegen bakinki kamar na Aku.â€
Hanan ta ce“Tashi kije ma ki tayata fira, Ummi abun Nata ba sauqi.â€
Abie ya murmusa ya ce“Ummi yanzu nai mgna da Abie2 akan ko yanada wacce zai tsayar, ya ce A'a ina take zuwa da zai samu wacce zai tsayar, inaga ki tuntub'i Meerah sabida tin kwanaki na masa harinta, idan ta amince ba matsala bayan biki idan mun nutsu sai muje Neman aurenta...â€
Jaddatu ta ce“Kai Masha Allah wlh naji dad'i bari ai da zafina na isketa tana ciki wajan Rahma.
Abie aransa ya ce“Wayyo My Baby baiwar Allah, I miss you so much.

Jaddatu ta miqe ta nufi ciki Hanan ta ce“Gaskiya Yayana ka kyauta wannan had'i zaiyi.â€
Abie ya ce“Allah ko?â€
Abby babba ya ce“Wlh sosai ma Allah ya tabbatar da alkahiri.â€
Abie ya amsa da “Ameen ya Allah. â€
Ya miqe ya musu sallama ya haye sama yanaji Haleesa da ummiterh na tsokanarsa yay murmushi ya tafiyarsa.

Rahma zaune tauna hirasu da Meerah cikin jin dad'i yayin da Latifa take linke kayan Rahma na bacci, Jaddatu ta shigo.
Rahma ta kalleta ganin bakinta awashe har kunne.
Rahma ta kirata.
“Ummi!â€
Jaddatu ta amsa da “Na'am takwara.â€
Meerah ta miqe zata fita Jaddatu ta ce“A'a ki zauna mgna zamuyi.â€
Meerah ta zauna cikin ladabi tana amsawa da.
“Tohâ€

Jaddatu ta ce“Latifa jeki sha'aninki Meerah zata qarasa linkewa.â€
“Tohâ€
Kad'ai ta amsa ta ajiye linkin kayan ta fice.
Rahma da idanu take bin Jaddatu.
“Yawwa Meerah daman mgna nakeso muyi akanki na ce dan Allah ko kin tsayar da mijin aure acan Morocco 'din?â€
Meerah ta sadda kanta ta ce“A'a Jaddatu babu gskya.â€
Jaddatu ta ce.
“Madallah amatsayinki na yarinya wacce bazata haura shekaru 25 zuwa da 27 ko zaki Iya auren Abien Rahma Abie 2? Karkiji kunyata ki fito ki gayamana gaskiya ba dole sai kinji za ki Iya?â€
Meerah kunya ya lullu'beta ta qara 'kasa da kanta ta ce“Wlh ba komai Jaddatu ni haka kawai nake kwa'dayin kasancewa daga d'aya daga cikin zuri'arku sabida dattakunku bakwa kyamar mutum ko ya yake, kuma damna Rahma tamun tayin banqi ba.â€
Kai Masha Allah, naji dad'i wallahi, amman takwara shine baki sanar damuba sai yau Abienki yay mgnar?â€
Rahma murna ya saka ta manta 'yar kunyar da take da Jaddatu ta haye samanta ta maqalqaleta tana jin dad'in lamarin.
Ta ce“Wlh Jaddatu ni bansan ta yadda zan faro miki zancan bane shine na bari har anutsu, kai gaskiya naji dad'i Meerah Allah ya saka miki da alkahiri.â€
Jaddatu tai dariya ta ce“Ameen dai, Allah ya tabbatar da alkhairi.â€
Rahma ta amsa da “Ameen tana qara shigewa jikin Jaddatu.
Jaddatu ta ce“Ni d'agani wannan k'amshi naki sai ya sakani mura ai.â€
Rahma sai lokacin ta dawo haiyacinta ta miqe aguje ta shige bathroom.
Meerah tana dariya qasa².


*Gabon*
Misalin 8 na dare Aishatu zaune gaban iyayanta, cikin shirinta tsaf na tafiya gidan mijinta, Tasha k'unshi da kitso ta yi kyau sai uwar Rama abinka daman da ramammiyar mace.
Abbanta ya ce“Aisha ki 'Kara hak'urin zama da 'dan uwanki, shima hkr take dake, dan idan zama ya ha'da na aure toh fa kowa hkr ne yake 'dan uwansa, dan haka kai Ma'aruf ka qara hkr da 'kanwarka Allah ya Baku zaman lafiya kutashi kuje. Au Hajiya qara musu fa'da.â€
Murmushi ta yi ta ce“Alhaji Ai ka gama gayamusu duk abinda zan fad'a musu kawai sai dai na bisu da addu'a Allah ya qara kiyayye gaba koma menene ya had'asu, Allah ya muku albarka Ku tashi kuje.â€
Aishatu ta share hawayen fuskarta ta ce“Ameen ta miqe ta fice.
Ma'aruf sanye cikin wata rantsatsiyar shadda maroon color ta masa kyau duk da ramar da yay,ya sake rusunar da kansa ya ce“abba nagode sosai Allah ya qara girma.â€
“Ameen ya Allah kuje Allah ya muku albarka.â€
Ma'aruf ya miqe zuciyar fal farin ciki yau Aishatunsa ta dawo garesa, duk da fargabar abun da zai biyo baya akan Rabi'ah yake mugun fa'dar masa da gabansa.

Tsaye ya isko gindin motar ta had'e fuska ba alamar walwala atattare da ita.
Bu'de mata gaban motar yay, ya ce“Bismillah Masoyiya.â€
Kicin² tai da fuska ta shiga ba tare da ta kallesa ba.
Rufewa yay yana murmushi ya bud'ema Uwani baya ta zagaya ya shiga 'bangaran direba ya tayar da motar ya nufi gate.
Cikin sauran jarumtarsa yake janta da hira, amman ko ci kanka bata cemasa ba, har suka isa gida.
Kai tsaye bedroom 'dinta ta wuce ta murza key bata bi ta kansa ba.
Ma'aruf sai da ya gama shirin kwanciya ya 'dauki ledar kajin da ya siya ahanya tin lokacin da zaije d'aukar Aishatu.

K'ofar ya mur'da yaji gam arufe da key, knocking 'din 'kofar yay,yana kiranta, amman shiru bata bu'de ba.
Ajiyar zuciya ya sauke ya ce.
“Masoyiya ga kaza nan na ajiye miki ki fito ki 'dauka, sai da safe Allah ya huci zuciyarki.â€
Azafafe ta ce.
“Bana so kaje kaci abunka wlh bazan d'auka ba, ehen.â€
Kai ya girgiza ya juya ya tafi, yabar ledar kajin anan, yasan halinta zata biyo dare ta 'dauke sbd tana son naman kaza sosai.
★★★
*Tchad*
10 pm Ibtisam zaune tana kallon Tv tsaf cikin shirinta, sai baza 'kamshi takeyi.
Jin horn 'din mota yasa ta miqe cikin farin ciki ta fito.
Gate ta bu'de masa ya shigo, ta mayar ta rufe ta nufi wajansa.
Parking yay a mutaqar gajiye ya fito.
Daidai lokacin ta iso wajansa ya ware Mata hannayensa ta shige jikinsa, ashagwab'e ta ce“Sannu da zuwa Mon amour nayi kewarka wai ina ka tsaya?â€
Fuskarta ya shafa ya d'ago da hab'arta ya sumbaci kumatunta, ya lashi labb'anta ya Mata rad'a a kunnenta.
“Mon cÅ“ur! Wlh jama'a ce basu barmuba, anata baqi sai da komai ya Kammala na taho hope kina lafiya?â€
Jikinsa ta k'ara shigewa ta ce.
“Masha Allah tinda kana lfy, ni ma ina lfy sai kewar rashinka.â€
Hancinta ya lakata suka nufi ciki.
Ruwan wanka ta had'amasa ta gudu ta barsa dan nauyinsa takeji.
Bayan ya fito daga wanka y'a shirya cikin kayan bacci masu taushi, yana k'amshi ya fito falon.
Abinci ta had'a musu dan bata ciba, tare suka ci yana mata fad'an idan ya yi dare ta dinga cin abinci.
K'walla ta taru a idanunta ta ce.
Haba! Mon amour taya zan iya cin abinci banga ka dawo lfy bâ?â€
Kiss y'a manna mata agoshi ya ce.
“No! Kina ci dan Allah ki sanyawa zuciyarki ina lfy insha Allahu. ta shi muje mu kwanta, kimin tausa.â€
Kunya taji ta rufe fuskarta tana murmushi.
K'ofar falon ya rufe ya kashe Tv da 'kwan wutar falon ya sureta sama kamar baby ya nufi bedroom 'dinsa da ita.
Da kansa ya shiryata cikin kayan bacci ya shafeta da turarensa, suka kwanta.
Tana manne jikinsa,ya kai bakinsa dab da kunnenta ya shafa wuyanta, cikin wata kasalalliyar murya ya ce.
“Mon cÅ“ur! Kimin tausa jikina ciwo. Bari kiga irin wacce zaki min.â€
Hannunsa 'daya ya 'dora tsakiyar bayanta, 'dayan a k'ugunta yana murwaza, ahankali, yana matsawa irin dau yadda ake special massaging. Ibtisam ta fara miqa sbd yadda takejin dad'in massage 'din, sai taji duk wata 'yar guntuwar gajiyarta na fita, sai numfashi take saukewa sannu ahankali.
Ja'afar ya kirata baby ya dai?â€
Ibtisam ta miqe zaune ta ce“Wlh massage 'din da dad'i ni har bacci ma nakeji.â€
Murmushi yay ya ce“Ok kwanta na miki.â€
Kafa'da ta maqale ta ce“A'a zan maka, ai ka fini buqata.â€
Ta 'karashe mgnar tana 'Dora hannunta gadon bayansa, ta fara matsa masa jikinsa sannu ahankali.
Ja'afar ajiyar zuciya kawai yake saukewa, dan yadda ya koya mata haka takeyi masa.
Can 'kasan maqoshi ya ce“Beby saura cinya da damtsan hannaye.â€
'Yar dariya tai ta ce“Tom an gama.â€
Ta 'karashe mgnar tana matsa masa cinyarsa da hannu 'daya, 'dayan tana matsa damtsan hannunsa.

Sannu ahankali Ja'afar ya shiga sauya salon nasu zuwa wani salon, tsabar fita hayyaci yasa Ibtisam ta biye masa dukkan abinda ya ce tai shi take shima yana Mata.
Jin bakinsa saman na shanunta yasa ta runtse idanunta tana sauke numfashi dan Sam bazata musaba sbd yadda takejin dad'in abun.
Duk wata hanya da yasan zai jiyar da ita dad'i ita Ja'afar yabi sai ga Ibtisam na mayar masa da duk martanin abinda da ya ke mata, hakan yasa suka susuta junansa, ba zato tajishi yana addu'ar saduwa da iyali, kafin me ya nemi hanyarsa Wanda wanna shine Karo na 4 sbd Ja'afar akwai hkr baya yawan kusantarta sbd yasan tana shan wuya bata Saba ba.
Yau da dama bataji azaba ba, kamar sauran ha'duwa, shiyasa tai muqus bata masa kuka ba, duk da akwai zogin ka'dan² amman yadda yake binta sannu ahamkali yasa ta jure tana amsar saqonsa, sai nishin dad'i da wuya take atare.
Ja'afar kuwa romansa yake kwasa yana sauke tagwayen ajiyar zuciya yana tambayarta.
“Mon cÅ“ur! Akwai zafi?â€
Ibtisam sai dai ta girgiza kanta ba réponse.
Sun jima cikin duniyar ma'aruta mai cike da dad'i kafin su gamsar da juna suyi wanka su sake kwanciya manne da juna, Ja'afar yana saka mata albarka.
Hancinsa taja ashagwab'e ta ce“Don Allah Mon amour kabar godemin, haqqinka ne fa!â€
Kissing bakinta yay ya ce“Ina sonki Allah ya barmu tare.â€
Ibtisam ta ce“Ameen mijina. Mon amour dan Allah gobe sai ka kaini gidan Baba Tsalha na wuni ko? Daga chan sai amun kitso da 'kunshi.â€
Ja'afar ya ce“Ok beby Allah ya kaimu, kinga kuwa bikin Abie sauran kwana 3.â€
Ta shige jikinsa ta amsa da “Amin ngd mon Amour,kace munada biki?â€
Kai ya 'daga yana shafa gashinta wanda yake jiqe da ruwa.
Ahaka bacci me dad'i ya sace su maqale da juna.

Abie2 tsakiyar dare ya 'daura alwalla yay sallar nafila raka'a biyu, ya roqi Allah idan akwai alkhairi atsakanin sa da Meerah Allah kasa Abie ya zab'a masa ita, idan kuwa babu Allah ya zab'a masa wacce zata fi zama alkahairi.

★★★

Washegari.
tinda sassafe Ibtisam ta gama breakfast, dankalin turawa ne ta soya da kwai sai tea, tana gamawa ta shirya tsaf, tana jiran Ja'afar ya tashi suyi breakfast su tafi, ajiyeta gidan Baba Tsalha.

Cikin shirinsa ya fito yana sanye da suit milk colour, sai baza k'amshi yake.
Ibtisam ta miqe cikin farin ciki ta isa wajansa da sassafar.
Hannayensa ya ware mata, ta shige tana murmushi, ahankali ta ce.
“Barka da safiya, Mon amour ina kwana?â€
“Lafiya lau, beby ke kam bakya son cika ladanki? gsky ni ke zakina shiryani daga yau OK? â€
Cike da jin kunyarsa ta ce“Uhm! Tom mon amour naji ni wlh kunya Allah... â€
Bakinta ya rufe Mata ya ce“Shiiiiit! Mon cÅ“ur bâ kunya tsakanina dake, ta wuce tin Randa muka dunk'ule, ina sonki kina sona, mu fahimci juna tinda Allah yasa kin gane ni ne masoyinki nine Wanda kikewa son so ba son rud'in zuciya ba! But kinsan halina nasan naki, bana son na dinga maimaicin mgna beby ki ajiye kunyata mu mori 'kuruciyaemu ok bebyn Ja'afar?â€
Jikinsa ta shige tana murmusawa, ta jinjina kanta, ta ce“An gama muje kayi breakfast.â€
Kai ya jinjina ya Kama hannunta suka nufi 'dan 'karamin dining area 'dinsu me kyau.

Anutse suka karya suka fito, ya kaita gidan Baba Tsalha, koda sukaje har Babba Tsalha ya fita, bayan sun gaisa da Falmata ya leqa wajansu Harisu ya kwashesu suka wuce company, dan ya basu aiki daidai Wanda zasu iya a companyn da izinin Abie.

Misalin 9:30 am.Gidan Abie
Zazzaune suke a akan dining area, har da Abie kasancewar yau juma'a ce da wuri yake tafiya masallaci, yayi ta addu'o'insa, na samun kusanci da mahaliccinsa, shiyasa duk juma'a yake breakfast tinda wuri, amman idan ba juma'a bace sai 11 am.
Sanye yake da wata d'anyar shadda, fara k'al, kallo d'aya zaka mata kasan eh mai tsada ce, anyi mata aikin da bluen zare,dole idan ka kalli Abie ka sake kallonsa, tsabar kyawun da yay, ga cikar zatinsa Uwa uba kwarjininsa.

Anutse yake shan tea yana latsa wayansa yana tura saqo email.
Jaddatu ta ce“Zahara! ajima ki tsantsarawa 'diyata henna biki Ja ka'dai, na amare ga su Chan na fito da su, idan kuma kema bazakiyi ba na saka Latifa ta nemo hamshak'iya wacce ta 'kware a Tchad ta yi abiyata.â€
Abie ya saci kallon Jaddatu ya kauda kansa, yana shan tea 'dinsa, yana latsa wayansa.

Haleesa ta ce“Oh! Wai Ummi fushi kikayi bakya son nawan? Da wasa nakeyi fa zan Mata, ya za'ayi mun Iya Abu Ƙanwarmu ace za'a kawo wasu su Mata, komai kalar namu zamu mata kiyi hkr maida wuqaqen kinji uwarmu.â€
Baki ta turo gaba ta ce.
“Ai ni lamarin Takwarane bana son aja min rai, ke kuma nasan iskancinki, yarinya nan yau da gobe kawai muke tare idan ya 'dauke min ita sun lulu wa yaga dawowarsu, saboda Allah fa! Ai gwara na kimtsa 'diyata tsaf ehen.â€

Abie dariya ta k'umeshi amman ya had'iye yana amsa waya.
Abby babba ya ce“Oh! Rahmu Allah ya taroki ke Uwa ke surukarsu duk, amman shi yarona wane shiri kike masa?â€
Jaddatu ta tafa hannayenta ta ce“Lah! Na banu, dattijon da shi gotai² me zan masa saboda Allah D'an Uwa ka fa'di gaskiya?â€
Hanan takai tea bakinta dariya ta kamata ta sarqe ta fara tari.
Ihun Rahma sukaji tana kiran Jaddatu da Abie.
“Ummi! Abie wayyo ga shi nan Ku temaka min...â€
Ai Abie wata irin zabura yay ya miqe aguje ya nufi hanyar falon, Inda yaji muryata tana kuka.
Dukkansu suka rufa masa baya hankalinsu atashe jin yadda take mgna cikin fitar hayyaci...

Whtspp number😊
_*+22796515805*_

_*🤲ðŸ¼Ya Allah ka jiÆ™anmu kayi mana rahama badan halinmu ba.ðŸ™ðŸ¼*_
5/17/22, 22:52 - Buhainat: ```D A```

```97```

_Rahmerh Ladingo😉_


Abinka da tsohon soja takun Abie bai fi taku biyar ba cikin wani irin gidu ya iso wajan Rahma.
Wani irin mugun birki ya taka ganin halin da Rahma take aciki.
Baki 'daya jikin Rahma ba komai sai towel rabin jikinta duk waje, tana zube saman carpet, alamu sun nuna ta suma.
Asakwane ya qarasa wajanta, ya zube saman guiwarsa, ya sanya hannunsa ya ciccib'eta baki 'daya ya'dora saman cinyarsa yana girgizata da qarfi had'e da kiran sunanta.
Jaddatu ta iso tana fad'in.
“Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Me ya sameta? Kai kubamu ruwa.â€
Abie yana shirin miqewa da ita ajikinsa idanunsa suka sauka, akan wani qaton k'adangare jajir da shi tsakanin k'irjinta.
Idanuwa Abie ya zaro ya koma ya zauna yana fa'din.
“A'uzu bi kalmatullahi,tammati min sharri ma halaq, k'adangare ajikinta ummi.â€
Ya 'karashe mgnar yana sanya hannunsa tare da bismillah cikin zafin zuciya ya ciro sa, bakinsa bai daina addu'a ba, sai da ya gama tofesa da addu'a koda ma ba k'adangaran gaskiya bane, yay masa wani irin bugawa saman carpet sai ga shi ya tsage yana fitar rai.
Hanan ta ba Abie ruwan da ta 'dauko ya amsa, ya shafama Rahma a fuska zuwa 'kirjinta, ta sauke ajiyar zuciya, tana bu'de idanunta tana shirin fasa ihu tai ido 4 da Jaddatu, ta wani irin tsalle ta haye samanta, jikinta na rawa tana neman sakin towel tana fa'din.
“Jaddatu wlh 'kadangare ajkina don Allah karku bari ya kasheni...â€
Abie ya ce“Baby Ummi ki nutsu kalli ga shi an kashe shi, Hanan kamata Ku shiga ciki...â€
Jaddatu ta ce“Wannan abun al'ajabi da yawa yake, toh sabida Allah ina aka samo k'adangare acikin gidan nan? Muje takwara ki nutsu an kashesa.â€
Rahma jikinta har yanzu rawa yake ta manne jikin Jaddatu.
Zainabu da Abby kusan tare suka ce.
“Abdul ka shigar da ita ciki baka ganin abinda yake jikinta? Kuje ka lallashe ta dawo hayyacinta ta sanya kaya.â€
Jaddatu ganin halin da Rahma take yasa batace komai ba, ta beqa masa hannun Rahma ta ce su shiga.
Kamawa yay ta miqe ya nufi hanyar da zata sadasu da bedroom 'din Jaddatu.

Bakin bed ya zauna ya zaunar da ita Sam bai sakawa Kansan komai ganin yadda Babyn nasa ta sauya, lokaci d'aya, yanzu ta lafiyarta yake.
Fuskarta ya riqo ya ce“Baby love! A ina ne k'adangaren ya shiga tsakiyar k'irjinki?â€
Rahma duk a tsorace take har yanzu tai saurin shigewa jikinsa ta maqalqaleshi ta ce“Na shiga bathroom na cire kayana nayi wanka kawai ina d'aura towel naji Abu namun yawo dubawar da zanyi na ganshi maqale atsakiyar k'irjina, wlh bansan ya akayi naje falo ba Abie.â€
Abie ya shafi wajan da ya ciro k'adangaran ya ce“Sannu Babyna insha Allah bazai sake tab'a min ke ba, yanzu me kikeji Babyna?
Rahma tai lamo ajikinsa tana qara maqaleshi ta ce“Abienah kasala, sai tsoro.â€
Sake rungumeta yay gam ya tallabo kanta yana mata wani irin kallo mai cike da so da tausayawa.
Cikin tattausa lafazi ya ce“Oya bu'demin bakinki na miki addu'a Babyna.â€
Akasalance ta kalleshi ta bu'de bakin nata.
D'an murmushi yay ya matso da fuskarshi dab da tata, har yana goga mata sajan fuskarshi, can 'kasa² ya furta.
“My Baby! Duk addu'ar da kikaji na tofa miki ki had'iye Ok my Ruhi?â€
Ashagwa'be ta d'aga kanta, tana lumshe idanunta.
'Dan qaramin bakinsa irin nata, ya 'Dora saman natan, tare da bismillah ya fara karanto Mata duk wata addu'a da yasan ta kariyace, duk tofawar da zai mata sai ta ha'diye cike da cika umarninsa, tana kallon k'wayar idanunsa.
Kusan 20 minutes yay yana mata addu'a acikin bakinta, cikin ikon Allah kuwa ta daina jin yanayin da takeji sai abinda ba'a rasaba.
Ya zare bakinsa acikin nata ya shafi fuskarta ya ce“Babyna me kikeji yanzu?â€
Rahma ta ce“Bana jin tsoron sosai haka ma kasalan sai abunda baza'a rasa ba Abienah.â€


“Masha Allah Baby ummi tashi ki saka kaya muje kiyi breakfast, Ok?â€
Kai ta 'daga tana janye jikinta.
Da kasan ya shiryata cikin kayan da ake b'oye komai nata, ba tare da ya sanyawa ransa komai ba, dan yasan shine zai wahala, ya kamo hannunta suka fito.
Jaddatu sosai taji dad'in ganin Rahmar ahakan.
Ganin kowa na nan-nan da ita ta saki jikinta tai breakfast amman har yanzu wani iri takeji, dan ma addu'ar da Abie ya mata, ajikinta ya bar wasu abubuwan da takeji a farkon, tana gamawa Jaddatu ta jata suka koma ciki.

Abie 10 am, ya tafi masallaci Sam aransa bai tab'a tunanin cewa k'adangaran na aikin sihiri bane an turosa zuwa ga shine amman ina qarfin addu'o'in jikinsa suka kasa kamasa shine suka shiga jikin Rahma.
Abie yafi tunanin dai tsautsayine irin na amare Wanda aljanu ma sonta sukeyi.

Ibtisam acan gidan Baba Tsalha ta wuni, Masha Allah ta Sha k'unshi da kitso, ta yi kyau abinta.
Sai bayan sallar Maghreb yazo ya 'dauketa, suka tafi gida.

Washegari

*Gabo*
Ma'aruf baki d'ayan dukiyar da ya sameta ta hanyar haram, ya kwasheta ya kai gidan marayu da miskinai, sadaka, bakin halalinsa kawai ya bari, Wanda ya kwashe dukkan dukiyar tasa ya zuba cikin wani wani hannun jari, wan Alhmdllh! Kayansa sun taso kwantina guda shaqe da kayan, wanda aqalla zai su kai kayan millions talatin da uku.
Zaune take cikin falo, ta ci uwar kwalliyarta, tsaf sai baza qamshi take Tv kunne amman, Sam ita ba kallon take ba, wayarta take latsawa, suna mgna da Kabeera.
Ma'aruf ne ya fito daga bedroom d'insa, sai binta da kallo yake, ya sauna kusanta, tai sauri zata matsa yay saurin damqeta, ya rungumeta, ya ce“Haba! Masoyiya, ya xamuyi haka? Don Allah ki saurareni muyi mgna.â€
Kwantar da kai tai ta ce“Ok cikani tukunâ€
Ba musu Ma'aruf ya saketa ya fuskanceta.

“Ina jinka?â€

Ta ce da shi.

Ma'aruf ya Kama hannayenta dukkan biyu, ya ce“Don Allah Ayshatuna kiyi hkr da dukkan abinda ya faru, ni nasan alhakin wasune Allah ya kamani da shi na aikata zina da Rabi'ah ba tare da ina hayyaci na ba! Ayau xan fad'a miki irin abubuwan da nayi arayuwata, wanda ba wanda ya Sani a family's 'dinmu, amman na tuba da zuciya d'aya da kuma kyakkyawar niyya, jin sakammakon masu irin halinmu, yadda k'arshensu yake kasancewa...â€
Wayarsa ta fara ruri, ya katse mgnar da yake ya duba mai kiran.
Ganin, Zubairu ne yasa yay saurin d'aukan kiran yana fad'in.
“Masha Allah inaga kayan sun iso.â€

Ya 'karashe mgnar da sallama.
Daga Chan Zubairu wanda hankalinsa yake amugun tashe, ko sallamar bai amsaba ya ce“Yallab'ai babbar musiba ta saukar mna wlh kwantinar kayan ta Kama da wuta ta qoner qurmus komai bai fita ba,banda rayukanmu nida yarona...â€
Ma'aruf da yake zaune sai da ya miqe tsaye zuwat, jikinsa na wani irin tsuma yake fa'din.
“Innalillahi wa'inna ilahir raji'un! Me kace Zubairu? Yanzu baki 'daya dukiyata ta qone?â€
Ya qarashe tambayar yana zama qasa dab'as zaman 'yan buri, yana sake maimaita kiran sunan Allah.
Aishatu jin abinda ya ce itama ta miqe da sauri ta iso gareshi tana zama gabansa, tana fad'in.
“Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un! Garin qaqa?â€
Ma'aruf, ya ajiye wayar yay tagumi banda sunan Allah ba abunda yake anbato a wannan lokaci, sabida baki 'dayan dukiyarsa ce ta salwanta.
_(Hammm Ma'aruf wa ya ce maka Ana tab'a Allah aga daidai, danma kayi gaggawar tuba, ai koda qaqane sai mutum ya girbi abinda ya shuka, ya Allah ka shiryemu, ka tsarkake mana zukatanmu, Ameeeeen.)_


*Niger*
Tanko zaune Laraba na masa fifita, sakammakon hadarin da ya gangamo kamar za'ayi ruwa, kuma ya baje cikin ikon nasa.
Laraba ta ce“Baban Ibtisam dan Allah ka yafemin abinda na aikata muku kaida Dadda wlh sharrin shaid'an ne, na yarda duk abinda Allah ya rubutashi babu Wanda ya isa ya gogesa a doron duniya, haqiqa kwad'iya da son abin duniya ya kusa sakawa na b'atar da kaina, ban tab'a zaton Ja'afar jarumi bane sai yanzu bayan bayan aurensu da Ibtisam, haqiqa ya cika d'an halak, ko attajiri ta aura yadda ya riqeta wlh sai hakan, don Allah ka yafemin.â€
Tanko ya ce“Wlh ba komai ai komai ya wuce, Allah ya yafemu, ba yau ba nake kwatanta miki, da mai ku'di da talaka duk Allah ya yimu ta ya ke talaka kice 'yarki sai me ku'di zata aura? Ai kinga bai ba, fatanmu Allah yaci gaba d aba yaranmu mazaje nagari masu tsoron Allah Wanda zasu riqesu amana ba wai me ku'di ba.â€
Laraba ta amsa da “Ameen ya Allah...â€
Sallama sukaji daga qofar gida, Tanko ya miqe yana fa'din.
“Madallah ga Jamilu nan na ha'damasa komai nasa, Taslim shiga 'dakin Laraba d'aukomi leda mai shar-shar.â€
Cike da ladaba ta amsa da.
“Tom Baba.â€
Ta miqe ta nufi 'dakin Laraba.
Bata jimaba ta fito da ledar, lokacin Jamilun ya qara sallama, Tanko ya amsa ya tafi.
Tsaye yake da qaton cikinsa da wata babbar Leda gabansa ajiye.
Tanko ya ce“Yawwa Jamilu ga kome naka na acikin ledar nan Allah ya horomin na biya.â€
Alhaji Jamilu ya ce“A'a Baba na yafe maka don Allah abar mgnar, ga kaya a baiwa yara.â€
Tanko cike da mamaki ya ce“A'a wlh bana so jeka da abonka, ka ha'da da na wajena, babu wata alaqa tsakaninmu.â€
Tanko na gama mgna ya juya ya tafi ya barsa awajan.

Mal Adamu zaune innah Hansatu gefe, kasancewar girkinta ne.
“Malam 'dazu Ja'afar ya kirani yana cewa mu qara tayasa da addu'ah.â€
Mal Adamu ya ce“Eh wlh munyi mgna na basa addu'o'in da zai qara akan Wandayake yi insha Allah bi khair.â€
Inna Hansatu ta ce“
Toh Allah ya qara karemana shi da sauran yaran al'umma baki d'aya.â€
„Ameen ya Allah, 'dazu munyi mgna da mahaifin Harisu Ashe Maimunatu soyayya suke da Harisu? Humm! Allah ya tabbatar da alkahiri.â€
Inna aka murmusa ta ce“Ai na Sani amin ya Allah. â€
Deluwa na jinsu bata tanka ba ta amsa da amin dai azuciyarta.

*Tchad*

Abei zaune kusan Rahma jaddatu da kanta ta ce masa yaje ya dubata, tin jiya da safe rabonsa da ita.
Rahma kanta qasa tana wasa da hannunta Wanda yasha wani irin fitinannan k'unshi.
Abie ya ce“Wow! My Ruhi wanga 'kunshi ya yi kyau, sai gobe zanga abina anutse ko? Hope dai kina lfy?â€
Rahma ta d'ago ta kalleshi.
Ido ya kashema ya d'aga Mata gyara.
Rahma ta kwakwab'e fuska ta ce“Abie ni fa wlh tin jiya da kamun addu'a ban kuma jin komai ba.â€
Ta qarashe mgnar tana kamo yatsarsa tana shafa sabon zoben da ya saka.
Murnushi yay yana Mata kallon qasa².
Bakinsa ya matsa dab da kunnenta.
Sai da ya sauke Mata numfashi me d'umi cikin wata irin murya ya ce.
“Oh! Ya Rabbi! Baby 'kamshinki zai zautani bari na gudu.â€
'Yar dariya tai ta shafi sajansa, taja dogon hancinsa, ta ce“Abienah ai wlh bazan tab'a kamoka qamshi ba! Yawwa Abie ashe anyi mgnar Meerah da Abie2?â€
Sumbatar gefen fuskarta yay ya ce“Oya zare zoben ki saka.â€
Cikin murna ta cire ta sumbaci zoben ta biqawa Abie.
Amsaya yay ya saka Mata ya sumbaci zoben, ya ce“Yes Abar 'kaunata sai na nutsu zamuyi mgna da iyayanta.
“Baby good night I love you.â€
Ya qarashe mgnar yana miqewa, ya fice da Sauri ganin zata shige jikinsa.
Rahma ta turo baki tana d'aga murya dan tasan nisan d'akin da falon bawanda zai ji, ta ce masa
“Abin nah! Ni ko? Ni nayi fushi.â€
'Yar dariya yay ya ce“No! Baby zan dawo.â€
Rahma murmushi tai dan tasan wane shi.

Sosai yasanyawa Kansa nutsuwa, yasan k'amshin Rahma da ya kwaso tona masa asiri zaiyi, ya shigo falon, ba tare da ya tsayaba ya ce“Ni kam na haye sama akwai wayan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment