Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

DAYA 200
BIYU 300
UKU 400
HUDU 450
BIYAR 500

*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*

2260792279
_MARYAM SANI_
_ZENITHBANK_

saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇
*07067124863*

*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇

*09032345899*

_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_



MX🧕🏼*ZAFAFA BIYAR NA KUDINE,IDAN KIKA GANI (DON GIRMAN ALLAH) KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA ZAKI TUNTUBI WANNAN NUMBER*

07067124863

*Ko kuma*

09032345899


*ku ziyarci tasharmu ta youtube don ganin shirye shiryenmu da sauraron litattafanmu tsofaffi da sababbi,karku manta ku dannan SUBSCRIBE kuyi LIKE sannan kuyi SHARING*🙏🏽

https://youtu.be/LxY42ErBf_8


*IGIYAR ZATO...💕*


_*1️⃣9️⃣_*


Yadda kukasan sabuwar mahaukaciya haka Bintalo ke tafe akan hanyar gidan su Haysam. Tana tafe tana magana ita kadai tana watsa hannu baya, Dayan hannun kuma tana sosa takashi,

“Sittin ta ubangiji ba zata sab’u ba. Y’ar ‘kundin uba, Sun gama kai sunan sa dana iyayen sa. Yo neme shi su kai m..”

Bata k’arasa ba sakamakon shan gabanta da wata mata tayi, Zasu yi sa’anni d’aya da alamun ma kawar ta ce.

“Ah Bintalo ina zaki ne kike ta magana ke kadai? “

“Hmm! Kede bari Ruma. Gidan Alhaji kabeer wafa zani ayi ta ta ‘kare.”

Ruman ta zare idanu tana dafe kirji,

“Me zakiyo agidan Haj Husnah?”

“Sittin ta ubangiji zuwa zanyi na ceto su daga hannun mayun gidan mu.”

Ruma tayi daria tana buga zani. Bintalo tai murmushi tana sosa takashi,

“Yasin tsutsa ce ke damu na, Yar kund’un uba ina komawa zan cusa mata marsaleta”

“A hayye! Shi yasa naga kina soshe soshe. Bakin kasuwa zani ko zan samu na tsiren dare.”

“Uhm! Nima fa so nake na kauda su Alawiyyah daga gaba na nayi auren nan a matse nake sittin ta ubangiji.”

Ruma tayi tsalle ta dire tana watsa hannu baya,

“A hayye! Har mula yadi (atamfa) zamu fitar muyi anko, Yasin cakarewa zamu yi. A hayye.”

Bintalo ta bata hannu suka tafa, Daga nan sukai sallama ita Ruma tatafi bakin kasuwa, Bintalo kuma ta cigaba da tafiya tana gwaggwafewa hade da cusa hannu ta sosa takashin ta dake radad’in tsutsa. Dakyar ta karasa gidan su Haysam tana harharde kafafu.

Tunda Bintalo ta shiga gidan Alhaji Kabeer ta fara kalle-kalle tana jinjina kai alamar girmama tsaurin ido irin na Batoul da har take mafarkin zama 'yar gidan. Da karfi ta dinga kwad'a sallama taji shiru, ta sake bud'e murya, kafin ta bud'e bakinta Inna Rabi ta fito daga wani d'an corridor tana amsawa. Ta dubi Inna Rabi ta mata kallon tara saura kwata ta watsar zata shiga cikin gidan Inna Rabi ta tsaida ita,

“Baiwar Allah sannu, daga ina haka?”

''Yauwa sannunki, Hajiyar bata nan ne?''

''Tana nan, amman dai bata tashi daga bacci ba, sai dai kije ki dawo zuwa anjima, lokacin nasan ta fito parlourn ta.''

Bintalo ta yatsina fuska cikin ranta tana girmama jin dad'in da Hajiya Husna keji, ace wai har zuwa yanzu mutum bai tashi ba. Kuma abin k'arin mamakin shine, matar gidan ce bata tashi daga bacci ba, tana kwance ana yi mata komai saboda jin dad'i.

“Toh baiwar Allah ko matar gidan tasan da zuwan ki ne?”

“Zanzo gamon kai na ne? Ai kema kinsan dole da akwai wani abun. Bama wannan ba. Shin kinsan kaltume me aiki anan?”

Inna Rabi tayi murmushin jin dadin Bintalo ta ambaci Kaltume mahaifiyar su batoul, Domin suna zaman mutinci silar aikatau din da suke tare. Cike da farin ciki Inna Rabi tace,

“Eh na santa. Da kinyi bayani t..”

“Ya isa Babah ba neman karin bayani nake ba. Daga ambatar sunan shegiyar matar nan har kin fara murmushi, Tab sittin ta ubangiji kema ta ha’da da sunan ki awajen boka. Ki taimaka ki taso min ita, magana ce nazo da ita mai matuk'ar muhimmanci akan Hashimu.”

“Waye kuma Hashimu?”

“D'anta mana, da yace ya tafi k'asar waje dan karya.”

Cewar Bintalo tana kallon k'ofar da take da yak'inin cewar nan ne Hajiya Husnah ke bacci. Inna Rabi ta gyara tsayuwa tare da cewa.

“Gaskiya sai dai ki hakura sai zuwa anjima, bana shigar mata d'akin baccinta, sannan zuwa na tashinta zai iya janyo min rasa aikina a gidan nan. Kije ki dawo kawai.”

Wani banzan kallo Bintalo ta aikawa da Inna Rabi na baki isaba, sannan ta sake wage murya tana kiran.

“Hajiya.. Hajiya.. Hajiya kinyi bakuwa.”

Inna Rabi ta dafe hab’a tana cigaba da kallon Bintalo, Sosai take mamakinta. Ajiyar zucia ta sauke tana jinjina kai,

“Toh Kaltume dai bata zo aiki yau ba a.”

“Dakata Baba. Ya isa, ba Kaltume nake nema ba! Nuna min kofar shiga ciki kawai”

Inna Rabi tayi shiru tana tunanin abinda zata gayawa Bintalo kada ta shiga ciki, Domin kallo d’aya zakai wa Bintalo kasan sharri zata had'a.

“Gaskia kiyi hak’uri baiwar Allah! An hanamu shiga sashen matan gidan. Kinga tafiya ta ni, bazaki jazamin masifa ba ina zaman zamana lafiya.”

Inna Rabi ta fad'a tana saurin barin wajan dan kar Hajiya Husnah tazo ta ganta tace tana sane ta janyo mata hayaniya.

‘Mtcew! Bintalo taja tsaki tana bugawa Inna Rabi zani, Tana tafe tana susar takashi haka ta karasa wajan Haj Husna, Irin kofar nan ce wadda ake janta ta bud'e (sliding door) Ta dubi kofar tana dafe haba, Kamar mudubi haka k’ofar take, Ta dubi kanta tana zare idanu, Hannu tasa tana nuna ‘kofar tana kallon jikin ta,

“‘Dan ‘kundin uba. Yasin karya kake kace haka kamanni na suke..”

Ta fad’a tana yiwa kofar dakuwa, Kasan mayafin ta ta nannade ta shiga durza hakoran ta na gaba tana kara matsawa kusa da kofar,

“Sittin ta ubangiji sunyi jajur kodan saboda goro ne. Gwara na goge kar matar gidan tayi tsantsami na.”

Duddurje hak’orin ta tayi sosai sannan ta gyara zaman mayafin ta. Kasa taba kofar tayi ta tsaya tana cizan lebe,

“Nashiga uku ni Bintalo, Ya ake budewa ne? Karfa naje na fasa musu su lakadamin na jaki.”

Matsawa tayi tana hangen gidan ko zata gano wani, Cikin sa’a ta hangi wani yaro yana baiwa fulawa ruwa, Yafito shi tayi da hannu ya taho,

“Nan kofa ce?”

“Eh tura ta zaki.”

Ido ta ware tana dafe kirji,

“Rufamin asiri haka kawai naje na fasa musu a gark’ame ni a folisitashon (police station).”

Yayi daria kawai yana girgiza kai, Hannun sa yasa ya tura kofar ta budu, Mamaki Bintalo tayi tana jaddada kai, Shiga ciki tayi tana bin ko’ina da kallo,

“Dankari Mak’ari! Aljannar duniya kenan. Kai kai kai. Kudi yayi kuka anan gidan.”

Ta karasa fada tana shafa kujerun. Harda su lumshe idanu ta zauna akai tana nanata,

“Bara na zauna na dandali arziki. Wohoho gidan masu hannu da shuni akwai dadi. Su Alawiyyah nama fa an kusa shiga daga ciki a hayye.”

Ta karasa fada tana sosa takashin ta, Ta taskawa takashin nata duka cike da takaici,

“Yar ‘kundin uban tsutsar nan sittin ta ubangiji ina komawa gida zan balle kan shegiya..”

Ta karasa fada tana sake dadawa takashin ta duka ji kake d'ass. Ai kuwa Bintalo tana daga zaune ta dinga kiran Hajiya Husnah tana d'an waige-waige, babu b'ata lokaci kuwa sai gata ta fito tana yatsina tana kumbura fuska. Haj Husnah ta sakko daga sama, Ta dubi Bintalo dake kan kujera a hakimce ta dalla mata harara, ba shiri Bintalo ta sauka daga kan kujerar tana sosa kanta. Zama Haj Husnah tayi akan doguwar kujera tana mata kallon ‘kask'anci. Bintalo ta fara matsawa kusa da ita tana dashe hakora. Haj Husnah ta dakatar da ita tana daga mata hannu,

“Hajiya an tashi lafiya?”

“Kin dai tashe ni, da uwar safiyar nan, daga ina? Wacece ke?”

Bintalo ta kuma washe hakora tare da jingina bayanta jikin kujera tace.

“Ai Hajiya mu 'yan nan unguwar ne, amman mu muna daga can layin Gali mai shago. In takaice miki dai ni a gidan *Mata tara* nake, gidan su mai aikin ki Kaltume.”

“Sai kuma aka yi yaya? Ko yanzu ma bata da lafiya ta turo ki? Dan naga yanzu haka take yi min, ta turo 'yar na hakura toh itama 'yar tace makaranta zata koma shine kema ta turo minke?”

Dafe kirji Bintalo tayi tana gwalo ido, cikin girgiza kai take cewa.

“Wallahi ba ita ta turo ni ba, ai wannan matar 'yar bakin ciki ce Hajiya, ko ciwon mutuwa take yi ba zata turo wani ba idan ba 'ya'yanta ba s...”

“Ya isheni, fad'i abinda ya kawoki, kar dai kice min taimako kika zo nema saboda kinsan ranar laraba ake yin sadakar kudi a gidan nan.”

Da sauri Bintalo tace.

“A'ah a'afa Hajiya, wannan batun da nazo gaya miki yaci uban kud'in taimakon da ake bayarwa ranar laraba. Bari kiji idan kudi na banki ma, wallahi tallahi zakije yanzu ki d'ebo dan kawai ki bani tukwici.”

“Ina jinki, ya aka yi?”

Bintalo aka tankwashe kafafuwa tamkar wace zata ci farfesu, ta dora da cewa.

“Wato Hajiya kina nan kina tarbiyantar da d'anki, ana daga waje ana lalata miki shi, koda yake ba yin kanshi bane ba sharrin sihiri ne.”

“Uhumm, ina jinki.”

“Wato Hajiya d'anki Hashimu a...”

“Badai Hashimu ba, kodai Haysam.”

“Kwarai kuwa sunan ne Hajiya, ihi..ihi ai kinsan da yake sunan ne irin na 'yan gayu. Toh in gaya miki su Kaltume sai tatsarsa suke yi, karki so kiga yadda yake yiwa 'yar b'arin kudi, kamar shuka su yayi yana zuwa d'ebowa. Na takaice miki labari Hajiya, ya samarwa Batoul makaranta daga can zasu dinga had'uwa. Wallahi Hajiya har kamo junansu suke yi, bamu yadda ba da sai yanzu da yarinya ta kafe cewar ita fa sai taje kuma duk tabi 'yan uwan mahaifinta ta zagesu tasss, Kaltume ta taya mata.”

“La'ilaha'illallahu ni Asma'u, Haba! Shi yasa yaron nan yake kasa yin sakat idan yarinyar tazo aiki gidan nan. Ooh ashe kullalliya suka shiryo min suna son su mallake min d'ah, toh ba zai yiwu ba, wallahi nafi karfin su koda k'asar shuri suke yawo nasha gabansu. Kinga baiwar ALLAH muna ta zuba zance ko sunanki ban sani ba.”

Bintalo ta sake bajewa jin yadda Hajiya Husnah tayi amanna da zancenta, sannan ta dashare baki tace.

“Hajiya kira ni da Bintalo domin dashi kowa yafi sani na, ko alheri zaki aika min kice ace ina Bintalo uwar Alawiyya, Hinde da kuma Hauwa'u, nice uwar mata masu farar laya.”

Kai Hajiya Husnah ta jinjina sannan ta cije leb'e da hakoranta. Numfashi taja ta kalli Bintalo tana fad'in.

“Na gode kwarai da wannan batun da kika zo min dashi, kinga nima sai na tashi tsaye akan su, domin d'ana bakalar 'yarsu bace. Kije gida zan yo miki aike na ladan zuwa tonawa matsiyatan can asiri, amman yanzu Haysam yana k'asar waje mu da kanmu muka kaishi airport sai da jirgin su ya tashi sannan muka taho. Ina kyautata zaton sun mallake min shi ne saboda ya zama saniyar tatsar su, toh wallahi basu isa ba. Makarantar da ta tafi kuma sasan uban da zai bata kudin karasawa.”

“Ai kuwa dai Hajiya, gara ki tashi tsaye dan Kaltume summun mukasau ce, (green snake), tana yin abubuwa na mugunta a cikin wannan salon nata na suffar salihai. Zan tafi Hajiya sai naji tukwici, ALLAH ya kara rufa muku asiri fiye da wannan wanda kuke ciki.”

Hajiya Husnah bata ce komai ba saboda tsantsar mamakin da ya kamata, lallai biri yayi kama da mutum, ashe kullalliya aka shirya mata akan d'an ta, shi yasa kila taga ko magana ta yiwa Batoul ko Inna indai na fad'a ne sai Haysam din ya nuna beji dad'i ba, ashe an asirce mata shi bata sani ba. Dole ta mike tsaye tasan duk yadda zata yi wajan raba idanuwan Haysam akan Batoul. Zuzzurfan tunani ta shiga, wanda yasa bata san lokacin da Bintalo tabar gidan ba.

Ita kuwa Inna suna dawowa ta nufi gidan aikinta, a cewar ta ba zata koma gida ba su b'ata mata rai ta kasa fitowa aikin. Tana zuwa ta ajiye Autar ta a can inda ake ajiye motoci tace karta sake taje ko'ina ta jira anan ta gama tazo su tafi. Juyawa tayi ta nufi cikin gidan bakinta dauke da sallama...*_IGIYAR ZATO_..........💕_*


_*NA_*


_*NANA HAFSAT_*
_*(MISS XOXO🧕🏼)_*


_®️ZAFAFA2020_*
_(TAKU NA BIYU)_


ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE, ME SO DAN GIRMAN ALLAH YA BIYA YA KARANTA HANKALI KWANCE😘❤️

https://youtu.be/LxY42ErBf_8


*2️⃣0️⃣*

*Kuma* yin wata sallamar tayi da taji shiru, Haj Husnah dake hakimce a kan kujera suna waya da wata kawarta tana gaya mata duk labarin da Bintalo ta gaya mata, jiyo muryar Kaltume na sallama yasa ta katse kiran. Ba tare da ta amsa mata ba, ta kwad'a mata kira cikin d'aga murya. Inna ta jiyo ana kiranta daga cikin parlour, hakan yasa ta nufi wajan fuskarta d'auke da kwantaccen murmushi, ta shiga ta durkusa daga bakin k'ofa tana gaishe da ita.

“Dakata min malama.”

Haj Husnah ta katse gaisuwar da Inna take yi mata, kanta a sunkuye tana jiran taji wane irin kwandon rashin mutunci za'a sauke mata yanzu, duba da yadda taji Hajiyar na yi mata magana.

“Toh yau duk wani kullin da kuke yi min keda 'yarki, an kwance min shi tass! Ke yanzu Kaltume banda cusa kai ina ke ina had'a jini da mu? Ki rasa ta inda zaki cucuni sai akan yaro na? Toh wallahi tallahi, idan ma jaki kuka binne, yau kuje ku tonoshi.”

Cikin rashin fahimtar inda maganar ta dosa, Inna ta d'ago kai tana kallon Haj Husnah.

“Kiyi hakuri Hajiya, amman wallahi ban fahimci inda maganar taki ta nufa ba, wane jakin aka rufe?”

Cikin b'acin rai Haj Husnah ta harari Inna, tare da cewa.

“Ki rufe min baki, yau asirinku ya tonu. Haysam ne ya zamar muku saniyar tatsa ko? Duk da kud'in watan da ake baki na aikin ki, ga kudin sadaka duk laraba da ake baku, amman sai kin janyo ra'ayin d'ana yayi muku abubuwan da koshi yi masa ake yi. Har Batoul ya biyawa kud'in makaranta, amman tsabar munafinci baki yi min zancen ba bare ki gode masa a gabana. Toh daga yauma kin dena aiki a cikin gidan nan, karna sake ganin k'afarki a cikin gidan nan. Sannan kuma ko kud'in watanki ba zan bayar ba, kunci kudinku na gurin Haysam, tashi ki b'ace min a nan wajan.”

Jikin Inna har rawa yake yi, saboda tsabar shiga cikin tashin hankali. Sai dai bata musawa Haj Husnah ba, ta mik'e kamar zata dora hannu aka ta fashe da kuka, amman ta jure ta sa takalmanta tayo waje inda ta samu Autar ta zaune tana ta wasanta ita kadai. Kamo ta tayi suka fita daga gidan zuwa gidan Mata tara.

*GIDAN MATA TARA*

Tunda Inna ta sanya kafarta cikin zauran gidan taji yo shewar su tasan suna cikin farin ciki, kome ya sanya su wannan jin dad'in oho. Ciki-ciki tayi sallamar ta shiga, ba ta kula kowa ba tana rik'e da hannun Autar ta suka fara k'ok'arin hawa sama,Da sauri Hafsatu matar kawu Dawood tayi saurin tare Inna wacce idanunta ke kallon k'asa.

“Wallahi Kaltume kin bani mamaki, wai da hannunki kije kisa sanya d'iyarki a mota ta tafi karuwanci. Kin lalace wallahi da son kud'i Kaltume, bayan kinsan shi arzik'i nufin ALLAH ne, yanzu idan ta kawo miki d'an shege ko 'ya zaki rik'e ne?”

“Kaji wani shirme a wajan Hansatu.”

Cewar Bintalo dake karkace baki ta dora da cewa.

“Ahhh ba ta saba rainon shegun ba? ko kin manta cewar suma Najibu da Batoul d'in babu tabbacin suna da sahihin uba. Tsab zata raini abubuwanta, ita ai yanzu so take kawai tayi arzik'i, a hayyeee nanayeee.”

Hafsatu ta buga tsakiyar zaninta, tare da dora yatsu biyu a saman katon hancinta tana gud'a.

“Aiyirrrrrrr shagali, kwarai kuwa na tuna Bintalo, wannan shi ake kira tuwo na mai na. 'Ya'ya shegu jikoki shegu, ALLAH ya shirya.”

“Amin.”

Sukaji Inna ta fad'a tare da ture Hafsatu gefe ta haye cikin sauri zuciyarta na barazanar fad'owa saboda tsabar tashin hankali. Gefe d'aya ta zauna bayan ta shiga d'akin ta, ta rungume 'yar autar 'yarta hawaye na zuba daga cikin idanuwanta zuwa kasa. Ta rasa wace irin rayuwa ce ALLAH ya zab'ar mata ita da yaranta, a ce kaf cikin dangi na kusa-kusa babu mai kallon su da mutunci bare a tuna maraicin su. Muryar kawu Ishaq taji yana kiranta daga can k'asa, amman tayi shiru saboda ba tason suci mata mutunci a gaban yara, dan a yadda yake kiran zai tabbatar maka da cewa rashin mutunci zasu yi mata.

“Ka dauka ni kawai ta raina a cikin ku? Ai kowa yanzu ganinsa kawai Kaltume keyi, amman babu wata maganar girmamawa”

Inji kawu ila yana tabbatarwa da kawu Ishaq cewar Inna bata da kunya. Tana jiyo yadda suke ci musu mutunci amman bata kula ba, a cikin maganganun nasu ne ma ta jiyo cewar ashe Bintalo ce taje ta fad'i karya da gaskiya a gidan Alhaji Kabeer wafa. Inna ta dinga girgiza kai saboda al'ajabi. Shi kenan sun rabata da aikin ta, kuma babu wanda zai kula da rayuwa ta da ta yaranta idan ba ALLAH ba, kuma yanzu zata sake kai kukanta garesa domin shine yasan gaskiyar zuciyarta.

Tunda wannan abun ya faru, shikenan wulak'anci ya karu akan Inna. Kowa ya kwaso iskancinsa sai ya juye a kanta, haka zata jure dan ma dai tana da hakuri ba komai take tankawa ba.

*BATOUL.*
(ABU SAMARU CAMPUS)
Toh masu karatu, A shafin baya wasu daga cikin ku sun shiga rud’ani kan tayaya Batoul tana zaria kuma ace ta hau motar zuwa ABU ZARIA? Toh duk da dai na bawa masu tambayan amsar su har sun gane sune su kai kuskuren fahimtar a d’aya daga cikin comments grp dinmu. Hakan yasanya kuma zan muku bayani domin cire rud’ani (To avoid confusion upon confusion)😂👏🏻
Ba mistake bane. Kaf igiyar zato ba inda aka saka unguwar su Batoul bare sunan area din da suke. Saboda yanayin tsarin gidan da suke ma da yanayin rayuwar plus gundarin labarin a gaba yake. Toh da farko dai A LIMANCIN KONA suke, Sannan ABU ZARIA guda biyu ce. Akwai SAMARU shine MAIN CAMPUS akwai kuma na CONGO shine ANNEX.

SANNAN DAGA UNGUWAR SU TA *LIMANCIN KONA* SUKA TAKO DA KAFA ITA DA INNAR MU DA AUTAR MU ZUWA KASUWAR ZARIA INDA SURAJ YA TARAR MATA MOTAN *PZ* DA GA NAN MAI MOTA YA KAITA INDA AKE LODIN SAMARU COMPUS👏🏻

Batoul kuwa cikin nasara ta isa ABU, (samaru campus) bata sha wahalar wasu abubuwan ba, saboda ta tarar da sababbin zuwa da yawa hakan yasa ta shiga cikin su har sai da ta samu hostel din da zata zauna wato *Amina hostel, Samaru campus*. Zuciyarta cike da tunanin Inna da kanwarta a haka ta gama shirya gadon ta da kayanta cike da kewar su.

*BAYAN WANI LOKACI.*

Tun lokacin da Bintalo tayi sanadin barin Inna daga gidan Alhaji Kabeer wafa, shine ita kuma da shishigi da kai zancen karya da gaskiya ta samu ta maye gurbin aikin Inna a gidan. Ai kuwa tunda ta fara aiki komai na ta ya sake gyaruwa saboda komai ta kyalla ido ta gani anyi wasarairai da shi a gidan, toh insha Allahu sunansa satacce, da ta kyalle ido taga ba'a ganinta zata zabare takai gida.

Ita kuwa Kaltume rayuwa ta sake yi musu zafi, ta buga ta bincika amman bata samu wani aikin da zata yi ba, ya zamana ko garin kwakin da zata had'awa Autar ta gagarar su yake yi. Wannan halin kuma ta da tsinci kanta a ciki ya yiwa ilahirin gidan mata tara dad'i domin basu da buri irin suga d'aya daga cikin gidan ya shiga kuncin rayuwa. Gashi ita Inna daman ba wani maula ta iya ba, bare ta dinga zuwa gidajen mutane tana neman taimako.

A yau ne ta kama su Alawiyya zasu je gano gidajen da samarin su suka ce zasu kaisu su gano. Bintalo sai murna ake ana yada habaici ana shewa a tsakar gida. Su kuwa su Alawiyya sai kara gyaggyara wa suke yi suna kara lafta hoda da gyatuma rad’au bakin su. Hinde ta dakko dankwalin ta na wata atamfa ta raba shi biyu tana cusa shi a kasan kirjin ta domin dago dasu, Alawiyyah ta kece da daria tana nuna kirjin Hinde,

“Duk kwaliiyar ganin Mu’azzam din ce?”

Hinde tayi fari da idanu tana girgiza,

“Iyyi! Ke kuwa harda sirikai fa zasu ganka gwara ka shirya.”

“Ai kuwa dai nima bari na ‘danyi cikon nan.”

Ta karasa fada tana dariya, Dariya Hinde ta ‘babbake itama tana sake lafta kayan cikon, Alawiyyah ma skirt uku ta ‘dora acikin zanin kayan jikin ta. Suna saka takalman a temaki wada, Kansu kuma zare-zaren jikin mayafin gyale suka soka a cikin ‘daurin yayi kamar gashi. A haka suka fara sakkowa daga bene suna taku ‘dai-dai tamkar yammatan agwagwa. Bintalo dake mattakalar bene ganin su yasa ta kara callara kara tana buga zani hade da shewa,

“A hayye nanaye! Sittin ta ubangiji kaf gidan mata tara babu kyawawan ‘yaya masu kalar matan manya da samari masu hannu da shuni irin su Hinde na. An buga daku an barku, An buga ‘kasa an nuno ku sittin ta ubangiji babu mahaluki a gidan nan daya zarta ku komai, A hayye nanaye..!”

Ta karasa kirarin tana taka rawa, Baba Usaiba dake tattare kayan shanyar ta a kusa da Bintalo ta buga tsaki ta haye sama cikin sassarfa. Kawu ila ma dake kan bokitin zaman sa sai kwararawa su Alawiyyah kirari yake yi yana tafa hannaye,

“Kaga dangin tsatson farin jini, Kaga wanda samari kewa layi a kofar gidah, Kaga wa’enda kuttin farin jini ya fashewa, Kaga ‘yayan iri na albarka, Gaisuwar ban girma gare ku, Allah ya kai ku a sa’a ya dawo mana daku lapia.”

Bintalo taja guda ta saki tana kururuwa,

“A hayye nanaye! Ameen kawun su. Fadi da kyau ka kara da karfi. Nasan anacan an haye kan buzu ana narka bakar addua, Toh bakunan ku su sari danyan kashi. A hayye na gaba yayi gaba wallahi na baya sai labari, Kai labarin ma ba wanda zai bayar. Me za’a fada banda tarin tsiya da shegan taka? A hayye nanaye!”

Har kofar gidah Bintalo ta raka su tana daga masu hannu, Alhazawan su suka dauke su sai hanyar kaduna. Ita kuma ta koma ciki tana cigaba da yada magana.


*KADUNA*

Alhaji Labaran Tumbin kudi shine sunan Alhajin Alawiyyah, Sai Mu’azzam kanin sa a cewar su. Alhaji Labaran dai sanadiyyar had’uwar su dasu Alawiyyah a yar kasuwar zaria ce. Alhajin da Mu’azzamun suka hada bakin su yan uwa ne na jini, Nan dai su Alawiyyah mai idanun cin nera ba tare da wani bincike ba suka fara lulawa duniyar soyayya.

Gate din wani gidah Alhaji ya zura kan motar sa, Gidan ba ginanne bane, An dai gama wasu sashen dake cikin sa (uncompleted building). Alawiyyah da Hinde suka hangame bakuna suna bin gidan da kallo. Lalle naira tayi kuka.

“Wohoho! Alhaji na gi..Gidan ne nan?”

Alhaji ya shafa tumbin sa yana gyatsewa,

“Iyyi Alewata, Gidan ku ne nan ke da Hinde.”

Alhaji Mu’azzam ya murmusa yana nunawa Hinde dayan sashen da hannu,

“Kinga can shine naki. Yanzu ake ginin..”

Hinde ta buga tsalle, Har kullin cikon ta ya kusa fadowa ta maidashi tana daria,

“Dankari Mak’ari! Yasin ji nake kamar mafarki.”

A tare suka shige cikin wani sashe, Shiru ba ma’aikata a gidan gaba d’aya. Alawiyyah ta dubi Alhaji labaran,

“Ina ma’aikatan kuma?”

Alhaji labaran ya sosa k’eya yana murmushi,

“Sun je gano gida su dawo.”

Alawiyyah ta dafe kirji tana zare idanu,

“Kasar wajen suka koma? Jar uban can! Lalle kudi na aiki.”

Alhaji labaran da Mu’azzam suka tafa hannaye suna kyalkyalewa da dariya. Cikin wani babban parlor suka shiga babu komai cikin sa sai taburma da kayan abinci fal akanta.

“Bismillah! Ku fara ci kafin muje wajen su hajian ko?”

Daga kai Alawiyyah da Hinde su kai sannan suka zauna gaba dayan su akan taburmar. Ba kunya haka suka zage suka dirki abincin nan tas. Alhaji ya tsiyaya musu lemo suka kafa kai suka shanye tas. Mikewa su kai bayan sun gama suna nuna musu yanayin gidajen, Sai murmushi su Alawiyyah suke zukatan su fal da farin cikin wai nan gidajen zasu zama mallakin su nan ba da jimawa ba. Jiri ne ya fara dibar su Alawiyyah da Hinde, Cikin watangariri Alawiyyah ta dafe kai ,

“Al..Alhaji ka...Ji.jiri na...”

Luuu tayi sai kirjin Alhaji labaran, Ya sunkuceta yayi cikin wani daki yana lashe lebe, Hinde tuni ta kife tana jan munshari. A takaice Alhaji Labaran da Mu’azzam sai da su kai masha’a dasu Alawiyya suka wanke garori tukun suka sarara musu. Akan

Please Login or Register in order to submit comment